Showing 153001 words to 156000 words out of 167047 words
Chapter 52 - Mar’adam’s Book 2 Hausa Novel Complete.txt
daina damuwa na yarda da qaddarata "aunty ta rungume maryam " yauwa princess ki kula da kanki kinji ,karki ji komai aunty in sha allahu zan kula miki da kaina ."
"Me zaki ce da rana ?kinga aunty ba sai kin wahalar da kanki ba wannan abincin da naci ma ya isheni har gobe aunty ta dan ware idanunta waje "a'a ki fad'a min kawai duk wahalarsa zan girka miki maryam tai murmushi bata ce uhm ba bare umh uhm sai ma ta daura kanta akan cinyar aunty yayinda ta saita idanunta akan takardun zanen jamaa dana kayan sawa a hankali tayi zurfi cikin tunanin makomar rayuwarta ta rasa komai ta rasa aikin yi duk inda ake bukata zanenta yanzu an daina nemanta ko tayi ta kai masu ma basanuna alamun ma yayi masu bare su karba dan mijin datasa mu ya tafi ya barta me kuma ya rage mata yanzu ?mutuwa !zuciyarta ta bata amsa da haka ta runtse idanunta gam saboda batason mahaifiyarta ta fahimci damuwarta aunty ta daura hannunta akanta hular kanta ya zame nan kwantaccen gashin kanta ya bayyana "princess dan Allah ki barwa allah komai kinji da sannu allah zai yaye mana komai numfashi ta sauke tana riko hannun aunty cikin nata "na gode sosai mamana allah ya tabbatar mana da alkhairi ."
Zaune suke a babban parlour'n hajiya zulaihert baba babba da babba qarami da uncle jay sai fahad gabansu kayan motsa baki ne aka kawo masu kowannensu cikin shiga ta alfarma acikinsu babu wanda bai taba abinda aka kawo masu sai baba qarami wanda yake cika yake batsewa sannan yake allah allah Adam ya sauko ."ahankali ATA Ke saukowa daga matattakala jikinsa sanye da kaya light blue kansa sanye da facing cap fari sol haka ma kafafuwansa wasu hadaddun silifas farare ne sanye dasu sai kamshi turaren REED ne Ke tashi ajikinsa a natse ya qarasa saukowa ya qaraso inda suke ya gaishesu gabadaya yana tsaye bai kai ga zama ba babba qarami ya zabura ya mike a matukar fusace ya soma magana "kai wani irin yaro ne ?"kawai kana son batawa yara kasuwanci dan kawai kayi certified din kanka ,dama ubanwa ka zauna kayi shawara ko kuwa kafanin naka ne kai kadai da zaka zarta da hukunci akaron kanka "?"akan ma wani dalili zaka qara farashin kaya ."
Ganin baba babba da uncle jay yasa bai dauki zafi ba ya kwantar da murya yace "nayi haka ne saboda ingancin kayanmu bawai da wata man.."karka fad'a min haka domin wannan maganar banza ce ai sai da yaya Ibrhim ya fad'a masa kar yayi haka amman yaki inji cewar fahaf " wani mugun kallo ATA ya daukesa dashi wanda yasa babu shiri yaja bakinsa yayi shiru "duk wasu yan kasuwa ku barsu suje wasu compaing su dauki kaya daga ingancinsu zasu rasa abokan kasuwancinsu ni nasan abinda nake ba yau na fara kasuwanci ba koma nace kasuwanci ajinina ya....."enough Adam karka wuce gona da iri yadda kake taimaka da kasuwanci muma itace silar zuwanmu duniya ba kuma zamu yarda ka batawa yayanmu kasuwancinsu dan muma munyi business sama da shekara talatin , so munsan kasuwanci dan haka bamu amince da wannan tsarin naka ba domin tsari ne da zai korewa kanfani kasuwa daga yanzu da nake maka wannan maganar ka janye kudirinka akai "wannan shine magana ta gasky baba abinda yaya Ibrahim yayita fama dashi kenan Faaha ya fada yana hura hanci abinda ma ya kamata da zai dauki wannan mataki ya zaunar daku gabadaya ya tautauna daku ba wai ya yanke hukunci a qaron kansa ba nan fa baba qarami ya dinga zuba ruwan bala'i ta inda yake shiga bata nan yake fita ba ,sauran yan'uwansa na bashi hakuri da kokarin kwantar da fushinsa dan bai iya fushi ba mutun ne mai tsananin zafin rai zuciya ".
