Showing 114001 words to 117000 words out of 167047 words
Chapter 39 - Mar’adam’s Book 2 Hausa Novel Complete.txt
mami tayi warning din glass din mota tace “bani wayarka !babu mutsu ya mika mta number mrym tasa masa tayi saving number da sunanta “ga number mrym nan na saka maka ka dinga qoqarin sauke nauyin dake kanka .”
Itama maryam tace mata “nasan kina da numbersa ki dinga kiran mijinki koda kuwa bazai d’auka ba duk runtse ki sauke nauyin dake kanki allah ya had’a hankulanu tace “Ameen tana daga mata hannu suna tsaye har mota data shiga da masu tsoron motar suka bar gida sannan suka shiga ."bayan tafiyar mami da kamar awa d’aya ya sauko sanye da wasu kaya ya ajiye wayoyinsa akan center table ya samu waje ya zauna ya dauki remut ya kunna tv ya qara karfin ac ya daura kafafunsa akan center table yana duban tashar labarai ahankali maryam ta fito daga dakinta cikin sand’a take saukowa sakamakon yunwar da take ji dan tun abincin safe ne acikinta ko kallonta bai yi ba ta shiga kitchen ita kuwa tayi haka né dan tasan yanzu sai wani ikon allah tunda mai shiga tsakaninsu bata nan bata ki bin umarnin mami ba kullum tana iyakar qoqarinta na kiransa kmr yadda mami tace wani lokacin ya dauka ya danqara mata bakar magana wani lokacin kum bazai dauka ba ahaka har suka zo qarshen wata .”
******
Alhamdulillah DG m malik ya fara samun lafiya sai dai baya iya magana sosai idan baka matso da kunnenka kusa da bakinsa ba bazakaji abinda yake fad’a ba ,haka zalika sansar jikinsa ba koina yake iya sarrafawa ba yana kwance yayi wa matarsa alamar ta d’auko wayarsa ,byn ta dauko ta tsaya kusa dashi kamar yadda ta saba, ganin magana zai yi ta rankwafo daidai bakinsa anatse ya fara magana sunan wanda ya ambata da abinda yake son tayi masa ne yasa ta soma rubuta text message ta turawa ATA sakon ya samu ata alokacin da yake zaune a a gurin shakawata a gidansa tare da yaronsa V.O ahmed ya d'auki wayarsa ya soma karanta sako Kamar haka "Assalam, mai gida yaushe zaka shigo saboda ina da magana da kai . ATA ya ajiye wayar cikin jin haushi yana kallon Ahmed "M Malik na yi maka uzuri saboda tunaninka ya canza idan ba hk ba zakayi magana dani me yasa bazaka fad'a min ba ko ta hanyar text message ne tunda zaka iya rubutu ya qarasa mgnr tare da yin shiru "ranka ya dade wannan gsky ne DG m malik yana cikin wani hali sai dai addua kawai "to allah ya bashi lafiya amman ni ko zan shiga wannan kasar ba yanzu ba watakilla ma har su dawo qasar nan bazan samu damar shiga ba ya juya ya kalli Musa. "musa Kai !"musa ya qaraso da sauri ya iso gaban ATA cike da ladabi "dauki buhunhuna nan na Ahmed ka kai masa bayan motarsa "to yalla'bai!ya juya da sauri suka cigaba da tautaunawa ."
"Gaskiya kema maryam da laifinki, taya zaayi ace har wata shida cikin na bakwai da yin aure amma ki kasa shawo kan mijinki ku zauna lafiya bare har wani abu ya shiga tsakaninku maryam ta girgiza kai tana cewa “ya kusanceni sau d’aya bayan nan ne dai har yanzu shiru gashi nayi duk abinda zanyi dan mu zauna lafiya dashi amman yaki bani lokacinsa "ki bude masa aiki kawai ko zama ko rabuwa maryam tayi saurin zaro ido tana cewa "kai ni’ima bazan iya ba gskiya ai sai ma ya kasheni da duka ."ni’ima diyar yayar mahaifiyar maryam ce da suke ciki daya aikin soja né ya kawota lagos daga zuru “duka ?”Ke kuma sai ki tsaya ?”idan dai zai huce idan ya dakeni sai na tsaya mana "to dama fa an fada min bakya son laifin mijinki,kowa yaga wannan abun yasan mijinki baya sonki kuma bakya gabansa amman ke har wani side dinsa kikeyi maryam ta zauna a kujera a sanyaye ko da yake " illar wani auren zumuncin kenan “wallahi ni’ima ba side dinsa nake ba kawai soyayyarsa ce tayi min yawa shiyasa nake hakurin zama dashi dan ko na bar gidan nan gangar jikina ne ya bar gidansa amman ruhina yana gidan nan “.
