Showing 57001 words to 60000 words out of 142169 words

Chapter 20 - Nadiya Book 1 Complete Hausa Novel

03 Feb 2025

477

hakuri take bashi.

Shine ya sake tura mata sakon cewa kada ta damu kanta saboda shi dai tsakaninshi da Allah ya hakura da ita, ba don baya sonta ba sai don zai fi son ya tayata yiwa iyayenta biyayya. Shima har da kara yi mata nasiha da wa'azin muhimmancin yiwa iyaye biyayya da kuma biyayyar aure. Daga karshe yace mata ta tura mishi da account number dinta yana so ya bada gudummawarshi ta biki.

Tayi murmushi ranta cike da jindadin hakan. Ta tura mishi da sakon ta gode dai kwarai da gaske da fahimtar da yayi mata, amma yayi hakuri ta gode da addu'arshi ma a hakan kawai.

Ta kashe wayar tare da janyo Aramide ta zaunar da ita. Itama sai a lokacin take bata labarin auren da zata yi.
Don kuwa zuwa lokacin ta fara sakewa da lamarin gabadaya.

Aramide ta rungumota cikin murna, tace, "kai kawata! Amma na tayaki murna sosai da sosai wallahi! Amma shine baki fada min tun a lokacin ba?"

Ta dafe kumatunta tana kara jingina da kujerar da take kai. Tace, "to me kike so in ce Ara? Har ga Allah auren nan fin karfina aka yi. Kin sanni sarai bani da akidar wai dole sai auren soyayya zanyi, amma ko babu soyayyar dai at least ace an samu fahimtar juna da gamayyar hali. Amma wadannan dinma bamu dasu ni da shi. Kada kuma ayi zancen irin rigingimu da nake hangowa zasu iya faruwa anan gaba ta dalilin auren nan wallahi. Bana son abinda zai iya dawowa daga baya ya karasa bata dan guntun zumuncin dake tsakaninmu da Hajiya Ummah, dama ba wani mai kwari bane."

Ara ta dafa kafadarta, "ke wallahi kada ki wani sanyawa ranki damuwa, wannan fa ba komi bane. Don soyayya da fahimtar juna zasu biyo baya jazaman ne, kin ganki kuwa Nadiya? Wane namiji ne zai ce wai ba zai so ki ba? Ai karya ne. Zancen zumuncin su Madam kuwa ki barsu a yadda kika gansu kawai. Idan ma ta dawo ta cabe musu daga baya dai babu hannunki a ciki, shi tsuntsun da yaja ruwa dama ai shi ruwa kan doka. Ki cigaba da addu'a kawai. Wa ya sani kuma ta dalilinki zumuncin ya kara karfafa?!"

Nadiya ta ajiye gwauron numfashi, "I doubt. Amma don addu'a kam ina yi sosai!"
Tace, "yauwa, sai ki kara zage dantse abinki. Yanzu dai da me-da me ake shirya mana na bikin?"
Tace, "babu abinda za ayi, aure kawai za a daura shikenan. Hakan kuma ni yafi min dadi."

Ta dan turo baki alamun ba haka ta so ba, "to Allah Yasa hakan shi yafi alkhairi. Amma dai ai naso ace bikinki na cashe sosai da sosai!"
Ita kuwa ta tabe baki, tace, "ai bikin da ake so da doki shi ake cashewa!"
Ara tayi dariya tace, "lokaci ne ai. Lokacin da zaki yi naki casun saboda murnar auren wa zai sani?!"
Ta wuce ta cigaba da ayyukanta Nadiya na binta da kallo tana girgiza kai.


*

Sannu a hankali sai gashi azumi har an yi na goma sha daya kamar da wasa.
Ta fito zata tafi shago da misalin karfe biyu na rana. Kasancewar daren jiya an kwana ana yin ruwa yasa garin yayi luf-luf, ni'ima ta samu.

A kofar dakin Mama ta ci karo da Amarya da Mama din suna gyaran gero da barzar kwakwa. A gefe guda kuma su Fatima ne da Amina da Maryam, wata na bare dabino, wata na gyaran ganyayyaki da Nadiya ta rasa ko na menene, wata kuma na aikin daka mazarkwaila gata nan kifi-kifi, tana zubawa a cikin wani kwano.
Nadiya tayi turus tana kallonsu, "yau kuma aikin me ake yi ne haka?"