"Ku daina bashi hakuri yayi duk abinda zai yi ".ATA ya fad'a a fusace sannan ya tsaida kwayar idanunshi akan baba qaramin "baka da wannan cikakken iko akan wannan kafanin magana ta karshe ka janye jikinka akan wannan kafanin ka maida idanunka akan wanda yake naka ne kai kadai "ni kake fadawa haka saboda baka da mutunci ?" Ata yayi shiru yana hura hanci tare da soke hannuwansa cikin ajihu "dan banza yaron kawai mai banza zuciya ni wallahi bansan inda uwarka tasamoka ba dan ubanka bashi da mugun hali da mugunta ,yaro kamar sheidan idan anyi nan yayi can dan iskan yaro kawai wallahi maza maza ka tattara ka kama gabanka kabar masu kamfani su cigaba da kula dashi ka tsaya iya mallakinka dan kai ne zaka hakura ka bar mana ."
shiru ata yayi yana kallon baba qarami zuciyarsa na tuttukin bakinciki wani irin tsanarsa yaji ya darsu acikin zuciyarsa ransa idan yayi dubu ya baci wallahi yaci darajan babba babba dake zaune da girman mahaifinsa da kuma uncle jay da yau ya gane kurensa domin kuwa da ya nuna masa ya zarta dan iskan daya kirasa dashi cike da fushin zuciya ya juya zai wuce baba babba ya kira sunansa "Adam ..!
Cak ya tsaya sakamakon jin sautin muryar baba babba "dawo nan Adam a gama magana gabadaya ya juyo a sukwane fuskar nan tashi ta sake rikicewa ta hade kwata kwata babu wani alamun annuri "me zance tunda ya zarta da hukuncin da yake so kuma ga dukkanin alamun yayi maku daidai ,"baba qarami ya kallesa ya watsar"ba haka bane adam !" baba babba ya fad'a tare da mikewa tsaye yayi taku zuwa inda yake tare da yin kasa da muryarsa "kafi karfin duk wannan adam ka janye hannunka tunda sun kasa fahimtar dalili dayasa kayi haka "kenan ka yarda da tsarinsu ?yes saboda zaman lafiya ne domin bazasu ta'ba fahimtarka ba idan ma da hali ka cire hannunka gbdy dan bana son na rasaka ,rayuwarka nada matukar amfani a gareni ."ata bai sake cewa komai ba ya juya a matukar fusace ya haye sama yana taka step cikin sauri sauri."
