Showing 156001 words to 159000 words out of 167047 words
Chapter 53 - Mar’adam’s Book 2 Hausa Novel Complete.txt
amsar tambayar data masa ba ya damke agogon sosai ahankali ahankali ya qara runtse idanunshi yayi pretending like kamar yana jin bacci "adamcy me ya kawo agogon mace hannunka neman mata ka fara ko me ?" "sweetheart I'm feeling sleepy ""Feeling sleeping?"ta maimaita abinda ya fad'a "yes sweetheart bacci ".mami taja numfashi ta sauke ahankali sannan tace "alright !amman karkayi dogon bacci dan laasar ta kusa idanunta akanshi ta fice daga parlour'n sai dai zuciyarta cike take fal da mamaki da zarginsa ."
********
"Maryama taso kizo gareni maryama ta mike da kyar dan gbdy jikinta babu laka ta dawo kusa da granny wacce ta kawo masu ziyara a safiyar yau din ta zauna granny ta kamo hannunta daya ta rike gam cikin nata cike da matsanancin tashin hankali ta soma magana "wai meke faruwa da rayuwar yarinyar nan ne ?gabadaya na kasa fahimtar abinda ke faruwa daita duk lokacin da zaayi mgnr aureta ko tayi saurayi sai wani mummunar abu ya samesa? yanzu kuma gashi wanda ya aureta shima ya mutu ya barta , maryama tai saurin girgiza mata kai " granny bai mutu ya barni ba fa an dai binnesa amman nayi imani bai mutu ba zai dawo domin ina cikin son yaya sadam dan duk cikin wad'an da suka nemi aurena babu wanda zuciyata ta yarda ta kuma amince dashi kamar yaya sadam ni kaina na kan zauna nayiwa kaina wannan tunani granny "why abubuwa suke faruwa dani haka ? daga wannan sai wannan tayiwa kakar sadam tambayar tana sheshekar kuka “ya allah laifin me nayi haka da wannan jarabawa tamin yawa ?yanzu ni nasan haka zan qare rayuwata matukar na rasa yaya sadam babu mai kuma Kuskuren sake zuwa neman aurena ". tayi shiru hawaye na zuba daga cikin idanunta "me yasa kuka min haka ? me yasa kuka nisanta da mijina wallahi zuciyata bazata iya d'aukar wannan tashin hankalin ba?me yasa ? Why why !!! ta qarasa mgnr tana wani irin kuka nan take suka rufa akanta har mahaifiyarta suna bata hakuri ".
ahankali zuciyarta ta tsaidaita daga kukan da take tare da bata kwarin gwiwa "sadam dinki bai mutu ba sannan bai barki ba zai dawo gareki ki bawa zuciyarki kwarin gwiwa ki kwantar da hankalinki domin kwanciyar hankalinki shine kwanciyar hankalin duk wani masoyinki Kiyi masa addua da yarda allah zai dawo gareki ."tun lokacin da granny ta kirata zuwa gareta ya qaraso bakin kofar shigowa parlour'n da fuskarta ya sama cin qaro tana zubar da hawaye wanda ke fita daga kasan zuciyarta kamar ance ta d'aga idanunta dan daman tana fuskatar kofar shigowa ne idanunta ya sauka akanshi ."shiru tayi tana dubansa tana ganin tamkar a mafarki ne kallon juna suke ido cikin ido kafin a hankali ta motsa bakinta ahankali tace "kai ne a gidanmu sir !?bai ce komai ba haka zalika bai shigo ba ya cigaba da tsayuwa "maryama! umma ta kira sunanta ta sauke numfashi tana duban umma "Kina bukatar wani abu ne ?batace komai ba ta sake yunkurin maida idanunta inda ta gansa sai dai wayam tagani babu shi babu alamun sa byn kmr minti goma ta sake ganinsa wannan karon mikewa tayi da sauri ta nufi kofar d'akin wanda hakan ya maida hankalinsu gurin cike da tsananin tashin hankali aunty hassana da aunty suka biyo bayanata haka umma tayi kokarin danne damuwarta ta biyosu "sannu da zuwa oga ammar ka shigo daga ciki mana ." yayi shiru yana kallonta dan gabadaya bata haiyacinta yaso ya wuce a tun ganin farko da yayi mata amman ya kasa "waye shi maryama ?umma ta tmbyeta "shine wanda ya taimaka ya bani aikin dana barwa subaia a Z&A .”
