Showing 126001 words to 129000 words out of 142169 words

Chapter 43 - Nadiya Book 1 Complete Hausa Novel

03 Feb 2025

1115

gagin barci, tace mata, "don Allah don Annabi Anty Shukurah ki kira min Mami ta zo, bayana zai cire!"
Tayi jifa da wayar tana sakin wani kakkarfan salati bayan da taji wani ciwon ya sake turnuketa.

Shukurah ta zabura ta tashi sakamakon jin wannan ihun da tayi, a ranta tace babu lafiya.
Ita kadai ce a sashen nata, don kuwa tun dawowarta har yau basu daidaita da shi ba, fushi yake yi sosai tun karfinshi. Itama kuma data gaji da ban hakurin sai ta koma ta zuba mishi idanu kawai, Allah Ya gani ai tayi iyaka bakin kokarinta, hakan kuma ba shi zai sa ta zubar da ajinta ba don tana so ya sauka daga dokin zuciya daya hau ba.

Ta dauki zane ta dora akan doguwar rigar barcinta ta fita da sauri taje ta bugawa su Ummah kofa.

Sai ga Mami da Ummah da Shukurah din bangarenta a sukwane. Da kyar ta iya tashi a duke taje ta bude musu kofar. Lokaci daya tayi wani wujiga-wujiga da ita. Mami tayi saurin tarota tana kamata, ta dubi Shukurah da jikinta ya dauki rawa gani?????
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
 n halin da Nadiya take ciki.
Tace mata, "kiyi sauri ki je ki bugawa Babangida kofa, ya dauko mota ya zo mu tafi asibiti."
Ta juya babu musu ta fita da sauri.

Nadiya ta kama hannun Mami ta rike kamar zata karyata, "ki taimaka min Mami, kuguna zai karye!"
Mami tace mata, "daure Nadiya, in shaa Allahu babu abinda zai sameki kinji?"
Tayi kokarin daga kai, amma abin ma sai ya gagara.
Tace mata, "wani abu zai fito..." ta tafi ta sake dukewa a wajen.

Mami ta zabura ta jata daki a sukwane, tana gyara mata kwanciya ta duba sai ga kan da. Ai nan da nan sai ta hau aiki.
Kafin dawowar Shukurah da Babangida daya rigata zuwa saboda saurin daya dauka har da hadawa da gudu-gudu, yar yarinyar ta fado tana ta tsala kukanta.
Anty ta dagata sama tana hailala, uwar sai ta koma kasan tiles ta yada kai tana salati tana karawa a matukar galabaice.

Ummah tana falo tana kaiwa-da-kawowa bakinta dauke da salati itama da sallallami, sai jin kukan da tayi. Shima da yaji kukan sai ya nemi danna kai cikin dakin a sukwane, tayi gaggawar dakatar dashi. Tace yayi hakuri ya bari a gama kintsasu tukun. Haka ya ja tunga shima ya tsaya anan, amma gabadaya ilahirin jikinshi bari yake yi. Kukan yarinyar jin shi yake har cikin kwanyarshi, so yake yi kawai ya sanyasu a cikin idanunshi.

Mami ta yankewa diyar cibi, ta nadeta a cikin shawl mai taushi bayan ta gogeta tas da man zaitun. Shiru-shiru uwa bata biyo baya ba.
Nadiyar na kwance ita dai gata nan, don kuwa maimakon ciwo yayi kasa ma sai wani sabo daya taso. Kafin ma Mami tace mata bari ta tadata tsaye ta jijjiga ko tayi kasa, sai ga sabuwar nakuda ta taso.
Mami tayi salati ta kara da hailala, sai ta sanya murya tana kiran Ummah. Dama ita kanta kara ce ta hanata shiga, sai kawai suka danna kai ciki ita da Babangida, Shukurah dai ta kasa shiga. In banda rawa babu abinda jikinta yake yi. Dama haka haihuwar take, take nemanta ruwa a jallo? Gaskiya da sake.

Suka shiga suka samu wani sunkucecen dan har ya ma fi yarinyar girma. Cikin ikon Allah kuma sai ga mabiya din ta fado.