Mmn sudai
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 29
Zuciyar ATA cunkushe da haushi tare da takaicin baba qarami ya tura kofar parlour'nsa ya shiga yana shiga kai tsaye bedroom dinsa ya shige ya rike kugunsa da hannu d'aya yayinda yasa d'ayan hannunsa ya dafe goshinsa da yaji yana masa wani irin mugun sara sakamakon'bacin ran daya shigo dashi ,babu abinda yake gani sai fuskar baba qarami ita ke masa gizo cikin tsananin 'bacin rai saurin runtse idanuwansa yayi yana mai sake jin bakincikinsa na nunkuwa wani irin zafi da suya zuciyarsa keyi,duk da ya murje idanunshi ya fad'a magana son ransa amman hakan bai masa ba yaso ya zage kunjinsa ne ya zabga masa rashin mutuncin da har ya mutu bazai manta dashi ba .kusan mintuna shabiyar yana tsaye yana zariya acikin d'akin tamkar wanda yayiwa sarki karya ."a can parlour'n kuwa baba babba ne a gaban baba qarami , bai damu da cewar shine babba ba ya kwantar da kai cike da tausasawa yake masa magana "dan girman allah baba qarami kayi hakuri karkayi fushi da adamu tunda ka rigada kasan halinsa kuma ... "ba maganar hakuri bane yayi saurin dakatar dashi ta hanyar fad'ar haka "kawai kasashi yayi abinda ya dace shine zaman lafiyar kowa idan ba haka ba zaayi wacce za'ayi "in sha allahu zai yi biyayya a gareka "dole ya sauke ra'ayinsa yabi naka domin kai uba ne agaresa "wannan haka ne dole yabi umarninsa "inji cewar uncle jay "kayi hakuri da duk ma abinda adamu yayi maka d'anka ne babu yadda zakayi dashi sai ma fatan alkhairi daka masa arayuwarsa .""baba qarami ya katse uncle jay ta hanyar d'aga masa hannu "dakata jamilu ya isa haka karka cika ni da surutu "adamu ba d'ana bane kune dai kuka d'aukesa amatsayin d'a dan d'an cikina bazai ta'ba maida min magana ba kamar yadda yayi a yanzu a gabanku adamu yasan ubansa ni kuma nasan ya'yan dana haifa ,sai abu na qarshe wallahi wallahi kunji na rantse ku gaya ma wannan gantalallen d'an naku ya kiyayaeni kar ya kuma yin gigin shiga hurumina dana ya'yana yayi lamarinsa muyi namu yayi na farko yayi na biyu kar yayi kuskuren aikata na uku domin idan yayi na uku bazai ji dadina ba "baba babba yace "shikenan in sha allahu bazai sake ba "baba qarami yace "da dai ya fiyye masa dan wallahi idan ya kuma yunkurin shuka min rashin mutunci ba wannan mgnr zaayi ba dan zan shuka masa wanda yafi nasa ."
" da kyar uncle jay da baba babba suka rarrashesa suka samu ya d'an sauko sai dai duk da haka ya fita yana zage zage tare da tsinewa ata din wanda shine abinda yafi komai konawa mami rai dan har sai data ta zubar da hawaye dan bakinciki ."
Ahankali baba babba ya numfasa ya cewa uncle jay " tashi muje mu samu adamu shima mu kwantar masa da hankali dan a samu komai ya wuce atare suka mike suka haura saman d'akinsa alokacin ata ya samu waje ya zauna a gafen gadonsa ya had'e fuska tamkar hadari duk wanda ya kalli fuskarsa alokacin sai tsoro da firgici ya kamashi ,suka tsaya a gabansa suna kallonsa na tsawon lokaci kafin su fara magana .ahankali baba babba ya fara da nasiha mai ratsa zuciya da shiga jiki akan yayi hakuri da yan' uwansa "shiyasa a kullum yake qara ganin kimar dattinjon domin dattijo ne da yasan yakamata bayan baba babba yayi shiru shima uncle jay ya soma nashi "kayi hakuri ata hakika mun san komai mun san kamfani na mahaifinka ne alfarma kawai yayi wa yan'uwa alokacin da yake raye hasalima babu wanda yasan cewar nashi ne sai mu shakikansa dan tun kafin rusuwarsa kamar yadda kasani ya fitarwa kowa da hakinsa amman kasan halin kawunka sam baya kyautawa kanshi kuma baa isa a fad'a masa gaskiya yaji ba duk da yasan gskyr aka fad'a masa kai dai abinda nake so da kai ka cigaba da hakuri dashi, kasa aranka duk abinda ya aikata agareka tamkar mahaifinka ne yayi maka ,kayi hakuri ka zauna lafiya da kowa wannan shine muradinmu da kuma kwanciyar hankalinmu dana mahaifinyarka" jiki a sanyaye ata yace "naji kuma a gode sosai da kulawarku "Allah yayi maka albarka sukai masa sallama suka fice daga gidan gabdaya."
