Showing 105001 words to 108000 words out of 167047 words

Chapter 36 - Mar’adam’s Book 2 Hausa Novel Complete.txt

baccinsa wai aka fad’a masa sweetheart dinsa ta rasu da mugun sauri ya farka ya shiga dakinta tana kwance abunta tana bacci ya Kai hannunsa daidai hancinta nan yaji tana numfashi wani naunayen ajiyar zuciya ya sauke gudu motar yake amman sam ATA gani yake kamar motar ba gudu take ba dan gabdaya ya rasa natsuwarsa daga jajayen idanunshi yayi ya sauke akan wayarsa daya har da wasu mintuna tsaki yayi yana jin zuciyarsa kamar zata buga sam baya ganin gudun motocin nasu yaji kamar ya karbi tukin watakila nashi zai fi nasu, tsaki yaketa yi yana qarawa kamar bazasu kai ba haka yake gani duk jikinsa tsuma yake kwakwa luwarsa ta hargitse kamar wanda sabon hauka ya kama a haka suka qaraso bakin get din gidan Aunty shahida tun baa gama daidaita tsayuwar mota ba ya fito da sauri ya shiga buga get din gidan da iyakacin karfinsa domin kana ganinsa zaka fahimci hankalinsa a matukar tashe yake tunda yayi bugun farko kowa dake cikin gidan ya farka a matukar tsorace ,mai gadi ma yayi takansa sai dayaji ya ambaci sunan aunty shahida sannan ya fito ya bude qaramin hujin get din nan take ya ganensa duk da cikin duhu ne .”


ya bude masa get da sauri ya shiga haraban gidan yana kwalla mata kira” shahida shahida !!”wani irin bacci ne haka?” meye amfanin wayoyinsku da karfi ya dinga buga kofar shiga falo masu aiki suka bude masa yaranta da masu aiki ya gani tsaye cirko cirko ya shiga yana cewa “ina shahida taje ?””mumy na sama inji cewar hamdiya second born din aunty shahida ,zuciyarsa duk a jagule ya diga kiran sunanta sai gata ta sauko da sauri “lafiya Adam ?lafiya zaki gani by this time ?” shima ya wulla mata tmby yana mata wani kallo “dan allah meye amfani wayarki data mijinki ?”zatai magana yace yanzu dai dauko kayan aikinki ran sweetheart a hannun Allah zan iya rasata akowani lokaci “ka kwantar da hankalinka zuwa da safe zan zo “ what “?ya fad’a yana mata wani irin mugun kallo sannna yace “dan allah idan wasa mike ki dawo hankalinki ki dauko kayan aiki muje ya riko hannunta .”

“bari na dauko kayan aikina “okay Kiyi sauri please cikin kankani lokaci ta daura hijab akan kayan baccinta ta sauko tare da mijinta yana rike da kayan aikinta yana ma ATA magana “a she mami ce babu lafiya “tsaki ATA yaja Tare kwace qaramin alkwartin kayan aikin aunty shahida dake hannunsa ya ja hannunta suka fice yana cewa “idan kukayi aure shikenan damuwar iyayenku ma bakwa damuwa daita sai ta mazajenku “karka sake ka fad’a min magana “an fad’a miki idan ma akwai abinda yafi haka zan fad’a miki ,nazo miki da matsala sai wani jan jiki kike yi kamar ba mahaifiyarki nace ranta a hannun allah yake ba har da wani jerawa da miji nonsense kawai “kai ne nonsense ai gara ne tun daga farko rayuwata har zuwa yanzu akan mata biyayya nake kai fa a matsayinka na nmj wanda hakinsa ne yayi biyayya ko dole ne ,kuma hatta aljannarka tana qarqashin tafin kafarta amman ka fad’a min meye kake wa mami na farantawa bare yanzu ka d’aga hankalinka akan rashin lafiyarta ?wallahi ko yanzu mami ta rasu alhamdulillah mun gama daita lafiya kai fa ?

