Showing 120001 words to 123000 words out of 167047 words

Chapter 41 - Mar’adam’s Book 2 Hausa Novel Complete.txt

na rawa sosai ga kuma zafin coffee da yake ratsa illahirin fatar jikinta  wanda har cikin naman jikinta take jin zafin, babu shiri ta bar masa ɗaki zuwa nata tana zubar da hawaye .”


ranar Maryam bata runtsa ba kuma tayi dauriya domin dai bata kira kowa acikin ahlinsa ba  washe gari kuwa tun da  asuba tabi mota zuwa abuja taso shiga jirgi amma saboda bata da kuɗin jirgi kamar  ta tambayi mami  kuɗin ticket amma tasan hakan zai sa ta gane akwai matsala shiyasa ta shiga motar haya
Tunda suka ɗau hanya  kanta na kife ,rufe ido tayi sosai tana zubar da hawaye masu zafi sannan acikin ranta tana ƙissima yanda zata hana rayuwar adam samun kwanciyar hankali  yadda bata ji dadi agidansa ba bazata bari Ya kawo wata yaji dadin rayuwarsa daita yadda gallazawa rayuwarta wallahi tayi alqawarin sai ya gallazawa duk wacce ta rabesa zatayi komai akan yanke masa duk wani jin dadin rayuwa .” ɓangaren ATA shima tana barin gidan ya bar ƙasar zuwa hollond .”



Mmn sudais

💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗


*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan  littafin  na kudi ne mai bukatar karantashi   byn na kammalashi zai  biya 1000 ta wannan  account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura  domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina  (Hausa bakwai ) a YouTube.


Page 22

Kwanaki hamsin kenan da ATA yasa anemo masa kwararrun masu zane wanda yayi daidai da sauran sati uku daurin auren maryama da yaya sadam acikin lokacin nan babu abinda maryama take sai zariyar zuwa AGC domin gabatar da zanenta, haka zalika ta saki jikinta sosai da yaya sadam domin ta fara cire rashin son da bata masa tana ta qoqarin dasa soyayyarsa mai karfi acikin zuciyarta ,shima kuma bangarensa yana qoqarin kyautata mata shiyasa a yanzu damuwarta ad’auketa aiki akar ka shin AGC ne .” idan kaga maryama da yaya sadam a yanzu zaka d’auka tun asali masoya ne wadan da suka d’auki tsawon lokaci suna son juna, abu d’aya ne kawai dai har yanzu yake damun zuciyar maryama shine yawon shiru da shiga tunani mai zurfi da yaya sadam din yake ko suna tare ko yana shi kad’ai ko ayita kiransa a waya baya d’auka agabanta wanda ita hakan na damunta, kuma haka nan take ji ajikinta kamar akwai wani abu dake damunsa wanda yake boye mata , tayi iyakar qoqarinta tasan meye damuwarsa amman abun ya cutura domin dai abu d’aya ne kullum yake fad’a mata babu komai al’amuran aiki ne .”



mami na zaune a had’ad’den parlour’nta na farko idanunta na kallon tv yayinda hannunta Ke rike da casbaha tana ja ahankali kira ya shigo wayarta, tasa hannu ta d’auki wayarta tana dubawa sunan d’anuwanta data gani yana yawo a screen din wayar ne yasa tayi saurin kara wayar a kunneta bakinta d’auke da sallama “wani irin mikewa mami tayi jikinta na rawa tare da furta kalma “inna lillahi wa inna ilaihi rajiun ,ya hayyu ya qayyum bi rahmatika astagisu aslili shaani kulluhu wala takilni ila nafsin d’urfata’ai “kace yau kwana biyu kenan da faruwar sakin ?ta tambayesa cikin tsananin damuwa da shiga tashin hankali “yayinda cikin tsananin fushi d’an uwanta ya cigaba da sheida mata abinda ya faru .”“wallahi Abdul ban san komai akan sakin nan ba”
ta fad’a jikinta na wani irin ‘bari haka ma zuciyarta
bayan ya katse kiran kuka mami tasa tare da jin wani kullin bakinciki ya tsaya mata a qirji yaki gaba yaki baya wayarta ta lalubo ta soma neman layukansa amman shiru bata shiga dan haka ta kira Amar nan ta samu labarin tafiya yayi zuwa hollond abun yayi mata ciwo fiyye da tunanin mai karatu ammar din ma yana tambayarta ko tana son wani abu amman tuni ta katse kiran .”



batayi sanya a gwiwa ba ta kira ya’yanta a waya ai kuwa washegari gabdayansu suka hallara a gidan cikin tsananin tashin hankali aiko mami tasa masu kuka tana kiran “adamcy zai kasheni shikenan ya zama sila shiga tsakanina da d’anuwana muna zamanmu gwanin sha’awa, kana ganinmu kasan akwai shakuwa da soyayya a tskaninmu, muna ta qoqarin had’a kanmu dana ahlimu, mun rungume juna babu kyarma muna tsananin son juna amman yau sanadiyar adamcy ran d’anuwana ya sosu yayi min abinda bai ta’ba min ba .Abdul ra’uf bai ta’ba min magana cikin fushi ko ‘bacin rai ba sai a jiya “ni zulai na shiga uku nah me yasa na had’a auren nan ?”wallahi dana san abinda zai biyo baya kenan da ban had’a ba dana bar adamcy ya cigaba da rayuwarsa haka babu aure dan duk abinda zai lalata zumuncina da yan’uwana bana qaunarsa”.”


