Showing 159001 words to 162000 words out of 167047 words
Chapter 54 - Mar’adam’s Book 2 Hausa Novel Complete.txt
fada ta nufi hanyar kitchen .”
Yusira ta biyota abaya "umma me zai hana da zaman nan da maryama take ta nemi aiki tunda ta gama tabarta,banki maganrki ba yusura amman maryama ce wani lokacin akwai taurin kai cewar umma “da kuwa datayi kokari ta sake applied din aiki daya fi, kinga akwai wani compaing AGC dake bukatar ma'aikata nima zanyi applied kinga da sai munje tare abinda ma ya kawo kenan amman sanin yanzu bata bukatar yin aiki yasa nace na fara miki magana dan kinsan yadda zaki shawo kanta ciki sauki ta amince” da zata amince hakika da naji dadi tunda zaman hk bashi da wani amfani banda tunani dake sa mutun amman Kinsan halinta idan tace bazatai abu ba to fa sai ahankali "Allah ya kyauta cewar yusura "amman Kinsan wani abu zan tura masu applications batare da saninta ba sai dai taji ankirata idan sun dauketa shikenan .” gaskiya umma hakan yayi kuma naji dadi sosai ina son duk inda zan kasance muje mu kasance tare ai kwanaki yayi min ciwo data bawa subai,a aikinta wallahi umma da ina gari bazai yiwu ba "to Ke kuma banda abunki ai taimako tayi kinga tafi maryama bukatar aikin duk halin tsananin dasu maryama suke ciki sunfi subaia tunda su ko babu komai muna nan kuma bazamu bari su rayu cikin kunci ba amman subaia da abinda zasu ci ma wahala yake masu ?."
"Haka ne kuma allah yasa mu dace mu samu aikin nan dan aikin a kafanin AGC ba karamin albashi ake samu ba ,samun aiki ma awurin yana daga darajan mutun shiyasa kullum cikin addaua nake akan na samu aiki a wajen ,” bari na baki mail dinsu da zaki tura masu sako tayi maganar tana kokarin ciro wayarta "to shikenan yusira na gode amman me zai hana ki tura min ta Kan waya kawai kamar zai fi sauki ? .""Eh ! Haka ne kuma bari idan na koma gida sai na turo miki duk wannna maganar da suke babu wanda maryama taji domin tayi busy akan zane
Mmn Sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
Book 2 end
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 30
Granny zaune akan kujera mai zaman mutun biyu rike da qaurin qafafuwanta tana mammatsawa tana runtse idanunta alamun tana jin ciwo sosai muryarta a sanyaye tace “ wayyo allah qaurin qafata, wallahi qaurin qafar nan yana damuna da ciwo sosai umma dake zaune tare da aunty hasana najin haka ta tashi daga inda take zaune ta shiga d’akinta aunty hassana ta dubeta kana tace “sannu hajiya “yauwa hassana na gode, amman mai yasa bazaki dinga kunsa lalle ba yana maganin ciwon qafa sosai “ina yi amman wani lokacin idan ya tashi dole sai na had’a da man zafi .”bata kai ga rufe bakinta ba sai ga umma ta fito daga d’akinta ahankali ta qaraso inda granny take zaune hannunta rike da man zafi “sannu hajiya bari na shafa miki man zafi nan zaki d’an ji saukin zugin da suke miki, kinsan abu idan ya had’e maka da girma sai a hankali “ai kuwa na gode allah yayi albarka daman yanzu nake son tambayrki aboniki dan nasan bakya rasawa umma na qoqarin tsugunnawa sai ga maryama ta shigo bakinta d’auke da sallama .”tana ganinsu tayi murmushi ta qaraso da sauri ta tsaya kusa da umma tana cewa “umma mai ya samu granny naga kamar bata da lafiya ?”wallahi maryama qafafuwanta ke mata ciwo shine zan shafa mata man zafi “.“ayya sannu kinji granny Allah ya baki lafiya umma kawo man na shafa ma yar tsohuwar nan dan nasan ke ahankali zaki yi mata ni kuwa da iya karfina zanyi mata amfani dashi na durza sosai man zafin ya shiga ko….”