“Ai kuwa kina da aiki ta yaya ma kike bashi kulawa muji idan akwai inda kuskure yake ki gyara ?babu abinda banayi masa na kyautatawa duk ta zayyane mata amma duk a banza ko kallona fa baya son yi “amman maryam kuma bakya tunanin ko wata ce take dauke masa hankali a waje ? maryam ta girgiza mata kai tana cewa “bana tunanin haka! dan miskilancinsa bazai bari ya kula mata ba abinda na fahimta kawai shine, yaya Adam yana son wata yarinyar mafarkinsa amman azahiri bai san meye so ba "ta yaya zaace mutum kamar wannan bai san meye so azahiri ba ?"To in ma dai ya sani banga hakan a zahiri ba sai a mafarkinsa ya sani , amma ina fatan wata rana ya dandani radadin so irin wanda nake dandana a zahiri ko hakan zai sa ya tausaya mini ya bani kulawar data dace. " ina zai dandana tunda kince bai san meye so a zahiri ba ?ni’ima ta fad'a sannan ta soma cin abincin da maryam ta kawo mata maryam tayi shiru dan itama bata san mai zata sake cewa ba .”
ATA V.O d Ahmed duk suna inda suke zaune Ahmed ya russuna cikin fara'a yace “nagode sosai sir ! Allah ya kara arziki yasa kafi haka.ATA bai ce uffan ba tunin musa ya soma daukar buhuhunan ya nufi bayan motar ahmed ,atare ahmed da ata suka mike suka biyo bayan musa ahmed ya shiga motarsa , masu gadi suka bude masa get ya fita.ATA ya kalli kofar fitowa daga falo a tunaninsa zai iske mrym a wajen tunda tasan fita zasuyi yau ya kalli agogon hannunsa ya d'an ja tsaki. “me wannan yarinyar ta tsaya yi ne tana bata min lokaci ? ya sake jan tsaki yasa hannu a ajihu ya ciro wayar sa ya soma kokarin kiran layinta ya saka a speaker ,wayar maryam dake ajiye a kujera ta soma ringing.ni'ima dake cin abinci da maryam wadda ke zaune a kujerar dake fuskantarta suka juyo suka kalli wayar ,maryam ta mike ta karasa ta dauki wayar ta duba sannan ta kalli ni'ima cikin alamun tsoro "mijinki ne ko? maryam ta gyada mata kai alamun"eh " Kar ki dauka, kyale shi ya karaci kira har ya gaji cikin tsoro maryam tace "saboda me?”wallahi Ina mugu mugun jin tsoron fad'ansa ke bai ma ta'ba kirana ba sai yau fa yau din ma nasan dan fitar da zamuyi ne “ tana rufe bakinta kiran ya katse cikin jin haushi tace"wai ke baki da 'yanci ne? bai ga kinyi bakuwa bane da zai dameki ? wallahi Ki rage jin tsoronsa haka ,idan ba haha ba bazaki ta'ba yin martaba a idanunsa ba "haba ni'ima ya kike irin wannan maganar bakiji nace miki fita zamuyi ba ? gidan mami zamu kuma Ko babu aure a tsakanina da yaya Adam, dan uwa nane fa!"To sai me...?ta fad'a adaidai lokacin da ATA ya shigo falon fuskar shi a daure yana kallon maryam a kaskance "bakya ji ina kiran wayar ki ne .”?
