Showing 99001 words to 102000 words out of 167047 words
Chapter 34 - Mar’adam’s Book 2 Hausa Novel Complete.txt
an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 19
Sosai mami ta dinga rarrashin maryam tana masu addua “allah ya daidaita tsakaninku ,Allah ya saka tausayinki acikin zuciyar adamcy ,allah ya kawo zaman lafiya a tsakaninku har qarshen rayuwarku “ahankali maryam Ke amsawa da “Ameen mami ,sai abu na gaba maryam na fahimci kina sakaci da addua ,Ina son kinsan wani abu ba’a nasara sai an rike Allah,idan ka rike Allah,Allah ta’ala zai taimakeka ki jajurce da adduoi maryam “ki rage wasu abubuwa ki maida lamarinki zuwa ga Allah maryam ta gyad’a mata kai alamun taji ,tana nan kwance ajikin mami har ta fara gyangyad’i alamun bacci .ahankali mami ta d’an buga bayanta tana cewa “maryam kwanta kiyi bacci da sannu allah zai kawo mana saukin wannan tashin hankali sannan ya kawo fahimtar juna a tsakaninki da mijinki .“maryam ta tashi daga jikin mami tana shafa idanunta sannan ta zame ta kwanta zuciyarta cike da soyayyar mijinta mami ta mike itama ta samu gurin nan kusa da maryam ta kwanta sai dai ita sam bacci yaki d’aukarta, kwakwaluwarta ne ya shiga cajin tunani
dan dole tasan abun yi tun kafin adamcy ya kashe maryam da bakincikinsa dan zuwa yanzu hakurinta ya fara qarewa akanshi .”
Juyi kawai mami take akan katifa kafin ahankali ta taashi ta sauko daga saman katifa ta tsaya gaban maryam tana kallon fuskarta bacci take, sai dai kana kallonta zaka san a matuqar wahale take baccin dan kana kallon yadda take sauke numfashi da ajiyar zuciya da karfi .”d’auke kwayar idanunta mami tayi ta fara zagaye d’akin kafin ta fara zance zuci ita kad’ai “dan dole zulai kiyi wani abu akan zaman ya’yanki “ to mai zanyi ?mai zanyi ? ta tambayi kanta har sau biyu tana cure hannuwanta waje d’aya “Kiyi qoqari adamcy ya kusanci maryam ko Allah zai basu rabo wata killa sanadiyyar hakan ya sauko ya sausauta mata ya rungume aurensu. “tabbas haka zakiyi zuciyarta ta bata wannan shawarar “to ta yaya zan masa magana ya fahimci abinda nake nufi ?”ta sake jefawa kwakwaluwarta tambaya shiru tayi yayinda ta koma ta kwanta akan katifa tana sauke numfashi tana mai sake had’e hannuwanta guri d’aya kafin ahankali ta soma sakin wani irin murmushi sakamakon abinda zuciyarta ta shirya mata wanda zai kawo mata saukin al’amuran ta, alokaci d’aya ta sauke wani naunayen ajiyar zuciya “dole dai kina bukatar shawarar shahida kafin ki aikata komai .”