Ummah ta karbi yarinyar ta rike, Babangidan ya rabe ta bayanta yana lekenta, kyakkyawar diya da ita Ma shaa Allah, babu abinda ta bari na uwarta, tana ta tsotson baki alamun tana neman tsotsa. Ummah na tsokanar 'daga gani wannan acici ce!' amma hankalinshi yana ga Nadiya da Mami da take kokarin gyara dayan yaron.
Ta gyareshi tsaf ta mika mishi shi, ya amsheshi cikin rawar hannu. Sai daya lalubi kujera ya zauna.

Mami ta taimakawa Nadiya ta tashi suka wuce bayi. Ta zaunar da ita akan stool yayinda take kokarin hada mata ruwan wanka saboda jiri.

Sai lokacin Shukurah ta shiga dakin. Sai ta lalubo kayan goge-goge ta shiga gyaran dakin.
Ita ta gyare wajen tsaf ta goge ko'ina, Mami kuma na can tana gasa Nadiya da tawul mai zafi. Don tace mata wanka zata mata mai suna wanka.

Kafin kiran Asubahi Maijegon da yan biyunta sun fito tsaf da su an gyaresu.
Ranar Ummah da kanta ta shiga kicin ta tukawa Nadiya tuwon dawa da miyar kuka, tana da kominta a ajiye dama, miyar ma dumamata kawai tayi tunda tana da ita a cikin firjin a ajiye. Ta zuba yajin daddawa wanda Nadiyar bata rabo dashi a cikin yan kwanakin da man shanu. Ta kuma hada mata kunun gyada mai kauri sosai.

Tana zaune a gefen gado Ummah ta shiga kwanon. Ji take kamar ta kwato shi saboda yunwar data ke ji.
Ta daure dai har ta kai mata kafin ta amsa. Ta gyara zama tana ci hannu baka hannu kwarya.
Shukurah da Mami na zaune suna kallonta cikin dan murmushi.
Ummah ta wuce sashenta don yin sallah, shima Habib din ya tafi masallaci.

Ta gama cin abincin tsaf, ta wanke hannunta, ta gyara kwanciya yaran na gefenta. Ta lumshe idanu sai barci mai dadi ya kwasheta.

Shukurah itama ta lallaba ta koma nata bangaren don ta huta kafin wayewar gari. Mami kuwa nan ta gyara zama akan sofa tayi kwanciyarta tana lazumi.

Zuwa wayewar gari su Mama sai jin labarin haihuwar kawai suka yi.

Duk da cewa Mami ita ta karbi haihuwar, amma ba bangarenta bane. Don haka sai da likita taje har gida ta dubata ita da jarirai, ta tabbatar musu da cewa lafiyarta lau babu wata matsala.
Mama taje gidan ita da su Maryam da Salame, suna falo tare da sauran yan'uwan su Mami da iyalan Uncle Hashim da suka je.

Ta fito daga wanka da misalin karfe sha daya na safe. Mami ta sake yiwa yaran wanka, yan barka sun gama ganinsu suna kwance cikin baby net dinsu suna barci.
Ta zura doguwar riga marar nauyi. Jin jikinta take yi shafal, kamar in aka hureta zata iya faduwa. Kai ita gabadayanta ma jinta take yi kamar wadda aka canza.

Ta fito ta sameshi zaune a gefen gadon ya kurawa yaran idanu yana kallo, Ammar a gefenshi yana tambayarshi, "Daddy wadannan duk kannena ne?" Yana dariya ya amsa mishi da, "ehh! Duk naka ne."

Ta karasa gefen gadon ta zauna itama tana kallonsu cike da murmushi, ya bita da kallo har ta zauna.

Kallonta yake yi da wani kallo da bai taba yi mata shi ba, da so da kauna da wata tsantsar girmamawa da mutuntawa irin wanda bai taba jinsu a ranshi ba akan kowa bayan Ummanshi.

Ya riga ya gama nuna mata irin godiyarshi tun da Asubahi din kafin ya tafi sallah, lokacin data fito wanka su kuma su Ummah sun fita don yin sahur, Mami na bayi tana wanke yaran, ya tattagota cikin jikinshi ya rungume yana rada mata irin farinciki da jindadin dake ranshi a lokacin, da dimbin godiya da alkawarurruka iri-iri na nuna mata so da kauna irin wadanda ba za su kwatantu ba ita da yayanta har su gama rayuwarsu a doron duniya. Amma ji yake kamar duk wadannan basu isa ba. Kamar bai ma nuna mata komi a cikin irin farincikin dake ranshi ba.

