Showing 147001 words to 150000 words out of 167047 words
Chapter 50 - Mar’adam’s Book 2 Hausa Novel Complete.txt
ba hk ba rayuwata zata qare cikin cakwakiya "Ameen Ameen in sha allahu zata kasance gsky ta fad'a cike da tausayawa hawaye na kokarin zubo mata .”ya mike ganin halin da mahaifiyar sa ta shiga sai dai saukowarta akan mafarkinsa ya bashi gwarin gwiwa sosai da kuma tabbacin zai sameta” na gode sweetheart bari naje na shirya naje office I have some work" bazakaci komai bane ? "No !kawai ya furta ya nufi kofar bathroom yana layi .”tabishi da kallo ina ma tana da halin ciremasa damuwarsa ina ma da yadda zatayi amman babu sai dai tayi imani babu abinda yafi karfin allah zan tayaka da addua adamcy Allah ya sausauta maka ."Idan kuma daga nice ya Allah ka sheida na yafe masa duniya da lahira ka yaye masa wannan danuwar .”
****
bayan ya dawo daga d'aya cikin ma'aikatansa yana sauka idonsa da abida sukaci karo dauke kanshi yayi ya cigaba da taku "AD !!!! ta biyosa tana kiran sunansa sai dai bai tsaya akoina ba sai parlour'n mahaifiyarsa "ka tsaya kaji me zance mana cak ya tsaya "uhm ina jinki ya fad'a yana duba file din dake rike ahannunsa "dan allah ka bawa sister dina sultana dama just give her a chance wallahi zata maka abinda kake so she can’t disappoint you zata maka zane kamar yadda zaka mata discreb din abinda take so wallahi ta kware sosai kalli yanayin zanenta ka gani ."
Yayi shiru yana dubanta tare da dage girasa daya domin dai duk ya fahimcesu so take ta karfi da yaji ta tura masa kanwarta batasan shi din kwararren mai basira bane ta miko masa takadar zanen da take rike dashi "just one chance AD." ke kikasan takware sosai amman ni babu abinda zanyi da zanenta "ni dai kayi hakuri dan allah to idan bazaka amince ba ka bata aiki akarkaahinka kamar yadda na nemi alfarma a tun farko do it sake of me please tayi kusa dashi sosai tana magana kamar zata shige jikinsa yayi saurin ja da baya yana mata wani irin mugun kallo "kace ka amince dan allah "nifa bazan kawota kanfani da sunana ba amman duk wanda zai kaita banida matsla da hakan "ya fad'a yana barin wurin gabadaya ya haye sama ta juyo a hankali ta bar parlour'n ."
Umma zaune a gefen gadonta cikin tsananin tashin hankali da alhinin rashin d'anta a lissafinta Kwanaki 90 kenan wanda yayi daidai da wata uku da rasa sadam dinta hawaye ne masu zafi Ke fitowa daga idanunta yayinda kwakwaluwarta ke hasko mata fuskar tilon d'anta "ta yaya zan iya jure rashin sadam arayuwata ?zuciyarta tai mata tambayar "duk runtsi duk wuya zan jure domin na barwa allah komai zan cigaba dayi masa addua kamar yadda na kewa mahaifinsa,shikenan sadam ya tafi ya barni ni kadai a duniya alhalin bani da kowa bani da komai sai shi kad'ai." ta qarasa mgnr wasu sabbin hawaye masu ciwo da radadi suna sauka akan kuncinta .”ahankali ta mike tsaye ta qarasa Inda tangamemen hotonsa yake manne da bangon d'akinta ta tsurawa hoton ido tana kallonsa "allah na gode maka akan wannan jarabawa da kamin kasan ina tsananin son sadam arayuwata amman ka rabani shi domin ka gwada imanina “allah nayi imani da qaddara da hukuncinka gareni ,na dai shiga damuwa ne saboda tsananin kewa da sabon da nayi dashi amman zan gargadi zuciyata zan sata tayi hakuri da rashin sadam domin nayi imani rayuwa da mutuwa duk naka ne zan daina kuka ..." a hankali ta dinga furta kalmar zan daina kuka amman still bata daina zubar da hawaye ba ."