nan take murmushi ya dan bayyana akan fuskar umma "Ke ki rufewa mutane baki da shegen karyar tsiyar "wannna ai mai gidan sadam ne " umma ta dubi aunty hassana cike sa mamaki a ina tasan ogan sadam ?amman dai tayi mata alamun tai shiru sai dai aunty hasana taki shiru ta cigaba da zuba magana " mai gidansa ne dan haka naji anata fada ranar sadakar bakwai hatta kayayyakin daakaita amfani dashi shine ya kawo yanzu nasan da wani abun arzikin yazo ,fuskar maryama bayyane da murmushi tun bayan rashin sadam datai sai yau annuri ya bayyana akan fuskarta kuma tayi imani na ganin oga ammar ne dan bata ta'ba expecting zai zo gareta ba to me ma ya kawosa ?ta jefawa wankakki yar kwakwaluwarta kafin ahankali ta mayar da kanta Ta sunkuyar a kasa "yallabai amar sannu da zuwa dan allah ka shigo daga ciki bai dace ka tsaya a bakin kofa ba cewar umma da kyar ya ra'ba ta gefen maryama ya shigo still tsayawa yayi kamar yadda maryama tayi ya tsura mata idanunshi masu shigar da mutun cikin wani halin " .
“ka tsaya yallabai dan allah ka zauna ga guri “
numfashi ya fezgo da kyar ya fesar saboda ba zaman bane abinda ya damesa tashin hankalinsa yadda yaga yanayin maryama yafi komai damunsa ta rame sosai sai dogon hanci da dogon wuya tsawon second goma ya dauka yana tsaye yana kallonta ya jiyo sautin muryar umma " ga guri ka zauna babu yadda ya iya ya dan dosana jikinsa ya zauna yana sauke numfashi "yallabai mun fa gode sosai da kulawarka allah ya saka maka da alkhairi idanunshi kawai ya lumshe batare da ya amsa ba duk da yaso yayi magana koda gaisuwa ce amamn hakan ya gagara sai dai ya balai tsurawa maryama idanunshi ta cikin glass yana kallonta kallo mai tattare da abubuwa dayawa ya shiga wani yanayi da bai ta'ba shiga ba adalilin ramarta tausayi ne menene shi dai bai sani ba amman yasan zuciyarsa bata son ganinta cikin damuwa .”a natse maryama ta dauke idanunta akanshi ta maida Kan hoton mijinta dake manne da bangon parlour'n "yallabai ga ruwa aunty hasaana ta ajiye masa tire mai dauke da glass cup da roban ruwa kwaya daya akan qaramin table ."naunayen ajiyar zuciya ya sauke da karfi yana mai dawowa haiyacinsa sai dai still idanunshi na kan maryama sai dai ya lura idanunta ba akansa suke ba hasalima wani guri take kallo fuskarta dauke da murmushi da
iya wannan murmushin kawai zata gama da duk zuciyar wanda ya daura idanunshi akanta ."
