Showing 117001 words to 120000 words out of 167047 words
Chapter 40 - Mar’adam’s Book 2 Hausa Novel Complete.txt
aiki na ba, a kira doctor nasir” da sauri mami tace. “Auta maza shiga ɗakina ki ɗauko min wayata” da sauri nana hauwa'u ta nufi ɗakin mami ta ɗauko wayar tana niman layinsa yayinda aunty shahida ke bata taimakon gaugauwa shi kuwa ATA mikewa tsaye yayi yana jan tsaki ya ra’ba ta gefensu ya fice yama bar gidan gbdy .”
Bayan awa uku
Maryam na zaune a kujera tana sauke numfashi ansa auduga da plasta an rufe raunin goshinta yayinda mami ke zaune a gefenta riƙe da hannunta Dr.Nasir Ya miƙe tsaye sanye da coat da farin gilashi hannunsa riƙe da first-aid box ya miƙawa mami Ƙaramar takardan magunguna “hajiya ga wannan takardar magungunan da zatayi amfani dashi ne insha Allah da zarar tasha a hankali ƙarfin jikinta zai dawo baboda naga Allah ya taƙaita babu wani babban rauni da zai sa muyi admitting ɗinta asibiti ko kuma yiwa cikin jikinta illa Wannan treating ɗin ma da nayi mata is okay for her” mami ta jinjina kai tana faɗaɗa fuska cikin farinciki tace. “doctor kace ciki gareta?” Doctor Nasir yace. “ƙwarai kuwa hajiya in sha allahu ranar monday akawota hospital domin yi mata scan dan mu san iya adadin kwanakinsa” “masha Allah Dr.Nasir nagode sosai ka min albishiri mai daɗi” na dade ba’a fada min maganar data saka zuciyata farinciki ba dr nasir ya kalli maryam da murmushi a fuskarsa “to hajiya Mar-Adam zance ko Mrs Adam? Allah ya bada lafiya” maryam tayi murmushin ƙarfin hali tana kallonsa zuciyarta na rawa dan tun daya fara maganar ciki ta shiga damuwa mai tsananin dan ita kanta tana zargin ciki gareta duba da watan ta na uku kenan bata ga period ɗinta ba. “Allah ya sauwaƙe ya bada lafiya” da “Amin” ta amsa cikin ƙarfin hali.
Dr.Nasir Ya juya ya fita daga gidan farinciki agurin mami da ƴaƴanta ba'a magana kowa ka kalli fuskarsa kwance yake da annurin farinciki gabaɗayansu murna suke har sun kasa ɓoye murnarsu mami ta riƙo hannun maryam cikin nata tana kallonta cike da kulawa tace “ke kuwa Maryam garin ya akayi kika samu rauni?” maraym tace. “walalhi mami muna qoqarin karya kwana ne akayi akasi wani me mashin ya kwaso a guje, ganin kamar zai yo kan motar ne sai ido na ya rufe daga hk ni dai bansan yadda akayi ba kaina ya bugu da stearing” mami tace. “yanzu banda Allah ya taƙaita ai da abun ya wuce haka ga ciki ajikinki” .nana hauwa'u tace. “Alhamdulillah da Allah ya taƙaita” cike da murna ta ƙarasa maganar. “ai duk adamcy ne ya janyo da yanzu wani abu ya samu cikin jikinta me za'ace?” nan da nan mami ta shiga zuba wa Adam faɗa da baya nan akan me yasa bai jira Maryam ta gama shiryawa sun fito tare ba? cikin raunin murya “daman ai duk shi yaja mana wannan matsalar, wallahi mami in kinga abubuwan da yayi mata agabana sai kin tausaya mata” cewar ni'ima “kamar wata baiwa ya ajiye a gidansa ba matarsa ba” mami ta tsurawa Ni'ima ido tana kallon fuskarta kar dai itace Ƴar iskar ƙawarta da yake faɗa? “ko abinci ta girka sai yaga dama yake ci, komai tayi bata masa gwaninta, sai yayi tayi mata tsawa yana hantarar ta wannan wani irin aure ne?” mrym tayi saurin take ƙafar Ni'ima “kinga malama ki bari ayi magana yanzu an daina auren wahala idan bazai iya ba ya sallame ki, ki kama gabanki idan kin haife abinda yake cikinki ki kawo masa ki dire ai namiji goma ba uba goma bane " Hjy zulai da mamaki take cigaba da kallon Ni'ima tana tunanin in da tasan fuskar “haba Ni'ima wai meye haka ne ?dan Allah kizo ki wuce gida dan Allah nace miki ina son rabuwa da mijina ne? koni na faɗa miki yana min duk abinda kika furta “au karesa zakiyi saboda baki da hankali ai duk abinda idanuna suka gane min kamar na faɗawa ummah na gama” tana gama faɗar haka ta juya cikin tsananin fushi.”
