Showing 42001 words to 45000 words out of 142169 words

Chapter 15 - Nadiya Book 1 Complete Hausa Novel

03 Feb 2025

451

janyo wayarta ta dannawa Anty Lima da yake karfe goma bata kai ga yi ba.

Tace mata ita dai gaskiya zata mayar mishi da kayanshi don bata ga dalilin da zai sa yayi mata wannan kyautar ba.

Anty Lima tace, "to wai sai me don ya baki kyautar waya da turare? Kin rokeshi ne kika ce ya baki?"
Tace, "wa? Allah Ya tsareni!"
Tace, "to kin gani? Shi yayi radin kanshi ya baki, don haka ki amsa da hannu bibiyu. Ina ruwanki da shi da kayan daya baki? Idan kin tashi ki war??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????e min turare guda don nasan zasu hadu sosai, na ji turarukan da yake amfani dasu masu kyau ne kuma suna da kamshi."

Tayi yard dariya, "Allah Yaa kyauta miki wallahi! Sai ki bari sai nayi tunani na tabbatar zan rike din sannan. Sai da safe, barci nake ji!"
Suka yi sallama ta kashe wayar.

Kwanciyarta tayi ta ajiye kayan a gefe.
Da asuba tayi mamaki da taji Abbansu ya fito ya bi daki-daki wai yana tashinsu sallar Asubahi.
Abin ya bata mamaki matuka, ta kame baki cike da tsananin mamaki. Mama da ta sallame sallah ta kalleta ganin yadda tayi hangangam da baki tana bin wannan lamari da kallo, tace, "Nadiya ki tashi kiyi sallarki kada lokaci ya kure kinji!"

Haka ta lallabata ta tashi tayi alwala tayi sallah.
Gari yana yin haske ta je ta gaishe da Abbansu.
Ta fito daga dakin nashi ta tsinci Salame tayi kerere a kofar dakin amarya, ita kuma amaryar ta ci kwalliyarta da wani mini skirt dinta da yar yaloluwar riga zata shiga dakin Abban nasu.
Tana ganin Nadiya sai ta hau fara'a, "a'ah! Antynsu kin tashi kenan? Ina kwana, ya gajiyar tafiya?"

Gaisuwar tata sai ta bata kunya, tace mata, "Gajiya fa Alhamdulillah. Ina kwana?"
Salame ta ja wani dogon tsaki, dai dai lokacin Lantana ta fito daga nata dakin da riga da zane daban-daban, fuskar nan tata dagaje-dagaje da alama dai ita ko sallar da aka tashesu bata kai ga yi ba.

Laminde tace, "oh ni Yaya! Jiya kinji tashin hankalin da naji kuwa?!"

Nadiya ta kalli Laminde din cike da mamakin abinda tace, a tunaninta ko rashin lafiya ta kwana da ita.
Salame ta dannawa Amarya harara, "jiya ke kika ga tashin hankali ko ni! Wallahi ban taba ganin rashin mutunci ba irin na jiya. Kawai aka hanani barci don tsabar jaraba da kwarzaba da rashin tunani! Kai baka ganin gidanka gidane na yara, kuma dakina da inda kake bango-da-bango amma ba zaka yi tunanin hakan ba? Wannan ai shiga hakkine da rashin sanin darajar dan Adam!"

Sai lokacin ta fahimci abinda ke faruwa a wajen, dariya ce ke kokarin kufce mata, ta sanya hannu tana rufe baki don kar ta fito.
Ita kuwa amarya bata nuna ta fahimci abinda suke nufi ba, sai ta bisu daya bayan daya ta gaishesu, ta juya ta fada dakin Mai gida ta barsu anan ba tare da ta jira sun amsa ba.

Suka bita da harara kamar idanunsu zasu fadi. Lantana tayi kwafa tace, "yar iska kawai! Da alama dai wannan karon tsohuwar karuwa aka kawo mana!"
Salame tace, "bar ni da ita, in takamarta iskanci, ni ai na fita iyawa! Wallahi sai na gasa mata gyada a tafin hannunta!"

