Showing 12001 words to 15000 words out of 142169 words

Chapter 5 - Nadiya Book 1 Complete Hausa Novel

03 Feb 2025

435

Indomie, sai ya zamana Nadiya din tana kula musu da wajen? Aka yi haka kuwa, cikin dan kankanin lokaci an samu waje an gyara shi, aka bude wajen inda kwastomomi suka fara tururuwa. Jajircewar Nadiya da sadaukarwarta ya kai wajen matsayin da yake dashi a halin yanzu, don kuwa ita kanta Aramide din ta san da hakan.
Daga farko ita Aramide din cewa tayi mijinta ne yayi mata kyautar kudade masu yawa shi yasa ta yanke shawarar ta bude wajen. Sai da tafiya tayi tafiya daga baya dai Nadiya ta fahimci kwata-kwata zancen ba haka yake ba. Iyayen Aramide din su suka bata kudin wanda ya kasance na sadakinta ne da kuma wasu kudade da iyayen suka saba ba 'ya'yansu mata idan sun yi aure domin su ja jari.

Ita dai Nadiya hakan bai dameta ba, tunda ko babu komi tana jifar tsuntsu biyu ne da dutse daya.
Na farko tana gudanar da abinda tafi so a duniya, wato girke-girke, na biyu kuma ana biyanta da kudaden dake daukar nauyin dawainiyarta. Don haka bata da wata damuwa sam.

Ta muskuta ta gyara zama tana fuskantar Ara dake shan shayi da cupcakes a lokacin. Tace, "me zai hana ku zauna ke da shi kuyi magana ta fahimta? Idan yaso sai ku ajiye ground rules (dokoki) da watakila zasu iya taimaka muku wajen rage yawan dukan. Saboda gaskiya baya da dadi ko kadan."

Ta girgiza kai, "kina tunanin bamu yi hakan bane tun farko? Lokacin farko dana tunkareshi ma da wannan maganar ai wani dukan ma na janyowa kaina. Wallahi wani mari daya falla min sai da naga taurari suna min yawo a idanuna!"
Nadiya ta jinjina kai cike da jimami, tace, "gaskiya dai yakamata ku canza taku, saboda hakan ba zai haifar muku da da mai ido ba. Nan gaba idan kuka fara tara iyali fa kuma mai zai faru? It's either ya dinga hadawa har diyan yana jibga, ko kuma su yaran suna ganin abinda ke faruwa su fara raina shi da tuhumarshi. Kinga hakan duk ba abu bane mai dadi gaskiya."

Tace, "nima hakan nayi tunani shi yasa kawai zan wuce wajen iyayenshi in fada musu abinda yake faruwa, watakila su zasu iya bullowa lamarin da mafita. Don kuwa kin san idan naje na fadawa iyayena abinda ke faruwa ba zasu taba tsayawa su kwatar min yancina ba kila ma sai dai su hada da min Allah kara. Don tun lokacin da yaje neman aurena sai da suka bani shawarar kada in aureshi don sun riga da sun yi min miji, amma na kafe akan sai shi. Yafi dai kawai inje in samu iyayen nashi."
Nan ma Nadiya dariya ta so ta saki jin yadda kalamanta suka saba da cewar data yi iyayenta suka matsa akan sai ta aureshi.

Iyayen AbdulGaniyyu mutanen Benue ne. Shi ya tashine a hannun kawunshi dake zaune a Kaduna wanda Allah Ya yiwa rasuwa jim kadan bayan AbdulGaniyyu din ya tafi jami'a. Shi kuma sai yaci gaba da zama anan har Allah Ya taimakeshi ya samu aiki.

Nadiya tace, "to Allah dai Ya. kyauta! Yaushe zaki tafi?"
Tace, "ai a yau ba sai gobe ba zan dauki hanya in Allah Ya yarda. Ni zan koma gidan wannan mutumin ya sabautani? So nake karshen satin nan a rufe shagon ma, ku tafi hutu ko da na sati biyu ne tunda dama bamu yi na shekara ba har yanzu. Nima hutun zan nema, saboda so nake idan naje in dan jima a can, wallahi garin ya fita a kaina gabadaya!"

Nadiya ta dan jinjina kai, "to shikenan, sai ayi hakan babu damuwa. Muma mun samu mu huta kafin ki dawo din. Dama na tara barci da gajiya sosai kwanakinnan."