Washegari da misalin karfe tara na safe maryam tana zaune akan kujerar sofa tana danna waya yayinda mami ke zaune akan salayya tana lazimi ATA ya shigo bakinsa d’auke da sallama sallamarsa kawai maryam ta amsa batare da ta kallesa ba ta cigaba da daddanna wayarta shima ko kallonta bai yi ba ya cigaba da tsayuwa mami ta d’an kallesa yana sanye da jallabiya yayi mata kyau sosai sai dai bata jin dadin ganin yadda ko yaushe fuskar nan tashi take a had’e’ ,sannan bata jin dadin ganin shi da maryam haka zaman su sam babu sha’awa kana ganin yanayinsu kasan gabad’aya zukatansu basa cikin walwala da jin dadi most especially adamcy wanda zaka fahimci baya son ko bisa kuskure ya kasance a duk inda maryam take .yayinda ita kuma tafi qaunar su kasance tare akoda yaushe ya rungumeta babu kyama ,mami na kallonsa ya juya cikin takun isa ya fita daga d’akin ganin tana lazimi ,bayansa mrym tabi da kallo har ya fice gabad’aya tasa hannu d’aya ta dafe goshinta tana jin wani tuttukin bakinciki tana jin zafi da ciwon abinda yake mata na kyarma da rashin son kallonta inda take ,amman ita ta rasa dalilin da yasa zuciyarta kullum take sake macewa akanshi ,a kullum zata d’aura kwayar idanunta akanshi to wallahi son shi da qaunarsa ne Ke sake huda zuciyarta da gangar jikinta” zata so ta mallakesa kamar yadda mahaifiyarta take buri amman hakan taki samuwa kullum babu abinda take hangowa attare dashi sai zallar qiyayyarta sam komai nata baya burgesa ita kuwa kwarjininsa kesa bata iya d’aukarwa kanta mataki ,bata iya tunkurarsa da komai tana matuqar jin tsoronsa aranta “da sanyi jiki mami ta qaraso inda take zaune ta kai hannunta ta dafata, ta d’ago tana duban mami da idanunta dake cike da ruwan hawaye mami tasa gefen hijab dinta ta goge mata hawayen da suka zubo mata batare da saninta ba wani wahallen ajiyar zuciya ta sauke tana kawar da fuskarta gefe“
“maryam !”
Mami ta kira sunanta ahankali maryam ta waigo inda mami take ta sake zuba mata idanunta tana kallonta fuskarta da tsananin damuwa ahankali ta sauke idanunta “ki daina damun kanki akan adamcy idan ba haka ba zaki rasa lafiyarki idan hakan kuma ta kasance babu ruwansa hasalima bazai ta’ba zama damuwarsa ba sai dai ta zama damuwarmu “kiyi hakuri ki dinga kawar da damuwar nan aranki sannan ki dinga kaiwa allah kukanki ,nasani maryam kina hakurin zama da adamcy ne saboda Kina matuqar ganin girmana da mutuntani da kuma qaunar da Kike masa nima kuma haka ne acikin zuciyata maryam ina qaunarki ina qaunar ku kasance a inuwa d’aya dashi .”numfashi ta sauke da karfi tana kallon mami “eh shine ma dalilin da yasa bakya son na rabaku maryam .
Maryam ta tsurawa mami idanunta “ko karya ne bakya sonsa ?zazzafan numfashi maryam ta sauke ta kasa cewa komai dan tasan gsky mami ta fad’a “kina dai danne sonshi ne saboda rashin qaunar da yake nuna miki amman ni naji ajikina kina qaunar adamcy ,maryam taji dadin yadda mami ta fahimci hakan sai dai kuma zuciyarta tayi rauni wasu sabbin hawaye suka zubo mata mami ta sake share mata “kuka bayayi miki kyau maryam hakan ya sake karya wa maryam gwaiwa ta fashe da wani kuka sosai .“wallahi mami ban san lokacin da son shi ya shigeni ba “nice silarsa maryam kuma nayi danasani had’aku aure ,mami ta fad’a da matsanancin tausayinta ,duk yadda mami take jin qaunar adamcy ji take tafita qaunarsa maryam ta tsananta kuka tana tuna tun lokacin data fara jin qaunar yaya Adam din acikin ranta rungumeta mami tayi tsam tana rarrashi alokacin wayar maryam ta soma ringing mami ta zare jikinta tana kallon maryam itama d’agowa tayi ta kalli mami sannan ta kalli screen din wayarta bata dauka ba ta cigaba da goge hawayenta yayinda kiran ya cigaba da shigowa still maryam bata d’aga ba .”
