Showing 183001 words to 186000 words out of 261165 words

Chapter 62 - Kwai Cikin Kaya Part 2 Hausa Novel Complete

17 Dec 2024

1756

da shi muke tsananin kama, musamman ma kai daka biyo har hasken sa, abubuwa ƙalilanne muka ɗakko Ummuna. Inada videos da dama da akayi lokacin da yake shugabancin ƙasarmu, ta hakane nakejin kamar na rayu da shi rayuwa mai tsaho...........”
Da sauri Anuwar ya ƙara ƙanƙame hannun Jawaad dake a cikin nashi yana faɗin, “Suna tare da kai yanzu?”. Murmushi Jawaad yayi ya kai hannu ya shafi kan Anuwar, “Da ganinka ɗan karan gaggawa ne da kai da rashin haƙuri yaron nan”. Yanda yay maganar da jan hancin Anuwar a ƙarshe ya saka Anuwar ɗin ƙyalƙyalewa da dariya, shima Jay murmushin sa ya sake faɗaɗawa yana maijin daɗin ganin Anuwar ɗin cikin nishaɗi. Wayarsa ya ɗauka ya lalubo folder da ta kasance duk hotunan Umm-Anum ne da Abban su sai shi. Miƙama Anuwar yay, jikinsa har ɓari yake wajen son amsar wayar abin tausayi, kallo ya shigayi yana hawaye sosai, hakan yasa Jawaad lumshe idonsa yana haɗiye abinda ya tarar masa a ƙirji na tausayinsu musamman ma Anuwar ɗin. Saurin buɗe idanu Jay yayi danjin yanda Anuwar ya fashe da kuka, ya kafesa da ido shima yana ƙoƙarin danne tasa zuciyar, “Haba my sweet Darling kamar ba namiji ba, kukan ya isa haka kaji lilly na”. Yay maganar da tashi zaune ya rungume Anuwar ɗin yana mai shafa masa baya, har saida yaji yayi shiru ya koma sauke ajiyar zuciya sannan ya barsa. Labarin ahalinsu da mahaifinsu ya cigaba da bashi cikin kulawa, wani gurin Anuwar yay kuka wani gurin yay dariya, haka suka kasance har akai kiran sallar la'asar, wanka Jawaad ya sakeyi da gaggawa suka fita massallaci.
Umm-Anum ma ta tada su Bilkisu sukayi tasu, bayan sun idarne ta saka mai aikinsu ta kawo abinci, zaunar da Bilkisu tayi tana faɗin, “Zauna na baki abincin nan da kaina, kwana biyu da zuwanku duk kun fara ramewa ke da mijin naki saboda rashin cin abinci, ina dalili”. Murmushi nayi cike dajin kunyarta, yanda take ƙoƙarin yin hausa sai abin keban dariya dan hausar kamar bata bahaushiya ba, wani wajenma kakarewa take ta kasa faɗa.
Duk yanda nakejin kunyarta haka na ringa amsar abincin da take bani da hannunta, sallamar su boss ta sakamu maida hankalinmu garesu, idanunsa a kaina dan haka nai azamar ɗauke nawa na maida ƙasa. “Kaima zo ka zauna” Umm-Anum ta faɗa idanunta akan Jawaad dake kallonsu cike da sha'awa dajin daɗi. Hannunsa ta riƙo ta zaunar ɗayan gefenta, ta ɗiba abincin takai bakinsa, “Haa!” ta faɗa kamar yanda akema yara. Ƙwallane suka cika idanun Jawaad ya buɗe bakinsa a hankali ta zuba masa, taunawa ya shigayi yana kallon yanda take sakama Bilkisu itama, gabansu Anuwar yazo ya durƙusa shima ya buɗe baki wai a basa. Umm-Anum ta zuba masa tare da dungure kansa. Anum ma zuwa tai ta tsugunna tana faɗin, “ALLAH nima sai an bani to, anma manta dani kamar banice autar ba”. Sosai abin ya bama Jawaad nishaɗi, su Bilkisu suka shiga yima Anum dariyar tsokana.
Hannunsa Jay ya ɗauraye, shima ya ɗiba ya kai bakin Umm-Anum, amsa tai tana murmushi ta shafa kansa da ƙoƙarin haɗiye hawayen da suke neman taho mata, murmushi Jay yayi ya ɗiba ya bama Anuwar shima, sannan ya bama Bilkisu da kunya ta kusan halakawa, Anum itace ƙarshe. Daka gansu kasan suna cikin farin ciki mai tsanani.
Haka suka ƙarasa wannan yini tare, har zuwa dare dan Abbu yau a gidan Uwargidansa ma yake ba nanba, hakan ne ya ƙara bama Umm-Anum damar sakewa da ƴaƴanta har dare ya farayi, daƙyar ta daure tace suje su kwanta haka nan gobe idan ALLAH ya kaimuma ranace ai. Da wannan kowa ya nufi makwancinsa badan sun gaji da kasancewa tare ba.



