Showing 72001 words to 75000 words out of 261165 words

Chapter 25 - Kwai Cikin Kaya Part 2 Hausa Novel Complete

17 Dec 2024

1109

ɗiyar ƴar uwarsa ce”. Hafiz yace, “To nima dai abin yasani wannan hasashen, amma kuma idan mukai dubi da yanda ya tada hankalinsa bayan faruwar abun harda suma hakan na nufin baisan su Momyn Shahudah sun shirya hakanba?”.
     Shiru duk sukai suna nazarin maganar Hafiz ɗin, Jawaad ya miƙe tsaye hanayensa duka cikin aljihun wandonsa, kallo ɗaya zakai masa ka fahimci ransa a ɓace yake, yace, “Basu  kaɗai suka shiryaba, hardasu Uncle Nasir, abinda yasa abin ya tsayamin

arai shine, miyasa shi Uncle Nasir zai zama munafuki a tsakaninmu? Shinefa ya jagorancemu wajen Dad ni da Alhaji baba akan maganar Miemaa ɗin, saboda Ummah ta matsa akan sai dai Alhaji baba ya nemamin aurenta tare da Hudah kodan hakan ya zama gargaɗi gareta, kenan yasan shirinsu da Momy, amma kuma ya amsama Alhaji baba cewar muje muyima Dad ɗin maganar a haɗamin auren Miemaa da Hudah? Sannan sarai yasan Qaseem an tsaida masa ranar aure da Miemaa! ɗin kuma?”.
         “To tabbas kam wannan matsalar daga nan take boss, Uncle Nasir yasan komai, amma kam bai ƙyautaba, dan nikam ina bala'in ganin girmansa wlhy saboda yanda ya riƙeka, ashe ba har zuciya bane, wannan wane irin zumincine muke fama dashi a wannan zamanin?, kaga yanda aka cukurkuɗe abu saboda kawai buƙatun wasu dason faranta musu, kuma duk idan kaje ka dawo zaka fahimci ita Mami itace akai shirin sakawa a tsaka mai wuya, miyasa sukaso mata wannan mugun ƙullin to?”.
        Duk hankalinsu suka maida ga Jawaad da yay shiru yana nazarin kalaman Jabeer na ƙarshe akan uncle Nasir da maganar ƙullin da akaso yima Bilkisu. Cikin son maidosa hankalinsa Hafiz ya zunguresa, kallonsa yay. Hafiz yace, “Mi muke ciki yanzun? Dan ko game da Mami muna buƙatar bincike mugano gaskiyar maganar Jabeer, mizaisa suyi shirin cutar da ita?”.
         Guntun Murmushi kawai Jawaad yay ya koma cikin kujera ya zana,  kwantar da bayansa a kujeran yana mai lumshe idanunsa, a hankali ya furta, “Wannan shine dalilin zamanmu anan, dan inaji a raina wannan ƙiyayyar da sukaso nuna mata tawuce naƙin son aurenta da Qaseem kawai, akwai wani abu da bamu saniba, dan haka inason sanin anahinma alaƙarta da mutanen gidan”.
         Jabeer ya ajiye cokali yana faɗin, “Kamar ta taɓa gayamin Dad yayan mahaifiyartane ubansu ɗaya, kaga kuwa bazai wuce Momy ta ƙitaba akan ƴan ubancin dake tsakanin Dad da mamata, sai dai kuma zata iya yiwuwa ɗin akwai wani abu a ƙasa damu bamu saniba harsai mun bincika tukunna”.
          “Kai lamarinfa akwai ɗaurekai, sannan akwai lauje cikin naɗi, aganina tunda basa sonta da ɗansu su rabasu kawai basai sun zalinceta sun haɗata aure da wanda bata saniba”. Hafiz yay maganar cikin takaici.
          Aliyu yace, “Kai dai bar son zuciya Hafiz, amma harma nawa Mami take da za'a mata irin wannan muguntar? Yanzu dai boss mikace kai akan batun? Tunda dai ALLAH yasa ta fita daga tarkonsu, yanzu aikin farko dake gabanmu shine Qaseem da Shahudah, baƙaramin yaƙi zasuyi a kankaba da Mami tunda. Shin Ka sanar musu kaine ka canja sunayen ne?”.
        Jawaad da duk yake saurarensu cike da nazari yace, “Eh na sanarma Alhaji baba ɗazun, na nuna masa nine na canja, nakuma saka masa zancen Azeema ciki, na tabbatar zuwa safiya zai nema su Uncles da maganar,  mukuma sai muyi amfani da wannan damar”.
        “Amma Boss baka ganin ka ɗaure kanka da yawa? Taya za'ai ka amshi laifin kai tsaye bayan bamusan mike a ransuba game da batun?”. .
         Muryarsa cike da damuwa yace, “Jabeer hakan shine kawai hanya mai sauƙi da zamu bama koma waye ƙafa, sannan Bazaka ganeba, rikicin tsohon nan ya wuce dukkan tunaninka, gara nafito na faɗa masa gaskiyar maganar, harfa ya kafamin sharaɗin saina saki Miemaa, yanzu dai nagama da matsalarsa”.
          Dariya sukayi a tare, cike da tsokana Jabeer yace, “To tsakani da ALLAH gaskiya Alhaji baba ya faɗa, ka bama Qaseem matarsa”. Banza yayma Jabeer ɗin, ya miƙe yana kallon agogon hanunsa, “Kunga ɗaya harta wuce, mu tsaida maganar iya haka, zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu nasan Alhaji baba zaisa ai zama akan batun, anan zan fahimci yaren kowa, daga nan saimu ɗora da abinda ya dace kawai”.
      Duk sunyi na'am da jawabinsa, kowa ya miƙe yana tattare kayansa kafin su fito, Jawaad tare suka tafi da Hafiz zai ajiyeshi gidan Alhaji baba saboda hanyarsa ce shi, su kuma su Aliyu kowa ya shiga motarsa.
        