Cike da ɓacin rai nana hauwa'u tace. “sister wannan fa wacece ita? Jiki a sanyaye ” Maryam tace. “ɗiyar sister ɗin ummammu ce “kai shiyasa nake ta mata kallon sani kar dai ɗiyar umaima ce?” Maryam ta gyaɗa mata kai alamun eh. “shine zata dinga faɗar magana akan yaya? kuma ai kice kika bata wannan damar” “kamar ya sister?” maryam ta faɗa jikinta na ɗan rawa “idan baki faɗa mata komai akanshi ba ya'akayi tasan irin zaman da kuke yi?” aunty shahida ta faɗa ranta a ɓace “karfa kiga duk muna bayanki ki ɗauka bama son shi ne, adam rayuwarmu ne kema kuma kinsan da haka Maryam ta runtse idanunta sai ga hawaye masu zafi cike da tashin hankali take jin yadda numfashinta ke sauka da ƙarfi. shi kenan Ni'ima ta haɗa mata bala'i “duk muna bayanki sakamakon irin tsanar da yake nuna miki da kuma irin ƙaunar da mahaifiyarmu ke miki” “ dan Allah aunty shahida kuyi hakuri ba'a bakina taji komai ba ummace ta faɗa amman..” katseta aunty khadija tayi ta hanyar cewa. “ita umman taki meye amfanin faɗawa mutane? mun sani sarai adam bai kyautawa amman kuma meye abun faɗawa mutane anan? mufa mun sani sarai ummanki bata ƙaunar danuwanmu, amman mu dai-dai rana ɗaya mun taɓa sauke haushin haka akanki ? kullum yanda rayuwarki zata samu cigaba a gidansa muke" .
Maryam tasa kuka cikin tsananin damuwa .”
“dan Allah ya isa karku saka min yarinya gaba da bala'i dame zataji ?da maseefar ɗan'uwanku ko da naku sai kun harbe mata zuciya ta mutu kowa ya huta ? kuma ai bai barku ba bare ku shigar masa” kuma karya aka fada akanshi ?halinsa ne fa ?“koma dai menene mami bazamu lamunta ba kuma kar mu sake jin taje gidanki daman shima yace ayiwa ƴar iskar ƙawarki congrent warning karta sake shigar masa gida ilai kuwa ashe ƴar iskar ce ai duk abinda kika ji yaya yayi mgn akai mai mahimanci ne” cewar zabiba nana hauwa'u kam tun maganar farko bata sake cewa komai ba, atare suka miƙe aunty shahida aunty Khadija da zabiba sukai ma mami sallama tayi masu addu'a tare da yi masu fatan alkhairi nana hauwa'u bata sake cewa komai ba mami ta laluɓo wayarta daga gefenta ta ɗauka ta soma ƙoƙarin kiran ATA “Bari ina zuwa na kirasa dani yake zancen wato cin mutunci da tozarci har agaban mutane?" maraym tayi saurin riko hannun mami tana kuka tace. “dan Allah mami ki rufa min asiri kar kiyi masa magana yanzu idan ma son samu ne karki ce masa komai” mami ta ƙara wayar a kunnenta tana cewa. “rabu dani gara na faɗa masa halin da'ake ciki tun kafin baƙin cikinsa yasa a rasa cikin jikinki .”
