Showing 108001 words to 111000 words out of 167047 words
Chapter 37 - Mar’adam’s Book 2 Hausa Novel Complete.txt
duba screen din wayarta sunan mahaifiyarta ce ta kalli agogon wayarta tana mamaki kiran me take mata adaidai wannna lokacin ? kamar bazata d'auka ba sai kuma ta kara wayar a kunneta ta shige bayinta tana magana qasa qasa ."ummah lafiya ?okay to shikenan amman karki aiko da komai sãi mami ta wuce “bayan ata ya idar da nafila ya zauna yana addua tare da neman zabin allah arayuwarsa ,wannan shine karo na farko da yayi wannna tunanin da kuma addua wa mahafiyarsa yana zaune har aka kira sallah asuba ya mike yayi alwala ya fita zuwa masallaci ya gabatar da sallah sannan ya dawo bai shiga d'akinsa ba ,ya shiga d'akin maryam domin duba mami wanda alokacin itama mrym tayi sallah tana kwnace abayan mami tsaki yaja tare da jan qafarta d'aya ."
firgigib ta bud'e idanunta ta mike zaune tana shafa idanunta bai tsaya wata wata ba yaja hannunta hanyar waje yayi daita ,maryam wanda keta rokonsa ya barta a kusa da mami amman bai kulata ba yana kaiwa waje yayi fillinging daita ta zube qasa tana dubansa "yayinda shi kuma yake jifanta da wani mummunar kallo,"bai ce mata komai ba dan idan ma ya nuna mata yaji ciwon rashin samunta a cikakkiyar budurwa zata iya cewa kishinta yake wanda shi kuma har ga allah ba kishinta yake ba, kawai yadda ta munafurci mahaifiyarsa ta nuna mata cewar ita din mutuniyar kirkice yafi damunsa "kiji abinda zan fad'a miki kar na sake ganinki a kusa da mahaifiyata domin ita din mutun ce mai tsarki "hannuwanta duka ta d'aura bisa kanta tana kiran "wayyo allah na shiga uku dan ko bai fito fili yayi mata dalla dalla ba ta fahimcesa fiyye da haka "shiiiiii ! karki kuskura ki tasa min uwa daga bacci idan ba haka ba wallahi kinji na ranste sai na d'agawa uwarki da ubanki hankali kin dai san halina, Kinsan abinda zan iya yi dan haka stay a way from my mum ."yana gama fad'ar haka ya juya ya koma d'akin ya zauna kusa da mami yana kallon yadda take sauke numfashi normal ba kmar d'azu ba ."
Maryam kam komawa tayi Kan step ta zauna ta raku'be jikinta waje d'aya tana tunani yadda zatayi "wani hanya zanbi ni maryam ya fahimci shine mutum na farko da ya fara sanina ya mace ?"babu wata hanya tunda rashin hakurinki ya janyo kika mallaka masa kanki baya cikin haiyacinsa zuciyarta ta bata amsa da haka “amman kuma ai kina da sheida ?tabbas kina dashi sister itace sheidata ta d’an ji natsuwa kad’an amman duk da hk hankalinta ba’a kwance yake ba .a hankali ta mike tsaye ta fara tafiya kamar mara laka ajiki jikinta ba qaramin sanyi yayi ba ganin irin kallon zargin da yake mata duk yadda taso taji haushinsa ko kuma taga laifinsa zuciyarta ta kasa kar'bansa amatsayin mai laifi ko wanda zataji haushi sai ma taga kamar ya fita gaskiya kuma kowaye dole irin kallon da zai mata kenan . idanunta taga suna ganin duhu akan kujera mai zaman mutun uku ta zube ta kwanta tana runtse idanunta ."