Ahankali ya kai dubansa inda take kallo nan yaga tangamemen hoton mijinta sadam take kallo tana murmushi hankalinsa yayi matukar tashi nan take daidai zuciyarsa ya dinga bugawa da karfi tamkar ana buga masa guduma hankalinsa ya sake tashi macen da abokinsa kuma danuwansa ya dauki tsawon lokaci sama da shakaeu shabiyar yana renon soyayyarta amman yau ga abinda sakacinsa ya janyo masa yasani idan ata yasan itace yake ta qoqarin ganin sun had’u to zai yi nadamar har qarshen rayuwarsa .ya furzar da numfashi yana jin wani irin zafi acikin zuciyarsa dan ya san da ata ya yarda ya ganta a tun farko a lokacin da ita din ba matar aure bace da ko sama da kasa zasu hade babu mai aurenta sai shi .waigawa yayi yaga babu kowa a parlour'n alamu sun basu wuri "dukkanin alamun sun nuna kina tsanin son mijin nan naki da sauri ta juyo ta tsura masa ido jin abinda ya fad'a ahankali ta lumshe masa idanunta tana tuno yaya sadam dinta byn kmr minti goma sai kuma ta fashe masa da kuka "yaya sadam his very special to me ya fiyye min komai dake cikin duniyar nan zuciyata zata rayu da qaunarsa ne kawai .”yayi shiru kawai yana kallon qaramin bakinta da take motsawa a natse a ransa yace “idan ata ya sameta sai yayiwa wannan bakin kaca kaca kai bama iya bakinta ba ita karon kanta sai ta gane kurenta sai ta gane tashiga hannu .”oga ammar ka kuwa san abinda ake kira da soyayyar gasky ? karkace kai yayi kawai yana sake tsura mata ido dan da alamun soyayya ta zautar daita abokinsa zai sha aiki ba qarami ba “tô yaya sadam yana mun fiyye da soyayyar gsk ...."sorry allah ya jikansa allah yayi masa rahma naso na qara dawowa tun bayan sadakar uku amman sai wata tafiyar gaugauwa ta sameni yau kwanaki goma kenan da dawowata nace nazo naga lafiyarki fatan dai kina lafiya baki da wata damuwa ?”
“bani da wata damuwa sai ta rashin mijina” miji miji !! ya fad’a acikin kasan ransa gbdy sukai shiru a tun bayan data furta haka bai sake cewa komai ba dan yana taya abokinsa jin haushin yadda take nuna son mijinta a fili parlour'n ya dauki shiru kafin ahankali maryama ta dago ta tsura masa idanunta "nasan subaia ce ta fada maka abinda ya faru ko ?yes itace zuciyata ta kadu sosai ban san sanda na janye fushin da nayi dake ba "na gode sosai allah ya jikan iyaye "ameen !”ya furta a fili wannan kalmar nata na cikin abinda take qara burgesa dashi ya dauki kamar awa daya tare daita sannan yace ni zan wuce daman nazo naga yanayin jikinki dan lokacin danazo ance bakya cikin haiyacinki shiru tai tana kallonsa kafin tayi wani hanzari har ya mike tsaye tare cewa " idan kina bukatar wani abu ki bari nasani yana gama fadar haka ya juya har ya kai bakin kofar fita ya juyo ya tsaya yana kallonta yana sake jin tausayinta na mamaye zuciyarsa ta yunkura ta mike da kyar tayi taku biyu ta tsaya tana watsa da yatsun hannunta "take care !"taji ya furta ahankali daga saman lip's dinsa kai kawai ta gyada masa bayan fitarsa da wasu yan mintuna sai ga yara suna ta shigowa da kayan abinci aunty hasana tayi tsalle cike da murna tace "kai gsky wannan mutumin ba qaramin mai kudi bane kaga abun arziki tunda akayi mutuwar nan yake aiko da kayan abinci bata rufe bakinta ba sai ga yaronsa ya shigo da bandir din yan dubu dubu guda biyar ya mikawa aunty hasana kasancewar itace a kusa dashi "gashi inji yallabai "da sauri ta kar'be tana zuba uban godiya aunty kinga wani sabon abun arziki ? gsky mutumin nan yana da matukar kirki sosai ai da gobe nayi niyyar zuwa gidan aunty fatima nayi kwana biyi amman yanzu gsky babu inda zani wannan abun arziki haka ai sai an gama lashewa dani tasss sannan zan..."haba hasana ke mutuwar nan ma kamar dadi kikaji daakayita karki manta duk wannan abun bazasu taba kwantar min da hankali ba d'a fa na rasa sukunta guda dan ma kwaya daya amman kike murna dan an kawo abun duniya gsky idan haka zaki cigaba ni da kaina zan sallameki ki koma bangarenki dan zuciyata bazata iya d'aukar wannan cin fuskar ba.”