“sannu muguwa! “Inji cewar Aunty hasana “maryama ta kalleta a natse batare da tace mata komai ba “nace sannu muguwa ko karya nayi da kike kallona a wulakance ?”daman babu abinda kika iya sai tsiya da mugunta muniyar banza kawai kin wani kafeni da wasu gwala gwalan idanuwa ko zaki cinyeni? still maryam bata ce mata komai ba idan da sabo ta rigada ta saba da halinta sai dai abinda take mata ita da mahaifiyarta yana matukar damunta koma tace ya fara isarta amman tasan duk runtse duk wuya baza ta’ba iya maida mata magana ba yadda batayi magana ba haka umma da granny basu ce ci kanki ba ,maryama ta cigaba da abinda take tana bawa granny labarai masu dadi da kwantar da hankali granny ta lumshe idanunta tana cewa “yauwa diyar albarka ya isa haka ma na gode sosai Allah yayi miki albarka allah ta jikan mahaifinki Allah ya rabaki da mahaifiyarki lafiya walalhi har naji saukin zugin da yake min allah yayi miki albarka allah yasa ki gama lafiya .”maryama ta amsa da “Ameen”. fuskarta da bayyanan ne murmushin na farinciki dan idan akwai abinda ke sakata jin farinciki da natsuwa bai wuce taji kana mata fatan alkhairi ba .”
ATA tsaye acikin office dinsa sanye da wasu hadaddun suit wondo da riga ash colour haka ma takalman dake sanye a qafafunsa ash colour ne masu kyau da tsada yayinda jikinsa ke fitar da wani sanyayyen kamshi turare mai sanyi da kwantar da hankali .muryarsa a dake ya kira sunan sectary dinsa “Some !da sauri ta amsa masa da “ yes sir!” tana mai dubanshi cike da girmamawa da tsananin tsoro bai ce mata komai ba ya cigaba da aiki a system dinsa . yayinda itama ta cigaba da tsayuwa tana kallonsa da bayyanan ne tsoro a saman fuskarta ,fuskarsa babu walwala ya sauke kwayar idanunshi akanta tare da mika mata system dinsa “gashi ki duba sakonin masu neman aiki ne yau tsawon sati d’aya kenan ban samu dama dubawa ba yanzu haka ina son na d’an huta kad’an . “okay sir angama yanzu zanyi komai na gama ,ya dawo kan kujera ya zauna yana lumshe idanunshi yayinda some ta soma abinda ya sakata tana kallonsa ya mike a kan doguwar kujera da yake zaune ya kwanta tare da yin pillow da duka hannuwansa yana kallon saman office dinsa .”
Bayan kamar mintuna talatin ya mike ya shiga bayi ya d’auro alwala ya shiga d’akin dake cikin office dinsa domin gabatar da sallama bai fito ba sai around 2 :30 yana fitowa ya kirata da wayar office ,ta shigo da sauri still rike da system din dan sauran kad’an ta gama duba wad’an da suka cancata tace ” sir gani ! “ya ake ciki ? ta d’ago da sauri tana
dubansa sakamakon ganin sunan maryama cikin jerin masu neman aiki “sir !! na duba duka sakonin amman wannna sakon na qarshe akwai ….” kinga kiyi abinda ya dace kawai hanyar fita yayi daga office din “but sir!” kinga akwai abinda zanyi yayi saurin katseta ta hanyar fad’ar haka ya qarasa ficewa ”
D’aya bayan d’aya take bin number masu neman aiki har ta kawo Kan number maryama, ta kira number ya kusan sai uku ba’a daga ba a karo na hud’u ne ta d’auka tare da cewa “hello!daga can bangaren aka amsa mata da” hello ko muna magana da maryam hussein ne ? “Yes of course itace muna kiranki ne daga nan AGC company bisa sakon neman aiki da kika tura mana mun duba takardunki da safur din zanenki duk babu wata matsala yanzu dai sai mun ganki domin yin interview ta qarasa maganar a lokacin da ATA ya dawo office din ya zauna ya janyo system dinsa yana dubawa ”nan take maryama ta rud’e ta shiga kallon umma a rikice “aiki kuma ?”ai ni ban tura wani sakon ai …”umma ta matso kusa daita da sauri ta dafa kafad’anta “ki ce kinji ni na tura masu sako neman aiki .”
maryama tayi shiru tana duban umma tana jin wani irin bugun zuciya” ki natsu kiyi magana dasu da girmamawa” nan take maryama ta ‘bata rai amman babu yadda ta iya dan bazata iyawa umma mutsu akan komai ba ,numfashi ta sauke da karfi tace “shikenan yaushe Zanzo domin interview din ?On 28 march tana gama jin haka ta katse kiran tana duban umma “why umma wani aiki kuma nifa wallahi babu wani tsarin aiki arayuwata tunda yusira tana samo min zan dinga yi a gida “.murmushi umma tayi tana cewa “a’a maryama Kiyi shiru kiyiwa kanki fatan alkhairi karki ja da ikon allah “bazan yi jayayya da ikon allah ba amman ni wallahi umma …” kar ma ki rantse idan kika ga bakiyi aikin nan ba mutuwa nayi amman muddin ina raye sai kin ci amfanin karatunki “maryama ta shagwabe fuska kamar zatayi kuka tace”zanje ne kawai saboda son da nake miki babu yadda zaayi kice nayi abu nakiyi “nima ina sonki maryama shiyasa ma na tura miki neman aiki domin nasan shine cikar burinki wani dalili ne dabam yasa kika ce bazakiyi aiki ba ta qarasa maganar tana riko hannun maryama cikin nata tana jin wani irin a zuciyarta yayinda idanunta suka cika da ruwan hawaye sadam dinta ta tuna .”
ahankali maryama ta zare hannunta cikin na umma ta shige dakinta da umma ta barma ta fad’a kan gado ranta duk babu dadi tunanin rayuwarta ta shig yi sannu ahankali har bacci ‘barawo yayi awon gaba daita .”