Amarya tace, "ai wannan aiki naki ne ke kadai, ki je ki dawo zaki sha mamaki!"
Tayi dariya, tace, "ni dai in tukudi ne zaku yi to a sanya kwakwa da dabino sosai a ciki fa, na fi son shi a haka!"
Mama tayi yar dariya, tace, "ai in dai tukudi ne har sai kin gaji da ci Nadiya, don kuwa wannan duk naki ne."

Tana shirin bata amsa sai ga AbdulBaqi yayi sallama ya shiga hannu riki-riki da leda, Amarya ta amsa ta bude tana ciro faifayen cukui da wasu karin ganyayyaki da itace. Nadiya ta kama baki, tace, "yanzu wannan tarkacen duk a cikin tukudi?"
Amarya tace, "wannan ai ba ma duka bane. Kin san mu da yake sana'ar gidanmu ce yin wannan tukudin musamman na matan aure da masu shayarwa da kuma amare, to duk nasan abubuwan da ake sanyawa. Ai gyaraki zamu yi da kyau amarya, sai kin amsa sunan naki na amarya da babbar murya!"
Ita sai lokacin ma ta fahimci ashe tukudin amare ne suke kokarin yi. Ta tabe baki ta musu sallama ta wuce.

Ta bar Lantana dake gefe daya tana bare gyada tana turo baki, "aikin banza aikin wofi! Allah sa uwar mai hada kayan mata ma za a ba mutum ya hadiya, aikin banza ne. Ita matar cushe ai bata daraja!"
Nadiya dai ta kada kai ta fita daga gidan abinta. Yadda bata tankata ba haka su ma babu wanda yace mata uffan.

Tayi tsaye a bakin titi tana jiran abin hawa. Sai kuma ta fito da wayarta daga jaka ta shiga WhatsApp. Kara dubawa take yi wai taga ko cingam din nata ya tura mata hotonshi daya saba tura mata a kowace rana.
Yawanci idan sun fita sallar la'asar a can yake tura mata, nan kuma din a Nigeria wajajen karfe biyu kenan lokacin da take tafiya wajen aiki. Sai ya tura mata hotonshi hade da maganganu na tsokana da neman magana, wasu lokutan kuma ya kan tura mata wani hadisi ko aya data dauki hankalinshi ne idan yana wajen tafsir.
Ko wanne ne dai daga ciki, bata taba tura mishi da amsa ba. Sai dai kuma a hankali, cikin rashin saninta balle yarjewarta, har ta fara sabawa da sakonnin nashi.

Lokuta da dama ta kan samu kanta da dariya ko murmusawa idan ya tura mata wasu hotunan da zai yatsine fuska, ko ya mata gwalo, ko ya kanne ido.
Gani take a girmanshi, da yadda ake fadinshi, kamar ba zai yi irin wadannan halaye ba. Amma sai ga shi yana yi mata hakan. Girman kan data fara ta'allakashi dashi sai ya fara wankewa daga ranta. Saboda wane mai girman kai ne zai iya yin abinda Habibun yake yi? Ta fara tunanin watakila duka fahimtar data mishi a baya, akasari ne na dan Adam kawai da kuma 'bad first impression'

Yau dai babu abinda ya aika mata. Haka ta je shago, bini-bini sai ta daga waya ta duba. Aka sha ruwa nan ma bata ji daga gareshi ba. Ranta sai yaki yayi mata dadi, abin ya fara damunta. Ta fara tunanin anya lafiya kuwa?

Tana shan tukudin da aka dama mata, wanda ya hadu fiye ma da yadda tayi tunani, don kuwa ya sha kayan hadi, ya kuma hadu da nono mai kyau wajen damun. Ta bude chats dinsu tana bibiyar sakonninshi, ta samu kanta da murmusawa kawai. Wani abu mai kama da kewa ya fara ratsata. Kawai sai ta kashe wayar da sauri tayi jifa da ita gefe daya.
Ita abin ma nema yake ya fara bata tsoro. Ta yaya tun kafin aje ko'ina Habibu zai sanyata zubar da makaman yakinta ne?

