Showing 132001 words to 135000 words out of 167047 words

Chapter 45 - Mar’adam’s Book 2 Hausa Novel Complete.txt

bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan  09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.


             Page 25

         Tafiyar awanni hud'u ta kawosu maryama ma'aikatan ATA dake jahar ogun state yaya sadam yayi  parking din motarsa acikin haraban ma'aikatan sannan suka fito atare yana gyara zaman farar shaddar jikinsa yayinda maryama ke qoqarin neman layin mr  segun kira d'aya mr segun ya d'aga sukai magana na second biyu sannan ta fuskanci yaya sadam fuskarta kwance da annurin  farinciki mara iyaka tace "kad'an yi hakuri yanzu za'a yi mana iso zuwa ciki " yaya sadam ya gyad'a mata kai kawai alamun babu komai yana sakar mata tsadaddaden  murmushinsa ,suka  tsaya suna magana kasa kasa kafin ayi masu iso .wani matashin saurayi ne ya sauko  sanye da bakaken kaya ya shigar dasu ciki .
a wani dogo office aka shigar dasu wanda gabad'aya nsa glass ne dan ana iya hango duk wanda yake ciki ,basu d'auki cikakken mintuna goma ba mr segun ya shigo yana tmbyr saurayin daya shigo da
su maryama "niyi ina bakuwar  daka shigo daita ?
"sir itace  a gabanka zaune”  mr segun ya d'an ware idanunshi akan maryama dake zaune yana mata barka da zuwa yana mai sake  masu iso  zuwa wani office din dabam wanda daga shi sai wanda ATA yake cikin zaune zaman jiran qarasowarta  .
   

     "kusa da maryama yaya sadam ya samu waje ya zauna kamar zai mata numfashi "madam ya hanya ?"
mr segun ya tambayeta cike da kulawa yana kallonta "alhamd sir tunda gamu mun samu mun qaraso lfy amman fa  da kyar dan hanyar nan taku bata da kyau tafiyar da ya kamata ace one to two hour's ne ya kawomu shine ya d'aukemu har four hours amman alhamdulillah "wannan gsky ne mutane na yawon complain akan hanyar nan tamu amman dai  alhamd tunda kun qaraso lafiya tun  mai gida bai gaji da zaman  jiranki  ba dan awaninsa biyu da qarasowa bari nasa akawo maku abun sha, idan kin gama wancan office din dake kallonki zaki shiga kafin nan ma zaki same aciki "yana gama fad'ar haka ya fita da d'an sauri ya barsu zaune maryama ta zuba ma yaya sadam ido har sanda aka kawo masu abun sha ta d'auka ta tsiyaya masa a glass cup ta mika masa ."
ahankali yasa hannu ya amsa cup din hannunta ya kur'bi kad'an yana mai lumshe idanunshi sannan ya ajiye cup din hannunsa yana dubanta a tsanake "ya naga duk kinyi wani iri ?"naji yace idan na gama na shiga  ni kuma nafi son mu shiga tare da kai banason na barka kai kad'ai zaman jirana "