mami ta d’an yi gyaran murya “wake kiranki ne tun d’azu ?ummah ce !ta bata amsa atakaice idanunta na cigaba da zubar da hawaye “me yasa bazaki d’auka ba kika sani ko kiran mai mahimanci ne ?shiru maryam tayi ta kasa cewa komai dan tasan kiran me take mata, ita kuma ta gaji da abubuwan mahaifi yarta ,kullum abu d’aya kuma babu wani biyan buqata “ki d’auki kiranta kar rashin d’aukar kiran yasa hankalinta ya tashi tayi tunanin ko wani abu ne“.ahankali maryam ta gyad’a mata kai tana “cewa mami bari naje na dafa miki ruwan zafi “to shikenan maryam amman ki hada min da abinci “bamu da komai fa mami ,karki damu ki dafa min abinda kuke dashi . Mrym ta mike tsaye ta fito tana qoqarin d’aukar kiran mahaifiyarta daya sake shigowa ta sauko kunnenta manne da waya “umma dan allah ki daina kirana na tura miki sako mami tana gidan nan bana son taji komai “ amman me yasa zaki fad’i haka ummah?” kema Kinsan mami tana matuqar qaunata “a’a umma nifa gsky na gaji kawai abarshi na hakura bazan iya ba dan duk abinda zaa zuba cikin abinci bazai ci ba tunda baya cin girkina ,shiru maryam tayi tana jin yadda mahaifiyarta ta balbaleta da bala’i ta inda take shiga bata nan take fita ba.”
“kiyi hakuri ummah ba wai bana ganin qoqarinki bane saboda mami idan ta fahimci akwai abinda muke shiryawa d’anta zata ji babu dadi to shikenan gara ma wannan zamu iya sake gwadawa ko za’a samu ya kwanta akai ,to shikenan amman dan allah ummah karki kirani kiyi chart dina muyi komai ta chart ta qarasa mgnr tare da shiga kitchen ta soma qoqarin d’aurawa mami abinda zatayi breakfast dashi cikin kankani lokaci ta gama dafa ruwan zafi ta zuba cikin flaks sannan ta dafa shinkafa da miya ta fito tana qoqarin qarasawa dining mami ta sauko tana cewa “sannu da aiki maryam ?murmushi ta saki tana cewa “kai mami wani aiki kuma byn shinkafa da miya ce kawai na dafa miki. murmushi mami tayi tana cewa “kawo min nan diyata ta qarasa inda kujeru suke ta zauna maryam ta biyo bayanta ta ajiye kular abinci akan center table maryam tace “nasan idan kowa yaci abincina yace babu dadi mamina bazatace babu dadi ba ?”ina sam bazan fad’a haka ba zuba min na matsu banji dandanon abincin my daughter ba “abincin dai mami sai dai kiyi hakuri babu komai aciki ta qarasa mgnr muryata a sanyaye “karki damu maryam fara had’a min shayi cike da kulawa maryam take hidima da mami yayinda mami ke nuna mata farincikinki a zahiri amman a bad’ani bakinciki ne cunkushe acikin zuciyarta suna zaune ata ya fito yana taku a natse akan step sanye da kananan kaya jikinsa sai fitar da sihirtaccen kamshin turarensa yake ,ya qaraso parlour’n qasa hannuwansa duka zube cikin aljihun wondonsa tun daga nesa ya hango mami zaune tana breakfast da ruwan tea zalla babu wani abun hadi danginsu soyayyen Kwai da bread ko arish da sauransu abinda yasan ba d’abiarta bace, abun yayi matuqar bashi mamaki dan haka kai tsaye store ya shiga adaidai lokacin maryam ta mike ta nufi hanyar sama d’auko chazar wayarta .”
yana shiga dube dube ya fara bai ga komai ba ya fito ya shig kitchen duk sai daya duba cabinet din kitchen din nan ma bai ga wani abun kirki da zaa had’awa mutun breakfast mai kyau dashi ba dan haka jiki a sanyaye ya fito yana kwallawa maryam kira yayinda mami tana nan zaune tana kallon tv tana cigaba da kora ruwan tea da sauri maryam ta sauko tana dubansa gabanta na wani irin bugawa da karfi muryarta a raunane tace “ yaya gani ?“meye haka ?me ya faru kuma ?itama tayi karfin halin tambayarsa har ya d’aga hannunsa ko me ya tuna ya sauke ya dafe goshinsa a fusace ya cire hannunsa ya d’an saci kallon mami ita kuma ta zuba masa idanu tana ji da ganin abinda zai faru maryam taja baya tana jin yadda zuciyarta ke rawa “meye wancan agaban mami ?ya sake wulla mata tmbya tayi shiru tana dubansa a tsorace ya zira hannunsa daya cikin aljihunsa yana sake yin magana a tsawace “meye haka ina magana kina jina ?abinci ne !”what ?!ya furta a tsawace .”