“ baki yiwa wannan yar iskar fada ba ko ki koreta a gidanki alhalin itace silar jefa rayuwar d'akin ciki halin mutuwa sai ni ?ai idan kora ne ga wacce ta fini cancatar ki kora bani ba, kai ni me ma nayi tukun ?tayi mata tmbyr tana dubanta a dage babu abinda tayi ita din yarinyar kirki ce datasan mutunci kuma har yanzu dana rasa d'ana bana jin komai akanta sai tsananin soyayya yadda nake matukar qaunar sadam haka nake matukar qaunar maryama domin ita din tamkar diyar cikina take." bata da wani bambamci da sadam a wajena hawaye ya zubo akan kuncinta "fatan kin fahimceni wannan family na bukatar kwanciyar hankali idan kuma kikayi kokarin kawo min tashin hankali wallahi zan ajiye duk wani zumunci agefe fatan kin fahimta,ina bukatar zaman lfy acikin gidan nan tana gama fadar haka ta nufi kofar d'akinta bata kai ga shiga d'akin ba ta jiyo sautin muryar maryama "tunda dai har zamana a gidan nan yana kawo tashin hankali atsakaninku ina ganin lokacin barina gidan yayi ."granny ta girgiza mata kai haka ma aunty wacce jikinta har rawa yake tsabar tashin hankalin maganr maryama .”
Yayinda gaban umma yayi wani irin buga
da mugun sauri ta juyo lokacin har maryama ta soma tafiya "tsaya !maryama ta tsaya cak tmkr yadda umma ta bata umarnin tana ko kuwa da numfashinta har sanda umma ta qaraso ta dafata "babu inda zaki kina nan har sai kin kammala takabarki idan kin yi raayin tafiya sai ki koma gurin mahaifiyarki idan kuma kinga zaki cigaba da zama dani duk daidai ne awurina amman a yanzu babu inda zaki kina tare dani ko kina son ki tafi ki barni Kmr yadda sadam yayi ?ta girgiza mata kai tana kuka "banason na barki umma amman ki duba ki gani kullum kuna samun matsala akaina da aunty hasana gani take nice silar komai alhalin bansan komai ba bansan meke faruwa da rayuwata ba umma da dai kin bari na tafi kawai ni yanzu bama zan cigaba da zama da kowa ba zan tafi inda babu wanda ya sanni na cigaba da rayuwata .”bazaki iya canza qaddararki ba maryama abinda zai faru ya rigada ya faru babu kuma wanda ya isa ya hana ko yasa "umma ina matukar qaunarki araina numfashi ummah ta sauke tace "muje ki zauna ki huta kinji maryama "kai ni ban ta'ba ganin mahaukaciyar mata kamarki ba "taya zaki maida wacce tayi silar barin danki duniya tamkar diyar cikinki kin sani nasani kowa na yasani maryama ba diyarki bace diyar yayar mijinki ce km dan wani baya ta'ba zama tamkar d'anka kina ganin zata zama kamar sadam ne?"