Sai da muka gama shirin barci muka kwanta, ina jikinsa a lafe kamar wata mage yana shafa bayana a hankali, fitar numfashinmu yana dai-daitane da sautin bugun zuciyarmu, “Miema kinyi barci?” ya faɗa a hankali cikin kunne na. Kaina na girgiza masa da ɗago fuskata dake cikin ƙirjinsa na kalli fuskarsa, shima kallona yakeyi. Murmushi mukaima juna, ya ɗan sumbaci goshina kafin ya sake maida idanunsa cikin nawa. Maida nawa nai na lumshe dan nakasa jurar cigaba da kallon cikin idanun nasa. Baice komaiba sai sake turani da yay jikinsa ya rungume da ƙyau. A haka barci yay awon gaba damu.
★★★★★★★
Mun cigaba da kasancewa a cikin Saudia tare dasu Umm-Anum cike da tsaftatacciyar soyayya da tarin ƙauna mai daraja daga garesu, tattalinmu take tamkar wasu ƙananun yara ni da boss, yayinda a koda yaushe ƙannensa ke nane da shi, yanayin waya sosai dasu Oga Hafiz musamman akan aikin da a yanzu mukasa gaba na ƴan fyaɗe, a yanzu haka dai su Jabeer suna ƙoƙarin miƙa wasu samari kusan goma sha uku kotu akan case ɗin fyaɗen, sannan sunce sun samu case huɗu masu kamanceceniya da nasu Amina. Duk da muna nan saudia muma aikin mukeyi musamman ma boss, danni wataranma A wajen Umm-Anum nake yini komu tafi makarantarta. Har gidan Uwargidanta an kaimu, abin ya birgeni sosai yanda aka tarbemu tamkar ba kishiyoyi ba, a raina nace ‘kaga inda ake kishin ilimi, ba irin na ƴan ƙasarmu ba na hauka’.
Randa muka cika kwanaki bakwai a saudiya boss ya fara samun kira daga wajen aiki, dan mun wuce ƙa'idar kwanakin da aka bamu na hutu, duk yanda yake da son aiki da ƙwazo saina fahimci bayason komawa yanzun, nima dai bason komawar nakeba sam, amma yaya zamuyi hakan tilasne a garemu kodan ɗunbin ayyukan da muka baro.
A ranar yayma Umm-Anum magana akan binmu, sai dai abin mamaki da al'ajabi a take ta nuna ɓacin ranta akan bazataje ba, shiru mukai kawai duk muna kallonta, yayinda fuskar Boss da Anuwar ta nuna tsantsar ɓacin rai akan hakan. Kafin suce wani abu akan hakan Abbu yaja hannunsu suka fice daga gidanma gaba ɗaya.
Wannan al'amari ya tsaya min a zuciya, dan yinin ranar gaba ɗaya wuni Umm-Anum tai cikin ɓacin rai, yayinda na yini nikuma cikin nazarin komai da fashin baƙi a kai.
★•°•★°•°★•°•★°•°★•°•★
A ɓangare su Jawaad suna fita daga nan wucewa Abbu yay dasu masaukin takawa, tattaunawa suka shigayi game da abubuwa masu dama, Abbu yace, “kuyi haƙuri kubar ɓacin rai kunji, itama ba laifinta bane, babu yanda za'ai taƙi son zuwa ƙasarta kodan shekarun data ɗauka bata cikinta, al'amarin bai baku mamakiba yanda har yanzu bata iya tambayar kowa daga ahalin nata ba, tunfa washe garin zuwanku har yanzu bamu sake zaman tattauna komaiba, tama ƙi ƙara nuna tana buƙatar jin komai, hatta da yanda ka rayuwu bayan barinta gida bata tambayeka ba Jawaad. Wannan babban al'amarine daya dace ace an zauna anyi dogon nazari a kansa. Shi sihiri a jikin ɗan adam abune mai wahalar yakicewa, musamman irin nata da ba'asan dalilinsa ba ma da sarƙaƙiyar sa, shifa mai sihiri baya gajiyawa da ƙoƙarin ɗaura wani akan wani, dan ya riga yayi imani da yin wannan shirkar itace ƙarfin ikonsa, har yanzu akwai sihiri tattare da mahaifiyarku, wanda inaji a raina akwai wani abu da aka