Karfe takwas saura maryam ta farka ta sauke idanunta akan agogo bata sake yunkurin komawa bacci ba ta tsaya ta gyara ko'ina tare da shiga kitchen da yin abincin da zasu yi breakfast dashi sai dai har lokacin zuciyarta cikin dar dar take ta kasa jin sukuni dan hango katoton matsala wa rayuwarta take . Karfe goma gabdayansu ya'yan mami suka harllara a gidan kuma a dakin maryam .maryam din ce kad'ai bata cikinsu tana parlour’n qasa cikin jimami yayinda ATA ke gabana mami yana magana cikin tsananin damuwa "dan allah sweetheart ki bari na fitar dake zuwa kasar Índia a duba min lafiyarki murmushi iya baki mami tayi tana cewa "adamcy kenan baka son na mutu ko ?mami tayi masa tambayar idanunta na kanshi "wallahi banaso sweetheart!"Yayi maganar kamar zai yi kuka kallonsa kawai mami take without saying a word to him sai dai wani irin tausayinsa ne ya mamayeta da sauran yanuwansa tabbas ta yarda kuma ta amince d'anta na mutuqar qaunarta damuwar dake yawo cikin rayuwarsa ne ya hanashi yi mata biyayya runtse idanunta tayi sai ga hawaye sharr yana sauka akan quncinta ".
hannunta ya riko gam cikin nashi yana cewa "why sweetheart?me yasa zaki zubar da hawayenki "ki daina kuka please idan wani abu kike so ki fad'a min am ready do anything for you sweetheart idan kuma tafiyar ne bazakiyi ba wallahi na hakura bazan takura miki ba amman dai bana son na rasaki, dan a yanzu idan kika mutu ba iya yan'uwana ba hatta mutane gari ma sai sun min gori akan rayuwata aunty shahida ta kallesa tasan sarai daita yake maganarsa ."an waye gari wai yar'uwata ce da kanta tamin gori sweetheart a karon farko naji na tsani kaina duk da nasan tayi min né akan abinda nake miki ,nasan na sakaki cikin damuwa sweetheart ki yafe min lafifukan da nayi miki abaya da wanda zanyi a gaba nasan kina sona da wannna yarinyar ne yasa kema kike takura min amman dan allah ki yafe min tsanar da nake fad'a miki inawa yarinyar a gabanki nasan tana sakaki cikin tsananin damuwa "wallahi sweetheart na sha fad'a miki Kiyi min addua ko allah zai saka min soyayyarta acikin zuciyata amman har yanzu shiru babu wata alama ta qaunarta "ya qarashe maganar muryarsa na rawa mami ta kallesa idanunta cike da ruwan hawaye tace "tabbas yawon fadar tsanar da kakewa maryam tana bata min rai amamn adamcy na yafe maka duniya da lahira burina allah ya had’a hankulanku waje d'aya ."
d’aya bayan daya yan'uwansa suka baro d’’akin zuwa parlour suka had'u gabadayansu suna hira har da maryam nan aunty shahida take basu labarin abinda ya faru "kai auntynmu dan allah da gaske ?wallahi ga maryam ku tambayeta "gaskiya auntynmu kin gama da yayanmu "inji cewar zabiba maryam ta mike tana mai jin tsananin farinciki yadda yan'
uwanta kuma dangin mijinta suke matuqar qaunarta aunty khadija tace "ai gara da,aka gama dashi baki ga yayi laushi ba duk ya canza kala kamar bashi ba ,yaro sai shegen taurin kai da fadin ran tsiya ai ni wallahi mami tayi min daidai ai da mun san d'an wannan shirin film din zai dawo dashi haiyacinsa da tunin an dade da wuce gurin aunty khadija ta qarasa maganar tana miqawa zabiba hannu suka tafa ."
“Allah dai yasa buqata ta biya." nana hauwa'u tayi murmushi tare da mikewa tana cewa “in sha allahu ta biya sai fatan alkhairi ta shiga kitchen inda maryam take qoqarin gama tuwon shinkafa da
miyar agushi .”