“kiyi hakuri mami ki daina kuka haka Allah ya qaddara kowani bawa da kalar qaddararsa wannna rabon dake tsakaninsu fa idan baa yi auren ba ta ina zaa samu ?inji cewar aunty shahida ,”kuka fa ya zamammin dole abdul’rauf na min biyayya duk abinda nace shi yake yi bai ta’ba sa’bawa umarnina ba "wai mami zaginki yayi ne ko me ?zabiba ta tambayeta “ko d’aya zabiba abdul bazai ta’ba zagina ba amman yayi min magana cikin fushi abinda bai ta’ba min ba sai jiya” nifa na kasa gane abubuwan nan na yaya adam mutun kamar babu tausayi a cikin zuciyarsa gsky mami yakamata ki san yadda za'ayi da yaya ga ciki ga saki dame sister zataji wallahi ni tausayi take ba ya dawo daita kawai .”nana hauwa’u ta qarasa mgnr tana sheshekan kuka aunty shahida ta numfasa kana tace “karki d’aga hankalinki auta kinga kema bake kad’ai bace za'a haukatar dashi bari ya dawo daga hollond lafiya amman dan dolensa ya maidaita ta haihu a gidansa idan ba haka ba wallahi wannan karon zai had’u da tashin hankali da bai ta’ba gani ba “ku dai bi komai a hankali domin dai acikinku babu wanda bai san waye yaya adam ba kusan yafi buqatar rarrashi da lalama muddin da tashin hankali zakuje masa wallahi bazai maku abinda kuke so ba .”


“da mamaki aunty khadija ta kalleta “abinda muke so kuma ke banda ke ?”gsky banda ni abinda kuke so am sorry to say dani yanzu bazan sake goyawa zaman aurensu baya ba ,ya kamata zuwa yanzu abarsu haka kada a takura masa ku kyalesa ya huta idan yayi ra’ayin maidaita da kanshi zai yi idan kuma iyakar zamansu kenan Allah yasa ya zama alkhairi ,sun d’auki lokaci suna tautaunawa a tsakaninsu sai dai zabiba ta tsaya akan raayinta wanda bai yi masu ba har mami .”
Bayan kwana uku ahankali oga ATA yake saukowa daga cikin jirki tare da yaransa mutu biyu kai tsaye in da driver da masu tsaronsa ke jiranshi suka nufa, ya qara kyau aciki kwanaki uku kacal farinsa ya sake fitowa ga cigaba da ya samu da nasarori akan business ,yana sanye da royal blue three piece suit daya daga cikin yarasa na sak'ale da bak'ar jakarsa daka ganshi kaga wayayye wanda yasan duniya ko nace duniya ke damawa dashi, yayinda idan ka kalleshi zaka d'auka d'an shekara talatin da biyar ne amma gaskiyar lamari shekararsa arba'in da wani abu yake, da sauri aka bude masa gidan baya ya shiga ya kame yana shan kamshi daya daga cikin wayoyin ne ta soma ringin ya dauka ya soma magana a natse yana ciccin magani har suka qaraso unguwarsu waya yake bai ji komai ajikinsa ba sai da suka shiga cikin haraban estate dinsu yaji gabanshi ya fad'i sakamakon bai san abinda zai tarar ba amman a kudurtawa ransa komai zai faru sai dai ya faru amman har abada bazai qara zama da mrym ba".



ahankali ya fito daga cikin motar ya nufi babban falon cikin isa da iza ga kamshin daddan turarensa Reed na tashi ,yasa hannu ya tura kofar glass din parlour’n ya shiga ya iske mami zaune kamar koda yaushe yayi sallama aciki fuskarsa a had’e tamkar zaki , itama aciki ta amsa masa ya ta’be baki yadda ta amsa masa yaso ya bashi dry amman sai ya maze ya d’age girarsa duka tare da dakewa ya gaisheta “sweetheart barka da rana “wannan karon kam shiru tayi bata masa ba bai qara cewa komai ba kai tsaye samansa ya nufa mami ta karkace tabi bayansa da kallo yana taku d’ay d’ay batare da wata damuwa ko tashin hankali ba sai ma wani kyau da kwanciyar hankali daya samu matsuguni ajikinsa su kuma ya bar zuciyarsu da tashin hankali.duk wani tarba da rawar jiki da mami take akanshi idan ta gansa yau kam babu dan kana kallon fuskarta zaka fahimci akwai damuwa .”yadda mami bata masa maganar wata maryam ba shima bai yi mata maganar ba abun ma yayi masa dadi ya cigaba da tsabgogin gabansa da mulkinsa daya saba dan babu abinda ya canja har kawo yanzu dan ji yayi kamar an raba zuciyarsa da matsala ne dan da kullum zuciyarsa cikin tuttukin bakinciki da kunci take idan ya tuna zai koma gida ya ga fuskarta kuma amatsayin matarsa .”