alokacin da mami take neman layinsa yana zaune acikin wani ƙayataccen gida me ɗauke da komai na manyan masu kuɗi da manyan ƴan boko gidan kamar aljanar duniya tsabar haɗuwa wannan gidan bana kowa bane face gidan ammar ATA na zaune a gaban ammar suna tautaunawa akan kasuwanci kiran mami ya shigo ya ɗauki wayar ya manna a kunne “hello kana ina?“ina gidan ammar” abinda ya faɗa kenan yana lumshe ido “to in ka fito kazo gida da gaggawa ina son ganinka” katse ta yayi da faɗin. “lafiya sweetheart?” Mami tace. “ita ta kawo haka bazaka ma tambayi Jikin maryam ba kaji halin da take ciki? ka bar ƴar mutane cikin wani hali gashi..” tun kafin ta faɗi abinda take son faɗa taji ya katse wayar “Hello.. Hello... adamcy” tuni ya sauke wayar daga kunnensa ya kalli screen ɗin sannan ya sauya kujerar sa yana dafe goshinsa da hannuwansa duka ammar ya dawo gabansa ya fuskancesa yan faɗin. “lafiya ?waya kiraka ?ya ɗaga maka hankali gashi bamu gama tattaunawarmu ba?” “sweetheart ce ni dai allah yasa karsu kashe ni akan ƴar iskar yarinyar nan..” “yanzu me ya faru kuma?” “ban sani ba ni dai na barsu wai ta suma” “wa kenan ta suma?” shiru yayi na second biyu sannan ya ɗago kanshi ya kalli ammar “Sweetheart ke son ganina amma zamu iya ƙarasa maganar Okay, Sai dai kuma ya kamata a ce ka ɗau tsanttsauran mataki akan sauran yaran daka faɗa min saboda har kullum shi kasuwanci tattalinsa ake. bana son kabar wata kofa da wasu zasu samu damar janyo mana asara dan bazan ɗauki asarar ganganci ba” “shikenan zan haɗa taron gaugauwa ranar monday zan yiwa P.A ɗina magana, zamu san abin yi kafin matsalar tayi nisa” ATA ya jinjina kai sannan ya buɗe wani file ya duba bayan ya gama dubawa ya miƙe “ni zan wuce” ammar ya jinjina masa kai a sanyaye atare suka fito .”
Can ɓangaren maryam kuwa kuka take sosai abun ya haɗe mata tana kallon nana hauwa'u ta miƙe ta yafa mayafinta tana yiwa Mami sallama “kema wucewa zakiyi ?” “eh Mami yaya hisham yana jirana” “to ai Shi kenan Allah ya tsare hanya” mami ta fada ranta a dagule saboda ganin ya’yanta sun hadewa mrym kai ,nana hauwa’u bata kalli in da maryam take ba ta nufi ƙofar fita, takun maryam taji abayanta tana magana cike da raunin maryam tace. “sister kema fushi zaki yi dani bayan kinsan kece ƙarfin gwaiwata” juyowa tayi ido cikin ido suke kallon juna “kiyi haƙuri sister nayi kuskure” nana hauwa'u tayi murmushi tana kallon cikin idanunta “shi kenan komai ya wuce Allah ya inganta mana babynmu” jiki a sanyaye sukai sallama tana jin kamar zata rasa rayuwarta ne dan gbɗy jin tana ɗauke da cikinsa bai saka zuciyarta samun natsuwar ɗari bisa ɗari ba ta dawo kusa da Mami ta zauna “ki rabu dasu karki wani ɗaga hankalinki akan ɗan wannna abun” Maryam tace. “allah Mami hankalina a tashe yake su aunty shahida sunyi fushi dani” “zan kirasu babu abinda zai faru ni dai fatana ki kwnatar da hanaklinki kar wani abu ya samu cikin jiknki”
Numfashi ta sauke sannna tace. “Mami dan allah karki faɗawa yaya batun cikin nan tukun Kinsan halinsa” Mani tace. “kai babu abinda zai yi sai farinciki aj wannna cikin sai ya kawo miki sauy arayuwarki Maryam tace. “ walalhi yadda yaya baya sona bana tunanin zai so abinda nake dauke dashi Shiru mami tayi tana sauraronta “ai kuwa da Adamcy bai kyauta mata ba idan yaki abinda mrym take dauke dashi “ko kuma za'a iya ƙin fad'a masa har ya gano da kanshi” kai kawai mami ta gyda mata ahankali mami ta dinga janta da hira sai dai jikin Maryam a mace yake kana kallonta zaka fahimci hakan.