binne wanda saimun tonosane komai dake jikinta zai iya warwarewa harmu fuskanci matsalar gaba ɗaya, bakuma wai dan addu'oin da muke basa ƙarɓuwa bane, ita rahamar UBANGIJI da kariyarsa bata taɓa gushewa ga wanda ya dogara da shi kuma yayi imani ya riƙe gaskiya, gaskiyar ɗan adam bata taɓa ƙarewa sai dai ace ƙaryar wane ta ƙare, dan haka mucigaba da bin komai mataki-mataki insha ALLAHU komai zai zama labari ne, Jawaad idan babu damuwa ka bamu haske dangane da family ɗinku ko zamu samu wani haske”.
Duk sun gamsu da maganar Abbu, dan haka Jay ya shiga basu tarihin rayuwar mahaifinsa da Umm-Anum kamar yanda kakarsa mama maryam ta shaida masa komai bata ɓoye masa ba. Ya cigaba da faɗin, “Ban taɓa zargin kowa a zuri'ata game da iyayena ba, dan babu wani alamun cutarwa dana taɓaji ya shiga tsakaninsu da mahaifina harya bar duniya, sai dai maganar gaskiya lalurar hauka da Ummuna ta gamu da shi a ranar rasuwarsa abin tambaya ce, ada ban taɓa ɗaukar hakan komaiba sai kwanannan da matata tai wata magana data kasa barin raina, na cewar a al'amarin Ummuna akwai alamomin sihiri, dan mutuwar Abba bai kai ace ta kasa jure ƙaddara ba har ta kaita da ciwon hauka, ciwo ma irin wanda mutum baison zaman gida, bayan duk musulmi yasan mutuwa wajibine ga mai rai. Abinda kuma naji daga gareku a yau da wanda ya faru ranar ya tabbatar min akwai abinda bamu saniba dake a ɓoye tabbas”.
Abbu ne ya sauke ajiyar zuciya yana gyara zamansa, yace, “Tabbas kamar yanda ka faɗa Muhammad akwai ababen tambaya masu yawan gaske akan al'amarin, ko sunanta sai a jiya na taɓaji, kai tsaye bamu da damar zarigin kowa akan wannan al'amarin, musamman idan mukai dubu da marigayi yayi shugabanci na ƙasa, ƙasarma babba irin taku, bazai yuwu ace baida maƙiyaba koda kuwa suna a kusa da shine. Sihiri gaskiyane, hakama addu'a waraka ce, sai dai wani lokacin sai kaga kamar ka ɗauki lokaci kana addu'ar babu biyan buƙata, ba haka bane, UBANGIJI maijin kukanmune a koda yaushe, mai kuma magance mana damuwarmu ne a koda yaushe, wani lokacin ita addu'a idan kayita takan jinkirta da ga abinda ka roƙo a kansa, saita zama kariyane ga wani al'amarinka ɓoyayye da kai kanka baka san da shi ba, mahaifiyarku ta jima cikin wani hali na jarabawa, mun kuma ɗauki lokaci muna gayama UBANGIJI, bamu taɓajin mun ƙosa ba, domin mun tabbatar shi kaɗaine mai badawa, yana jinmu, kuma yana ganinmu, yana kuma sane damu, jinkirtawar warwarewar komai ba yana nufin bai karɓi kukanmu ba. a yanda kuma nakeji a raina addu'armu ta kasance da kai, kai kanka, dan duk waɗanda suka iya tauyeta kaima abune mai sauƙi su ɓaddaka, inaga damuwa akan saita biku ba shine ya kamata ba, bincike akan ainahin miya faru shine ya dace domin mu samu bakin zaren, dan ko Anuwar bai kamata ya biku ba”.
Kallon Abbu Anuwar yayi cikin tsagwaron tashin hankali, kafin yace wani abu Takawa yace, “Wannan tunanin shine a raina nima Abu-Sufyan, Anuwar kayi haƙuri kaji, indai ƙasarmu ce zakaje ka rayu har saika gaji ma, amma ba a irin wannan lokacin ya dace ba, dan abubuwa da yawan gaske na zuwarmin a zuciya game da al'amarin nan, sai dai banason furta komai nafison matsayin Jawaad na jami'in tsaro shi yay wannan tunani, zuwan Umm-Anum da Anuwar ba shine abu mai muhimmanci ba a yanzu ƙwarai da gaske, dan komai ma zai iya faruwa inhar azzaluman da suka ƙulla al'amarin suna tare dasu ne, kai koma nesa da su suke suna bibiyar al'amarin komai dan nima nayi makamancin wannan rayuwar nasan sarƙaƙiyar cikinta, amma kai Jawaad minene a ranka?”.