tun daga falo kamshin miyar ke shiga hancin nana hauwa'u har sai da yasa yawunta tsinkewa "matar yaya wannan kamshi haka kamar zaa tafi gasar abinci "kai sister yau kuma tsiya zaki min "?”ke mu bar wannan maganar yaya had’uwarku da yaya ta kasance daren jiya ?"nan da nan yanayin maryam ya sauya idanunta suka canza kala alamun zatai kuka "babu wani jin dadi sister yayanki wani kallo yake min wanda bazan iya fitowa na bayyana shi ba .nana hauwa'u ta dafa kafad’anta "karki wani daga hankalinki ko sarewa "me yasa zaki fad'i hka wallahi sister a matukar tsorace nake "ba gani ba meye abun tsoro ?nana hauwa ta fad'a cike da kulawa maryam bata san sanda ta rungumeta ajikinta ba tana share hawayenta ."shadaya da rabi daidai ata ya sauko ya fita daga gidan kuma alokacin maryam ta gama komai har da miya suna tsaye suna hira da nana hauwa’u inda nana hauwa’u take fad’a mata ciki gareta wani ihu mrym tayi ta rungumeta “gsky sister am very happy for you Allah ya hada miki komai da komai “kema sister kiyi ahankali fa dan baki sani ba ko ciki gareki mrym ta zaro ido waje “sister ina jin tsoron abinda zai biyo baya “ina nufin an samu a daren jiya “allah yasa ai da ni kad’ai nasan irin farinciki da zanyi dan ko baya so zan rike abina bare ma da gudu zai kwace suka dariya basu gama rufe bakinsu ba kawai suka jiyo sautin muryar ATA cikin hargagi da tashin hankali .”
"ku yanzu daku zaa had'a baki ayi min haka "? a she yadda nake qaunarku ku ba haka kuke qaunata ba ?"daman na dade dasanin haka ,na gode allah ya saka da alkhairi ku tashi ku bar min gidana gabandayanku bana son ganin fuskokinku” ya qarasa maganar adaidai lokacin da su maryam suka fito rike da hannun juna a bakin kitchen suka ja suka tsaya jikin maryam banda rawa babu abinda yake ".dan kwata kwata bata son ganinsa cikin tashin hankali
“Ya kalli inda maryam suke tsaye ya nunata da yatsan hannunsa “kema bazan qara zama dake ba ki tattara duk abinda kikasan naki ne acikin gidan nan ki bar min gidana na sake ki saki u…”cike da tashin hankali aunty shahida tayi wani Irin qarasowa inda yake ta rufe masa baki tana girgiza masa kai tare da nuna masa yatsanta d’aya alamun d’aya zai furta maryam kuwa tun kafin ta gama ji ta d’aura hannuwanta duka bisa kanta tare da shiga wani sabon tashi hankali"wani laifi suka masa haka ?ta jefawa wankakkiyar kwakwaluwarta tambayar ."
inna lillahi wa inna ilaihi rajiun shine abinda nana hauwa'u ta shiga furtawa tana maimatawa wanda yasa maryam ta kama tana yi bakinta na rawa wannan wace irin maseefa ce inji cewar aunty khadija dan gabadayansu babu wanda jikinsa bai d’auki rawa ba maryam kuwa tashin hankalin da take ciki ya hanata kwakwaran motsi a inda take tsaye magana take son yi koda kalmar hakuri ce garesa amman ta qasa furta komai numfashi kawai take ja ta bakinta tana fitarwa dashi da kyar .”
alamarin ATA ya girmi tunanin yan'uwansa suna kallonsa ya buga ma aunty shahida razananniyar tsawa bayan ya cire hannunta “cikin tsananin tashin hankali da fad’uwar gaba take rokonsa "Adam ba’a saki cikin fushi idan kuma ya zama dole sai kayi kayi d’aya wani mugun kallo yayi mata yana mai janye jikinsa daga nata ya sake maida kallonsa ga maryam “tsayuwar me kike yiwa mutane maza ki fara qoqarin bar min gidana ,kuma haka banason ganin kowacce acikinku wallahi na tsaneku sannan na cire kaina acikinku aunty khadija ma tayi karfin halin qarasowa inda yake yayi saurin ja baya "bana son jin komai kawai kuje tunda kunfi son farincikin yarinyar nan akaina shekara nawa ina fama da zazzafar qaddara amman acikinku ko sau d'aya babu wacce ta zaunar dani ta fahimceni amman dan rashin Imani irin naku daku aka had'a baki na kusanci wannan guntuwar yarinyar wallahi kun cuceni .””ai tun daga zuwa d’auko shahida ya kamata ace na fahimci akwai wani abu a qasa amman babu komai kuje na gode .”