tana cikin wannan halin maryama ta shigo d'akin cikin yanayi na sanyi jiki dan zaune take a falo kananan maganganun su aunty salma ne yasa ta baro falon dan bazata juri jinsu ba .kowa ya ganta yasan ta zube sosai akan yadda take daman kuma ba wata mai kiba kirki bace sosai ta d'ashe tamkar mara jini dan haka ramarta ta sake bayyana .”ahankali ahankali take d’aga qafafuwanta har ta qaraso ta durkusa a daidai kafafun umma "umma ki daina kuka ."ta furta mata idanunta na kawo ruwan hawaye "umma ta d'ago idanuwanta ta kalleta da tarin damuwa sannan ta d'auke idanuwanta "umma nasan da wuya ki iya mantawa sadam koni bazan iya mantawa da yaya sadam a rayuwata ba bare ke da kikayi silar zuwansa duniya amman dan girman allah umma kuka nan ya isa haka kar wani mummunar ciwo ya kamaki na shiga uku ,".
“ wallahi ummah ban san ina matukar son yaya sadam zuciyata ba sai dana rasa shi zuciyata na cike da matsanancin soyayyarsa "nasani maryama allah ya jikan sadam ke kuma Allah ya baki hakurin rashinsa "ki daina furta hakan umma jikina na bani yaya sadam bai mutu ba tunda na ji ajikina bai mutu ba tabbas bai mutu ba zai dawo garemu ."umma tayi shiru tana sauke numfashi tare da ajiyar zuciya a duk lokacin da taji maryam ta furta hakan ta Kan samu saukin zugin da zuciyarta keyi cike da matsanancin soyayya ta kamo kafad'an maryama ta d'agata tsaye bisa kafafunta ta rungumeta tsam ajikinta"maryama maganarki tana kwanatar min da hankali duk da nasan da wahala ace sadam dina yana raye ."kusan minti goma suna rungume da juna kafin daga baya maryama ta zare jikinta ta tsurawa hoton yaya sadam ido ."
A hankali ta kai hannu ta d'auki hoton ta koma kan gadon umma ta zauna tana cigaba da kallon hoton tana shafa fuskarshi yayi matukar kyau sosai fuskarsa kwance da murmushi "umman kin tuna ranar daya d'auki hoton nan ?cewar maryama" na tuna ranar daurin auren mashkur abokinsa ne ta fad'a tana zama kusa da maryama"yaya sadam ka dawo garemu karka barmu zuciyar ni da umma na matukar qaunarka bazamu iya jurar rashinka ba dan allah ka dawo garemu ." shiru sukai gabadaya zuciyarsu cike da tunani umma ta janyo akwatin kayansa ta fito da kayan sawarsa tana nikewa tana maidawa cikin akwatin ,maryama ta d'auki jeans dinsa ta rike tana kallo kafin ahankali ta motsa bakinta "karki damu umma zai dawo fa ".umma ta kalleta kawai dan ita tasan bazai dawo ba har abada mutumin da'aka binne da ransa ta yaya zaayi tunanin zai rayu har ya dawo ?"cike da sheshekar kuka tace "ya allah kabamu hakuri rashin sadam domin zuciyoyinmu sun gaza hakuri akansa maryama ta matso sosai ta kwanta ajikin umma cike da tsananin qauna "d'ana sadam mutumin kirki ne, d'ana sadam mai kyakkyawan zuciya ne ,d'ana sadam mai hakuri ne gashi ya tafi ya barni batare da kowa nasa da zan kalla naji sanyi araina ba."