Nadiya da har lokacin take wajen tana kallonsu da murmushi akan fuskarta, ta kyalkyale da dariya har da tafa hannuwa, suka hau binta da kallo kamar wadda ta samu tabuwa.
Tace musu "ai shi yasa masu iya karin magana suke cewa wai a dinga sara ana duba bakin gatari. Kuma dai sannu bata hani na zuwa sai dai fa a dade ba a je din ba!"

Suka zaburo mata a lokaci guda, "me kike nufi?!"
Ta haskesu da wani murmushin tura haushi, "abinda nake nufi kenan!"
Ta shige ta barsu anan suna ta sakin maganganu sai kace wadanda ke shirin tada bori.

Da ta nunawa Mama wayar da Habibu ya bata da kuma abubuwan da suka wanzu a Maiduguri. Itama dai shawarar da Anty Lima ta bata ta maimaita mata, tace ta amsa tayi amfani da su tunda dai shi ya bata kyauta ba roka tayi ba. Kuma dai babu mai mayar da hannun kyauta baya sai shaidan. Don haka ta amsa kawai.

Maryam da take jinsu kuwa tayi tsalle ta dafe tsohuwar wayar Nadiya din, tace, "dama ina ta jiran ranar da zaki yi sabuwar waya ki bani wannan, sai in ba Amina ta wa."
Da yake ta hannun nata karama ce.

Nadiya tayi murmushi, tace "to shikenan. Bari idan na dauke kayan cikinta sai a bada a canza screen din, sai a canza."

Suna karyawa suka fito da kayan wanki jibgi guda, ranar haka suka yini suna aikin wanki ba kama hannun yaro. Da suka gama suka shiga dakin Mama shima suka gyara har da canza zaman kayan dakin.

Zuwa yamma ta dauke duk abubuwan da take bukata daga tsohuwar wayarta zuwa sabuwar, ta bada a kai tsohuwar wajen gyara.

Ta kira Aramide tana tambayarta game da wajen aiki, ta bata tabbacin an je an share komi an gyara, don haka idan sun je gobe aiki za a hau yi kawai babu bata lokaci. Tace itama satin sama zata dawo saboda wajen aiki. Suka yi sallama akan hakan.

18.


Kwana da kwanaki suna ta wucewa a hankali. Nadiya ta koma ta cigaba da gudanar da ayyukanta kamar da. Tuni ta manta da abin wani Habib da kurar data kwasoshi. Musamman da tun barinta da shi na karshe bata kara gani ko jin labarinshi ba.

Wata ya shige a haka, sai gashi har an fara zancen shigowar azumi nan da wata daya.
Zaman gidan nasu sai ya rikide ya koma wani yanayi na daban. Yadda su Salame suka so shine idan amarya ta zo, su yi kokari su janyeta ta koma cikinsu, su dinga muzgunawa Mama. Sai abin ya juye ya koma kansu.
Don kuwa ita dai amarya ba ta tasu take yi ba, ta kama Mama da 'ya'yanta ta rike kam da hannu biyu. Babu abinda ya dameta, yadda kowa yake kiranta Mama itama abinda take kiranta da shi kenan. Haka zata zage ranar girkin Mama ta tayata kamar ita ke girkin, ita kuma Mama ranar girkin amaryar sai su Maryam da Amina su tayata. Itama Nadiya idan tana nan ta kan tayata din.

Nan da nan kuma sai suka saba sosai, ya zamana dakin Mama nan ne wajen zamanta. Hakan kuma sai ya zama abin gulma da maida magana a wajen su Lantana. Su ce Mama ta asirceta, su ce ta mallaketa, su ce ta maidata baiwa. Zance dai kashi-kashi. Ita kuwa Mama da yake dama can ba kulasu take yi ba, sai tayi kunnen uwar shegu da su. Itama amaryar da Allah Yayi ta marar son rigima, sai take kyalesu bata shiga harkarsu.
Har yaran gida suka sa wai su dinga yiwa amarya rashin kunya, ko kuma Idan ta aikesu su ki zuwa. Shi din ma da ba don Nadiya ta taka musu burki ba da sai abin ya fi haka.