★★★★★

       Da sanɗa Jawaad ya shigo bedroom ɗin duk dan karyay motsin da zai tada Alhaji baba, a bazata yaji yace, “Daga ina?”. Tsam Jawaad yay ya kasa ƙarasawa, cikin sauke ajiyar zuciya yace, “Nafita akan wani aikine”. Alhaji baba baice komaiba, hakan yasa Jawaad

nufar toilet dan ya watsa ruwa.

_________________________________

            A asibiti kam daƙyar mama ta kwantarma Batool hankali, Cikin sarƙewar numfashi da tsananin tsoro tai mata bayanin abinda ta gani a toilet,  shiru maman Amina tai tana nazari da haɗa komai a mizanin daya dace, a fili kuma sai tayi murmushi tana mai girgiza kanta, cikin bama Batool ƙwarin gwiwa ta umarceta akan ta tashi tai sallarta koma minene ALLAH zaiyi maganinsa. Jiki a sanyaye Batool tabi umarnin Mama.
     Haka suka kusan kwana akan abin salla suna gayama UBANGIJI damuwarsu, gabannin asuba bilkisu ta farka tana ambaton a bata ruwa. Fita Batool tai ta kira Doctor'n daya kwana duty, babu jimawa suka dawo tare. saida ya tabbatar babu wata matsala tare da Bilkisun sannan yace su bata ruwan tasha.
          Tunda ta kafa kai a babban goran ruwan da Batool ta saka mata a baki sai da ta shanyesa tas sannan ta ɗauke kanta, dukansu kallon mamaki suke mata hatta da Doctor ɗin kansa, sai dai babu wanda yace komai.
      murya a sanyaye tace, “Mama zanyi sallah”.
         Taimaka mata batool tai ta sakko a gadon, mama ta rakasu har toilet ɗin ta sirkama bilkisu ruwan wanka da ruwan dake cikin flask, fita batool tai, mama ta taimakama bilkisu tai waka da gasa jikinta dukda tana ta noƙewa saboda kunya. Itako mama sai tayi kamarma bata gantaba. Bikisu taji daɗin wankan sosai, takumaji karifin jikinta, sallolin dake kanta ta shiga ramawa harda sallar zuhur ɗin jiya data tabbatar batayita cikin nutsuwaba.