mamaki da matsanancin tsoro suka kama maryam “daman akan ya kusanceta ne ya zartar da wannan hukuncin akanta? ganin maryam bata da niyyar bar masa gidansa ya qarasa inda take ya kamo hannunta yana ja bata iya ce masa komai ba sai ma binsa da take har ya kai bakin kofa ya bud'e tare da hanka d’ata waje ya maida kofar ya rufe da karfi wasu hawaye masu zafi da ciwo suka zubo mata tasa bayan hannunta tana gogewa wasu na sake biyowa kuncinta ."ATA na gama juyo idanunshi ya sauka akan mami tsaye ,cikin tsannain tashin hanakali take kallonsa muryata na rawa tace "me ka aikata haka adamcy ?yanzu sweetheart har za’a had’a baki dake a cutar da rayuwata ?ban shirya yin rayuwata da wannan yarinyar ba saboda me zaa min karya da ciwonki ?numfashi mami ta sauke tana kallonsa "dan haka na saketa saki uku dan bazan qara zama daita ba gabad’aya babu wanda bai furta kalmar “inna lillahi wa inna ilaihi rajiun ba har mami dan kam sai data dafe qirjinta dan wani luguden bugu yayi .”
nana hauwa'u ta qaraso inda yake cikin rud’ewa da rawar jiki ta riko hannunsa ya fixge "har ke ban cireki acikinsu ba kuyi rayuwarku nayi tawa tunda bakwa sona nima na hakura daku har abada zabiba ta bud'e baki ta soma magana cike da in ina "ni ..ni dai yaya wallahi banda ni dan ba dani aka shirya komai ba hasalima yau din nan nasan komai aunty kahdija ta ta'bata alamun tayi shiru amman ta zame jikinta "dan allah yaya karka mana haka wallahi muna tsananin sonka muna qaunarka ta durkushe kasa tana jan gwiwowinta zuwa garesa ya tsaidaita ya juya ya haye sama a matukar fusace yake taka step ."wani irin naunayen ajiyar zuciya suka sauke atare "mami ta kallesu daya bayan tace "garin yaya kuka yi wannan kuskuren ?yaakayi kuka bari yasan komai ? tayi masu tambayar ajere cikin tsananin tashin hankali,gbdynsu sukai shiru dan basu da bakin magana ta sake sauke ajiyar zuciya "ina maryam take ? tana waje ! nana hauwa’u ta bata amsa cikin kuka kai tsaye kofar mami ta nufa ta bude inda taci karo da maryam durkushe tana zubar da hawayen mami ta kai hannunta ta d'ago ta ta rungumeta ajikinta tana shafa bayanta .”
jinta ajikin mami yasa ta sake fashe da wani sabon kuka mai ta’ba zuciya " dan allah mami ki fad’awa yaya bani da masaniya akan komai ,kuma allah danasan shiri ne ciwonki da bazan ta'ba amincewa ba gara na cigaba da rayuwata haka dashi "kukan ya isa haka abinda ya faru ya wuce ba kuma zai gogu ba ta zareta ajikinta suka koma parlour'n ta zaunar daita akan kujera sannna ta zauna a gefenta tana rarrashinta "yanzu mami ya zaayi kenan ? "ku da kuka tona asirin komai sai kusan yadda zakuyi dan babu ruwana ,ban da son jawa mutane tashin hankali meye abun baje hira a gidansa alhalin kusan halinsa? Kiyi hakuri mami ki yafe mana inji cewar aunty shahida "mami dan allah kije ki shawo kansa ya janye sakin ya maidashi d’aya Ke kadai ce zaki iya shawo Kan yaya nana hauwa’u ta fad'a tana share hawayenta "da sauri maryam ta kalli inda take zaune “sister saki ukun yayi min kenan ?nana hauwa’u ta gyad’a mata kai alamun “eh!ahankali ta runtse idanunta gam tana jin wani irin rad’ad’i da ciwo acikin zuciyarta wallahi tayi wa kanta alkawari muddin ba ita ce acikin gidansa ba babu wacce zata zauna cikinsa cikin jin dadi, duk inda ake zuwa dan biyan buqata zata domin ta hanashi jin dadin rayuwa kuma duk runtsi sai ta dawo gidan zaman lafiyarsa ya janye sakin kamar yadda sister ta bada shawara bata gama fita daga wannan tashin hankalin ba taji muryar aunty zabiba ta karad’e parlour’n “.