Ta maida hankalinta ga Ammar dake watsa mata nata kalar tambayoyin, ta biye mishi tana amsawa a nutse, wani tayi dariya. Yana saurarensu yana murmushi a tausashe shi kuma. A haka Shukurah ta shiga dakin ta samesu. Taji wani abu ya dan taba mata zuciya, ga su nan dai idan ka gansu ka ga the perfect family. Masu son junansu da kulawa da juna sosai, ita kuma tayi saken da bata kasance a cikinsu ba. Ta ji jikinta yayi sanyi kwarai, tana son ta gyara kuskurenta amma ta rasa ta yaya? Shi kuma Habibu ya ki bata damar yin hakan.

Ta kalli Nadiya a sanyaye tace mata, "Ummah ce tace a tambayeki idan da abinda kike son ci ki fada sai a dafa miki."
Tayi dan murmushi tana girgiza kai, "a'ah, ba ni da zabi gaskiya. Duk abinda aka dafa zan ci. Nagode."
Ta gyada kai, ta juya ta fita.
Shi kuma ya gyara zamanshi yana kallonta a nutse. Yace, "kinga har zuwa yanzu bamu yi maganar abinda kike ganin ya dace a sanyawa yaran nan ba."
Ta girgiza kai kanta a kasa, "ai ni duk abinda ka sanya musu ba ni da zabi. Allah Ya raya su."
Ya jinjina kai, "to ameen ameen Maman biyu!"
Ta jefa mishi hararar wasa, ya yi murmushi.

Yayi Bismillah ya dauki babbar yayi mata duk abinda Uba ya kamata yayi, kafin ya dauki namijin shima ya maimaita mishi.
Ya dora mata su duka akan cinyoyinta, "to ga Abdur-Rahman da Ummulkhairi!"
Ta kankamesu a jikinta tana dan murmushi, a ranta take addu'ar Allah Ya bata ikon kulawa da tarbiyantar dasu bisa tsari da tarbiya na addinin musulunci.

Ummah da taji anyi mata takwara kamar ta dauki Nadiya ta goya a bayanta saboda murna.

Wannan haihuwa taje musu da sauyi mai matukar dadi a rayuwarsu. Don kuwa a ranar da Hajiya Hadiza taje ganin yaran lokacin kwana hudu da yin haihuwar kenan, sai ga shi Ummah ce da kanta tayi mata jagora zuwa bangaren Nadiya. Ta dauki yaran ta mika mata su, ana ta raha da tsokanar juna da hira su biyun kamar wasu tsofin aminai. Haka da zata tafi ma sai da Ummah din ta rakata har waje, tana kuma kara maimaita mata lallai fa ta zo wajen rantsarwa. Ita kuma tana dariya take ce mata, "ai ko bata zo ba, ita Ummah din ta wadatar!"
Ummah itama tayi dariya sosai, tace, "ke dai Hajiya ki zo, saboda zuwan naki shi zai sa komi ya zamana a kammale kuma a tsare."
Sai suka yi sallama da ita akan haka din. Zuwan da tayi cikin dar da taraddadin me zata tarar? Sai ta koma gida cikin farinciki da sukunin zuciya kwarai da gaske.

Madam da ta tashi zuwa ganin jikoki kuwa abin ba a magana. Aka dinga sauke kayan jinjirai na sa wa da na wasa yadda kasan za a bude shago, don wasu kayanma sai sun girma sannan za su fara sanyasu. Yini guda tayi anan, kafin ta tafi da cewar ba zata dawo taron suna ba saboda washegari Abuja zata je.

Haka suka cigaba da yin jegonsu mai dadi suna karbar yan barka. Ranar suna aka yi hidima kwarai da gaske. Abinci dai a ranar an ciyar da masu azumi bila adadin, a masallatai da gidajen marayu. Kyautuka da sadaka iri-iri haka Habibu da Hajiya Ummah suka dinga yi.
Aka yi hidimar suna aka gama lafiya, aka tafi aka bar maijego da Abulkhairi da Khairiyya, -yadda suke kiran yaran- suna karbar jego mai suna jego a wajen Mami da Ummah. Ga Mama itama da take a gefe, hadin tukudi mai kyau ta bada Amarya ta yo mata, da tsumi jarka-jarka haka aka kai mata da sauran abubuwa.