Gajiyayyun idanunshi ya ware sosai akanta kafin ahankali ya hadiye wani abu daya tsaya masa a makoshi sannan yace "karki manta aikinki  kika zo ,kuma kema Kinsan ke kad'ai zasu bukaci  gani banda ni  ?" duk da haka idan a son raina ne mu shiga tare "ta fad'a tana mai tsareshi da narkakkun idanunta ." suna zaune wnn saurayin da yayi masu iso  ya  shigo yana cewa "madam ki shiga ke kad'ai mai gida yake jira "ok but dan allah ko zamu iya shiga mu biyu ?cike da jin haushin maganarta yace "tare zakuyi aikin ne ?no ni kad'ai ce !to ke kad'ai ake buqatar gani aciki dan mai gida baya son hayaniya "ya qarasa maganar tare da ta'be baki sannan ya fice ya shige wani office ."
hankalin maryama ya tashi matuka dan har ga allah haka nan taji bata son shiga ita kad'ai qarara damuw ta bayyana acikin kwayar idanunta da shi kad'ai yaya sadam yake iya gani har ya fahimci halin da take ciki ,ahankali yaya sadam ya tsiyaya mata drik ya miko  mata ta girgiza masa kai alamun bazata sha ba ,"why ?! ya tmbyeta yana sake tsareta da idanunshi dafe goshinta tayi tana cewa "bana jin shan komai a yanzu ,tun daya ga haka yasan ko me zai yi 'bata lokacinsa  kawai zai yi dan bazata kar'ba ba, dan haka ya mike tsaye suka fito tare tana gabansa yana take mata baya har suka fito dogon hanyar da zata kai su office din ATA wanda alokacin yana tsaye  acikin tangamemen office dinsa  ya hard'e  hannuwansa duka a faffad'an qirjinsa idanunsa kyam  akan maryama da yaya sadam ta cikin glass door ,har  ta fara taku domin qarasowa zuwa  inda office dinsa yake yaga ta tsaya  ta koma baya kad'an tana magana da wani da bai san ko waye ba ,sai dai idanuwanta  yana kansa ,kwakwa luwarta na hasko mata fuskarsa daga nesa kamar tasan fuskar yayinda shi din ma  kallonta yake cikin shigarta ta mutunci kamar ranar farko daya fara d'aura kwayar idanunshi akanta ."doguwar riga ce sanye ajikinta har qasa  mai dogon hannu  da qaramin hijab dinta mai zip a gaba,sai  nikaf kalar hijab din da take sanye dashi wanda iya kwayar idanunta kad'ai ake iya gani ,tsaki yaja da karfi fuskar nan tashi babu wani annurin kirki dan babu abinda ya tsana arayuwarsa kamar 'bata lokaci ,yana wasa da komai arayuwarsa amman baya ta'ba wasa da lokacinsa ,ita kuma abinda ya fahimta kenan daga gareta  tana da matukar wasa da lokacinta da kuma damarta  ".



"ya kuma kika tsaya  madam bayan  an fad'a miki ke kad'ai mai gida yake jira ?"ta jiyo sautin muryar segun  daga bayansu ta juyo a natse idanunta kyam akan  yaya sadam sannan tace  "yanzu zan shiga na d'an tsaya muna magana da mijina ne "miji kuma alokacin aiki ? yayi mata tambayar da mamaki akan fuskarsa dan shi a tunaninsa bata da aure tunda ta amsa gayyatarsu a weekend mutumin daya gansu tare kuwa ya d'auka d'an rakiya ne ko kuma saurayinta ."a natse ta gyad'a masa kai tana cewa "Eh mijina ne kuma yayana ne   ". ATA wanda yake tsaye yana ciza lip's dinsa da karfi  cikin zafin rai  bai san wainar da'ake toyawa ba amman haka nan yake jin matsanancin bugun zuciya da kuma 'bacin rai mara misaltuwa "any way kiyi sauri ki shiga kiyi abinda ya kawoki dan mai gida baya wasa da lokacinsa ,akan lokacinsa zai iya aikata komai kafin ta bashi amsa  yaya sadam yayi murmushi ya matso kusa daita sosai tare da zuba hannuwansa duka cikin aljihu wondonsa fuskarsa a sake  "karka damu yanzu zata shiga  kuma zata maku abinda kuke so "ya fad'a masa haka sannan ya maida hankalinsa kan maryama  kamar zai mata numfashi"k'anwata kuma amaryata karki wani damu da jiran da zan miki ni kad'ai abinda  nake so dake ki  natsu sosai kiyi abinda ya kawoki ina sonki ina kuma alfahari dake na kuma yarda dake a duk inda zaki kasance nasan zaki kame min kanki da kuma mutuncina "nan take idanuwanta suka cicciko  da ruwan hawaye "yaya sadam na gode sosai ,na gode da yarda daka min ya allah ka yarda dani kamar yadda mijina ya yarda dani "ameen ya hayyu ya qayyum "ya fad'a tare da ciro handkey fari daga gaban aljihun rigarsa ya goge mata hawaye  then ya kai bakinsa yayi kissing foring head dinta yana mai karfafa mata gwiwa murmushin gamsarwa ta sakar masa sannan tayi gaba tana d'aga masa hannu ."