Ranar juma'a ta taso daga shago da dare dai-dai lokacin data saba dawowa. Tayi sallama ta shiga gidan, da yake girkin amarya ne ranar bata tsaya ta sayi abinci ba. Tunda tana da tabbacin kwanon abincinta yana nan.
Su Salame dama ba a zancensu, tuni ta fita ta harkarsu akan abinci dai. Saboda su dai farko ba kasafai suka cika tsayawa su dafa abinci mai dadi ba. Na biyu kuma abincinsu suna saukeshi a tukunya, da shi da babu duk daya ne. Idan kana kusa da su kayi wuf ka mika kwano su zuba maka, idan ka zauna jira kuwa sai su ce maka ai ya kare yara sun cinye. Ta sha biye musu akan hakan su yi ta fada, su mata gori su zageta tas, shima Abbansu idan ya dawo ya sameta yayi ta zagin har ya dinga hadawa da zagin 'katuwar banza da ita ta zaune mishi a gida yana ciyar da ita a banza! Idan ta ji haushi ta bar mishi gidan mana ko ta dinga ci da kanta!'

Da taga abin ya kai ga haka sai ta yiwa kanta fada. Tunda dai Allah Yasa tana da rufin asirinta dai-dai gwargwado. Shagon da take zuwa shi ya taimaka mata take sauke nauyin al'amuranta da dama. Sai ta kara da lissafin abinci a ciki. Idan ba girkin Mama ba dama ba abincin su ke ci ya ishesu ba. Don haka ta kyale musu kayansu.

A dakin Mama ta ci karo da Basira ta je gidan, da 'ya'yanta uku. Ta zauna suka gaisa da ita tana tambayarta ya kwana biyu, saboda sun jima basu gaisa ba. Gwara Zainab suna yawan yin waya da ita tunda da waya a hannunta, ita kuwa Basira da yake bata da wayar a hannunta sai idan ta samu aro sannan ne take kiransu. Shima kiran sau tari bai wuce ta ce Nadiyar ta tura mata kudi ba ko kaya.

Ta kunce ledar sauran doughnuts da suka yi da cupcakes, ta bada biyu aka ba amarya, su Fatima ma ta basu biyun su raba, ta ba yaran Basira dai-daya sauran kuma ta barwa su Maryam.

Tayi sallah, ta zauna aka zubo mata abinci zata ci. Daga Basira har yaran suka zuba mata idanu yuu! Suna kallo kai kace sauran yunwa ne. Sai kawai ta mika musu kwanon, suka karba suka hau ci hannu-baka-hannu-kwarya. Kafin kace me! sun tada faranti guda. Suka tsaya suna lasar hannu da kwano.

Ta kallesu da tausayi zane akan fuskarta. Tace, "ko baku ci abinci bane? Maryam je ki tambayi Anty amarya ko da sauran abinci a basu."
Maryam tace, "wallahi sauran abincin kenan dama na ki ne ya rage, sai na Abba. An zuba musu tun dazu sun cinye!"

Taga yanayinsu dai su duka taga babu alamun sun koshi, ita kanta Nadiyar yunwar take ji saboda ko da rana bata tsaya ta ci abincin ba sosai.
Don haka ta bada aka sayo musu shayi da biredi suka kara da shi.

Tayi tunanin idan Abba ya dawo su Basira din sun gaisa, tafiya zata yi kamar yadda ta saba. Sai taga da yazo ma Basirar bata je ta gaisheshi ba. Yaran ma bata bari sun fita wajenshi ba. Sai tasan ba lafiya ba.

Wannan shine karo na kusan barkatai da Basira din tayi yaji ta je gidansu, a wannan tsakankanin kuma mijinta ya saketa har sau biyu.

Ta tambayeta, 'yau kuma lafiya?'
Ta bude baki tace, "yaji na yi!"
Nadiya ta kama baki, tace, "yanzu yaji kuma saboda Allah da Annabi? Me ya faru ne?"
Tace, "menene ma bai faru ba? Aure idan mata tana ciyar da kanta da 'ya'yanta ai babu shi, don ban ga abin yi ba a gidan da miji ba zai fita ya nema ya kawo min ba. Sai dai idan ni na samu in ciyar damu. Sakina ma zai yi wallahi, Mali zan tafi neman kudi!"