Adai cigaba da bibiya
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kuɗi ne mai buƙatar karantashi bayan na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number ɗin 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan Number 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntuɓii chaneel ɗina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 21
Shiru maryam tayi tamkar ba da ita yake magana ba, sai dai ta tsura masa idanunta yayinda acikin zuciyarta tsoro ne daskare muryarsa a tsarƙe ya cigaba da magana. “fito mu tafi karki ɓata min lokaci” jarumta ta aro ta sanyawa jikinta tana faɗin. “kayi haƙuri kafin nayi picking ne kiran ya katse kuma kaga ai nayi baƙuwa bai kamata na tafi in barta ba” ATA ya kalli Ni'ima dake zaune a wulaƙance sannan ya kalli maryam. “Ke ban son iskanci ni zaki faɗawa kinyi baƙuwa ?ina ruwana da ita?” yayi maganar a tsawace wanda yasa hantar cikinta kaɗawa nan da nan tsoro da matsanancin firgici ya bayyana a gbdy ilahirin jikinta. “darajan sweetheart kikaci if tace nazo mata dake kema Kinsan har abada bazan taɓa haɗa tafiyata dake ba” yana gama faɗar haka ya juya da sauri ya fita daga parlour'n . “maryam ta dubi Ni'ima cikin tsananin damuwa tace . “Kinga abinda nake gudu ko? gashi har yayi fushin nashi zuciyarsa iya wuya ne kamar jira yake ya hau zubama mutun faɗa” Ni'ima ta miƙe tsaye tanabin ƙofar daya fita da kallo sannan ta kalleta cikin fushi. “wallahi maryam wannan mijin naki bai ɗaukeki da daraja ba, hatta komai ma dake cikin gidan mai amfani da mara amfani ya fiki muhimmanci agurinsa” maryam tayi shuru kawai tana kallon Ni'ima da sauraronta “wannan auren zumuncin da akayi muku gsky ke aka cuta”
Maryam ta karkata kai tana cigaba da kallon Ni'ima “haka kike gani?ai kinfi kowa sani wannan maimaci ne nayi miki amman kinsan ke aka cuta” “nifa ba cuceni ba ni'ima dan ina son yaya adam tun asali in takaice miki tun kafin mahaifiyarsa tayi tunanin haɗamu dan gsky da ban samesa ba da haƙurina zai gaza domin kuwa ciwon zuciya ne zai kamani”
“ke da Allah rabani da maganar wata shegiyar soyayya uwarsa tasan duk wannan cin kashin
da yake miki?” “tasan komai kuma tana iyakacin ƙoƙarinta, bata son duk wani abinda zai ɗaga min hankali duk abinda yayi muddin zata gani ko taji labari sai inda ƙarfinta ya ƙare” “dai-dai kenan idan ya ɗaga miki hankali ki dinga kirata ki ɗaga mata hankali, idan kuma tsoronsa ya hanaki aikatawa sai ki zauna da baƙin ciki” Ni'ima ta soma yafa gyalenta tana kallonta “zo mu jera sai mu rabu a titi” maryam ta gyara zaman mayafinta ta ɗauki wayarta tare da sakala hand bag suka nufi kofar fita daga parlour'n .
Mai gadi ya buɗe tafkeken get ɗin gidan motocin ATA suka nufo kofar a hankali zasu fita a dai-dai lokacin maryam da Ni'ima suka fito daga parlour suka ga motocinsa. “lah Ni'ima kinga bai tafi bama ashe, bari in tsaida shi basai naja mota ba kema ki shiga mu rage miki hanya” ta nufi motar da sauri tana ɗaga masa hannu “yaya Adam! Yaya Adam..!!” yana kallonta amman bai bada umarnin a tsaya ba motocin a guje suka fice daga gidan ."maryam ta tsaya tana kallon Ni'ima mai gadi ya rufe get din Ni'ima ta iso gaban maryam cikin fushi tana kallonta. “haba maryam! akan me zakiyi irin wannan zaman rashin darajar kamar wata baiwa?wallahi in baki ƙwaci ƴancinki ba ciwon zuciya ne zai kasheki a banza da wofi” cike da damuwa Maryam tace.“To ni yanzu ya zanyi? babu abinda ban masa ba tun daga Kan tsafta biyayya duk nayi kamar yadda na fad’a miki hatta taimako umma tasha aiko min akansa amman duk a banza ko kallon arziki ban ishesa ba” “na baki shawara?” da sauri maryam ta gyaɗa mata kai. “Kawo kunneki” maryam ta matso kusa daita sosai tayi mata raɗa a kunne nan take maryam ta girgiza kai “ke kan wannan mutumin fa baya jin komai gara kawai na cigaba da zama haka idan da rabon zai canza ina fatan haka .”