“Wallahi sai kafi kowa shiga damuwa da tashin hankali “gori zaki min?” ya tambayeta cikin tsananin damuwa “eh anyi maka idan kayi zuciya ka canza rayuwa kayiwa mahaifiyarka biyayya ,kaso duk wani abinda take so “tana gama fad’ar hk ta shige bayan mota, shima kuma ya shiga gaban mota ya zauna maganarta na ci masa rai “abun har ya kai ayi masa gori ?uwarsu daya ubansu daya ma tayi masa gori inaga mutanen waje ?”allah ne kadai yasan abinda jama’a suke fad’a akansa” ya salam ya furta yana dafe goshinsa ahaka suka kawo gidan da sauri ya fito yana bud’e mata mota kallo d’aya zaka masa ka fahimci yana cikin damuwa da tashin hankali hannunta ya riko cikin nashi suka nufi kofar shiga parlour’n gidan .”



Mmn sudais

💗💗💗💗💗💗
     MAR'ADAMS
     💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗


*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan  09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.


             Page 20


Tunda ATA  ya  bar gidan  hankalin mami a matuqar tashe yake ganin maryam rasa  babu wata alamun an kusanceta domin ta lura kamar  babu wani abu daya sauya atattare daita "kar dai qarya adamcy ya girba mata bai aikata abinda tayi masa umarni ba?" hakan yasa taji wani sabon tashin hankali ya shigeta . bangaren ATA kuwa tafiya yake  hannunsa rike dana aunty shahida har suka shigo parlour'n gidan, sauri sauri yake janta suna taka step, kallonsa kawai aunty shahida take zuciyarta cike da matsanancin  bakinciki da tausayinsa ,bakincikinta saboda yadda yake janta, tausayinsa kuma saboda yanayin da yake ciki dan yanayinsa kawai zai tabbatar maka da baya ciki natsuwa da kwanciyar hankalinsa .  kai tsaye d'akin maryam suka  nufa inda suka iske maryam zaune rike da hannun mami tana zubar da hawaye nan da nan hankalin ATA yayi matuqar tashi , jikinsa har rawa yake ganin yadda maryam take hawaye ,ba iya jikinsa ba hatta zuciyarsa rawa take .jin motsin shigowa d'akin ne yasa da sauri maryam ta d'ago tana duban kofa idanunta ya sauka akansu ta share hawayenta da sauri ckin muryar kuka tace  "aunty shahida ina kika ajiye wayarki ?"
“mami tana cikin wani hali  har ta fita haiyacinta numfashinta baya sauka da kyau please aunty shahida ki taimaka banason  wani abu ya samu mami ."ta qarasa maganar tana wani irin kuka ."


Jin ba mutuwa mami tayi ba yasa ATA yayi mata wani mugun  kallo tare da yi  mata alama da ido ta fita ta basu wuri ."babu musu maryam ta mike ta sauko daga kan gadon cikin mutuwar jiki ta  biyo ta ra'ba ta gefensa ta fita tana  kuka .bayan fitar maryam jingina bayanta tayi da bango corriedor  tare da sake  fashewa da wani kuka mai ta'ba zuciyata "mami bana son na  rasaki  ,domin kuwa ke  din babbar jigo ce ga rayuwata da kuma rayuwar aurenta  allah ya baki lafiya allah ya tashi kafad'arki".cikin taku mai tattare da damuwa da tashin hankali ATA ya matso inda mami take kwance numfashin ta na fita ahankali ,kafin ya bawa aunty shahida umarni ya tsurawa mami idanunshi tare da zama a gefenta yana qare mata kallo yana jin kamar ya fashe da kuka ya d'auki zazzafar qaddara rasa mahaifinsa na tsawon shekaru yanzu kuma idan ya rasa mahaifiyarsa a halin da yake ciki na tarin damuwa da matsalolin rayuwa ya zai yi ?"yaja zazzafan numfashi tare da sa tafin hannunsa ya share hawayen daya d'an cika gefen idanunshi . duk yadda mami  take jin idanunshi akanta batayi kuskuren bud'e idanunta ba tana jira daga garesu  ,lallausar tafin hannunsa ya kai saitin wuyan mami yana jin saukar numfashinta yana jin d'umin jikinta  ahankali mami ta bud'e idanunta tana cewa "adamcy nah har ka dawo ?ina shahidar take  ".