Hakan kuma ba shi ya hanata jan wayarta da sauri ba ta daga bayan kamar mintuna ashirin. Ta duba sakon da aka tura mata, ta ga shi dinne dai da take jira.
Shigar larabawa yayi yau, har da su lullubin nan da manyansu ke yi. Fadar kuma irin kyawun da yayi ma bata baki ne. Ta samu kanta da zama tana karewa hoton kallo na fiye da mintuna goma. Kafin kuma ta fita daga cikin gallery dinta da taga ya tura mata wani sakon ta kasar hoton.
'Nasan ke ma kina kewata Nadiya! Ina jin hakan har a cikin raina da ruhina da gangar jikina.'

Kuma da yaga bata mayar da amsa ba na yan mintuna, sai ya kara tura mata da,
'kiyi ta kauce-kaucenki dai. Kwanaki ashirin da tara ne suka rage. Na miki alkawarin sai bakinki ya furta min hakan a cikin kunnuwana!"
Ta saki wani wata yar dariya kawai tana girgiza kai, kwana ashirin da tara yace ko? Sun zuba ita dashi kuwa!
Ta kashe wayar tayi kwanciyarta.

24


Wajen karfe goma na safe ta tashi tana nade abin sallar data hau tana yin lazumi da yake kwana biyu ta tashi da fashin sallah ne.
Maryam dake zaune akan kujera tana kallonta, tace, "Wallahi Anty kin ji dadi abinki ke kam. Kinga azumi rabi amma har kin sauke Al-Qur'ani Mai Girma kin juya. Dama ni ce ke!"
Tayi dan murmushi, "to Maryam in banda abinki ai zage dantse ne yake kawo hakan. Ke ma idan kinyi kokari sosai, sai kiga kin ma zo kin wuceni."
Tayi yar dariya tace, "Anty kenan!"

Mama ta shigo dakin a daidai wannan lokacin. Tace, "yauwa Nadiya, ga abu can na ajiye miki a firjin zaki gani cikin gallons na ruwa, ki tabbata kullum kin sha kofi biyu safe da dare."

Ta yamutsa fuska jin hakan. Ita fa abubuwan da ake bata dinnan sun fara ci mata tuwo a kwarya. Mama da Amarya sun dage tun karfinsu gyarata suke so suyi, su basu san cewa shi gyaran sai ana dokin miji da aure ba sannan ake yin shi ba? Ko kuwa fada musu aka yi cewa zaman auren take muradin yi da mijin ne da zasu dameta da wannan gyare-gyaren? Idan kuma kace ba zaka sha ba Mama ta hau fada.

Yanzu ma Mama tana ganin yadda take tabe fuska da mele baki tace mata, "saura kuma in ga baki sha ba ko kuma ba kya sha kamar yadda nace kiga abinda zai faru!"

Ita sai abin ma yaso bata dariya. Ta girgiza kai kawai, Allah sarki Mama. Tana ta kokarin tayi mata abinda mahaifiyarta ma wadda ta haifeta ta kasa yi mata shi.
Tunda zancen auren nan ya motsa sau biyu ta kirata. Na farko shine lokacin data kira ta tayata murna dinnan har ta bita da fada da gori. Na biyun kuma sake kiranta tayi da gargadi da fadan ta fa kama kanta ta kuma mike tsaye tun karfinta. Tayi kokari ta tsaya tsayin daka domin ganin ta zama ta farko a wajen mijin da zata aura.
Ta koma lallashinta da tausarta, akan ta kwantar da hankalinta, ta dangwali arziki ta sha romonshi tunda har yazo har inda take ba tare data nemeshi ba.
Nadiya dai bin ta ta dinga yi da 'to' kawai har suka kammala wayar. Shikenan ta kashe bayan nan tana mai kara jaddada mata lallai fa ta nacewa Habib, kiran safe daban, na rana da dare daban. Haka kuma kada ta sanyaya wajen aika mishi da sakonni da kalamai na kauna. Abinda ya hadasu kenan. Babu zance ko tambayar ya tsarinta yake? Me take tanada ta kuma shiryawa rayuwar auren da take kokarin sanyawa kafa?