Zama Jawaad ya gyara cike da kaifin basirar da ALLAH ya azurtashi da ita shima yace, “Na gamsu da duk abinda kuka faɗa, dan nima a kwanakin nan sune suka zama abin nazarina, rashin tambaya ta komai da Ummuna batai ba yafi komai tsayawa a raina sosai, ni a yanzu shirina na farko shine lallaɓata naji waɗanda sukai rayuwa dasu kamar ma'aikatan gidan da sauransu”.
“Tunani mai ƙyau” cewar Takawa da Abu-Siddiq. Jawaad ya cigaba da faɗin, “Sai abokai makusanta da Abbah ya rayu da su kafin shigarsa siyasa da hawansa mulki, abu na uku ne bamu da dama a kansa, dan a wajen Ummuna ne kawai zamu iya jin wasu sirrika game da rayuwar Abba da ƴan uwansa a lokacin da yake mulki, dan haka wannan na ajiyesa gefe zanyi anfani da waɗancan damar guda biyu mugani ko za'a dace, amma nima na gamsu da basai sun bimu ɗinba kam yanzun”.
“ALLAH yay maka albarka” cewar Abbu yana dafa kafaɗar Jawaad dake a kusa da shi. A tare suka amsa da amin. Abbu ya cigaba da faɗin, “Nima nanda sati guda zan biyo bayanku dan inason ganawa da Abba (Alhaji Babba). Kai Jawaad ya jinjina masa yana ɗan murmushi da faɗin, “ALLAH ya tabbatar Abbu”. Da Amin duk suka amsa..
Akan wannan shawarar taron ya tsashi, shi dai Anuwar badan yasoba ya haƙura akan binsu Jawaad, dan yay masifar ƙwallafa ransa da zumuɗin son ganin ahalinsu.
★★★★★★★★
Cikin hikima Abbu ya samo sunayen ma'aikatan da su Umm-Anum sukai rayuwa dasu a gidan gwamnati da kafin hakan, harma da sunayen abokan Abban Jawaad ɗin data iya tunawa da ƙyar.
Sai kuma ta nema tada hankalinta akan komawar su Jawaad ɗin, ta kafe akan ita bazata barsu su koma ko inaba sunzo kenan. Duk yanda Jawaad dake cikin damuwa shima yake ƙoƙarin mata bayani akan aikinsu da buƙatarsu da akeyi taƙi fahimta, tamaƙi sauraren komai, saima ta saka masa kuka daga ƙarshe. Wannan abu ya sake tada hankalin Jawaad sosai, dama dauriya kawai yakeyi. Da ƙyar aka shawo kanta da lallashi akan Jawaad da Bilkisu zasuje su ajiye aikinsu ne su dawo nan da zama gaba ɗaya wajenta.
Wannan batu ya sakata yarda, amma sunsha gargaɗi akan karsu daɗe basu dawo ba, dan da farko ma catai Jawaad yaje shi kaɗai yabar bilkisu ita anan, sai da Abbu ya sake wata sabuwar dabarar ya lallaɓata sannan tadai barsu suje ɗin, sukuma dawo akan lokaci kamar yanda ta faɗa, inba hakaba zata aika a ɗakkosu koda basu gama shiryawaba.
Da wannan yarjejeniya daba tabbatacciya ba muka baro ƙasar saudia cike da kewa ni da boss. su Ummu kam can muka barosu dansu sati biyu zasuyi.
Saukar yamma mukayi ƙasarmu ta haihuwa, inda muka iske Sadiq yazo tarbarmu, dan shikaɗai yasan da dawowar tamu, dama tunda muka tafi boss bai yarda munyi waya da kowaba bayan su oga Aliyu, su Ummah duk yaƙi yarda yay waya da su, dan baiso suji komai da wuri harsu kasa daurewa su sanarma Alhaji babba, a yanzunma da muka dawo bazai faɗa musu komaiba gudun matsala.............✍



