Showing 162001 words to 165000 words out of 167047 words
Chapter 55 - Mar’adam’s Book 2 Hausa Novel Complete.txt
son ya zaga ya fake da zagin d’anka “numfashi mami ta sauke tana cewa “karki damu shahida idan da sabo na rigada na saba da halinsa kuma hausawa sukance dan kuka mai jawa uwarsa jifa duk wa ja min koda zagina yayi ?ni dai fatana allah ya canza adamcy allah kuma ya tsaresa daga sharrinsu Allah yasa kafin mutuwa naga canzawarsu aunty shahida ta share hawayen daya zubo mata “menene kuma abun zubar da hawaye ?wallahi mami kalmar tayi min zafi bansan me yasa yanzu baba qarami yake nunawa adamcy kiyayya haka ba ,ji nayi kamar na tanka masa “gara da baki tanka masa ba ai sai ya tabbatar da rashin tarbiyar da yace allah dai ya sawaka kawai zamu ce ahankali suka dinga tautaunawa wanda kusan duk akan adamcy ne .”
*******
On 28 cikin sauri sauri maryama tayi abinda zatayi ta shirya cikin riga da siket blue da ratsin yellow ta dauko after dres ta daura akan kaya tayi rolling din kanta da mayafin after dress din ta rufe koina ajikinta ga kyau ga qarancin shekaru wanda yasa tayi looking very attractive ta fito zuwa parlour’n sai dai duk ranta babu dadi , da granny ta soma cin karo ta durkusa har kasa ta gaisheta “barka da safiya granny “barka maryama fatan kin tashi ?”Lfy ina umma? bata rufe baki ba umma ta fito daga dakinta ta qaraso ta tsaya kusa da maryama ta dafa kafadanta “har kin shirya masoyiya ? maryama tayi murmushin jin dadin sunan da umma ta kirata dashi tace “na shirya umma barka da safiya “kin tashi lafiya ?ta gyada mata kai tana cewa “ alhamdulillah gamu zamu yakin karshe grany ta matso sosai kusa daita “maryama ki bi komai a hankali ki kiyaye banda shiga abinda bai shafeki ba allah ya baki saa a dukkanin abinda kike sa gaba .murmushi maryama tayi tana “cewa Ameen angama kakata ta kaina zan kula da duk abinda kikace, ta juya bangaren umma tana kallonta “sai ku tayani da addua, in sha allahu zakiyi nasara amman kamar kinso kiyi late ?” Aa banyi latti ba zamuyi daidai sai na dawo umma “ai baki karya ba ta fad’a tare da mikewa ta janyo hannuta bata tsaya koina daita ba sai inda ta ajiye mata plet din abincin data zuba mata ta zaunar daita ta soma bata abinci a baki tana ci tana duba mata lokaci har ta koshi ta sha ruwa ta mike tsaye tare da jiran adduarta “fatan alkhairi diyata karki sawa zuciyar karaya ki karfafa zuciyarki kisa aranki matsalarki tazo karshe da yarda allah ki kula da kanki please “in sha allahu ta kalli inda Aunty Hasana take zaune akan kujera wacce ko kallon inda take batayi ba a tun sanda ta fito daga daki sai man karanta wani littafi take .”
jiki a sanyaye kamar kartace mata komai tunda tasan ba fatan alkhairi take mata ba amman dai ta barwa allah komai kuma ko babu komai kanwar mahaifinta ce sai datai adduar samun nasara akanta sannan ta bude bakinta da kyar tace “aunty hasana ni zan tafi interview” fuskatar ta babu yabo babu fallasa ta dago tana cewa “in sha allahu bazaki samu aikin nan ba yadda kika fita da murna in sha allahu da bakinciki zaki dawo gidan nan kinyi sanadin kashe mana d’a amman Ke har kin manta kin fara neman aikinyi jikin maryama yayi sanyi hawaye ya cika kwarnin idanunta “hasana bai kamata ki dingawa diyar danuwanki haka ba “to mama ni meye nayi mata bayan gsky na fad’a aiki ne a gabanta ko zama tayi tunanin abinda Ke damun rayuwarta muddin kina son zaman lafiyarki damu ki kiyaye takurawa yarinyar nan kinji na fad’a miki “ai daman nasan duk kun tsananeni akan wannan yar iskar yarinya irin tsiya irin jaraba kawai masu mugun jini taja tsaki ta dauke kanta akansu .”