“shikenan na rasa mai sakani dariya na rasa mai kawar min da damuwa na rasa mai dibe min kewa."
ta qarasa maganar tana zubar da hawaye."maryam ta kai hannunta ta shiga gogewa umma hawaye tana cewa “ karki damu umma zanyi miki duk abinda yaya sadam yake miki sannan kuma kisa aranki zai dawo garemu mu cigaba da yi miki komai tare "
"Zo zo!! ku ga wani abun mamaki Aunty salma ta jawo hannun baba gali da aunty hasanaa zuwa bakin kofar d'akin umma, kalli ku gansu "wannan matar anyi shasha an kashe mata d'a amman dan shashanci ku kalli shirmen da take "ke yanzu wannan ne ya dameki ? baba gali ya fad'a tare da juyawa ya samu waje ya tsaya suka biyosa suka tsya kusa dashi suna dubansa bakinsu na son furta wani abu "salma ki rabu dasu kawai mu dai muyi yadda zata dawo daidai kafin wannan yarinyar ta gama takaba araba gado ,aunty salma ta saki murmushin jin dadi burinta zai cika "kai wallahi ina cikin farinciki saboda kaso mai yawa zaka samu “sosai kuwa dan kaso biyu zanci tunda ni nmj ne "ya qarasa maganar cikin tsananin farinciki wannan kuma haka ne bari kama gabanmu su kuma suje su qarata da kukansu hawaye ne yayi masu yawa" wallahi nima allah allah nake lokaci yayi araba abani kasona inji cewar aunty hasana baba gali ya saki murmushi "ni Allah yasa a mallaka min kamfanin burodi gbdy aunty salma tasa dariya murna kmr su rungume juna a wajen ."baba gali da aunty salma suka fice suna dariya aunty Hasana ta shiga kitchen domin daurawa umma abinci dan tun daaka nemi sadam aka rasa kusan rabin yininta anan take yi ."
Umma ta kai hannu ta shafa sumar kan maryama "allah yayiwa rayuwarki albarka ,allah ya qara mana hakuri, muyita hakuri da sannu allah zai mana sakayy.. “qarar wayar umma ce ta katseta maryama ta mike da sauri ta shiga duba inda wayar take "gashi can a karkashin pillow ta fad'a tare da d'auko wayar ta mika mata cike da ladabi ta d'auka "assalamu alaikum, wallahi alhamdulillah mun godewa allah ya kunfan jiki Aa da kanki ai da kinyi zamanki hjy ba sai kin wahalar da kanki ba to shikenan allah ya kawoki lafiya sukai sallama " umma waye zai zo ?granny ce "shiru tayi tana tunani , tashi muje parlour'n tare suka fito zuwa parlour umma na kiran sunan "hassana "kanwar hajiyata na nan zuwa in sha allahu gobe ,hasana ta fito daga kitchen tana goge hannunta tana cewa "kai allah ya kawo mana ita lfy ta kalli maryama ta galla mata katuwar harara "maza ki d'auke wad'an mugayen idanunki akaina aí mu dai wannan yarinyar ki zame mana balai a danginmu wai aunty yaushe zata bar bangaren nan ne ta koma can gurin uwarta kar muma ta lashe mana kurwa ?wallah duk san dana daura idanuna akanta ina jin kamar na kasheta ta mutu kamar yadda ta zama silar kashe min dan danuwana dan girman allah ki sallema ta bar bangaren nan mu huta da jaraba "ke dan Allah ya isa haka ina zata alhalin tana cikin takaba? wallahi hassana banason abinda kike wa yarinyar nan yana matukar kona min rai dame kike son yarinyar nan taji ?Ko ance miki ita ta kashesa né ?Kiyi hakuri aunty in sha allahu na daina umma ta juya mata baya tana danne hawayenta ".amman Aunty ya kamata ki fito da kayan sadam tunda yanzu ya zama na magada sai bawa yara su yi amfani dashi tunda ya mutu kafin wannan mayar ta gama takaba araba gadonsa .."