Nadiya ta dafe baki cikin mamaki, Mama kuwa ta hau sallalami da salati. Tace, "ke yar nan! Yaran kuma kiyi yaya da su?"
Tace, "yo in barsu wajen ubansu mana tunda ba dasu naje gidan ba! Yau ma don nasan idan yaga yaran ba lallai ya biyoni ba, ai da wallahi a can zan baro su. Amma yanzu daya bani takardata, kayan dakina zan sayar inyi tafiyata sai in kai mishi yaranshi!"

Mama ta sanya musu baki, tace, "a'ah fa Basira! Ita rayuwa da kike gani fa yar a bi ta a hankali ce. Shi kuwa zaman aure dama ai ya gaji haka. Musamman ga mutum marar tsayayyen aikin yi. Dole fa sai matarshi tana hakuri, itama kuma idan da hali ta dinga taimaka mishi. Sai kiga watarana hakurin yayi mata rana!"
Ta tabe baki, tace, "ai wallahi in dai da cuta a ciki fa ba zan yi wannan hakurin ba! Zaluncin ai yayi yawa!"

Nadiya kallonsu kawai take yi, Mama tana ta kokarin tausar Basira ita kuwa tayi biris da ita.
Tasan halin Basira sarai, bata da hakuri, kuma akwai kafiyar kai idan ta yankewa kanta abu.

Ta numfasa tace, "ke ma fa Basira kina da naki kason laifin a ciki! Waye yace miki mijine kadai yake hakuri da mace ita ba zata yi da shi ba? Kin san halin mijinki sarai, ai yana da kokarin yi. Kuma lokacin da yayi miki hidima ai yayi, me yasa baki taba korafi ba sai yanzu? Ashe ke ba zaki iya zama ki rufawa mijinki asiri ba a lokacin da ba shi? Shikenan ke kullum kina tafe akan hanya yau kinyi yaji gobe kin kaso aure? Yanzu kuma kice wai kasar ma zaki bari kwata-kwata ki tafi neman kudi? Saboda rashin wadatar zuciya da rashin godiyar Allah irin naki? Sau nawa ana baki jari iye? Ina ce ko wancan watan da ya wuce Yaya AbdulHadi dubu saba'in ya tura miki ki ja jari, me kika yi da ita ne cikin abinda bai gaza wata biyu ba?!"

Budar bakinta sai cewa tayi, "yo wai kema kina ta wani tada jijiyar wuya kina fada. Me kika sani ne a cikin rayuwar auren da abinda ke cikinta? Gaskiya ki daina yi min irin wannan katsalandan din! Ki bari idan kinyi auren kin hadu da miji irin nawa kin fahimci ko me kenan. Yauwa!"
Ta saki tsaki.

Nadiya tayi wani dan murmushi dake nuna bacin ran da kalamanta suka haddasa mata.
Tace, "kwarai kuwa, ban yi aure ba Basira, ban kuma san me ke cikin rayuwar auren ba don haka Allah Ya baki hakuri da katsalandan din da na miki. Sai dai ita duniya ai ta fi bagaruwa jima, kuma ni nasan wallahi da ni ce a yanayin da kike ciki, ba zan tattara in kashe aurena ba wai in tafi duniya neman kudi. Su yaran nawa su yi yaya kenan? Tunda haka ne kuma, ki tanadi wajen zaman yin idda kin dai san Abba ba zai barki ki zauna mishi a gida ba!"

Yana daya daga cikin dokokin Abban nasu, mace in dai ya aurar da ita, to daga ranar ta bar gidanshi har abada. Shi da ita sai dai zuwa gaisuwa da yini, amma kwana ma shi bai amince ba saboda yace hidima ce suke kai mishi.
Don haka da ya fuskanci ma wai yaji kika yi ko auren ya mutu, yake rufe ido ya zabga miki rashin kirki, komi dare kuwa sai kin bar mishi gida, babu sassauci.

Sai idanun Basira kuma suka raina fata, tayi narai-narai da ido.
Tace, "yanzu ya zanyi to? Gashi Innata itama tana gida fa, yanzu idan na kwasa na tafi can abubuwan sai suyi musu yawa!"
Nadiya ta tabe baki tace, "shi yasa ai masu iya magana dama su kan ce wai a dinga sara ana duban bakin gatari!"
Ta juya tayi kwanciyarta ta kyale Basirar anan tana maida yadda aka yi.