bayanta yabi da kallo  cike da tausayawa take taka kasa kamar bata son takawa yana tsaye har sai daya ga ta tura kofar office din ahankali ta shiga kusan second biyar ya d'auka tsaye yana kallonta ya kasa d'auke idanunshi akanta ,ATA wanda yake rike da  waya a daidai bakinsa da hananu d'aya  yayinda d'ayan hannunsa  ke rike da wata farar takarda yana magana yana  kai kawo acikin office din hakazalika segun na tsaye a gefe guda cike da girmamawa bai kalli inda take ba .”
ahankali yaya sadam ya  juya ya fara taku zuwa kasa jikinsa a matukar sanyaye ya bud'e mazauninsa na direba ya shiga ya zauna yana sauke wani irin naunayen ajiyar zuciya sannan ya d'auki wayarsa ya rike yana dubawa missed call's din nadiya  ya gani rututu ya sauke numfashi sannan ya kirata tana d'auka ta fashe masa da kuka "menene kuma abun kuka ?"na fad’a miki zan cika miki alkwarin da nayi miki bazan ta’ba cin amanarki ba nan da wasu watanni masu zuwa zamu kasance tare amatsayin ma’aurata ,oh my god dan an d'aura aurena shi yake nufi me ?kinga nadiya banason abinda kike min wallahi kukanki yana mugun 'bata min rai ."



"a natse ATA  ya juyo mata fuskarsa sosai tare da tsayawa ya tokare hannunsa dake rike da farar takardar a makeken table din gabansa yana cigaba da wayarsa ."idanun maryama  suka sauka kan kyakkyawar fuskar ATA wanda zuwa lokacin ya  runtse  idanunsa gam zuciyarshi da bakinsa ne kawai ke aiki ,ta tsura masa idanuwanta sosai tana cigaba da kallonsa " tabbas ba gezo idanuwanta suke mata ba shine  shararren d'an kasuwan nan data d'auki tsawon lokaci wajen  zanashi wanda a qarshe ta kai zanensa ma'aikatansa babu wata gamsashiyar magana mai dadi daga ma'aikatansa ."tayi shiru tana dubansa a tsanake tana shakar kamshn turarensa mai sanyi da ratsa zuciya "tun daga ranar data kai masu zanensa suke nemanta a waya "to mai yasa suke bibiyarta ?"mai yasa suka jawota zuwa nan ?"
ta yiwa kwakwaluwarta tambyr da bata da mai bata amsa wani irin mummunar fad'uwar gaba take ji  babu abinda kwakwaluwarta bata hasko mata akansu  ba amman tai qoqarin sharewa  ta cigaba da tsayuwar jiransa ."bakinta na furta  hasbiyallahu la ila a illahuwa alaihi tawakkaltu wa huwa rabbul arshil azim sakamakon wani sabon tsoro da ya shigeta ."



maryama na tsaye har kusan mintuna shabiyar  ATA bai gama wayar da yake ba haka zalika  bai bud'e kwayar idanunshi ya bata umarnin zama ba haka ma segun na tsaye bai zauna ba adaidai lokacin da qarfe d'aya na rana ta buga  wanda a daidai lokacin wasu masallatan sun tada sallarsu dan haka ranta ya soma 'baci ta soma tunanin an janyota ne kawai dan a sake wulakantata a karo na biyu ji tayi kamar ta juya ta wuce shi da segun ta kama gabanta ,ta kalli inda segun yake tsaye  shima ya kalleta haka nan ya tsinci kansa da shafa mata qirjinsa alamun tayi hakuri "segun !yes sir ya fad’a cike da girmamawa ya mika masa farar takardar dake rike a  hannunsa batare daya bud'e idanunshi ba "ina bukatar copy's dinsu "okay sir ya amsa ya fita da sauri  ."ko bayan fitar segun ata bai bud'e idanunshi ba bare yayi mata magana sai kuma taga bai kamata ace tana jiran sai shi ne zai fara mata magana ba   dole dai  sai itace zata fara masa magana kafin ya saurareta ,dan haka ta qara taku d'aya ta tsaya daidai saitin kunnensa  cikin muryar dake nuna alamun gajiya "ta gaishesa bai amsa ba sai ma ya matsa baya ransa a 'bace yayinda zuciyarsa na tafasa dan ya tsani yazo jira duk abinda zaayi masa dole shi  zaa jira karo na farko kenan daya zauna jira jiran ma akan itace zata qaru dashi .”