★★★★★★

             Zuwa 10:30am na safe dukkan mai alhakin tofa albarkacin baki akan wannan matsalar ya hallara a gidan Dady, bisa umarnin Alhaji baba daya buƙaci hakan, dan yanason jin gaskiyar magan akan abinda Jawaad ya faɗa masa gameda zancen Azeema da yace sunsani. Jawaad yana jerin waɗanda sukazo a farko-farko dan tare yake da Alhaji baba, hakan kuwa yaso bama kowa mamaki dan sunsan halinsa sarai da iya ƙin zuwa wajen meeting akan lokaci saiya gama shanya jama'a, amma yau abin mamaki sai gashi cikin masu sakkon zuwa.
             Bayan isowar Imam da wasu daga cikin manyan massallacin da aka ɗaura auren Salman da Qaseem daya rame sosai tamkar wanda ya kwana biyu yana jiyya suka shigo suma, ya ƙara haske da tsayi abin tausayi, Jawaad dai baiko kalli inda Qaseem yakeba, amma shi Qaseem sai binsa yake da wani irin mugun kallo tunda suka shigo.
     Imam ne ya buɗe taro da addu'a, a kuma dai-dai lokacinne Shahudah da Mom da suka taho daga asibiti bisa matsawar Shahudahn suka shigo suma, wajen zama suka samu idon Shahudah akan Jawaad tana mai kwarar da hawaye, itama harta rame kwana ɗaya kacal. Bayan imam ya kammala addu'oi ya ɗaura bayani da cewar, “Nasan kowa dake nan yana neman amsar tambayarsane a gareni, wadda yinin jiya har zuwa dare na ɓata lokacine wajen nemota nima amma har safiyar yau ban samo amsarba, narasa wannan wane irin cuɗaɗɗen al'amarine mai sarƙaƙiya, a hasashena har junnu saida na kawo dukda bani da tabbacin haka balle hujja, ban saniba shin ko a cikinku wani nada amsar da nima nake cikin ruɗani da bulayin nemanta?”.
        Shiru falon yayi babu wanda ya iyayin koda tari, sai shashshekar kukan Shahudah kawai ke tashi. Uncle Nasir ne yay ƙarfin halin bama Shahudah umarni akan ta tashi ta fita. kafaɗa ta maƙe alamar bazata tashinba, ta koma jikin Momy ta lafe tana masa kallon harara dukda kasancewarsa wan uwarta. Babu wanda ya iya sake cewa komai game da tashin Shahudah, dan kuwa anga iyayenta basu tankaba alamar basu da damuwa da zaman nata su. Jawaad yay gyaran muryar da kowa ya maida hankali kansa, batare da ya kalli kowaba yace, “Imam kayi haƙuri, babu ta inda zaka iya samo amsar sarƙaƙiyar jiya kaida duk wanda keda alhakin sanin sirrin massallacin nan. Ni dasu Momy mune kawai masu wannan amsar, dukda inada tabbaci da yaƙinin bayanmu wasu sunsan komai koda ba duka ba”. kaf falon babu wanda bai sagade yana kallon Jawaad ba, yayinda Momy ta miƙe zumbur tana nunashi, “Amma kai dai Jawaad anyi shaiɗanin yaro, a gidan ubanwa nake da amsar? Ni dama tun jiya da akace an nemeka an rasa nasan kaine shaiɗanin daya dace a nema dukka