mami dai bata gaji ba ta sake tara ya’yanta “har yanzu shiru adamcy bai ce min komai ba ga mrym da ciki har wata uku akace dame zataji saboda Allah ga ciki ga kuma gurb'ata mata raywua da yayi, gashi ya dawo yayi wa mutane shiru kamar bashi yayi sakin ba , ni na gaji wallahi nayi waya daita mrym din ta fad’a min abinda ya faru akayi sakin taki sai kuka take min ,shi kuma ya dawo ya min dif wallahi na kasa komai gashi bana son lokaci ya tafi batare data koma dakinta ba dan da zarar mrym ta haihu a gidansu shikenan abu ya sake dawowa baya bazai ta’ba maidaita ba mami ta fad'a tana kallon ya’yanta d’aya byn d’aya da suke zaune.aunty khadija tace "kwantar da hankalin ki mami zamu san abun yi bubuwa daya ne kawai ya tabbata a aurensu samun cikin mrym in sha allahu sauran ma zasu tabbata ne"Yaushe? Kusan shekaru ana abu d'aya ace har yanzu an kasa cimma komai babu wanda adam yake shaka daga mami har mu na gaba dashi kowa shakkarsa yake gsky zuwa yanzu dai ya kamata mu tashi tsaye .”inji cewar aunty shahida .”


kallonsu kawai mami take zuciyar na karye wa “zaku cimma daman amman dole sai kunyi hak'uri sannan ku bisa ahankali dan karku dinga mgn kuna manta waye shi b'angaren zafin kai da zuciya dole sai kun sha wahala kafin ku samu ku ya sauko ya saurareku ni wallahi dan tani da an bar kome nan kowa ya huta “wai meye haka zabiba?” sai ki dimga magana kina cire kanki acikinmu idan Kinsan bazaki goya wa mami baya ba me yasa kika zo ?Inji cewar aunty Khadijat “to yanzu me nayi kuma ?ai bazan ki zuwan kiran mahaifiyata ba haka zalika bazan goyi da bayan a sake tursasa wa yaya ba “haba Auty zabiba ya kike magana kamar babu tausayi a zuciyarki ?karki manta kema fa mace ce inji cewar nana hauwa’u “hk ne nima mace ce amman da zaku fahimceni ma gata nayi mata dan banga amfani aure da wulakanci ba shi yace bayayi ita tace tana yi ita Ke aure ko shi ?“dan allah yasa isa karki sake saka baki tashi ma ki wuce an sallameki nan da nan parlour’n ya hargitse sai da mami ta tsawatar masu sannan sukai shiru suna cika suna batsewa “wannan wani iri bala’i ne adamcy duk ya dagula min lissafi ya hadani da dan’uwana yanzu kuma zai raba min kan ya’ya .” a zuciyar zabiba tace “babu ruwan yaya duk kece kika dagula lissafin komai .”


Bayan kwana biyu wanda ya kasance weekend tun karfe tara suka hallara da niyyar ayita ta qare ahankali yake saukowa daga saman mattakala jikinsa sanye da farin yadi inda kafafunsa ke sanye da farin silifas , agogon rolex ke daure da tsintsiyar hannunsa ,idanunshi na manne da wani hadadden farin glass ,a hankali ya cigaba da takowa cikin isa da izza shi din wani ne a fadin nigeria ,yana saukowa sanyayen kamshin turarensa REED ya soma tashi kamshin turarensa ne ya kaiwa hancinsu sakon fitowarsa . gabad’ayasu suka dago idanuwansu a natse suka tsura masa suna kallonsa tamkar ranar suka soma ganinsa shi kuwa ko kallo su bai yi ba hasalima yi yayi kamar bai ga wasu halitta a wajen ba .kai tsaye dinning área ya nufa yana shan kamshi , har ya samu guri ya tsaya tare da soke hannunsa daya cikin aljihun wondonsa ,basu dauke kwayar idanunsu akanshi ba ,gabdayansu an rasa wanda zai fara masa magana shi ya kamata yayi gaisuwa amman yaki “aunty khadija ta zunguri aunty shahida ta kalleta “gashi ya fito ya kenan ?