Fita tayi suka cigaba da gudanar da ayyukansu kamar kullum. Bayan abubuwan sun lafa, suka fara shirye-shiryen rufe shagon da shawarwarin yadda hakan zai kasance. Sun saba yin hakan dama a duk karshen shekara, to kuma wannan shekarar data wuce ayyukan suka cunkushe musu basu yi hutun ba gashi har sun ci kwata. Nan da wata daya cikakke ma Azumi suke tunkara.

Saboda shirye-shiryen ranar bata koma gida da wuri ba sai wajen karfe tara na dare. Tayi sallama tana jan kafa saboda tsananin gajiya. Abbansu yana tsakar gida, matan sun zagayeshi zaune akan tabarma. Ko kwanukan abinci da aka kai mishi ba a kwashe ba. Ana ta hirar da bata da kai balle kafafu. Da alama ma su biyu kadai ke hirar, don shi hankalinshi yana kan wayarshi yana ta latsawa. A ranta tace 'har an gama fadan da fushin sake auren kenan?'

Ta durkusa a gefensu tana mishi sannu da gida, ya daga kai yana kallonta, "ke kuma fa daga ina da wannan daren? Wai ba na hanaku kai dare a waje ba?"

Tace, "wallahi ayyuka ne suka tsaremu a shagon saboda muna shirye-shiryen tafiya hutun shekara ne."
Yace, "to, to, na gane. Ai nayi zaton yawon banza kika tsaya. Ni dai kullum ina fada muku, a dinga kiyaye yin dare a waje. Saboda mutane basu cika ganin mutuncin mace mai yawace-yawace da kai dare a waje ba."
Ta gyada kai, "hakane Abba. In Allah Ya yarda zan kiyaye!"
Ta tashi ta tafi daki.

Ta tarar su Maryam har sun mata shimfida. Don haka tana gama shirin barci kwanciyarta tayi.

Ranar Litinin bata tashi da wuri ba, da tayi sallar Asubahi komawa tayi tayi kwanciyarta. Cikin ikon Allah kuma hayaniyar yara bata dameta ba don sai wajen karfe tara da rabi ta tashi. Maryam zata raka wajen registration din Jamb dalilin da yasa ta tashi da wuri kenan. Saboda daren jiya bata kwanta da wuri ba. Ta rasa dalilin da yasa yan kwanakin barci yake gagararta sosai musamman na dare.

Maryam ta shiga dakin dai-dai lokacin da take kokarin nade kayan shimfidar tata. Tace, "yauwa Adda, kin tashi? Dama ke kadai nake jira saboda tun dazu na gama shirina."
Ta gyada kai, "ok! Bani mintuna talatin, yanzunnan zan shirya. Abba yana gida ko ya fita?"
Tace, "yana nan. Naji yana cewa Lantana yau sai bayan Azzuhur ma zai fita saboda yana da meeting da ko wani Sanata ne ko me?!"
Nadiya ta tabe baki. Ta hade kan kayan ta mikasu daki kafin ta shiga wanka.

Cikin mintuna talatin din da tace kuwa ta gama shirinta tsaf. Riga da siket ta sanya na wani leshi ruwan madara, bata daura dankwali ba sai gashin kanta data kame a cikin band babba, ta dora bakar hijabi wadda ta tsaya mata a gwiwa. Kamar kullum ba wata kwalliya tayi ba ta a zo a gani, amma tayi wani irin kyau mai daukar hankali.

Suka fita tsakar gida inda ta samu Mama tana gyaran masara saboda ranar ita take da girki. Su Lantana kuwa da alama suna dakin Abba don bata ga giccinsu ba.
Suka mata sallama akan zasu tafi. Dubu biyu ta kunto a habar zaninta ta ba Nadiya wai su kara kudin mota, tace, "a'ah wallahi Mama, ki bar kudinki saboda da isassun kudi a hannuna. Ki ajiye kayanki kinyi wata hidimar dasu."
Mama tace, "to Allah Yayi albarka Nadiya, Allah Ya amfana!"
Tayi murmushi tace, "ameen ameen Mama! Mu ai addu'ar muke so!"