kai ya gyad'a mata tare da kallon inda aunty shahida ke tsaye yace "ya kika tsaya dan allah ki fara aikinki mana  "ya fad'a kamar zai fashe mata da kuka  alokacin ya d'auke hannunsa akan  wuyan mami ganin bata da alamun qarasowa yace "wai meye haka dan allah naje na taho dake da kyar yanzu kuma kinzo kin ja kin  tsaya kin zuba mana ido kodan kinsan idan wani abu ya sameta ni ne zan fi kowa shiga damuwa yasa kike min haka ?.yayi mata tamabyar a rud'e yana zufa "wai ..."mami tayi saurin katse shi ta hanyar cewa "adamcy nah zan sha tea "da sauri ya mike tsaye  ya fita  cikin tashin hankali yana fita maryam tayi wuf ta fad'o d'akin ,sai dai abun mamaki mami ta gani ta  dawo haiyacinta ba kamar sanda ta barota ba tana kallon  aunty shahida, bata gama mamakin ta ba taji fitowar muryar mami  rasa. "zo nan maryam" ta yafitota da hannunta ta nuna mata kusa daita tana cewa  "shahida sai kuma kika ga wannan rigimemen yarona yazo d'aukarki ?.


“wallahi kuwa mami ,da yake nasan shirinki shiyasa nayi masa wulakanci, yana fad'a ina fad'a har muka baro gidan   mami tayi murmushi kawai"amman fa ya bani tausayi sosai  ,da fatan dai komai ya tafi yadda muka shirya ? tô ya dai ce min ya aikata amman bansani ba ko karya yayi min duk da nasan karya ba d'abiarsa bace idan bai yi ba ,zai ce bai yi ba " mutuwar zaune maryam tayi agurin   tana dubansu a matuqar gigice saboda tsananin tsoro "kenan ciwon mamai shiri né dan yaya adam ya kusanceta ? “Ita kuwa wani irin só mami take mata haka ?kwakwaluwarta bata kai ga bata amsar tambayoyin ba taji sautin muryar aunty shahida tana cewa "ke maryam !"maryam tayi saurin d'agowa ta kalli aunty shahida a gigice "wani abu ya shiga tsakaninki  da adam né ?maryam tayi shiru alamun kunya "kinga karki 'bata mana lokaci idan kinsan babu abinda ya shiga tsakaninku a canza wani shiri ?"ahankalai ta gyd'a mata kai kawai "ki bud'e baki mana ki min magana ita kam  bazata iya amsa wanan tambayar agaban mami ba fahimtar haka yasa aunty shahida tace "zan yi magna idan wani abu ya shiga tsakninku ki gyada min kai idan bai shiga ba kuma ki girgiza min kai.”


mami kam maganar aunty shahida  kusan dariya yaso bata ,dan haka ta kawar da kanta gefe tana murmushi "wani abu ya shiga tsaknain ku ?maryam ta gyad'a mata alamun "eh "alhamdulillah ! ta furta a fili tare da cewa yanzu kuma sai muyi  fatan allah yasa ya zame mana alkhairi " in sha allahu zai zama alkhairi fara dubani kafin ya shigo ya gane shiri ne kinsan halinsa da shegen ganiyar tsiya  ". Inji cewar mami batare da 'bata lokaci ba aunty shahida ta bud'e qaramin jakar kayan aikinta ta soma duba jikin mami suna magana qasa qasa."otsin shigowa d'akin maryam taji hakan yasa tayi saurin waiwayo
wa ATA ta gani  yana qoqarin shigowa hannunsa rike da cup din tea   ganin ana duba mami ya ajiye cup  din akan bedside ya tsaya idanunshi kyam  akansu ko kifta idanu baya yi ,burinsa kawai mahaifiyarsa ta samu sauki . yayinda maryam take kallonsa kawai ta rasa abun yi saboda jin ciwon  mami duk shiri ".