“kowa da yanayin rayuwarsa hasana ni haka tawa rayuwata take da d'ana da ba nawa ba duk abu d'aya ne agurina qaunar da nake ma maryama yasa na hadata aure da dana duk da na fahimci yanayinta a tun farko na nakin auren amman daga baya ta amince saboda qaunar da take min kuma da ina da wani dan a duniya bayan sadam wallahi zan sake aurawa maryama shi kuma ina da tabbacin ko itace ta mutu bilkisu zata sake daukar diyarta ta bawa sadam ya aura "dan hka kije kiyi abinda ke gabanki ko ki bar min gidana na rasa me yasa hasana kike yin haka shin maryama ba diyarki bace ba ,idan ma baki dauketa matsayin diya ba wannna qaddarar da ta sameta idan ta samu diyarki ya zaki ji ? "wannan shine karo na biyu da kika ce na bar miki bangarenki to zan bar miki bangarenki amman karki sake hada yayana da maryama domin diyata bazata ta'ba tursasa mijinta lallai sai ya kaita har wani gari kawai saboda wani zanen banza da wofi ba kar ma ki sake hada maganrki da diyata banaso amman ki rubuta ki ajiye dai maryama zata juya miki baya tunda dai bakece kikawota duniya ba ."naji komai zakice allah ya raka taki gona “a’a abun bai kai ga haka ba duk kuyi hakuri Ke hassana kiyi zamanki amman fur tace tafiya zatayi da kyar granny ta shawo kanta ta hakura sai dai duk sanda zasu hada ido da maryama harara ne ke biyowa baya “
*****
Maryama zaune shiru duk da zuwa yanzu hankalinta ya dan kwanta amman bata wani cin abinci yadda ya kamata haka ne ma yasa jikinta yaki dawowa daidai umma da granny suka zo suka sakata a tsakiya "maryam taso muje kici abinci ta sauke naunayen ajiyar zuciya tana girgiza kai "bana jin yunwa "haba maryama ina lura dake tun jiya baki sakawa cikin komai ba karki cutar da kanki domin rayuwa babu ci babu sha akwai matsala idan wani ciwo ya kamaki yaya kike son muyi da rayuwarmu “. tayi murmushi kawai tana duban umma “idan ma bazaki tausayawa kowa ba ki tausayawa ummanki cewar granny umma bata ce komai ba ta koma hannunta daya fuskarta dauke da murmushi granny ta riko dayan hannunta suka nufi kan kujera mai zaman mutun uku daita atare suka zaunar daita "umma da kun barni wallahi bana jin cin komai Aa bazai fa yuwu ba ko bakya jin cin komai ya zama dole ki sakawa cikinki wani abu kafin ta sake yin magan granny ta kai spoon din abinci bakinta murmushi kawai maryama tayi ta karba ta soma ci granny na bata umma na bata ."ta kai hannu ta karbi spoon din hannun umma” nasan kema baki ciki komai ba ta dibi abinci ta kai bakinta "umma nah kici abinci “ta girgiza kai tana shafa fuskar maryama sannna ta bud'e bakinta fuskarta dauke da murmushi.”
****
Maryama zaune a parlour'n ummah sanye take cikin wondo da riga yan kanti kanta babu dankwali yayinda gashin kanta ya zubo gadon bayanta gabanta qaramin table ne wanda ta daura farar takardar zane kasancewar ta samu aiki ta hanyar wata abokiyar aikinta yusira ,gefenta kuma tarin fararen takardu ne datai zane bata samu abinda take so ba ,sosai ta dukufa gurin ganin ta zana abinda ake bukata ,tana nan zaune umma tazo ta wuceta ta shiga kitchen byn wani lokaci ta fito ta dan tsaya tana dubanta kafin daga bisani ta koma ta cigaba da abinda take duk maryama bata dago ba dan sosai tayi nisa sai dai har zuwa wanna lokacin bata samu nasara ba ."har yanzu banga kinyi abun arziki ba keda zane baya baki wuya “ta dago a galabaice tamkar zatai kuka "wallahi umma bansan dalili ba na kasa samun abinda nake so ni ma rasa abinda Ke damuna gabadaya na manta komai umma ta qaraso ta dafa kafadarta” karki damu yarinyarta ki ajiye ki huta zuwa wani lokaci zaki samu abinda kike so
Suna Cikin haka kawarta yusira ta shigo bakinta dauke da sallama sam maryama bata dago ba , ta dai amsa sallamar ta cigaba da abinda take umm ta fito daga kitchen tana murmushi "yusira ce agidanmu ? .
"Nice umma ina yini ?Lafiya lau yusira ya mamanki ? tana lafiya ta fad'a tana zama kusa da maryama maryama kardai har yanzun baki qarasa ba gashi dashi nake son na wuce ?ta fad'a tana leka zane jirgin sama ne " uhm wallahi gashin nan fa yusura har yanzu ta kusan awa daya kenan banga alamun zata gamasa ba, kai tunda nake daita ma ban taba ganin zane data bata lokaci irin wannan ba”. cewar umma tana gama