Sun samu Abba zaune akan kujera da takardar kilishi a gabanshi yana ta tauna, su kuma iyalan nashi suna gefe sun hade kawuna suna kus-kus. Salame sai kaiwa takardar naman hari take da idanu tana hadiyar yawu amma ya ki bata fuskar tagawa ma balle ta rokeshi.
Nadiya ta danne dariyar da take ciyota, da alama yau Abban cikin yan rowar yake.

Ta durkusa ta gaisheshi ya amsa mata sama-sama. Da yake itama ranar izgilanci take ji, sai ta juya gefen su Salame su ma ta gaishesu, sai dai daga jin gaisuwar bata kai ciki ba, suma haka suka amsa mata kadaran-kadahan babu yabo babu fallasa. Ko a kwalar rigarta ita kam.
Ta juya tana kallon Abban nasu, tace, "Abba zamu je ne wajen registration din jamb ta Maryam."

Jin haka sai yayi kicin-kicin da rai ya fara hura hanci kamar wanda aka aikawa da sakon mutuwa, "to! Sai kun dawo ko?"
Ta wani langwabar da kai gefe guda, "wai dama cewa nayi ka bamu kudin registration din ko? Dubu shida ne da dari uku, ga kuma kudin abin hawa..."

Kafin ma ta karasa ya katseta, "... ke dakata min don Allah da wannan lissafe-lissafen naki! Kudin kin bani ajiyarsu ne? Ko kuwa ni din asusunki ne da zaki dirar min da zancen kudi kai tsaye in dauka in bada! Ce miki aka yi sharo kudin nake yi a kasa ne ko kuwa shukasu nake yi?!"

Tace, "amma fa Abba tun wancan satin fa na fada maka haka kuma kai kace Allah Ya kaimu!"
Jin haka sai ta kara tunzurashi ma, ya fara sakar mata lissafin kudaden daya kashe a wannan satin wadanda rabinsu duk wajen amarya suka nufa, sai kuwa kudin fadar kishiya daya ba matan wanda dukansu dubu goma-goma ce ya basu.
Ita dai tayi kasa da kai tana bashi hakuri. Daga karshe dai ya tashi ya shiga daki, ya dawo ya jefa mata yan dubu-dubu guda uku suka zube akan cinyarta, "gasu nan kuyi maneji da wannan. Idan kuma bai zasu isheku ba to ku bani kayana, tunda ba neman kai nake dasu ba!"

Ta tsincesu tas ta zuba a jaka tana mishi godiya. Ta yunkura zata tashi kuma sai ta koma ta zauna, ya daga kai yana kallonta warily don yasan maganar bata gama mutuwa ba.
Murmushi ta dan yi, tace, "Abba nace wai ka dan bani kilishin mana in kore mugun yawu!"
Tsabar rasa abinda zai ce mata da yayi a lokacin, takardar naman ya cukuikuye gabadaya ya mika mata, duk da cewa saura yajin kilishin kawai da dan guntun nama, haka ta amsa tana zabga mishi godiya, ta fita tana dariyar mugunta a ciki ita kadai.

Maryam ta girgiza kai tana kallonta, "wallahi wani lokacin ba ki da dama ko kadan Adda! Kin rabashi da nama kuma kin rabashi da yan canjinshi!"
Tayi dariya tace, "ke raba mugu da makami ibada fa! Idan ba ta haka ba ta yaya ma wai ake cin kudin Abba ne?!"
A haka kuma sai ta jinjina kai, "hakane kuma!"

Kai tsaye KASU suka wuce. Bayan an gama duk cike-ciken da za ayi, aka basu slip dinsu. Daga nan sai suka gangara unguwar Rimi gidan Yayansu Yaya Hannafi, mahaifiyarshi bata gidan kuma shima kusan sa'an su Anty Jamila ne.
Matarshi tana da kirki Anty Aisha, yana da rufin asirinshi dai-dai gwargwardo. Yana aikine da wani kamfanin kera robobi da reshensu yake nan Kadunar.
Anan suka yini a gidan. Da yake Nadiya ta iya jera lallen salatif, ta jerawa Anty Aisha shi kafa da hannu, Maryam kuma ta tayata tsifar kai. Da suka tashi tafiya ma da yamma ita ta hana tace dole su jira Magriba Nadiya ta sha ruwa tunda Azumi take yi, watakila kuma kafin nan Yayan nasu har ya dawo su samu su gaisa.