Shiru maryama tayi tsaye ta kasa kwakkwaran motsi tana duban Aunty hasana cike da sarewa gbdy sai taji zuwa interview din ma ya fita ranta domin tana ji ajiknta kotaje bazatai nasara ba granny ta janyota zuwa jikinta “maryam ki maida hankali lokaci na tafiya fa karki damu da maganar wannan mayar in sha allahu zaki samu aiki “okay granny na gode sosai “abinda granny ta fada in sha allahu haka ne zai kasance karki manta cewar hasana ba itace takawoki duniya ba dan haka babu abinda bakinta zai miki inji cewar umma idanun maryama suka kawo kwalla muryarta a raunane tace “ni dai ku bata hakuri idan wani laifi nayi mata ta yafe min dan banason tana fadar mummunar kalamai akaina umma idan kin sani bayan babu ran iyayenka addaur yanuwansu tamkar adduar iyayenka ne “.
“haka ne amman ita mummunar adduarta bazatai tasiri akanki ba saboda baki mata laifin komai ba ai baza ta’bawa yiwa diyar cikinta mummunar addua ba “Aunty ki daina hada diyar cikina da wannan yarinyar ita din ba diyata bace ya kamata ki fahimta “allah dai ya ganar dake gsky dan ni banga amfani kiyayyar nan ba , idan uwarta tana da laifi dan ta auri danuwanki ai danuwanki ma yana da laifi daya nace sai daya aureta .”inji cewar granny “Ni wallahi umma da nayi zamana dan ina ji ….”bazaki zauna ba kuma babu abinda kike ji sai alkhairi maza kama hanya ki wuce fatan alkhairi allah yayi miki albarka “Ameen ta juya cike da sanyin jiki take daga kafafunta .”
Ganin haka yasa umma ta mike ta biyota tana cewa “ki shiga wajen Auty ku gaisa kafin ki wuce amman kiyi sauri karki yi latti kinji masoyiya maryama tace” to umma na wuce sai na dawo “to sai kin dawo allah ya tsare “fatan alkhairi maryama allah ya bada saa ta fito bangaren mahaifiyarta ta shiga bayan ta gaisheta tayi mata sallama itama fatan alkhairi tayi mata “aunty ina after dad?yana ciki yana bacci “okay ki fad’a masa na tafi interview ku tayani da adduar samun nasara tana qoqarin fita daga part din aunty ta kira sunanta “princess ! ta tsaya cak tare da juyowa ta fuskanci mahaifiyarta tana mai gyara zaman Jakarta a kafadarta“kinyi breakfast kuwa da kike kokarin fita ta qaraso gabanta hannunta rike da cup din tea mai kauri tare da bread bata tsaya jiran mai za tace ba ta kai cup din tea bakinta “bude bakinki ki sha ko kadan ne bana son kina fita batare da kin sakawa cikinki komai ba .”ahankali ta bude bakinta tace “naci abinci daga hannun umma kuma na koshi amman bari naci daga hannunki ta soma kurban tea ba wani mai yawa ta sha ba tace “ya isa haka na gode sosai ta rungumeta tare da yi mata sallama tana fitowa daga part dinsu ta rufe fuskarta da qara min nikaf .”
********
Babban hall ne aka tanadar masu ,suna zaune gefenta yusura ce itama sanye cikin shiga ta kamala kowanne ka gani acikin hall din rike yake da takardunsa na makaranta wasu acikin jaka, wasu rungume dashi ,tun daga Kan matakin diploma har zuwa kan digree na biyu .bayan wani lokaci aka fara kiran suna daya bayan daya har aka kawo Kan maryama da addua ta shiga inda zaa mata interview tana shiga ta yaye nikaf din fuskarta kasancewar taga mace ce ,sectary ta sakar mata murmushin dan ita tun ranar data soma ganinta taji ta kwanta mata arai yarinyar tana da natsuwa gashi tana shiga ta mutunci ko yanzu duk masu neman aiki babu wanda yayi shigar mutunci kamarta “ga guri ki zauna “na gode” maryama ta fad’a a natse tare da zama tana ma kanta addaur samun nasara .” bayan awa daya aka gama daita tare da daukarta aiki “maryama hussein idan allah ya kaimu gobe zaki fara zuwa aiki amman wannna abun da kike rufe fuskarki dashi ba lalla sir ATA ya yarda dashi ba .”
shiru maryama tayi tana jin da kamar wuya ta iya fita babu shi a fuskarta domin ta rigada ta saba tsawon shekaru haka ta taso idan ma bata saka shi ba bata jin dadi” muryarta can kasa tace “zan dai gwada zuwa dashi idan ya bukaci na daina zuwa dashi zan kiyaye na gode sosai.” ta fad’a tana mikewa ta bar office din a wajen ma’akatan ta jira yusira itama cikin ikon allah ta samu suka nufo gida cike da murna yanayinta ya tabbatar ma yan gidansu ta samu aiki ta rungume umma cike da farinciki.”