Mami kuwa gyara take mata na ainihin Bare-bari din kamar wata sabuwar amarya. Don haka kafin zagayowar ranar arba'in dinsu, ita da yaran sun yi wani irin kubul-kubul dasu yadda kasan rainon yis. Duk inda ta baza a gidannan kamshi kawai yake tashi, jikin nan ya kara budewa ma shaa Allah komi ya zauna daram.
Shukurah dai ta lallaba a wannan dan zaman sun daidaita da Ubangidan, wai masu iya magana suka ce a rashin uwa akan yi uwar daki. Kuma in dama ta ki sai a koma hagu. Amma fa duk da haka, idan yaga gilmawar Nadiya a gidan nan sai ya dinga binta da kallo yana hadiyar yawu kamar wani tsohon maye. Don kuwa Nadiya din ce tayi wani irin canzawa ta ban mamaki.


51.



Gab da sallah sai ga Safiya ta je, hutun karshen semester suka samu. Don lokacin da aka yi haihuwar suna tsaka da jarabawa. Nadiya ta ji dadin zuwanta sosai da sosai, musamman da tun bayan auren nata babu wata maganar kirki data kara hadasu da ita. Ita dai bata taba neman Nadiya ba, ita kuma idan ta nemeta din bata samu. Sai ta hakura da neman nata.

A dan zaman da tayi da Nadiya sai take bata hakuri akan abinda ya faru kafin aurenta, ta fada mata cewa kunyar abinda tayi ne a lokacin ya hanata kiran Nadiya kwata-kwata, saboda bata san me zata ce mata ba. Ita kuwa Nadiya tace mata ita dama can bata taba riketa a cikin ranta ba, kuma in dai akan wannan zancen ne, to don Allah ta ma daina bata hakuri.

A wannan lokaci suka zauna suka yi hira irin ta yan'uwantaka a karo na farko a rayuwarsu. Nadiya ta fahimci ashe kallon da take yiwa Safiya a da ba haka bane, kwarai akwai sangarta da rashin sanin girman na gaba a tattare da ita wanda hakan ya biyo bayan rashin tsawatarwa ne daga Madam. Amma kuma tana da saukin kai da wayon zama da mutane. Don haka a dan wannan zaman da suka yi, Nadiya tayi kokarin nuna mata sakacin tarbiyantar da ita da Madam tayi, da kuma kokarin gyara mata a duk inda taga ta kuskure.
Da yake tace tana nan har a rantsar da Habib kafin ta wuce Maiduguri, sai kawai aka gyara mata daki anan wajen Nadiya ta zauna.

Zaman nata ya yiwa Nadiya dadi sosai, don kuwa duk da cewa ga Ummah da Mami suna tsaye a kanta babu gajiyawa, amma akwai wani abun da dole sai shakikinka zai yi maka shi ko kuma ya sani.


*****

Aka yi sallah lami-lafiya lau, sati ya zagayo aka yi bikin rantsar da su. Ranar da za ayi rantsuwar suka yi ankon wani dandatsetsen swiss lace ita da Shukurah din, daga Nadiya din har Babangida basu san da shi ba, don kawai ita Shukurah tace ya bata kudin kayan fitar ranar rantsuwa, ya dauka ya bata babu musu. Itama Nadiya sai ya dauki adadin abinda ya ba Shukurah ya bata, yace ta sayi abinda zata dinka din. Da ce mishi tayi ma ya bari, tunda ita dai kayan lefenta ma bata gama sanya ko rabi ba, ga na fitar suna ma bata sanya wasu ba. Tace mishi a ciki ma ba zata rasa na sanyawa ba, sai yace to ta rike kudin shi dai ya fita hakkinta.