*

Ranar bayan an sha ruwa, Hajiya Ummah tana dakinta wanda aka tanadeshi musamman saboda shan iska. Waya suke yi da Madam wadda take fada mata irin nasarori da maganganu masu dadi da suke samu a wajen mutanen da take tunkara da zancen Habib.
Don a halin yanzu ma haka ta samu nasarar zama da Jagoran jam'iyyar da ita Hajiya Ummah take ganin da ita zasu yi tafiyar, ya kuma tabbatar mata da cewa lallai Habibun shi zasu tsayar a matsayin dan takara.

Ta kuma kara da shaida mata da cewa a yanzu haka, ta tashi mutane bila adadin, suna shiga kauyuka suna bada tallafi iri-iri, duk da sunan shi Habib din. Juma'ar da zata yi kyawu tun daga Laraba ake ganeta, tana kuma ganin cewa lallai sun gama samun nasara a wannan tafiya.

Hajiya Ummah tayi murmushi cike da jindadi, "shi yasa dama tun farko banyi kokonto akanki ba Zahra'u. Nasan lallai-lallai sai kin kai hakarmu ya cimma ruwa."

Madam ta saki wata yar dariya, "ai Ummah ba yabon kai ba, amma ni nasan duk wani buri da zan sanya a gaba, to hakika sai na cimma nasara a cikinshi. Don haka ki kwantar da hankalinki, in Allah Ya yarda nan da dan kankanin lokaci, Kaduna sai ta zama tamu. Idan kika rike hannuna kuwa, na miki alkawarin har Nigeria ma baki daya sai na sanya ta durkusa a gabanki!"

Murmushi take saki sosai, jin maganar da Madam din take yi. "Hakika da babu abinda zai kai hakan faranta min rai Zahra'u. Allah Yayi mana jagoranci dai."

Madam tace, "ameen." Kafin kuma ta dan dakata.
Sai kuma ta nisa, tace, "to Ummah ina zancenmu kuma ya kwana?"
Tace, "Zahra'u baki da matsala game da wannan ko kadan. Kamar yadda na fada miki tun ba yau ba, bana magana biyu. Idan nace zan yi, to zan yi din babu mai canza min shawara. Fili naki ne, babu kuma wanda zai hanaki shi da yardar Allah. Nan da dan kankanin lokaci za a damka miki takardunshi da komi a hannu!"

Madam tayi tsallen murna, "nagode sosai Ummah, Allah Ya kara Girma da daukaka. Ai ni tuni na gama hada komi ta bangarena, go ahead kawai nake jira daga gareku muje mu fara gini."
Murnar da take ciki ta hanata sauraren maganganun da Hajiya Ummah take mata. Itama data fahimci hakan sai kawai ta mata sallama ta kashe wayar.

Suna gama wayar Madam ta tashi ta hau tikar rawa a dakinta cikin murna da farinciki.
Kamun kafar data samu a wajen Hajiya Ummah yasa ta bi wasu shaguna dake kusa da filinta inda take so tayi gini, ta siya domin ta kara fadada wajen. Duk wani abu da zata yi, tuni ta riga ta gama tattarawa, an fitar mata da tsarin wajen, an tanadi kamfanonin da zasu kai mata kayan aiki da kuma wadanda zasu yi aikin. Kai tsaye rana daya sai aka je mata da labarin ai wannan waje data saya ba a wajen ainihin mai wajen bane, don haka zance ya tashi. Don kuwa mai waje yace ba zai sayar da waje ba. Aka mayar mata da kudinta.

Ta nuna musu zata iya kaisu kara akan wannan maganar tunda ta riga ta gama sayen waje, kuskuren data yi a yarjejeniyar sayen wajen bata sanya idan an yi abu kamar wannan ba zata iya shigar da kara ba. Saboda bata taba sanin irin haka din zai faru ba
Da taga dai babu Sarki sai Allah sai ta koma bin kafa wajen Hajiya Ummah. Wadda cikin dan kankanin lokaci ta samo mai wajen, Alhaji Tijjani, da kuma sanyawar bakinta ne yace zai sayar da wajen amma sai yayi shawara. A hakan ma kuma sai da Madam ta kara mishi da wani gida flat da take dashi a Kinkinau bayan ainihin kudin data sayi shagunan dasu.