Don haka suka shiga kicin har ita suka hada abincin dare. Ta samu kunun tsamiya ta dama, don ya zame mata ka'ida, matukar tana Azumi dolene ta dama kunu ko ta hada shayi.
Suna cikin shan ruwan kuma sai ga Yaya Hannafi din ya dawo, yaransu uku, kuma dukansu sun tasa. Yanmata biyu suna boarding school sai karamin ne Ammar yake nan.

Ya tsaya suka gaisa suka mishi sannu da zuwa. Hira suka dan yi dashi sama-sama kafin ya tashi ya shige dakinshi. Dama can dai shi ba mai yawan jan yan'uwanshi a jiki bane, tunda zumuncinma da ba don jajircewar matarshi ba to da ba lallai ayi shi ba.
Da zasu tafi ya basu dubu biyu su yi kudin mota suka mishi godiya sosai kafin suka dauki hanya.

Suna gab da karasawa gida taji wayarta tana vibrating a jaka. Duk a tsammaninta Mama ce take nemansu shi yasa bata daga wayar ba.
Suna komawa gida kuma sallah suka yi, suka zauna cin abincin da Mama ta ajiye musu suna mata hirar Anty Aisha.

Sai da tayi shirin kwanciya can wajen karfe goma da rabi sannan ta tuna wayarta dake cikin jaka. Ta bude ta ciro wayar tana so ta hau whatsapp ta tabo Aramide taji ya ake ciki. Sai lokacin taga missed call din da aka bar mata.
Jikinta ne ya dauki wani irin sanyi ganin sunan mai kiran. Madam Zarah!

Mahaifiya ce, amma tafi jinta a matsayin wata dangi ta nesa, wadda babu sanayya da kusanci a tsakaninsu ko na azo a gani.
Kiran wayarta ba wai yana nufin tana so taji muryarta ko ta tanbayi ya take bane, tana da tabbacin ko dai wani abu ne ya taso a cikin dangi, ko kuma tana bukatar tayi mata wani abu ne. Tana da tabbacin hakan.

Canki-canka take yi, akan ta mayar mata da kiran ko kuwa. Laifine dai ta riga da tayi shi. Don kuwa idan akwai abin da Madam Zarah ta tsana, bai wuce ta kira wayar mutum ya ki dagawa ba.
A matsayinta na mace mai influence a cikin Kasarnan, gani take yi ba karamin nasara bane a gareka idan ta dauki wayarta ta kira ka ba, a ganinta ka ciri tuta sosai. Bata duba da cewa 'ya'ya da iyaye da yan'uwa bai kamata su shiga cikin wannan tsarin ba.

Ganin tunane-tunane ba inda zai kaita yasa ta mayar mata da kiran. Amma har ta katse ba a daga ba. Dama tayi tunanin haka.
Ta daga kafada ta gyara kwanciyarta abinta ta fara addu'ar barci.

Washegari kuma tunda safe sai ga kiran nata. Ta gyara zama akan abin sallar da take kai zaune ta daga baki dauke da sallama, kafin gaisuwa ta biyo baya, "Assalamu alaikum. Mommy barka da safiya, kun tashi lafiya?"
Daga can bangaren aka amsa mata a gaggauce, babu ya kike babu ya kwana biyu, kawai kai tsaye zuwa dalilin da yasa ta kirata.

Tace, "Nadiya kin tuna Hadiza yar wajen Kawu Kabir ko?"
Tace, "ehh, na tuna ta."
Duk kuwa da cewa ba tunata tayi din ba. Dangin Mamanta ba wani sani ta musu na azo a gani ba sai na kusa dasu sosai.

Tace, "satin wannan da zai kama za a fara bikinta a can Maiduguri. Don haka ki shirya kije sai mu hadu da ke a can. Zan turo miki Invitation card, at least kije a day before a fara events saboda a fara dake. Kin gane?"
Tace, "ehh... Amma Mommy....!"

"...Ba ki da kudin zuwa ne?" Ta katseta da wannan tambayar.
Tace, "a'ah, dama..."
Nan ma bata bari ta karasa maganar ba tace, "yauwa, to sai na turo miki da katin. Sofia tace a gaida ki!"
Ta katse wayar ba tare data bari Nadiya ta kara cewa wani abu ba. Tayi zaune da waya a hannunta tana kallo kamar wata sakara.
Shikenan duk wani tsari da tayi na hutun da zata yi an wargaza mata shi cikin dan kankanin lokaci.