“gsky mami ya kamata mu ajiye son rai a tsaya a duba lamarin yaya shima tunda ya nuna baya son aurenta kar a wani maidashi a hakura kawai allah ya hada kowa da abinda yafi zama alkhairi .” da sauri maryam ta bud’e idanunta ta kalli inda take zaune qirjinta na wani irin bugawa "bayan ya gama maidaita qaramar bazawara zaki fad'i haka ? aunty khadija ta fad'a a fusace "to meye amfanin wannna auren tun kafin ayisa yace bai so ?tunda akayi auren nan ku fad'a min rana daya wanda muke da kwanciyar hankali ?”kullum zuciyarmu cikin fargaba take, yin aure halal ne haka barinsa halal ne idan ma zai gare rayuwarsa haka abarshi mana matsawar bazai dinga biye biyan mata ba ,”tunda suka fara magana a tsakaninsu mami bata ce uffan ba har Qarfe uku ATA bai sauko ba gabdaya cikin damuwa da tashin hankali suke most especially maryam wacce har wani rama tayi nana hauwa’u dake kusa da maryam ta dinga kwantar mata da hankali “sister karki d’aga hankalinki yaya zai janye sakin da yayi miki yanzu fa kin rigada kin zama jinin jikinsa jininsa gauraye yake da naki wata killa ma akwai ajiyarsa ajikinki shiru kawai tayi dan bakinta bazai iya furta komai ba dan hatta miyon bakinta ya qafe idan tayi qoqarin had’iye wa jinsa take tmkr mad’aci ."
Da misalin karfe biyar ne mami ta mike ta haura sama ta shiga dakin ATA ta iske shi zaune akan kujera kwaya d'aya dake dakin yayi baya da kujerar yana kallon saman d’akin ganin shigowarta ya runtse idanunshi gam .da sanyin jiki mami take qarasowa inda yake stood ta janyo ta zauna gabansa ta zuba masa ido tana kallonsa tana nazarinsa dakin yayi shiru tamkar babu kowa aciki har tsawon minti goma mami na zaune agabansa yadda batayi magana ba haka bai bud’e idanunshi ba ta kira sunansa "adamcy nah! shiru ne ya sake biyowa baya ta kai hannunta ta kamo hannunsa ta kai bakinta tana sheshekan kuka saukar hawayenta yaji a hannunsa ya d’an bud'e idanunshi akanta tabbas hawaye ya gani yana sharara akan kuncin mahaifiyarsa abinda ya tsani gani kenan naunayen ajiyar zuciya ya sauke da karfin gaske sannan ya kai dayan hannunsa yana d’auke mata hawayen fuskarta dake kwarara sannan ya motsa lips dinsa da kyar "why sweetheart?Bata ce masa komai ba illa cigaba da zubar da hawaye "da fatan ba Adam bane yayi sanadiyar zubar hawayen nan ?ahankali ta gyada masa kanta alamun shine.”
numfashi ya sauke yana son sanin dalilin kukanta "adamcy kana son saka sweetheart dinka kuka,baka jin damuwa yadda kake saka sarauiyar dad dinka kuka ?mami ta furta tana dago da idanuwanta ta zuba masa da matuqar damuwa "ina cikin damuwa adamcy !"nima acikin damuwar nake” jin sautin muryarsa cikin tsanani bacin rai ya qara d’aga mata hankali ya zame hannunsa ya mike ya qarasa qarahen dakin ya tsaya rike da kugunsa yana jin zafi da ciwon abinda mahaifiyarsa da yan'uwansa suka masa "."Adamcy na !ta sake kiran sunansa a karo na biyu yana jinta yaki juyawa mami ta cigaba da magana "ka sake min wani alfarma a karo na biyu adamcy .” ya d’an juyo a natse ya kalleta "kayi hakuri ka janye sakin da