Bayan fitarsu da kamar mintuna talatin sai ga mami ta shigo inda ta iskeshi a zaune a parlour'n akan one siter hannusa rike da waya yana daddanawa a yadda yake operating din wayarsa zaka d'auka kwata kwata baya tattare da wata damuwa ne ballanatana wani abu makamancin matsala amman ala hakikanin gaksy kallo daya zaka masa ka fahimci yana tattare da zallar damuwa masu tarin yawa cike da tausayawa mami take kallonsa .
ahankali ata ya d'ago tsumammun idanunshi da suka gama canza kala tsabar tashin hankali da yake ciki ya tsurawa mahaifiyarsa ido yana kallonta cike tsananin qauna ,waje ta samu ta zauna a gefensa murya a raunane ta kira sunansa"adamcy !gabadaya ya juyo bangaren da take zaune ya natsu sosai domin yaji abinda zata fad'a itama dan ya rigada yasan taji komai daya faru kawai fitowarce taki yi shima yasan dan gudun abinda zai biyo baya ne yanzu ma yasan fad'a ne da nasiha ya shigo daita "yayi maka kyau adamcy da duk abinda ka janyowa kanka ."shiru yayi kawai yana sauraranta kafin ahankali ya runtse idanunshi ya kasa cewa komai ,mami ta cigaba da magana "wallahi adamcy ka rage wannnan zafin zuciyar karta jawo na rasaka . ina umartaka ka janye hannunka bazan so wani mummunar abu ya sameka ba domin duk abinda ya sameka ya sameni dan sai yafi min ciwo akanka bazaka san yadda iyaye suke ji akan ya'yansu ba sai randa ka mallaki naka wallahi bana son nayi kukan rashinka dan allah ka hakura ."
"yanzu sweetheart kina ganin akwai abinda zasu iya min ?ya fad'a ransa a 'bace ta gyada masa kai alamun "eh !"kinyi imani da allah sweetheart ?"sosai kuwa nayi imani da allah "to kisa aranki babu abinda zasu iya min ni ban ma yarda akwai wani dan Adam din da zai iya cutar da wani ba fashe da izinin allah ya qaras maganar yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa "tabbas nasan da haka amman dai fita hanyarsu "shiru yayi mata "kenan bazakayi abinda nace ba ?tayi maganar cikin zafin rai "wallahi da ana canza mutun adamcy da tunin na dade da canzaka kowa ya huta acikin danginka dan kwata kwata baka da kirki "ata dake zaune yayi shiru tare da cigaba da duban mami batare da yace mata komai ba dan ya ma rasa abinda zai ce mata ne yasashi yin shirun
sai dai cikin zafin rai ya kamo lips dinsa na kasa ya soma cizawa da karfi "ina sake umartarka da ka sausauta komai idan ba haka ba zaka ruguza gida d'ayan da amafinka ya had'a "
" kada kayi Kuskuren ruguza ahli dangin mahaifinka adamcy domin cikar muradinka idan ka aikata haka mahaifinka bazai ji dadi ba dan girman allah ka bar ruhinsa ya samu salama "ta qarasa maganar muryarta na rawa alamun tana son yin kuka "sweetheart zaki fara ko ?ya fad'a yana riko tafukan hannunta cikin nashi "kai din ne adamcy baka da kirki wallahi ban san wani irin zuciya gareka ba sam sam baka da tausayi "sweetheart ba haka bane kema kinsan adamcy dinki na iyakar kokarinsa akan ahlin mahaifinsa yana yin komai dan jin dadinsu ne ,babu abinda bana masu suna jin dadi ta koina tare da qoqarin sanyasu farinciki burina mu amafana da wannan kamafanin gabdayanmu nayi qarin kudi ne domin suji dadi ba dan mugunta ko dan jin dadina ba amman sweetheart ki duba kiga abinda baba qarami yayi ,wallahi banyi haka dan zalinci ko son rai ba kayanmu suna da ingancin da ko nawa muka saka farashinsu zaa siya idan baa siya ba wallahi tabbas zaa dawo daga baya saboda ingancinsu ."ya qarasa maganar zuciyarsa cike da rauni ."