A galabaice ya shigo parlour'n mami ya zauna tare da runtse idanunshi gam mami dake zaune ta tsura masa ido ruwan bala'i take son sauke masa amman yanayin yanda ya shigo yasa tayi tunanin kar ta masa faɗan sai tasa aka kawo masa abinci buɗe idanunshi yayi ahankali yace. “gani sweetheart ina son na wuce gida na kwanta na huta” mami tace. “kaci abincin da akawo maka tukun sai muyi magana” kaɗan yaci abincin sannan ya tsurawa mami ido yana son yaji kiran me take masa suna zaune sai ga maryam ta fito daga ɗakin mami jiki a sanyaye ta zauna kusa daita wani mugun ɓata rai yayi “Adamcy!” mami ta kira sunansa ya ɗan kalleta tare da faɗin. “ina jinki sweetheart” mami tace. “me yasa kaci zarafin Maryam a gaban ƴaru'warta?” baƙaramin fusata yayi ba shi kam bai san randa mahaifiyarsa zata barshi ya huta da maganar yarinyar nan ba “amma ajiye wannan maganar ma tukun, ka fita ka bar matarka cikin wani hali baka kira kaji a wani hali take ciki ba bare ka mata sannu da jiki” daga haka ya miƙe ya fice daga parlour'n dan bazai zauna ya cigaba da jin magana akanta ba “maza tashi ki bishi kuje zan zo wani sati sai na daukeki muje scan din “to mami na gode allah ya qara girma “Allah ya tsare da ɗan saurinta ta ɗauki mayafinta ta fito alokacin tuni ya shiga mota ta zagaya da sauri ta bude bangaren da yake ta shiga ta zauna suka wuce gida ."
Bayan kwana biyu da misalin ƙarfe goma kiran Ni'ima ya shigo wayarta tana kallo kiran na shigowa taƙi ɗauka sai a karo na biyar ne ta ɗaga tana ɗauka tace “lafiya Ni'ima kiran me kike min bayan kin kusan jefa rayuwata cikin uku bala'i ? babu ruwanki da duk halin da nake ciki zan gargaɗeki da babban murya karki sake zuwa mijina yace baya son ganinki a gidansa idan kuma kinyi taurin kai zaki gane ke ƙaramar mara mutunci ce” shiru tayi tana sauraron Ni'ima “ni dai nace karki shigo tunda kince saƙo ne daga umman zuru ki tsaya a wajen get idan kinzo zan fito na karɓa amman karki zo ” washegari kuwa da misalin karfe bakwai Ni'ima ta kirata ta fita cikin sanɗa kasamcewar ranar tun safe ATA na gida bai je koina ba wanda alamunsa Ke nuna tafiya zai yi taje ta karɓo saƙon umma zuru irin tukunyar farko da aka aiko mata dashi ne. cikin sauri ta shige ɗakinta dashi ta fito parlour'n ta zauna , tana zaune ATA ya shigo ya haye sama bayan Kamar mintuna talatin ya sauko yana fita, ta miƙe da sauri ta haye sama kamar a mafarki taga kofar ɗakinsa a buɗee wani kyakkyawan murmushi tayi da sauri ta faɗa ɗakinta ta ɗauko tukunyar ta dawo ɗakinsa ta tsaya tare da buɗe tukunyar tsafi ta soma ambatar sunanshi da abinda take son yayi mata kamar yadda aka fad’a mata bayan ta gama ta ajiye tukunyar ta ɗaga katifa ta ajiye a gefe, ta ɗauko tukunya zata saka taji taku tare da tafi daga bayanta ai da wani mugun sauri ta juyo ganinsa tsaye yasa ta saki tukunyar aiko nan take ta fashe sai ga wani mummunar hayaƙi ya shiga fitowa daga ciki .