“alhamdulillah umma mun dace “kai masha allah masoyiya gsky naji dadi sosai da kyakkyawan albishiri da kika min ,zuwanki aiki zai rage miki damuwa sosai allah yasa ki fara a saa” maryama ta qarasa ta rungume granny” na gode matuka da adduarku da bani kwarin gwiwa ta shafa kanta “babu komai maryama gabadaya parlour’n umma ya cika da murna aunty da habib ma murna fal anan yusura ta wuni currr suna murna sai yamma tayi masu sallama ta koma gida da zumar sai sun had’u gobe .”
Washegari da misalin karfe bakwai daidai a AGC company tayi masu babu ‘bata lokaci aka nuna kowace office din da zata dinga aiki tare da basu file file da zasu fara aiki akansa basu kasance guri daya da yusura ba ,tare da sultana suka kasance a office daya sosai maryama ta dukufa aka aikinta tana Kan aiki sectary ta shigo ta mika ma maryama wasu file “please ki cike yanzu ki kawo min office dina “okay ma”! ta fad’a tare da amsa ta ajiye aikin da take ta fara wanda aka bata .”sultana kam ko ta Kan aiki batabi ba wayarta ma take opereting can ta soma magana da alamun vioce note take yi “kinsan wani abu qawata gani zaune babu abinda nake takardun banza daakawo gasu agabana haka zasu karaci yininsu bazan cike komai ba kuma bazan zana komai ba dan ba abinda ya kawoni kenan ba.” ta tura tai shiru tana murmushi can sautinta ya sake karade office din “wa wannan mutumin ai bai yi ba wani office aka kaini dabam ba idan yake ba amman duk bata ‘baci ba komai zai tafinmin yadda nake so ai bari Ke dai qawa mutumin nan ya hadu fiyye da tunaninki sai ma kin gansa a zahiri sai kin kusan sumewa .”ta qarasa mgnr tana kam kamkame jikinta .”alamun tana jin shauki akansa .”
Maryama na ciki aiki sai ga subai ta shigo office din hannunta rike da wasu file yayinda wuyata ke makale da ID card mai dauke da cikakken sunanta da tambarin Z&A da sauri ta qaraso gurinta tana dafa kafadanta“wa nike gani haka kamar maryama ?maryama ta dago a natse tana dubanta “a’a subaia wallahi nice ya kike ya kwana biyu ? lafiya kar dai kina cikin sababbin ma’aikatan daaka diba?maryama tai murmushi tana gyada mata kai alamun “eh !”kai gaskiya naji dadi dana ganki a matsayin maaikaciya anan .” Maryama ta maida hankalinta ta cigaba da abinda take ai nasan daman allah bazai barki haka ba kullum ina sakaki cikin adduarta na gode sosai da taimakonki gareni “kai karki damu ai yiwa kai ne fatan alkhairi “thank you dear .”har subaia ta juya maryam ta mike tana kiran sunanta
ta tsaya “Yauwa subai’a ina ne office din madam some?muje na nuna miki suka fita tare tana sauke nikaf dinta suna qarasa fitowa ta nuna mata da dan yatsanta”gashi can sai mu sake haduwa nima wani aiki ne ya kawoni sukai sallama ta karya kwana “.
ita kuma maryama tayi kokari shiga office din data nuna mata ta tura kofar glass sannan ta sanya jikinta ciki adaidai lokacin da idanun ATA ke Kan cctv “wacece wannan data shigo yanzu “?ya tmby yana dauke idanunshi ya maida kan fara takardar dake gabansa ya juyo mata compute daake ganin shiga da fitar mutane .”
Some ta sauke idanunta akan computer maryama ta gani muryar some na rawa tace “maryama hussein!”
“wace ce haka ?”sabuwar maakaciya ce “baki fada mata baa zuwa mana da irin wannna shigar bane ? “na fada mata sir “!yayi shiru yana maimaita sunan acikin zuciyarsa maryama hussein sannan yana sake kallon cctv tabbas itace yarinyar “ wannna ba yarinyar da muka bukaci zanenta bane watanin baya ba ?“muryarta na rawa tace “ita itace sir .” what ! ya fad’a tsawace “nan take jikin sectary ya dauki rawa “dan allah kayi hakuri sir “ itace yarinyar da akayi interview akan kasuwanci daita , yarinyar da take da kwarewa sosai akan zane itace yarinyar da kace anemo ta watanin baya “ kenan the same person ce “? ya fad’a yana ciza lips dinsa da karfi “yes sir duk mutun daya ce itace take zane but sir yarinyar tasan kan aikinta duk a rud’e take masa wannan bayanin.”
shiru yayi yana jin wani irin mummunar faduwar gaba from no where sai dai bai dago ba ya cigaba da typing din da yake cikin zafin rai .”kana kallon yadda yake daddana keyboard din system din kasan baya cikin natsuwarsa “bana ce kar a Kuskura a dauketa aiki ba ?kuma kikayi son ranki har ma kina min dogon bayani akan yadda ta wulakantamu”sir !sir !!kayi hakuri nayi ta kokarin na fada maka saboda gudun faruwar haka amman kaki bani dama “.