To kuma sai ga kayan a dinkensu inji Shukurah, ta musu anko. Duk da cewa zaman nasu har zuwa lokacin kadaran-kadahan ne, in ka gansu ba zaka ce sunyi irin wannan kusancin na a zo a gani ba, amma kuma suna zaune lafiya. Sannan babu jan magana da jan fada, akwai kuma girmama juna cikin zaman nasu yanzu. Musamman bayan haihuwar Nadiya din, Shukurah tana kokarin leka Nadiya din a duk safiya bayan da Ummah ta hanata fitowa, a cewarta tayi zamanta a bangarenta ta huta. Abinci ma sai dai a dafa a kai mata ko kuma ita ta dafa. To Shukurah din kan shiga wajenta su gaisa, watarana ma har ta dauki yaran ta musu wasa ko ta tafi bangarenta ko na Hajiya Ummah da su. Aka ce wai mai da wawa, kusan da wannan zan iya cewa ta shawo kan Babangida din. Gashi a yanzu shi kanshi Ammar din ya sake da ita.

Haka suka yi shigar wannan leshi ruwan sararin samaniya da adon kananun fulawoyi masu kalar giwaiduwar kwai da kuma brown. Gyale da takalma kadai suka bambanta su, Nadiya ta sanya gyale brown, da takalmi da jaka ta LV suma brown ne. Shukurah kuma sai ta sanya ruwan Gwaiduwar kwan.
Suka tsaya a bayan maigidansu lokacin da ake rantsar dashi, su Khairiyya suna hannun su Mami da ke zaune a can kasan step suna kallo, aka yi handing over da komi, yan jarida da masu video suna aikin dauka.

Daga nan kai tsaye gidan Gwamnati aka wuce da su, inda suka hada yar kwarya-kwaryar liyafa ga abokansu na kusa da kuma yan'uwa da abokan arziki. Aka ci aka sha mai kyau, aka basu souvenirs din jakunkuna madaidaita masu dauke da hoton Habibu da mataimakinshi, da lemuka da snacks a ciki da memo da biro, kyauta daga Madam.

Duk suna zaune akan kujeru da aka zagaye wajen da su, tattausan kidan wakar 'Mad Over You' ta Runtown take tashi a wajen. Mami ta tashi ta wuce filin rawar a hankali ta fara takawa ita kadai, sai mutane suka fara dan murmushi da yar dariya ana kallonta. Zuwa can kuma sai Madam ta bi bayanta, ta fara manna mata sabin yan dari biyu a goshi suna dariya. A hankali wajen sai ya cike da yan rawa, aka fara liki da casu kamar ba gobe.
Shukurah itama dai ta mike daga baya ita da abokanta biyu, take tambayar Nadiya din ba zata shiga bane? Tace mata inaa, su je dai suyi tayi. Don haka ta tashi ta barta ita da Aramide da Anty Lima da itama taje wajen taron.

Suna ta hirarsu ta abokan da suka jima basu hadu ba, yan rawar suka fara dawowa suna zaunawa su ma. Sai ga shi an bar Safiya ita kadai a filin rawa.
Anty Lima tace, "kai, Allah Ya shirya mana Sofia, wai dama yarinyar nan har yanzu bata daina wannan shirmen ba?!"
Nadiya ta kalleta kasa-kasa, "kaji fa dan wuta yi da konanne, ke baki yin rawar ne a wajen biki? Naga dai daga ke har ita din za ni ce ta tarda muje mu?"
Ta kyalkyale da dariya kuwa, tace, "ke ki kyaleta tayi kinji? Lokacine. Mu ba gashi mun girma mun daina ba?"
Tace, "babu wani girma wallahi, shiriya dai!"

Suna wannan tattaunawar sai ga Fu'ad ya shiga filin rawar ya fara yi mata mannin yan dari biyar shi kuma. Nan fa kallo ya koma sama, don kuwa shima rawar ya biyeta suka fara anan. Nadiya sai baki kawai ta sake tana kallonsu kamar wasu mahaukata. Musamman da taga wai iyaye da yan uwa na musu shewa da tafi. Ta girgiza kai cike da takaicin wannan al'amari, a ranta take cewa ko yaushe Madam da Safiya din zasu gane Annabi ya faku?

Sai ga Safiya din tazo ta zauna dabas akan kujera tana goge zufa, ta dauki gorar ruwa mai sanyi ta kafa a baki ta shanye. Ana canza waka wai Fu'ad ya hau daga mata hannu taje, zata mike Nadiya ta zabga mata harara, tace, "na rantse da Allah kina komawa wajen rawar wannan sai na tadeki kin fadi akan wannan dan iskan 6 inches din takalmin naki!"

Ta kuwa koma ta zauna amma tana kyalkyala mata dariya, "wallahi ke dai Adda

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login