Asha sauran weekend lafiya🤒😣🚶🏻🚴🏼



ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.[1/17, 7:26 PM] HASNA✍🏻: Amina Wada:
ƘWAI cikin ƘAYA!! - 51 - Wattpad

Turƙashi, wannanfa shine cakwakiyoyi ba cakwakiya ba, bamma san yanda zan musalta muku kitimurmurar dake cikin book ɗinnan ba sam, dan wani irin ruɗaɗɗen labarine mai cike da abubuwan mamaki da tarin al'ajabi harma da ban haushi, labarin ya taɓo wa...


*_Shin kina ko kana sa sha'awar koyon ilimin ICT?_*

*_Ko kuna da sha'awar yadda ake hada cartoon?_*

*_Ko kana da sha'awar yadda zaka bunqasa kasuwancinka ta hanyar online?_*

*_Matsalarki ko matsalarka rashin makarantun da zasu koyar dake/kai ilimin computer ta fannnin larabci?_*

*ALBISHIRINKU KANAWA*

*_Kukanku ya qare,matsalarku tazo qarshe,shahararren kantin nan na yanar gizo wato RAHAMALLS yazo muku da makarantar koyon sarrafa computer a sauqaqe wato RAHA COMPUTER INSTITUTE(RACI)_*

_Sun tanadarmuku qwararrun malamai wanda zasu koyar daku bisa tsarin da kuma cikakkiyar qwarewa ta yadda zaki fahimta fiye da yadda kuke zato_

*ga masu buqatar aji na musamman har cikin gidajensu,makarantar ta shirya tsaf don baku darussa har cikin gida*

*sannan akwai tsarin ajujuwa na musamman bisa yanar gizo wato(online classes)*

*kaidai maza garxaya ka tuntubesu akan wanannan lambar waya*

08033990209

*_akwai ragin kaso hamsin cikin dari na kudin registration ga kowanne dalibi_*👌🏽👌🏽👌🏽👌🏽👌🏽👌🏽