Cikin zare ido yace “Meye wannan?” tambayar daya jefa mata kenan bakinta da jikinta ya kama rawa “kina son kashe ni saboda bana sonki ko?" Girgiza masa kai tayi tare da faɗi. “a'a ba kashe ka zanyi ba.." cikin daka tsawa yace. “shut up with your dirty mouth! you want kill me?” zatayi magana ya sake buga mata tsawa “shut up how dare you enter my room kuma riƙe da tukunyar tsafi?” nan da nan jikinta ya kama rawa “daman naji ajikina kina son kasheni” sake girgiza masa kai tayi jikinta na wani irin rawa “why you this girl ?me nayi miki da zaki kashe ni ? duk da bana sonki duk da yanda nake ji araina kamar na kashe ki na sha faɗa miki ni ne ajalinki amman na taɓa ƙoƙarin kashe ki?” jikinta na rawa ta girgiza masa kai “why you want to kill me ?” cikin rawan murya tace. “Wallahi ba kashe ka zanyi ba, ka fahimceni wallahi ba wata illa zan yiwa rayuwarka ba kawai dai..” sai kuma tayi shiru ta kasa ƙarasa maganarta “baki da abinda zaki iya kare kanki kije na sakeki saki ɗaya " .
mutuwar tsaye tayi cikin tsananin tashin hankali da matsanancin gigita jin furucinsa, yayinda hawayen idanunta ya ƙaru suka shiga kokuwa da juna gurin silalowa ga wani irin ƙyarma da jikinta ke yi, sai dai rawar da jikinta ke yi ya sanyata saurin durƙusawa a gabansa domin ƙafafunta sun tabbatar mata bazasu iya cigaba da ɗaukar gangar jikinta ba, baya ga haka ma ga wani iri jirin tashin hankali dake ɗawainiya da ita .Wani irin bugawa kanta ke yi tamkar zai rabe gida goma , cikin wani matsanancin rashin Hankali muryanta na rawa tace. “da gaske ka sakeni yaya adam? dan Allah ka janye sakin zan maka bayanin komai domin idan kana tunanin zan...” dakatar da ita yayi ta hanyar faɗin. “shiiii na sake ki kuma babu wanda ya isa ya sake takurani nayi rayuwa dake, dan haka ba abinda ya rage miki a gidana gari ya waye ki bar min gidans kuma bance kije gidan mahaifiyata ba, ki wuce gidanku gidan ubanki tunda ke ɗin ba shegiya bace” shiru kawai tayi tana dubansa cikin tsananin faɗuwar gaba domin dai a kallon da take masa ta rigada tasan bazai taɓa daina tsananta ba a cikin zuciyarsa” maganar sa ne ya katse mata tunaninta. “bazan taɓa daina tsanarki ba, abinda kika kasa ganewa shi so halitta ne..” cikin matsanancin kuka ta dakatar dashi da faɗin. “yanda yake halitta nima haka nake ji akanka me yasa zaka rabu da zuciyar da batasan sanda ta fara sonka ba ?sonka shine mafarin kasancewata a karkashin mahafi....” cikin daka tsawa yace. “bar ɗakin nan stupid! tun kafin nayi losing control , dan ina jin baƙin cikin kasancewata dake ahalin yanzu yayi maganar a zuciye cikin tsananin fushi da tashin hankali mara misaltuwa.”
bata bar ɗakin ba kamar yanda ya furta sai rarrafawa tayi ta koma gefen doguwar kujerar kushin ƙwaya ɗaya dake ɗakin ta rakuɓe , tana kallonsa ya miƙe ya shiga bayi batare daya cire kayan jikinsa ba saukar ruwa a bayin yasa ta fahimci wanka yake a hankali ta rike gefen kanta dake sara tana haɗeye wani ƙululun baƙin ciki tare da share hawayen dake tsiyoyo mata, ta tattara tukunyar tsafin ta kai dakinta ta ajiye ta dawo ɗakinsa ta zauna dan babu in da zata aurenta dashi mutu ka raba ya saketa amman bata saku ba dan tayi imani mami naji zata maidaita."Da mamaki ya fito ya isketa kallon mamaki da naci irin nata yake “zaman me kikewa mutane a d’aki ?” ya faɗa Yana kallonta “babu fa inda zani har sai ka maidani ” wani mugun kallo yayi mata sannan ya ɗauki jug din coffee da zafinsa wanda ta kawo masa bai sha ba ya dawo inda take ya juye mata tsab a jikinta wata razananniyar ƙara ta saka da sauri ta shiga kakkaɓe rigar dake jikinta , cikin faɗa wanda bai hana zazzaƙar muryarsa fitowa ba yace. “banace ki bar min ɗakina ba ?” Ya faɗa yana ware mata idanunsa dake cike da bala'i jikinta