"sadam bai mutu ba"maryama ta fada da iyakacin karfinta tana juyowa ta fuskanceta tare da dafe qirjinta "tabbas sadam bai mutu ba ta qarasa mgnr tana kuka "yanzu ke hasana har kina tunanin abinda ya mutu ya bari sun zama na magada ku kenan ?dan kune magadansa sai ni da matarsa maryama nan da nan idanun umma suka cika da kwalla ta shiga girgiza kai "wallahi hasana ki bani mamaki sam banyi tunanin haka daga gareki ba "idan ma kiyi hakuri ni da kaina zan nemi araba duk abinda ya bari domin allah ne yace araba gado ni ban isa nayi jayayya da hukuncinsa ba amman at least kunyi hakuri ku daina daga hankalinku ,baku barni na huta ba baku bar yarinyar mutane ta huta ba wai me yasa haka né ?karki manta maryama jininki ce domin kinfini kusanci daita dan diyar yayankice uwa daya uba daya wallahi naso sadam ya rayu kodan ya kula min daita ya gatanta min ita ya bata kulawar da duk wani miji yake bawa matarsa ."ta qarashe mgnr tana kuka ".
maryam ma ta fashe da kuka ."Umma ko zaa raba abinda sadam ya bari dan Allah a d'an jirkinta tukun har zuwa wani lokaci saboda har yanzu police suna Kan invesgetion idan ya zamo yana raye fa bai mutu ba kuma an rigada an raba komai nashi ni dai a nawa shawarar kar a ta'ba komai nashi hatta suturarsa abarshi tukun nan." da wani irin mugun kallo ta d'auketa dashi " yanzu ke maryama kina tunanin yana raye ? " bai raye yana raye ya kamata abari hukuma ta gama bincikenta alabashi komai zaa yi sai ayi amman for now abar komai gsky
Tunda tasoma magna Aunty hasana tayi shiru tsaye tana mka maka mugun kallo, da ashariya daga cikin zuciyarta "kaji min tsinanniyar shegiyar yarinya suka jiyo muryar aunty salma gabadaya suka juya bayansu suna kallonta ahankali ta dinga taku har ta qaraso inda suke "lafiyarki ma kuwa maryama ?gsky akwai alamun kin zauce ayi hanzari akaiki asibitin mahaukata a duba lafiyar kwakwa kuwarki,"kece fa da kanki kika tabbatar mana yaro nan ya mutu tunda a gabanki kika ce an binnesa da ransa amman ki kekashe kasa akan bai mutu ba " wallahi aunty bai mutu ba dan ina ..."ke jaira kiyi mana shiru anan kafin na zuciya na soma yar yar fa miki mari sadam ya mutu kuma bazai dawo ba har abada idan ma zaki cire hkn aranki ki cire ki fara tunanin wata rayuwa."
ta fad'a tana huci “wallahi bai mutu ,kuma babu mai raba gadonsa hasalima babu takabarsa akaina ina nan ma tsayin matarsa har tsawon shekaru hudu “lallai hasashena ya tabbata yarinyar nan ta samu tabin hankali “to tsaya kiji da kyau duk macen da mijinta ya bata ne zatayi dakon aurensa na tsawon shekaru hudu sannan bayan haka tayi idda idan kin haukace ne gara tun wuri musani amman rabon gado tabbas zaayisa acikin gidan nan inji cewar aunty salma .”
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 28
Kwanciya maryama tayi a kasa tana wani irin kuka mai ta'ba zuciya da ban tausayi sai dai duk wannan kukan da take sautin muryarta bata fita sosai ,tana jin ina ma sautin kukanta ya fito fili da hakan zai fiye mata sauki fiyye da rashin fitowarsa bugu da qari ko yasa yan'uwan mahaifinta sun sauko daga tsatsauran raayinsu su tausayawa rayuwarta ta jurewa kowance irin jarabawar da Allah yayi mata amman ta kasa jurewa wannan jarabawar, ta kasa jurewa jarabawar rashin miji da kuma d'anuwa gareta."meye tarin zunubina?tayiwa kanta tambayar hawaye na sake gangarowa akan kuncinta "ya Allah ka sausautawa rayuwata domin idan abubuwan dake faruwa akaina suka cigaba da faruwa zuciyata zata buga ."idanun umma dake cike da ruwan hawaye ta zubawa aunty salma tana kallonta cikin wani irin yanayi na tsananin damuwa da bakincikin mummunan kalamanta ga maryama ."cike da tsananin tausayawa maryama umma ta qaraso gareta ta durkusa ta riko tafin hannunta cikin nata cikin yanayin tashin hankali tace "kukan ya isa haka maryama kada kanki yayi ciwo ."