ta sake ja baya kar ya wanka mata mari dan a yanayin da yake kallonta babu sausauci “amman zaki iya bawa mahaifiyarki irin wannan breakfast din ? gabanta yayi wani irin mugun fad’uwa ya tsura mata ido hakan ya bala’i bata tsoro gbdy ya sake canza mata ya fara taku zuwa inda take tsaye tana yar kyarma tana baya baya yana biyota har sai data kurewa bango “wallahi ba da gangan nayi ba babu komai a store ne komai ya qare iya abinda muke dashi na bawa mami .” afusace ya d’aga hannu zai wanka mata mari cikin wani irin masifaffen tsawa yaji sautin muryar mami “wallahi idan ka ta’bata ban yafe maka ba .” cak ya tsaida hannunsa tamkar an dasashi zuciyarsa na tafasa cike da zafin zuciya ya sauke hannusa yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa sannan ya juyo ya soma taku cike da ‘bacin rai ya qaraso ya zauna kusa daita kamar mai neman gafara ya fara kame kame “umm umm ummm nace ba “kace me ?”shiru yayi yana kallon mami yayinda maryam tayi sauri ta haye sama tana wai wayensu “ina jinka adamcy ?”Kiyi hakuri sweetheart banji dadin yadda naga kina breakfast haka ba “ bana zama a gida bansan babu komai a gidan nan ba sannan wannan yarinyar bata fad’a min babu komai ba ya qarashe maganar kamar zai yi kuka.”
mami ta kallesa sosai ta gano halin damuwar daya shiga adalilin breakfast dinta, daman kuma tayi hakan ne dan ya gani numfashi ya sauke yana sosa keyarsa yana cigaba da kallon mami ahankali mami ta tabe baki “to ka bata damar da zata fuskanceka bare ta fad’a maka babu komai acikin gidan nan “?amman !”sai kuma yayi shiru yana runtse idanunshi .”amman me adamcy ?kai kanka kasan baka da wata kalmar da zaka fad’a min na yarda a matsayinka na magidanci baka bawa matarka wannan damar ba sam matarka bata da cikakken iko acikin gidan nan yadda kake nuna baka qaunar jamaa da yanuwanka haka kake nunawa matar aurenka ,kai kanka kawai kasani baka damu da damuwar kowa ba dan haka karka rainawa kanka hankali ka nemi daurawa yar mutane laifi “ta qarashe maganar cikin fad’a saboda halin adamcy baqaramin damunta yake ba ,shi mutun ne wanda babu ruwansa da damuwar jama’a sai dai kanshi da aikinsa ya kamo hannun mami ya soma rarrashinta “sweetheart Kiyi hakuri kema Kinsan yanayin aiki ne sai ahankali ,ni kaina bana samun time din kaina kamar yadda kika sani amman at least data fad’a min zan sa a kawo komai “ta bishi da wani mummunar kallo “wai yaushe ka bawa maryam wannan damar yarinyar nan haka take rayuwa cikin qunci acikin gidan nan ga rashin so ga yunwa dame zataji ?”allah sarki maryam baiwar allah allah dai ya qara miki hakuri amman na cuceki na hadaki da damuwa ,na hadaki da mutun mara kirki ,na hadaki da mutun mara zumunci wanda ko yan’uwansa baya so bare wata aba maryam wallahi adamcy baka da tausayi da amana nayi danasanin hada auren nan allah dai ya gyara maka wannan bakar zuciyar taka .”