wani irin numfashi mai zafi ya fesar kamar ance ya kalli inda maryam take zaune yaga shi take kallo wani mugun kallo ya bita dashi mai tattare da tsana taga irin kallon tsanar da yake mata amman tayi kamar bata fahimta ba ta cigaba da kallon faukarsa har alokacin tana cikin yanayi na damuwa da tashin hankali ,mami kuwa hankalinta na kansu  addaua take masa acikin zuciyarta "allah yasa qarshen wahalarsu ne yazo, allah ka dubeni ka shirya min adam ka  fidda  shi acikin halin da yake ciki ka dauke masa tunanin mafarkinsa ka mantar dashi komai akanta ka daidai tsakaninsa da matarsa ."kamar wanda aka tsinkara haka yayi kanta yana cewa "kallon iskanci me kike min ?".wani irin tari mai karfi mami tayi tana kiran sunansa da yafitosa da hannunta dole tasa ya dawo da sauri ya rike yatsun hannunta gam yana mata sannu amman idanunshi na Kan aunawa maryam mugun kallo da harara  ."



har tsawon   mintuna talatin  aunty shahida tana Kan   aikinta sannan ta samu numfashin mami ya dawo daidai ta mata allurar bacci sannna  taja baya kad'an ta tsaya tana yiwa mami sannu ."yauwa shahida allah yayi maku albarka gabad'ayaku da ya'yanku allah yasa ina da rabon ganin ya'yan adamcy da auta "in sha allahu mami zaki gani allah dai ya baki lafiya "wani mugun kallo ATA ya watsa mata yana jan tsaki "da fatan dai baku sheidawa kowa halin da nake ciki ba  ko ?nasan babu wanda d'an naki ya sheidawa dan nasan daya sheida masu da yanzu sunzo ko sunyita kira a waya amamn yanzu zan  kira khadija , zabiba da auta na sheida masu halin da'ake ciki sai su zo gobe su duba jikikin zazzafan  numfashi ya sauke  dan kuwa  babu wnada ya sheidawa cewar mami ta kusan mutuwa ya kai hannu ya d’an d’ago mami yasa mata pillow ya jingina bayanta ya d'auki cup din tea din daya shigo dashi ya kai bakinta yana bata tana kur'ba ahankali rud'ewarsa bai bawa mami mamaki ba dan tasan halinsa akan ya rasata zai iya aikata fiyye da haka dan duk  iskancinsa idan zai ga 'bacin ranta ko rashin lafiyarta yanzu né hankalinsa zai  tashi ,bai son ya rasata gashi kuma mutuwa tana Kan kowani bawa dole watan wata rana zaa wayi gari  a sheida masa ta mutu ko ta mutu a hannunsa allah dai ya bata ikon cikawa da imani shine fatanta ".


bayan ta gama sha tea ya gyara mata kwanciya  yana mata sannu tare da lullu'be mata jiki ya zauna a gefenta hannunsa na rike cikin nata yana jin qaunar mahaifiyarsa fiyye da komai, ahaka bacci ya d'auke mami ,ya tsura mata ido "ya  allah ka bani karfin zuciyar yiwa mahaifiyata biyayya ba komai ya hanashi son abinda mahaifiyarsa ke so ba illa  soyayyar princess daya ma zuciyarsa  mummunar kamu ."hannun maryam aunty shahida ta kamo suka fito daga cikin d'akin,ahankali suke takowa zuwa parlour'n qasa  "maryam ina tayaki murna allah yasa ku samu rabo a wannan had'uwar farkon da kukayi da adamcy." cikin yanayi na tashin hankali maryam ta sauke  numfashi tana jin sabon  tashin hankali na shigarta "abinda basu sani ba ai wannna had'uwar itace kusan ta biyar a tsakninsu dashi har bakin mota ta  raka aunty shahida  tana karfafa mata gwiwa ta bud'e mata gidan baya ta shiga ta zauna "allah ya tsare min aunty nah zaki shigo gobe né  ?sosai kuwa zan zo gobe ai idan ban zo ba wannan muskililin zai iya kiran likitansa kuma zai iya gano  komai allah ya kai mu gobe aunty shahida ta wuce gida ta barsu duk da taso tayi magana da adam amman ganin yanayinsa akwai tsananin damuwa koma tace haushinta yake ji .