wulakanci da yayi mata yayi mata ciwo, dan ta tsani disgi da wulakanci kamar taja masa tsaki ta fice daga office din sai kuma tayi wani tunani su manyan nan haka halinsu yake kafin kayi nasara akansu dole sai ka kwantar da kai dan haka ta sanyawa zuciyarta hakuri tayi kasa da muryarta da kanta tana wasa da yatsun hannunta "ranka shi dade lokaci na tafiya yana da kyau abani aikin daya kawoni nayi ga kuma lokacin sallah yayi ina buqatar nayi sallah "sake jin sautin zazzakar muryarta ya sanyashi bude idanunshi ahankali tamkar mai tsoron ganin wani abun agabansa  ,ya zuba mata tsumammun idanunshi masu mugun rikitarwa  yana kallon cikin  qwayar idanunta dake d'auke da zara zaran gashi ido itama shi take kallo tana jira daga garesa ".
shiru yayi yana cigaba da kallon cikin kwayar idanunta gabansa na wani irin luguden bugu da karfin gaske,kallon da yake wa kwayar idanunta kallon né na sani "jiki a sanyaye ya  nuna mata wata kofa dake manne da office din "ki shiga kiyi alwala  "yana gama fad'ar haka ya juya mata baya .”


shiru tayi kafin ahankali cikin sanyin jiki ta juya ta shige toilet ta d'auro alwala ta fito ta tada sallah a natse yana zaune yana kallonta yana waya ,ganin har ta idar da sallah bai tashi ba bare shima  yayi tunanin ya tashi yayi sallar  yasa  tayi zaton ko ya  manta daita acikin office din ne hakan yasa ahankali ta matso kusa dashi ta motsa labbanta"sir abani aikin da zanyi bani da ishashen lokaci da gefen idanunsa ya kalleta a d'age sannan muryarsa ta biyo baya  a dake "kece kika zana ni? muryarta a sanyaye tace "eh nice sir !kinsan ko ni waye ?"shiru tayi har kusan mintuna goma tana nazarin maganarsa sannan cike da girmamawa tace "eh sir !
"Waye ni ?ya sake tmbyrta a dake tamkar bashi yayi maganar ba "kai ne shararren dan kasuwan nan  da kasar nan dama duniya gabad'aya take ji dashi "tana gama fad'ar ya juyo a matuqar fusace ya fuskaanceta yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa "shine dan iskanci kamfanina ya  buqaci yin aiki dake amman kikayi rejecting?ya qarasa maganar a matukar tsawace yana zare mata idanunshi .”


nan da nan hankalinta yayi matseefar tashi tayi saurin matsawa baya jikinta na kyarma "aikin banza kawai yanzu haka ke din ba diyar kowa bace amman kin d'auki girman kan tsiya kin d'aura wa kanki nonsense" yana gama fad'ar haka ya mike ya barta tsaye sake da baki "nice nonsense? ta tambayi kanta cike da mamaki jin abinda ya fad'a mata “nonsense!ta sake maimaitawa a fili tana mai jin d’acin kalmar domin tunda take ba’a ta’ba dangantata da kalmar ba .tana kallonsa  ya nufi wani  d'aki tana mai jin wani irin tuttukin bakinciki tare da damuwa mai tarin yawa har ya tura kofar zai shiga sai kuma yaja ya tsaya yana jan tsaki "give me ten minutes "
yana gama fad'ar haka ya qarasa shigewa .”
runtse  idanunta tayi "wannan kuma wani irin sabon salon wulakanci da 'bata lokaci né ? ya kuwa san me ake kira da zane ?"abu ne da yake bukatar isashen  lokaci "ita bama kanta  take ji ba kamar yaya sadam mutumin daya sadaukar da farincikinsa ya biyota cike da zafin zuciya ta juya zata fita daga office din sai ga mr segun , ya tsaidaita yana cewa  "ina zuwa kuma ?zan wuce ne dan bana tunanin aikin nan zai yuwu "calm down madam  ki samu natsuwa kiyi abinda ya kawoki baqaramin sa'a kika taka ba da mai gida ya bukaci yin aiki dake "yana 'bata min lokaci gashi tare da mijina muke "nasani yanzu me yace ko tunda na fita bai yi magana dake ba ?"Yayi a qarshe  wai na bashi ten minutes ."tayi mgnr kamar zatayi kuka "ok kiyi hakuri ki bashi lokacin dayace kin 'bata sama da awa acikin office din nan sai mintuna goma né kawai zai gagara watakilla ma bazaki yi aikin a yau ba ,zai baki ne kije gida kiyi idan kin gama sai  ki kawo cike da jan hankali ya dinga karfafa mata zuciyarta  dan haka ta cigaba da tsayuwar jiran ATA  ."