..................Gidan duk ya ajiye ƙananun ƙura, duk da ko'ina a rufe yake, haka na daure naɗan gyara ɗakinsa dan mu samu inda zamu kwanta, kafin a kira sallar magriba na kammala, shikam wanka ma yayi ya fita tun fara aikin nawa. Bai dawo gidanba har saida akai sallar isha'i, kusan tara sai gashi ya dawo mana da abinda zamuci. Gaba ɗaya banajin daɗin yanayinsa, ya koma min Boss ɗin dana sani a office mara walwala da yawan magana, komai nake sai dai yayta bina da ido kawai, abincinma da ƙyar na samu yaɗan ci yace ya ishesa, nima cire hannuna nai a ciki na ɗauke kaina gefe. “Miye hakan?”. Ya faɗa muryarsa can ƙasan maƙoshi. Ƙoƙarin miƙewa nai tsaye nace, “Na ƙoshi nima...” kafinma na gama rufe bakina naji caraf ya cafko hannuna ya maidoni ya zaunar, kallonsa nai ina kumbura fuska, ya zabgamin harara tamakar idanunsa zasu faɗo ƙasa, “Ina wasa da ke ko?”. Ƙasa nai da kaina dan bazan juri kallon nasaba, “ALLAH nima na ƙoshi to”. Banza yaymin bai tanka ba, ya ɗebo ya kawo bakina, zan ɗauke kaina yay saurin faɗin, “Kinsan ALLAH idan baki shiga hankalinki ba sai na sauya miki kamanin wannan fuskar taki, malama haa”. Idanuna cike da ƙwala na buɗe bakin, ya ko zubamin yana sake zabgamin harara da yin ƙwafa, inaji ina gani yaymin ɗurar dole, shiko yaƙi ya ci, sai yogurt yaɗan sha, hakanne yasa naɗan samu kwanciyar hankali. Kasancewar a gajiye muke ga mai gayya mai aikin baya tare da walwala, gashi zamu koma aiki gobe idan ALLAH ya kaimu sai mukai kwanciyarmu da wuri.

WASHE GARI

           Tun kiran sallar farko na tashi, cikin sanɗa na fita daga ɗakin nasa, kasancewar barcin da muka kwanta da wuri sai na tashi jikina babu nauyi sosai, da wannan damar na fara rage aiki. Koda ya fito zai tafi massallaci ya ga ina aikin gyaran babban falo baice dani komaiba ya fice abinsa, ajiyewa nai nima na koma ɗaki nai salla, ina idarwa ban hutaba na sake fitowa na cigaba, ana idar da salla shima bayan wasu ƴan mintuna sai gashi ya dawo, bayan mun gaisa shima sai ya cire jallabiyar jikinsa ya shiga tayani aikin. Duk da na roƙesa ya bari zan ƙarasa tunda na kusa bai saurareni ba, sai da yaga ya rage bedroom ɗina kawai sannan ya barni na ƙarasa.
          Ƙurar dana gani tasa nake sharo har ƙarƙashin gado kamar yanda nayi a ɗakinsa da ƙarƙashin kujerun falo ma, abu na sharo a ƙarƙashin gadon, wanda ya sakani dakatawa da sharan nasaka hannu na ida jawosa dan naga minene, wallet ce ƴar karama dan bata kai girman normal wallet dana sani ba, kamar zan buɗe sai kuma na ajiye da tunanin ko tashice, saman mirror na ɗaurata na cigaba da sharan harna kammala komai, ganin lokaci yaja na shiga bayi dan yin wanka sauri-sauri, ban wani ɓata lokaciba na fito.

Idanuna ne suka sake sauka akan wallet ɗin nan, duk yanda naso na share a yanzun sai na kasa hakan, na matsa gaban mirror ɗin ina goge fuskata da ƙaramin towel dake a hannuna da hannun haggu, na damar kuma sai na fara ƙoƙarin buɗe wallet ɗin, ɗan ƙaramin hoton dana fara cin karo da shine ya sakani

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login