n amsoshinnan a wajenka.......”
       Murmushi Jay yayi, sai dai baice komaiba, hasalima kansa a duƙe yake bai kalli kowaba har yanzun. Alhaji baba ne ya tsaida Momy jin tanata aibanta masa jika, “A'ishatu, inaga mubashi dama muji ina maganganunsa suka dosa kafin mu yanke hukunci koda na furucin bakine, mudukanmu nan a ƙage muke dason jin amsa, yakamata muji yaya akai aka kwana a ragaya bayan munsan shirinmu a tandun mai ne”. Magana Momy zata sakeyi Qaseem yace, “Momy Please ki zauna miji munafurcin dazai faɗa”. Ƙwafa Momy tayi ta koma ta zauna saboda gargaɗin da Uncle Uwaisu yay mata da idanu.
        Shirun da akaine ya saka Jawaad ɗagowa, yace, “Inaga kafin warware dukkan sarƙaƙiyar massallaci yakama musan wacece Azeema da aka ɗaurama Qaseem aure da ita? Domin wannan shine kawai zai zama mabuɗin buɗe mana gaskiyar abinda muke son sani baki ɗaya”. Tsit falon yay saboda bugawar da zukatansu sukai a lokaci ɗaya babu zato ko tsammani da zuwa furucin Jawaad ɗin a garesu. Alhaji baba ya katse shirun da cewar, “Banda abunka Muhammad Jawaad muma ai duk amsar da muke nema kenan akan Habib da Azeema?”.
         Jawaad yace, “Hakane Alhaji baba, amma ina ganin karmu jata da nisa, domin su Uncle duk sunsan wacece Azeema da Habib, idan ka cire Imam da jama'arsa, kai da Uncle Sulaiman, Uncle Sadiq, Qaseem, kune kaɗai kuke neman ƙarin bayani”. Uncle Sulaiman yace, “To mukam saiku amsa mana kunata sake dilmiyar damu a hasashe”. Fuskar Uncle Nasir a matuƙar ɗaure cikin kafe Jawaad da idanu yace, “Mikake nufi da waɗanan kalaman naka?”.
         Jawaad yace, “Babu abinda nake nufi Uncle, kawai dai ina son kowa ya fahimci daga ina matsalar take harshi Qaseem ɗin da aka ɗaurama aure.......”
      Cike da masifa Momy ta sake katse Jawaad da faɗin, “Inma wani munafurci ka ƙulla kai zai ƙaremawa, inace dai sokake kace mune muka haɗa auren Azeema da Qaseem batare daya saniba, to ai mun isane, yarinyar da ya kawo yanason zai aura batai manaba, tayaya idan shi baisan ciwon kansaba mu zamu biye masa duk muzama mahaukatan?”.
       Cikin ɓacin rai Jay yace, “Amma miyasa ni da nazo neman a bani na aura kukace Qaseem shi zai aureta?”. Yanzukam tamkar Momy zata mari Jawaad ta bashi amsa a matuƙar zafafe “Saboda Shahudah tafi ƙarfin yin kishi da ita, bandama rashin mutunci da raini irin naka Jawaad, bakaji kunyar zuwa a gaban idanunmuba kace mu haɗa maka ƴar cikinmu da wadda mukema alfarma mu aura maka”. Sosai zuciyar Jawaad take sake hasala, sai dai ƙoƙarin dannewa yake dan koba komai Momy yayar mahaifinsa ce ita, cikin ƙoƙarin danne fushinsa yace, “Amma Momy dan kawai baƙwa ɓuƙatar marainiyar ALLAH ta jingini da jininku sai kuje ku biya wani kuɗi dan ya aureta bayan kunsan shiɗin ba mutumin kirki baneba? Wai shin nawa ita wannan duniyar take da har muke tunanin wanda muka tseramawa bazai taɓa taddomu ba? Baƙwason ta auri ɗanku, baƙwason tayi kishi da ƴarku, tominene fa'idar biyan wani ya aureta? Saiku barta ALLAH ya kawo mata wani mijin, shi kuma Qaseem ku sanar masa bakwason alaƙarsa da ita bawai saikun cutar da itaba ta hanyar da batajiba bata ganiba.......”
        Qaseem ya miƙe a fusace zaiyi magana Uncle Sulaiman da baƙin ciki ya lulluɓe yay saurin katseshi daga shi har Jawaad ɗin, yace “Kai Qaseem kaga zauna, ku kuma Kunga kudaina mana magana a cuɗe daga kai har Humaira, shin minene ya faru?”.
           Sosai zuwa yanzu fushin Jawaad ya kasa dannuwa, cikin zafin zuciya da kowa yasanshi da ita idan aka kaisa bango yace, “Wato Uncle yarinyace suke riƙo a gidansu, har takai maganar aure ya shiga tsakaninta da Qaseem, kuma sune suka amince masa, amma kuma sai suka koma ta bayan fage suka nema masa auren Azeemar gwaggo Hajarah. Bayan kuma Alhaji baba yaje akan su bani auren yarinyar amma suka nuna min cewar shi Qaseem ɗinne zai aureta. Abinda kuma zai baka mamaki ita kuma yarinyar suka samu wani da sam ba mutumin kirki bane suka biyashi akan zasu aura masa ita yarinyar batare datasan da shirinsu ba, kuma sun nuna masa duk badaƙalar da za'ayi karya sake ya saketa, wannan shine dalilin dayasa na koma nima ta hanyar da sukabi na canja nasu shirin