Kuka yaci karfin mami .”
jikin ATA yayi mugun sanyi babu abinda ya tsana kamar hawayen mahaifiyarsa da bai da kamarta jin kukanta yake har cikin zuciyarsa ya sake matsowa kusa daita yasa kanshi akan cinyarta yana jin yadda zuciyarsa yake tafasa yana jin kukanta yana ganin laifinsa amman yafi ganin laifinta domin kuwa itace sanadin da yasa ya kasa sauke nauyin da allah ya daura masa sannan ya kasa mata biyayya ta matsawa rayuwarsa dayawa akan maryam ,shi kanshi baya jin dadin abubuwan dake faruwa ,jin kukanta yake aransa yana jin kamar yayi kuka .“
ahankali yayi amfani da karfin zuciya irin tashi ya fara bata hakuri da rarrashinta “sweetheart Kiyi hakuri nasan bana miki yadda kike so Kiyi min addua wallahi a shirye nake da na canza in zama mai faranta miki ,kuma wallahi ina son yan’uwana sweetheart wani dadi ne ya ziyarci zuciyar mami dan abinda tafi bukata kenan ta dade tana adduar ya canja .”
ya qara gyara kanshi akan cinyar sweetheart dinsa “sweetheart ki yafe min ko zan samu sausaucin abinda nake ji araina kada zuciyata ta buga sweetheart ,damuwa tayi min yawa wallahi ni kadai nasan halin da zuciyata take ciki a haka kamar lafiyayyen mutun ne amman sam ba haka bane mutun ne mai dauke da mummunar ciwo a qirjinsa da zaki barni haka babu nauyin kowa akaina zanfi ji dadin rayuwata sai dai zuciyata taji da damuwa daya amman yanzu damuwa tayi min yawa na rasa ya zanyi da rayuwata wallahi zan gwamaci mutuwa sweetheart akan rayuwar da nake .”mami tayi saurin saka hannu ta rufe masa bakinsa bata son taji batun zai mutu idan ya mutu tayi yaya ai ita babban burinta ta mutu ta barshi a duniya, tana shafa kanshi tana jin sonshi har acikin bargon zuciyarta “ki yafe min sweetheart “adamcy baka min laifin komai ba ban ta’ba rikeka araina ba kullum addau nake maka d’ana sai dai abu daya nake só kamo. ina son ka sausautawa maryam ka zauan da mace mafi cancanta ,maryam ta cancanta kowani nmj idan ya sameta zaka ji dadin rayuwa daita mace ta gari ya dago kanshi yana kallonta ya saka hannu shi ya rike kunnuwansa bazan iya ba sweetheart “but I promise you in sha allahu zan kawo miki matar da zan aura in sha allahu zan faranta miki zakiyi farinciki da zabina amman batun wannan yarinyar fa gsky sweetheart sai dai kiyi hakuri .he ending the talk with a smile .”
mami tayi shiru tana dubansa sam adamcy baya ganin girmanta baya tausaya mata duk son da yake ikirarin yana mata abaki ne bai kai har zuciyarsa ba .”shiru kawai tayi tana jin babu dadi ko kadan acikin ranta tana son zubar da hawaye amman data tuna irin matsifar da hakan zai jefa rayuwarsa da alamuransa sai ta fasa sai dai yadda zuciyarta take tukuki ta tabbatarwa kanta tana cikin tsannain damuwa akanshi, idan batayi gaugauwan kawar da hakan aranta ba shima wani bala’i ne ga rayuwarsa runtse ido tayi zuciyarta na shirya mata yadda zata kawo qarshen komai “Sweetheart me kike tunani haka ?”muryar ATA ne ta katse mata tunani , harara ta maka masa tana cewa “ina ruwanka da abinda nake tunani ?wayarsa ya ciro ya kira daya daga cikin yaransa ya bashi umarnin a shigo da komai na kayan abinci enough .”
Cikin kankanin lokaci aka dinga shigo da kayan abinci sai daaka cika store tab da kayan abinci babu abinda babu na amafani haka ma fridge tun a ranar komai ya sauyawa maryam sunci mai kyau ita da mami su sha mai kyua, sai abinda suka ga dama suka girka kuma basuyi wa ATA tayi ba shima bai damu ba