Acan d'akin kuwa a hankali  ATA ya runtse idanunshi tare da motsa labbansa "princess you want to kill me ba ?kina son sonki ya kasheni ba ?duk tsananin soyayyarki ne ya hanani yiwa mahaifiyata biyayya why kika kasa bayyana min kanki a zahiri gashi komai zanyi sai da tunaninki ".ya fad'a yana sauke ajiyar zuciya da numfashi atare ya tuna lokacin da yake saduwa da maryam karfin tunaninta ne yayi tasiri a zuciyarsa har mazakun tarsa ta mike if not da  bazai iya aikata komai daita ba "nima ina sonka sosai zuciyata da gangar jikina kai kad'ai suke jira saboda zuciyata da gangar jikina mallakinka ne har abada ,yaji sautin muryarta acikin dodon kunnensa suna masa kuwa ahankali ya bud'e idanunshi yana kallon d'akin  .wani naunayen ajiyar zuciya ya sauke yana furta "why princess ?ina son na ji sautin muryarki a zahiri kullum sai dai naji a bad'ini ya fad'a da wata irin murya kamar tana tare dashi ya dade zaune har goshin asuba sannan ya zare hannunsa cikin na mami ya fito ya nufi d'akinsa kamar ya d'an kwanta ya huta dan wani irin sara kanshi ke masa amman yasan ko  ya kwanta bazai ta'ba iya runtsawa ba saboda halin da mahaifiyarsa take ciki ."


kai tsaye hanyar bathroom ya nufa ya tura kofar ahankali ya shiga  domin tsarkake jikinsa bayan ya zare jallabiyarsa wanka tsarki ya soma alokacin da ruwa ya fara sauka ajikinsa zuciyarsa ta fara hasko masa komai daya faru a awanin da suka gabata "sweet heart kinga irin matar da kika za'bawa rayuwata ko ?" Kin aura min mazinaciya ,kin aura min macen data gama zubar da mutuncinta a waje “Ko adadin maza nawa ne suka kusanceta ?yayiwa kanshi tamabayr yana furta kalmar subhallah acikin zuciyarsa   "a gaskiya sweetheart baki kyauta min ba ,shiyasa raina yaki amsarta zuciyata taki sonta, babu shakka wannan dabi'ar ce yasa zuciyata ta qasa amsarta amatsayin  mamata "nan da nan zuciyarsa ta fara tafarfasa yana jin tuttukin bakinciki sakama kon yadda yaji maryam akan gado "sweetheart kin sadaukar da rayuwarki akan mazinaciya batare da kinsani ba wani zazzafan numfashin ya fesar kana ya cigaba da wanka da wannan tunanin yayi wankan tsarki Ya gama ya d'auro  alwala ya fito ya sauya wani jallabiaya mamadin ya kwanta ko ya zauna sai kawai ya tsinci zuciyarsa da són gabatar da nafila "gara ya koma zuwa ga ubanginsa ko zai fita daga cikin maseefun da yake ciki na tsawon shekaru  ."


Cike da tashin hankali maryam ta shiga d'akinta ta samu waje ta zauna tana duban mami "wani irin soyayya mami take mata haka ?ta furta a saman lip's dinta tasan mami na matuqar qaunarta amman bata ta'ba tunanin zata aikata haka akanta ba ,kanta ta kifa a daidai hannun mami hawayenta na zuba "allah sarki mami kina sóna da yawa ,kina son cigabana  ta kowani hanya kina  nan kina shirya min yadda zanji dadi a gidan d'anki ni kuma mahaifiyata tana nan tana shirya yadda zan cutar da d'anki domin kuwa da magungunan  da sukai masa  sunyi tasiri sai abinda tace masa zai yi  amman duk runtse duk wuya bazata ta'ba barin yaya adam ya juya wa mami baya ba idan sukai nasara akanshi sake kwantar da kanta tayi tana tunanin irin kallon da ATA yake mata wanda ke d'auke da tambayoyi kuma tasan duk akan yadda ya sameta ne ."hakika maryam kinyi gaugau wa arayuwarki "ko a wani matsayi yaya adam zai  dauketa  fatanta allah yasa yau né cikin zai shiga dan kuwa idan ya shiga kafin yau akwai kutirin bala'i a gidan ."


sosai tayi zurfi cikin tunani qarar wayarta ce ya dawo da ita daga  tunanin da take ta yunkura ta mike da kyar ta  d'aga tana

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login