Tare suka jero inda motar maryam take a parking space ni’ima na cewa “ki samu lokaci ki shiga Zuru da kanki yarinyar wallahi sai yadda kikayi dashi duk wannan taurin kan sai kin nema kin rasa “akwai wata tukunya da umma tace zaa aiko min daga can , “eh nasan dashi ai zuwa wani sati zaa aiko zan sa a hado miki da wasu abubuwa ma ,”ta fad’a adaidai lokacin da suka shiga mota suka bar gidan niima na cigaba da magana “ai ina fad’a miki muddin kikayi masa amfani dashi zakiyi mamakin yadda zai rikice ai wallahi sam ya’yan zuru basu cancaci wulakanci a gidan miji ba mu dake juya maza son ranmu amman ace ke kin bigi a wulakance a gidan mini “wallahi ni’ima ni kaina abun na damuna kamar na tattara na bar gidan amman bazan iya ba darajan mami da kuma karfin soyayyarsa “masu aikin mami ne a sunkuye a gaban dinning suna jere food flask.
Mami ta fito daga kitchen Riƙe da tray me ɗauke da lemuka a hannunta ta nufo dinnig dasu.tabawa mai aikinta ta iso gabanta da sauri ta karɓa taje ta ajiye mami ta ɗauki air-frshner ta soma feshe falon sannan ta ɗan tsaya alamun sauraro, ta juyo ta kalli tabawa mai aikinta tabawa ta juyo ta kalleta sanda take ƙara gyara zaman kujerun. “Tabawa!” “Na'am mami” “naji tsayuwar mota ina zaton adamcy ne suka iso , hanzarta ki bawa sauran masu aiki umarni su ƙarasa gyara wajen su bar nan tun kafin ya ƙaraso”
ATA ya shigo cikin parlour'n da sallama mami ta amsa da “Amin wa'alaikas salam” ATA ya iso gaban mami ya rusuna yana gaisheta “sweetheart barka da rana” cikin sakin fuska mami tace. “barka da zuwa adamcy Nah ɗan albarka ya gida ya kuma ƙarfin jikin?” “Alhamdulillah” Mami tace. “ka ganmu muna ta shirin tarbanku kamar wasu baƙi ko?” ya miƙe yana kallon ɓangaren dining sannan ya zauna.
Yana cewa. “sweetheart da kanki kikayi komai?” “Ƙwarai kuwa, ni da tabawa muka shirya muku abinci sai sauran masu aiki da suka taimaka ” ATA yayi shiru kawai suna cikin magana suka jiyo sallamar zabiba ta karaɗe falon mami ta ɗago ta kalleta tana cewa. “Zabiba har kin ƙaraso?” Zabiba tace. “Eh mami na ƙaraso suma suna hanya yanzu muka gama waya dasu ina yini?” “lafiya lau zabiba ya yaran suke?” “suna lafiya suna gida tare da babansu khaira ce ta maƙale wai lallai sai ta biyoni taga hajiya mami nace ban zuwa daita tazo takurawa rayuwata” “ai wannan takwarartawa sai ahankali last time da kuka zo ta dameni da aunty girl”. mami ta faɗa cike da farinciki tana murmushi .”