Ita fa ba zuwa bikin bane yafi damunta, shiga cikin dangin Madam Zarah ne bata so. Ba a cikinsu ta tashi ba, shi yasa bata saba dasu ba. Akwai wadanda suke magana dasu suna gaisawa ta waya, amma suma yan'uwan Madam dinne na kurkusa wadanda yawanci daga 'ya'yan yayunta, sai ko na kannen mahaifanta dai. Amma sauran ba saninsu tayi ba, suma kuma basu santa ba.
Tana so ta sansu din, amma ta yaya? Da yawa wasu daga cikinsu kallon hadarin kaji suke mata idan taje wajensu, ta rasa dalili. Ko gani suke yi bara da roko zata je wajensu?

Dangin Mahaifiyarta mutanene da suka hada masu arziki da kuma masu rufin asiri. Suna zaunene a garin Maiduguri.
Mahaifiyarta rabi shuwa ce rabi bare-bari, iyayenta suna da rufin asirinsu dai-dai wa dai-da.
A cikin yan dakinsu akwai masu kudi sosai, su dai sune suka kasance masu rufin asiri. Watakila ko shine dalilin da yasa ma iyayenta suka yarda ta auri Babansu Nadiya din. Ko kuwa kaddara ce da tsananin rabo? Allah kadai Ya sani.
Tana da masaniyar a danginsu idan kaga wani ya auri bare wanda ba Kanuri ko Shuwa ba, to kudi yake dasu ba kanana ba. Saboda su sun fi yin auren gida ya-su ya-su kawai. Idan kuma sun fita to dukiya suka gani.

Shi yasa fa ita sam tsarin mutanen bai mata ba ko kadan. Shi yasa bata cika shige musu ba take baya-baya dasu.

Ta san dai cewa shi Alhaji Kabir mai aurar da diyar tashi, kawun mahaifiyarta ne. Dan wa da dan kani suke da kakarta, Dada Iyani, wadda itace Mahaifiyar Madam Zarah da sauran yayunta biyu, Hauwau da kuma Yasir. Wadanda dukansu suna zaunene a can Maiduguri din banda Madam Zarah, wadda take zaune a Jos.

Ajiyar numfashi ta ajiye mai nauyi, rufe wayar tayi tare da tashi ta nade abin sallar. Ta tashi taje ta gaishe da Abbansu, ta koma daki suka gaisa da Mama. Kafin ta fita tsakar gida ta fara shara.
Mama ta fito ita kuma ta shiga kicin ta fara kokarin hada abin kari.

Kosai suka yi shirin yi da koko. Da yake waken an gyara shi tun jiya, sai aka ba almajiri ya tafi markade.
Kafin ya dawo Nadiya ta gama hada kan tsakar gidan, Mama kuma har ta dama koko. Ta shiga kicin din ta zauna tana tayata suyar kosan suna hiransu kamar dai wasu manyan abokai.

Yaran gidan da suka fara fitowa don shirin tafiya makaranta, nan da nan suka kara wartsakewa. Murna kamar su yi me, don kuwa su ranar take sallah a wajensu.

Kowa idan ya zo zai amshi abin karinshi, sai Mama ta kulla mishi wani a cikin leda wanda zai tafi makaranta dashi. Abu ne da bai cika faruwa a gidan ba sai a dai-daikun ranaku wadanda suka zama na girkinta kawai. Don shi dai Abbansu baya bada kudin kashewa ko cin abinci a makaranta. Wanda Mahaifiyarshi taga zata iya sai ta bashi, amma ba dai shi ba. Su kuwa da mugunta ta cikawa ciki da shegen mako, babu mai iya wannan aikin. Shi yasa ma yaran duk basu cika mayar da hankali kan zuwa makarantar ba.
Lokaci zuwa lokaci dai Nadiya ta kan basu na kashewa a hanya, amma itama ba kullum ba.

Su Salame suka fito daga dakinsu suka je kofar dakin Abba suka coge suna ta harare-harare da yada maganganu. Nadiya dai kai kawai take girgizawa cikin tu'ajjibin wadannan mutane. Daga tashi tun da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login