jikin mami yayi mugu mugun sanyi da gane da jin abinda ya fad'a ta matso sosai kusa dashi tare da d'aura hannuwanta duka ta riko fuskarsa dashi tana kallonsa wani irin matsanancin tausayi ne mai tattare da qaunar d'an nata taji ya sake nunkuwa acikin zuciyarta yayinda taji kuka from no where ya kufce mata, kawai ta rungumesa ajikinta tana wani irin kuka mai ban tausayi "wallahi nasani adamcy duk abinda zakayi akan agc babu mugunta acikinsa amman bana jin dadin furuncin babanka akanka haka zalika bana jin dadin yadda kake masa ko babu komai uba ne agareka kanin mahaifi ne albarkarsa albarka mahaifinka ne haka zalika tsinuwarsa tsinuwar mahaifinka ce ,ina neman alfarma agareka ,na rokeka dan allah kada ka sake fad'a masa bakar magna akan komai shi din ubanka ne halak malak duk duniya baka da kamrsa ka cigaba da hakuri da yanayinsa haka halinsa yake tmkr naka duk da dai yace bai san inda na samoka ba bayan ya manta cewar duk wannna halin naka shi ka d'auko amman in sha allahu zaka canza ,zaka canza da izinin Allah,allah yayi maka albarka ina maka addua allah ya baka abinda kake so duniya da lahira wannan yarinyar mafarkinka da kake so ina maka addua Allah yasa gaskiya ce.
wani irin yanayi ya tsinci kanshi ciki mai wuyar misaltuwa wanda bai ta'ba jin irinsa ba babu alokaci d'aya zuciyarsa ta tsunduma cikin tunanin princess dinsa nan da nan kuma yarinyar data zanashi ta fad'o masa tun daga ranar farko daya soma ganinta har zuwa had'uwarsu a ogun, shiru yayi zaune tare da rungume hannuwansa duka a qirjinsa yana tunaninta, muryarta sak irin muryar yarinyar da yake mafarki, yaso kwarai yaga fuskarta a wancan ranar sai dai cewar ita din matar aure ce yasa ya hakura amman wasu wurare ajikinta duk irin na princess dinsa ne hatta yatsun hannunta irin na princess ne haka ma yatsun kafafunta kawai fuskarta ce ta rage masa ya gani ya tabbatar da ko ita ce. oh my godness god ! allah karka sa yarinyar nan tazo min amatsayin matar aure dan ban san yadda zanyi da rayuwata ba"kayi shiru ." bai motsa ba dan bai ji abinda ta fad'a ba "ka daina zurfafa tunani ni dai a kullum ina maka adduar idan mutunce kuma alkhairi ce arayuwarka Allah ya gaugauta had'aku idan ba gaskiya bace Allah ya kawar maka da tunaninta ka huta "
Agogon tsarka hannuta daya zamo hannusa lokacin daya matso kusa daita yana shafa zanen lallen hannunta tayi baya da sauri sauran kadan ta kai kasa yayi sauri riko tsintsiyar hannuta sosai alokacin suke kallon juna ido cikin ido suke kallon cikin kwayar idanun juna nan ma sai da yayi kokarin bude nikaf din tayi saurin kawar da fuskarta ."ahankali ya mike tsaye ya shiga bedroom dinsa ya d'auko agogon tsarka ya fito ya tsaya yana qarewa agogon tsarkan kallo mai cike tsananin sheki yana jin kamar suna tare daita ne a lokacin a hankali ya shiga kai kawo acikin dakin yana cikin wannan halin mami ta mike ganin kamar ma ya manta da zamanta acikin parlour'n "Adamcy ta kira sunansa ya dan gigice ya waigo yana dubanta "meye damuwarka ?daga magana ka fita haiyacinka "ya girgiza mata kai alamun babu komai "ta sauke numfashi tace "ya babu komai daga magana ka shiga tunani daga tunani ka bazama ka d'auko agogo kana kallo agogon waye kamar na mata ?"bai ce mata uffan ba illa ya samu waje akan three siter ya kwanta tare da lumshe tsumammun idanunshi "ka fad'a min agogon wacece a hannunka ?kwanciya sosai yayi ya mike akan kujera batare daya bata