"mai yasa abubuwa suke zuwa min haka umma ?"ya zanyi da wannan rayuwar ? ya Allah ka d'auki rayuwata na mutu na huta da wannan duniyar da babu komai acikinta sai tarin bakinciki ya Allah ka d'auki rayuwata tunda haka rayuwar duniya take "daga wannan tashin hankali sai wannan tashin hankali meye laifina ?nan take tausayin maryama ya sake ninkuwa acikin zuciyar umma tare da jin wani irin tarin qaunarta mara misaltuwa "kiyi hakuri maryama ki daina furta wad'an nan kalaman haka rayuwa take cike da kudirorin ubangiji ,sannan dukkan rayuwa d'an adam rubutaccen al'amarin ne daga Allah,na shafa fad'a miki duk mutumin da Allah yake so shi yake yiwa jarabawa." wani sabon kuka ta fashe dashi tana jin kamar ranta zai fita ya bar gangar jikinta aunty salma ta kwa'be baki tana duban umma da maryama a kaskance kafin ahankali ta cigaba da cewa "da dai kin daina wannan kukan munafurci da kike yi da bazai ta'ba miki maganin halin da kike ciki ba, mutuwa ce da bakinki kika ce agabanki aka binne sadam da ransa to me kuma yayi saura ?Jin haka ya qara sa ran umma yayi matukar 'baci ta d'ago idanunta cikin zafin rai ta kira sunan aunty salma "salma !"
Yanayin yadda ta kira sunan cikin tsawa ya d'aga masu hankali gabad'aya sukai tsuru suna kallonta domin wannan shine karo na farko da suka ga tarin damuwa da 'bacin rai acikin kwayar idanunta,"salma karki bari 'bacin raina ya sake ninkuwa akan wanda nake ciki ,nayi ta qoqarin na danne zuciyata akanku amman naga alamun so kuke sai na nuna muku fushina da 'bacin raina"me maryama ta tsare maku ?wani irin numfashi mai zafi umma ta fesar kamar an tsikareta haka umma ta tashi daga gaban maryama "wallahi wallahi !!kunji na rantse akan maryama zan iya 'batawa da kowa dan haka ku shiga hankalinku ku san irin magangun da zasu dinga fitowa daga bakinku saboda kuma kuna da naku ya'ya,allah yasa mata kuka haifa dayawa kusani duk mugun nufinku ga maryama kanku ko kan ya'yanku zai dawo domin allah baya zalinci kuma baya son mai zalinci amman nasan rashin ilimi ke damun rayuwarku domin da kusan dukkan rayuwar rubutaccen
lamari ne daga rabbi, kilan da baku tsaya ' batawa kanku lokaci ba gurin matsawa kanku da hassada da hankoron neman duniyar da wani ba ."
aunty salma ta kalli umma wacce har lokacin kwayar idanunta na kanta cike da tarin 'bacin rai sannan ta waiga inda baba gali da aunty hasana suke tsaye suma cike da mamakin umma .aunty salma ta daure zuciyarta da maganar umma tace "irin fatan da zaki mana kenan ?"irin fatan dai da kukewa kanku kenan." da sauri umma ta bata amsa da haka sannan tana cigaba da cewa " maza ku fice min daga parlour bana son ganinku kuma wannan ya zamo karo na farko dana qarshe da zaku shigo inda nike kuyi lamarinku nayi nawa bana son ganin gaba d'ayanku a inda nake kowa ya zauna inda allah ya ajiyesa ."saboda an ta'ba miki yar so zaki fad'a mana haka ? Inji cewar aunty hasana "kwarai kuwa zan ma iya yin abinda yafi haka matuqar akan maryama ne aunty hasana ta numfasa kana tace "idan bake ba aunty ai murna zakiyi da abinda ake wa yarinyar nan yarinyar da ta zama silar rasa tilon d'anki "sadam dai d'ana ne dana haifa da cikina duk kuma wanda