da nawa, tabbas nine na canja takardar da akaba Imam da tawa a lokacin da yake ƙoƙarin shiga massallaci.. Bayan duk an kawomin bayanai akan shirin da sukai na cutar da yarinyar saina shiga nazarin neman hanyar daya dace na hana faruwar mummunan ƙudirinsu, a kaf hanyar danake gani zata zama yarinyar za'a sake cutarwa, dan haka daga ƙarshe sai na yanke shawarar bin hanyar da suma sukabi, wato ta ƙarƙashin ƙasa. Imam idan har baka mantaba bayan isowarka massallaci wani yazo ya sameka akan batun wani aure, har ya roƙi afuwa akan rashin kawowa da wuri, kaikuma ka amshi uzirinsa tare da bashi takardar list ɗin sunayen waɗanda za'a ɗaurama aure a ranar kace ya rubuta sunayen waɗanda yazo dasu a gurin, to ba kowa bane face ni, da wannan damar nai amfani na canja takardarma baki ɗaya bayan na kwafe sunayen dake can nakuma canja namu a yanda naso”.
          Salati manyan suka sanya da wannan al'amari, yayinda Cikin ƙaraji Qaseem yace, “ Momy!!!, mikuke nufi da hakan da kukayi to? Minai muku da zafi haka kuka zaɓi zalintata ni da Bilkisu?!, to wlhy, na rantse da ALLAH, ku kwana da sanin...........” da sauri Momy ta rufe masa baki, sauran ƙarfinsa da wanda ɓacinrai ya kawo masa yanzu ya tattara ya hankaɗe Momy gefe ta faɗi. Jawaad ne yay saurin miƙewa yana faɗin, “Qaseem minene haka? Baka da hankaline?”.
         “Eh bani dashi kaikuma? Idan kai haƙuri kaima ina tafe kanka,  garama kayi gaggawar sakarmin mata kafin kanema numfashinka a ƙirji ka rasa”.
      Wani banzan kallo Jawaad yay masa, kafin ya bashi amsa Shahudah ta katsesu da jehoma duk wanda ke falon tambaya cike da rashin kunya. “Kai broth kamaji munafukan da suka ƙulla maka naka makircin, nikuma saiku faɗamin wanene Habib yake koma wane oho muku, kaikuma Bb kai gaggawar sakin waccan ƴar iskar yarinyar tamaje ta auri Uban Qaseem a yanzu wannan bai dameniba dan kaina kawai na sani, gwarama kowa yasan abinda zanyi sai yafi naka ɗaga hankalin kowa dake gidanan wlhy”.
        Jin komai ya warware Imam da tawagarsa suka miƙe domin tafiya, a ganinsu wannan matsalace ta cikin gida, sukam tunda sun fita gara su kama gabansu. Godiya su Alhaji baba sukai musu sannan suka fice.
         A take falon ya kaure da hayaniya har babu maijin maganar ɗan uwansa, Jawaad na shirin ficewarsa Shahudah dake kuka tana zubama mutane rashin kunya tai saurin riƙoshi, “Wlhy bazaka fitaba saika saki tsinanniyarnan bb”. Bai tanka mataba, sannan kuma bai juyoba, sai ƙoƙarin fisgar jikinsa da yay zai fice abinsa. Ƙara Shahudah ta ƙwalla wadda ta dawo da duk hankalin ƴan falon kansu, sosai ran Jawaad ke tafasa, ji yake badan wani daliliba da sai yayma Hudah dukan mutuwa yau, saida kuma shi a tsarinsa babu bugun mace. Alhaji babane yace, “Jawaad dawo ka zauna”. Umarnin Alhaji baba yabi, ya juyo tare da zubama Shahudah wani mugun kallo daya sakata sakar masa riga ta durƙushe a wajen tana kuka, kota kanta baibi ba ya koma inda ya taso ya zauna. Ran Alhaji baba a ɓace yace, “Wanene Habib ɗin to dakasa ya aurar musu yarinya?”.
        Shima Jawaad ɗin ran nasa a ɓace yake, amma dai sai ya danne cikin ladabtaccen harshe ya bama kakan nasa amsa, “Alhaji baba shine wanda suka biya ya auri yarinyar”.
     Kuka Momy ta saka mai ƙarfima kuwa tana zagin Jawaad da ja masa ALLAH ya isa.
        Cikin rawar baki Uncle Nasir ke faɗin, “Yanzu nan Jawaad ɗan fir'auna ka aurama Shahudahr?.........”
      Uncle Sadiq yace, “Wane irin sunane haka kuma Yayah?”. Kasa magana Uncle Nasir.
       Dad kam ai hawaye kawai yakeyi kashirɓan, saboda wani irin ruɗani da wautarsa akan sakarma Momy ragamar gidansa yake hangowa. Falon yay tsit kowa na jiran ƙarin bayani daga garesu, yayinda Shahudah dake jikin Momy keta ribzar kuka. Qaseem kansa kawai ya dafe saboda tafasar da zuciyarsa ke masa da matsananciyar ƙuna.
          Kowa dai ya fahimci su Mom sune suka gina ramin mugunta wa marainiyar ALLAH daga ƙarshe ya rufta dasu batare dasun fargaba, Alhaji baba ya katse shirun da faɗin, “Bin ƙwaƙwƙwafin komai a yanda yake baida amfani, tunda su bamusan manufarsu ba, a ganina yanzu mafita kawai ya dace mu nema kamardai....”
     Qaseem ya

ɗago kai, cikin ɗacin rai yace, “Mafita itace wannan yaron ya sakarmin mata tunkafin rayuka suyi ɓacin da yafi na

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login