An fi sati biyu da yin hakan har yau kuma babu wani cikakken bayani data ji daga garesu. Amma maganar da suka yi da Hajiya Ummah sai ta karfafa mata gwiwa sosai da sosai.
Ta ci wa wannan waje da zata bude buri fiye da tunanin mai tunani. Akwai kuma mutane da dama da suma suke jiran budewar wannan waje. Saboda bayan shaguna da wajen wasanni da zata bude, akwai wani bangare na daban da zasu bude wanda wannan waje, na musamman ne. Na manyan kusoshin Gwamnati ne da suka ci suka tada kai da nera. Ba zata bari wani abu yazo ya gittawa wannan buri nata data kwashe shekara da shekaru tana ayyanawa ba.

*

Ita kuwa Hajiya Ummah suna kashe waya, wata wayar ta dauko daga cikin drawer ta kunna. Kai tsaye ta shiga cikin jerin contacts dinta, ta dannawa wata lamba kira.

Tana shiga aka daga babu bata lokaci, Alhaji Tijjani yace, "barka da dare Hajjaju, da fatan kun sha ruwa lafiya?"
Tayi wani murmushi cike da ginshira, "lafiya lau Alhaji. Ya Iyali?"
Suka gama gaisawa dashi cikin girmamawa, kafin ta fara mishi zancen daya sanya ta kirashi.

Tace, "ina aka kwana game da zancen shagunan nan ne?"
Yayi wata irin dariya, "zance ai yana nan a yadda muka barshi ne, ko kin canza shawara ne?"
Tace, "ko kadan! Ina so to zuwa satin da zai kama ka kawo min takardu da komi da komi, ka kuma bari sai satin ya kama ayi cike-cike saboda kada kwanan wata ya saba!"
Yace, "na gane Hajiya. To za a yi kamar yadda kika ce."

Tayi dan murmushi a hankali, "yauwa nagode, a gaida yara."
Shima yace, "mu ne da godiya Hajiya!"

Ta kashe wayar ta mayar da ita inda take. A karkashin wayar ta zaro wasu takardu, ta zauna akan kujera tana dubasu daya bayan daya tana sakin murmushi a tausashe, ranta fal da farinciki kamar an mata wata babbar kyauta.
Ta gama karancesu tsaf kafin ta ajiyesu a gefe, wani murmushin ya sake subuce mata. Ta jinjina kai a hankali wani tunani yana darsuwa a cikin ranta.
'Lallai yaro bai san wuta ba sai ya takata!'


****

Vibrating din da wayarta take ta yi ne babu kakkautawa ya tasheta daga barcin da bata jima da farawa ba. Nan da nan taji kanta ya fara sarawa, wannan shine bugu na uku kenan. Kafin ta kai ga dagawa har ya katse.
Ta sake yada kanta akan bargo tana kokarin komawa barcin, ba a dauki wasu mintuna masu yawa ba aka sake kiranta. Wannan karon har sai data zabura, kafin ta warci wayar ta daga. Karfe goma sha biyu saura na dare a dinga yiwa mutum irin wannan kiran sai kace wani yaki! Ta daga wayar rai a bace.

"Wai waye ne haka don Allah?!" Saboda bata ma tsaya ta ba lambar wayar data gani ba wani dogon tunani ba ta daga kiran tunda babu suna.
Sai taji shiru ba a amsa ba. Ta duba wayar don dai ta tabbatar mai kiran yana kan layi, taga dai kiran yana kai amsawa ce ba ayi. Ga kuma dai alamun kara nan ta background tana ji, balle tace ko network ne ya hana.

Ta sake cewa, "hello... waye wai?!"
Wannan karon da taji shiru sai data saki tsaki, tace, "in an san ba za a yi magana ba menene na yiwa mutane waya da wannan daren in banda rainin wayau?"
Ta tafi zata kashe wayar tana mita, "... kawai an katsewa mutane barci saboda wulakanci..!"

Sai kuma ta jiyoshi yana magana. Yace, "ki godewa Allah ke kin ma samu kinyi barcin. Bayan ni gani anan kin hanani!"

Ta mayar da wayar kunne tana jin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login