kusan mintuna goma sha ya d'auka sai gashi ya fito tare da furta "kika ce kice kika zana ni? Kamar tace masa a'a dan taga abun nasa akwai rainin hankali ciki .amman sai ta tsinci kanta da jin tsoro dan haka ta maida kwayar idanunta ta lumshe masa tana wasa da agogon tsarka hannunta wanda ya qara wa zanen lallenta kyau ,lallen yabi da wani shu'umin kallo tun da yake bai ta'ba ganin zanen lallen da yayi masa kyau har ya d'auki hankalinsa ba sai nata yaji kamar ya kamo yatsun hannunta ,ya d'ago idanunshi a natse ya kalli fuskarta nan da nan  idanunsu ya tsarke cikin juna wannan karon sauri cire kwayar idanunta cikin nashi tayi tana mai kawar da fuskarta gefe tare da danne bugun zuciyarta "shi kuwa wani yanayi ya tsinci kanshi ciki mai sarkakkiya da wuyar misaltuwa sakamakon idanunsu da suka sake tsarkewa cikin juna abinda ya lura atattare daita itama tana da jin kai da miskilanci"a natse ya sake bin zanen lallenta da kallo wani irin kallo ta watsa masa gabanta na fad'uwa wanda ta rasa dalilin jin haka ."



Ahankali ya samu waje akan  kujerun kushin dake office din  ya zauna batare daya bata umarnin zama ba  "bata zauna ba sai ma idanunta data tsura masa tana kallonsa tana sauke numfashi dan itama taci alwashin bazata yi mgn ba har sai yagaji dan kansa yayi . abinda batasani ba shi  ko ajikin ATA da zasu  kwana  a haka ma  bazai damu ba abinda yasani ne ba zai barta taje koina ba har sai tayi masa abinda yake buqata daga gareta ."ya lumshe tsumammun idanunshi yana jijiga kafarsa d'aya yana jira daga gareta ."a qalla sun kusan minti talatin yana zaune ita da segun suna  tsaye ta kalli agogon dake d'aure a hannunta a karo na kusan biyar a kasan ranta taja qaramin tsaki bata san me ya janyota zuwa wannan aiki ba nan take kwakwaluwarta ta shiga aikin neman mata mafuta ."kafin ahankali ta samo zance zuci"maryama dole ki ajiye komai ki  qarasa gabansa Kiyi masa magana idan aikin nan zai yuwu ayi idan bazai yuwu ba ya sallameki ki kama gabanki tun kafin hakurin mijinki ya qare"da sanyi jiki take qarasowa zuwa inda yake ahankali ahankali har ta iso ta zauna a kujerar dake facing dinsa "wani irin zane  zanyi "? tayi tmbyr cike da sanyi murya "ahankali ya motsa lip's dinsa "ina kayan aikinki ?da hanzari ta bud'e jakar kayan aikinta   ta fito da kayan aikinta tare da janyo kujerar gabanta zata ajiye ta jiyo sautin muryarsa "ba'a nan zakiyi ba” ya fad'a tare da mikewa tsaye "biyoni ! "


fitowa sukai daga office din yana gaba tana biye dashi haka ma segun  yayinda gbdy hankalinta ya rabu gida biyu wani yana gurin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login