Washegari tunda farar safiya sai ga Abbansu ya dira a kofar dakin Maman.
Dama Nadiya tasan dole sai ya san da zuwanta, tunda ko ita ta buya bata je inda yake ba ko 'yay'anta, dolene matan gidan zasu bashi labari.

Ya kankance idanu yana kallon Basira din data tsuguna tana gaida shi. Ko amsa gaisuwar bai yi ba ya hau watsa mata tambayar, 'me take yi a gidan?'
Ta karkace kai zata hau kora mishi bayani, yayi gaggawar dakatar da ita, yace, "kinga, ba dogon bayani nake nema ba, ga mijinki can ya doko min sammako ya zo nemanki da 'ya'yanshi, don haka ki kwashesu ku tafi salin alin. In ya so idan kun koma gidan sai kuyi duk wadda zaku yi dai, amma ba anan gidan ba. Kin sanni sarai, kin san bana daukar wannan rashin hankalin da hauka! Idan ma auren kika kashe daga karshe, kada ki kuskura in ga ko mai kama dake ne a kofar gidana. Don wallahi sai na sanya katako na sassake miki su, kin dai ji na fada miki!"
Ya juya fuu! ya wuce yana mai kara maimaita mata lallai nan da yan mintuna ta bar gidan.

Basira ta dora hannu aka zata kurma ihu, Nadiya tayi gaggawar dafe mata baki data hango su Salame suna lekensu ta kofar dakinta ita da Lantana.

Samu suka yi ita da Mama suka tausheta akan tayi hakuri ta bi mijinta tun kafin Abba ya tata mata rashin kirkin da yake ikirari.
Nadiya tace mata, "idan ma rashin sana'a ne matsalarki, kinga wajen aikinmu muna neman masu wanke-wanke da goge-goge, idan kina so sai a baki, tunda albashin babu laifi yana da dan kauri!"

Nan da nan kuwa sai ta hau zubda fara'a, tace, "Yo Anty Nadiya da tun wuri kika yi min wannan bayanin ai da bamu kai ga haka ba. Aiki ni ko wane irine in dai za a biyani ai wallahi ina so!"

Nadiya tace, "tun farko idan baki manta ba ai na miki zancen aikin lokacin kina cikin ganiyar jin dadin arzikin mijinki, kika ce min ke mijinki ya tsaye miki don haka baki bukata ko?"
Sai ta hau nade tabarmar kunya da bori, ta hau dariyar jin kunya, tace, "dadina da ke Anty Nadiya ba dai riko ba! Ni dai don Allah ki min kokarin aikinnan kinji? Kuma don Allah kiyi hakuri akan maganganun dana fada miki jiya, raina ne ya baci da yawa."
Nadiya tace, "ni kuwa me yasa zan yi fushi don kin fada min gaskiya? Ai gaskiya ce, ni da ba sanin rayuwar aure nayi ba meye nawa na baki shawarar yadda zaki zauna da mijinki?!"

Da haka dai ta musu sallama ta bi Mijin nata bayan Mama ta bata kayan masarufi dangin su sabulai na wanki da wanka da su omo da kayan su maggi da su daddawa, har da dora mata da dubu biyu. Haka tayi ta musu godiya ta tafi.


*****

Kamar yadda tayi alkawari kuwa, a satin daya biyo baya Basirar ta fara zuwa shagonsu. Aka bata aikin goge-goge da wanke-wanke, biya kuma mai kauri ake mata wanda Nadiya take da tabbacin zai iya rufa musu asiri a rayuwar takatsantsan.

Sati biyu da yin haka suka je Kano gidan Anty Jamilah ita da Maryam. Mijin Anty Jamilah din aka yiwa aikin koda a asibitin Murtala dake nan Kano din suka je dubashi.
Da suka je din kuma sai suka tarar ana yiwa kanwar abokiyar zaman Anty Jamilah din biki, don haka suka shiga ciki aka yi ta fafatawa da su.

Daga zuwa wajen dinner da dare, Yayan amarya ya tafi ya saukesu ita da su Rabi'ah da abokan amaryar guda biyu da aka yi musu masauki anan gidan Anty Jamilah din, sai bawan Allah Ya mannewa Nadiya.

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login