“Da alamun abinci zai ci bari ya gama ya samu waje ya zauna ya had’a coffee ya fara sha yana lumshe idanu su kuwa sai faman satar kallonsa suke ba qaramin kyau yayi musu ba cikin shigar da yayi ko dan bai fiyye saka kayan hausa bane yasa yayi masa kyau haka yunwa yake ji sosai amman ya kasa zuba ma kanshi abinci dan haka ya ja dogon tsaki mami ta fito sanye da doguwar rigar atamfa itama tayi kyau sosai ga tsufa ga tarin damuwa amman dake jikinta mai kyau ne wallahi bazakace tana da diya mai shekara 49 a duniya ba dauke kallonsa tayi ta girgiza kai kawai sannan ta zauna acikin ya’yanta .
zabiba ce ta fahimci abinda yake buqata dan haka ta mike a natse ta qarasa inda yake “ina kwana yaya ?lafiya !ya fad’a aciki batare da bata lokaci ba tayi serving dinsa ta ajiye masa plet din abinci gabansa. a hankali ya dauki cup ya kai bakinsa ya kurbi tea yana lumshe sexy eyes dinsa yana sosa keyarsa .”



Ahankali aunty shahida da aunty khadija suka mike suka nufi inda yake hajiya zualai tabi su da kallo gabanta na wani irin faduwa nana hauwa’u ta riko tafin hannunta “mami ki kwantar da hankalinki kiyi addua cike da sanyin jiki take duban kyakkya wan fuskarsa ya hade fuskarsa sosai ta yadda idan ba jarumta kayi ba bazaka iya fuskantar sa ba “karki damu mami everything will be fine “Allah yasa auta allah ya sanyaya zuciyarsa dan mrym na bani tausayi ina jin duk nice silar shigarta cikin damuwar nan nana hauwa’u ta damke hanunta sosai cikin nata tana danne kukanta dan itama mrym na bata tausayi tun shekaranjiya da sukai waya bata qara daukar wayarta ba saboda qara mata damuwa take .”a tare suka zauna suna fuskantar shi tun daya gansu ya fahimci abinda Ke tafe dasu kusan minti shabiyar suna zaune yaki daina cin abinci yasa ahankali aunty shahida ta soma magana “adamcy me yasa ka saki maryam ?”laifin me tayi maka ka saketa alhalin ga mami a raye baka sanar daita ba ka yanke hukunci kai tsaye ?”.



“bani ya kamata ki tmya ba ita da tace an saketa me tayi ?kuje ku tmbyeta abinda tayi aka saketa “nan da nan ran aunty khadija ya baci “wannan wace irin maganar banza ce ?”ta fad’a a fusace “ai mun san daita muka zo tmbyrka mara mutunci kawai so kake ka kashe mana uwa ka barmu da asara dan tuni mun kula baka da buri sai na ganin kasa mahaifiyar mu cikin bakinciki,to wallahi kasani zamanka da marym dole ne dan shi kadai zai sanyaya ran kowa acikin gidannan ,wallahi sam baka ma mami adalci ba kai kadai gareta amman kullum cikin sakata hawaye kake, kamata yayi ka dinga share mata hawaye amman tun baka kai haka ba kake sakata cikin damuwa.jin haka yasa mami ta share hawayenta . ta inda take shiga bata nan take fita ba sai zazzaga masa ruwan bala’i take shi kansa yayi mamaki maganganunta amman yayi shiru yana sauroronta yana tsakurar abincin gabansa batare da ya furta komai ba “.



“To kasani idan ka saki maryam dan ka yar da kwallon mangaro ka huta da kuda kasani kayi aikin banza dan ciki ne daita na wata uku kaga kayi aikin banza duk kinka daita kun zama abu daya “What ?” ya furta da mugun karfi yana sakin spoon din hannunsa “eh !yanzu haka jininka na can a jininta yana yawo idanunshi ya tsura mata yana nazari kafin ahankali ya mike tsaye yana girgiza mata kai
dukkansu kallonsa sukeyi yadda jikinsa ke rawa kamar anjona masa shocking , nan da nan idansa yayi wani irin canzawa " impossible! waitt,hw can dis even b possible ?tana dauke da cikina na wata uku alhalin ni duka wata guda kenan da sati biyu dana kusanceta”to kaga dole dai cikin dake jikinta naka ne, a ina aka tabayin haka? ya fad’a a fusace taya za'ayi cikin jikinta ya zama nawa “?gbdy hankalinsu ya tashi har mami wacce batasan sanda ta qaraso inda suke ba tana dubansa “bamu gane nufinka ba ?ko dai ka sha wani abu ne ?babu abinda na sha garas nike amman wallahi cikin jikinta ba nawa bane cikin wani kato ne a

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login