muryar zabiba cike da tsoro tace. “yaya ina yini?” bai ce mata komai ba dan tunda ta shigo ya maida fuskarsa wani ɓangare. Mami tace. “adamcy ana gaisheka” a taƙaice yace. “Lafiya” ahankali ta samu waje kusa dashi ta zauna “yaya Adam!” yana jinta yayi mata banza ahankali tace. “please yaya kayi hakuri ka yafe mana wallahi bazamu sake ba” tsaki yaja yace. “ai daman haka kukeyi idan kuka ɓatawa mutun rai kuyita nacin ban haƙuri kamar bazaku sake ba amman da zaran mutun ya haƙura ƙoƙarin aikata wani kuke yi dan haka gara ku riƙe haƙurinku dan ni tuni na cireku a rayuwata” nan da nan zabiba ta shiga aikin nan wato bashi hakuri da kuka amman ko ajikinsa girgiza kafarsa ɗaya kawai yake zabiba kuwa kuka take kamar ranta zai fita ahaka sauran ƴan'uwanta suka shigo suka isketa gabaɗayasu suka sakashi a tsakiyarsu suna masa magana amma ko motsa laɓɓansa bai yi ba. “ku rabu dashi Ke kuma zabiba ki daina asarar hawayenki kuna zaune zai huce” cewar Mami dogon numfashi ya sauke yana taɓe baki.aransa yace “ai kuwa zan baku mamaki .”
Nana hauwa'u tace. “mami ina auntynmu take?” nan da nan mami ta kallesa sai lokacin kanta ya kawo wuta “Ina Maryam ɗin da nace kazo min daita Ko tana cikin mota ne?” ATA ya ɗan sosa ƙeya “na barota a gida a cewarta tayi baƙuwa” da mamaki mami ta tsura masa ido “ka barota a gida adamcy acewarta tayi baƙuwa kuma?”eh !haka tace idan ta gama zata taho don bazan iya zaman jiranta ba, kuma wallahi sweetheart kiyi ma yarinyar congret warning dan kwanakin nan wasu ƴan iska qawayenta take tara min a gida alhalin ni gidana ba dan ƴan iska na ginashi ba” cikin fushi mami tace. “adamcy kasan me kake faɗa kuwa? Ƴar tawa da take aurenka zaka cewa Ƴar iska tana tara ƴan iska ?” “ai sweetheart wannan yarinyar ta wuce ƴar iska a gaban ita wanna Ƴar iska ƙawartata take ce min wa..” hannu mami ta ɗaga masa cikin fushi ta fara magana. “saurara! bana son jin komai daga bakinka, ka tashi yanzu ka koma gidan ka ɗaukota tun rai na bai gama ɓaci ba...” ATA ya gyara zamansa cikin damuwa yana kallonta kafin ahankali ya motsa laɓɓansa “haba sweetheart me yasa kike nuna mini wariyar launin fata a tsakanina da yarinyar nan ? Ni fa kika haifa ba ita ba” cikin fushi tace.“dan kana ɗan cikina sai in goyi bayan riƙon sakainar kashin da kake mata?” ATA yace. “To ai bata gama shiryawa bane tana hira da Ƴar iskar ƙawarta”
“Yanzu ka tashi ka koma gidan ka jirata har sai ta gama kimtsawa idan ma sai ta sallami ƙawarta ne ka jira sannan kuzo min tare yanda nace” mami bata kai ga rufe bakinta ba Ni'ima da maryam suka shigo cikin falon Ni'ima na riƙe da Maryam a kafaɗarta wanda goshinta yake a fashe yana ɗigar da jini, mayafinta da ɗankwalinta yana a hannun Ni'ima nana hauwa'u ce ta fara lura dasu ta soma salati tare da faɗin.“lnnalilahi wa'inna ilaihir raji'un!”jinj !
Nan mami da sauran ƴaƴanta suka juya da sauri suka kalli maryam “Subhanallahi!” mami ta furta a ruɗe tana kallon ATA “Adamcy kaga abinda ka janyo ko? don me ka barta a gida Kashe min ƴa zakayi?”Adamcy ya kalli mami a natse ya juya ya kalli inda maryam take gbɗy ya kasa magana juwa ne ya ɗibi maryam ta sulale ƙasa a sume, nana hauwa'u ta ƙarasa da gudu suka tallafo ta ita da Ni'ima
mami da ƴaƴanta suka nufi wajenta da sauri suna jijigata jikin mami na rawa tace. “ku kwantar da ita akan kujera shahida taimaka ki duba min ita” duk mami ta ruɗe shi kuwa gogan ko ajikinsa dan haka nan yaji ajikinsa suman ƙarya tayi.Mami banzo da kayan