“me kke nufi ni ban fad’a miki ba karta samu aiki har karshen rayuwarta ba bama a wannan company din ba har other companies?Ke ma kinsani bana bawa kowani irin mutun second chance dan haka kije ki sallameta bana son ganinta acikin company din nan “oya go out ! ya nuna mata hanyar fita jikinta na rawa ta fito .”tana fita ya zabura ya mike tsaye ya daura hannunsa daya akan hannun kujerar daya tashi gabansa na wani irin mummunar faduwa zuciyarsa na tuttukin zafin kamar ya dakatar da some amman bakinsa ya kasa furta komai .
ya bar wajen ya koma jikin window yana kallon haraban maakatan yaso kwarai ya samu nasara sake ganawa daita amman ina bazai iya daukar iskancinta ba har kamar shi ya sauke girmansa ya kirata amman taki daukar wayarsa har ma da kashe masa waya ga mummunar sako data fadawa james bayan haka ya nemi ganawa daita a ogun shima batayi masa abinda ya bukata ba sai ma qara masa damuwa datayi jin abun yayi kamar alokacin ya faru babu wani sausauci da zai mata wanda ya wuce ya koreta daga karkashinsa .”
da sauri sectary ta fito zuwa office dinsu tana shiga ta isketa zaune da farar takadar agabanta tana zana mutun sanye da suit da wondo har ma da takalmi acikin mintuna da basu wuce ashirin ba ta tsaya tana sauke numfashi, ganin ita kadai ce a office ta qaraso sosai ta tsaya akanta tana tunanin yadda zatai mata magana dan sam babu dadi ka samu aiki ranar da ka fara zuwa ace an koreka tsayuwarta batasa maryama ta dago ba dan bata ma ji alamun shigowarta ba kokari take ta kammala aikin da ta fara dashi amatsayin aikin farko .”muryar some a sanyaye ta kira sunanta “maryam hussein ! maryama ta dago da sauri tana cewa “yes ma ,akwai wani aikin da zan miki “?”No you’re fared cak numfashin maryama ya nemi ya dauke sakamakon jin mummunar labarin datayi nan take dakin ya dinga jujjuya mata wani irin tashi hankali tashig mara misali kafin a hankali ta janyo numfashinta dake kokarin barinta ta dawo dashi gangar jikinta ta fuskanci sectary sosai hankalinta na qara tashi “wannan hukuncin MR ATA né “.
“Hukuncin Mr ATA”. ?ta furta da karfi tô kaifin me nayi masa nida yau na fara aiki anan ?tayi mgnr Kmr zatai kuka cike da tausayawa sectary ta dafata sai dai ta kasa cewa komai “ko zan iya magana dashi dan haka kawai bazaa dakatar da mutun batare da wani laifi ba ?tayi mgnr a fusace .”no no !! ba sai kingansa ba ,dan ni kaina a halin yanzu ina cikin matsala dan allah ki bar nan yanzu kafin ya shigo “ba maganar na bar nan bane ko kina cikin matsala ina son nasan dalilin da zai sa akoreni tunda nasan sai da dalili akewa mutun irin wannan korar lallai sai nasan meye matsalar kafin na bar maakatan nan ,”ki natsu please maryam sir bazai ganki ba a yanzu .”
“Kema kiyi hakuri kiyi min iso Ke bari ma naje da kaina .”fuuuuu ta nufi kofar fita da sauri some ta biyo bayanta tana kiran sunanta “maryama ki tsaya karki sake yin wani kuskure ta riko hannunta cikin zafin rai “bazai yuwa ma ki shiga inda yake ba wannan ya sabawa doka .”
“Doka wani doka kuma ?wallahi kusani kun tafka babban kuskure na korata ,bari ma kiji bani nayi applied din aiki a kamfaninku ba yi min akayi dan haka yanzu ma ban damu ba kije ki fad’a masa ko bansamu aikin a anan ba zan samu aiki adalilin baiwar da allah yayi min kuma bare ma zan samu aiki da takarduna” dan allah kiyi hakuri nima ba laifina bane .”shiru maryama tayi kafin ahankali tace”madam some ko zansa exactly laifin me kika min da kike bani hakuri ?ai nice yafi dacewa na baku hakuri ku da ake nema a wurinku ,amman ku kuwa wani irin tsarin ne da maakatarku hk ?a dauki mutun aiki rana daya da fara aikinsa a koresa ?kiyi hakuri maryam ki wuce kawai karma kisa rai ko a wani guri ma zaki samu aiki domin sir nada karfin iko a koina “to ni laifin me nayi masa haka ?ki tmbyr min shi laifi me nayi masa haka ?tai mgnr tana kuka “ai