“sir ina son nace wani abu shiru yayi bai amsa mata ba sai qarar daddana system dinsa kawai akeji sai data maimaita maganarta sannan yace “okay ina jinki na gama duk abinda kasani na kira wad’an da suka cancata “nasan zasuyi matukar murna dan babu wanda zai samu kiran daga kamfanin AGC bai ji dadi ba “sai wacan banzar yarinyar ba .” ya fad’a aciki ransa amman a zahiri cewa yayi “okay !sectary dai tayi shiru taso ya bata dama tun kafin ta kira number maryama amman yaki ,alamarin mai gidan nasu ne sai hakuri shi kawai zaiyi abinda yake so kuma alokacin da ya ga dama amman wani bai isa ba .”parlour’n mami dauke yake da manyan baki domin kuwa baba qarami ne tare da uncle jay da mami da aunty shahida har ma da aunty abida tare da sultana ,table din gabansu cike yake da kayan motsa baki wanda mami tasa aka kawo masu hira tayi dadi sosai inda aunty abida ta sako batun aikin sultana nan take baba qarami yace “ kai diyata karki damu ta shirya kawai ta fara zuwa aiki bama ita ba idan kina da masu bukatar son aiki akarkashinmu ki kawo muna maraba dasu “.
“wani irin murna tayi tana mai jin dadin maganarsa ita dai mami bata ce uffan ba aka cigaba da hira har sanda ATA ya shigo mami na ganin shigowarsa ta mike zuwa kusa dashi dan tasan baya son azo acika masu gida da hayaniya kuma baqaramin aikinsa bane yayi abinda zai korasu gabadaya “abinda ya bawa mami mamaki bai wuce yadda sultana ta mike tazo ta tsaya gabansa ba tana wani irin rausaya da lumshe masa ido “thank you so much for giving me the job ,gsky naji dadi sosai zanyi aiki a qarqashin AGC company “what ?ya fad’a a matukar tsawace yana kallonta kafin ahankali ya motsa lip’s dinsa “ina ganin kamar kin fara shaye shaye wa ya baki aiki a company “?baba qarami !”tayi mgnr tana duban inda baba qarami yake zaune”ni na bata kuma zatayi aiki alokacin dataso saboda itama uwarta nada ‘yanci acikin AGC “gsky baba qarami kana da matukar kirki amman shi wannan d’an naka ya fiyye jin kai ya manta cewar ni dashi asalin mu d’aya “to ai shi Adam bai da wannan kirki kuma duk cikin zuriarmu babu mara mutunci kamarsa amman wannan karon ko yana so ko bai so yarinya dole kiyi aiki a kamfani kwana nan ma zan dawo na cigaba da kula da kamfani dan nasan kan kamfani fiyye da wannan gatalallen yaron mara kunya idan ma naga dama zan iya dakatar dashi dan dama bai iya tafiyar da kasuwanci ba hauka da shirme kawai yasa a gaba saboda rashin sanin kan kasuwanci komai cikin zafin rai da fushi yake.”
ATA yayi shiru yana dubansa a kaskance har ya soma taku zai isa inda baba qarami yake aunty shahida tayi sauri ta mike tare da rike masa hannunsa gam cikin nata tana masa alamar kar yace komai “amman da kin bari nace wani abu saboda yarinyar sam bata dace da aiki a company dinmu ba dan babu abinda ta iya sai hauka “koma dai menene kayi shiru ka barsu qanin mahaifi ne kuma tmkr mahaifi ne abinda kasan baza kayi wa dad yana raye ba karka yi masa albarkasa albarka dad ne ,dan haka ka tafi d’akinka ka huta” mami tace ko akawo maka coffe “no !ya bata amsa a fusace tamkar itace ta ‘bata masa rai, me zakaci ko sai zuwa anjima ?”bana bukatar cin komai ni kawai ku bani dama nayi magana da wancan mutumin” ina mai baka umarni adamcy karka ce masa komai dan Allah kaje d’akinka kuma a yanzu idan kace masa wani abu ban yafe maka ba .”
shiru yayi kafin daga baya ya nufi hanyar d’akinsa har yayi taku uku yaji sautin muryar abida ta kira sunansa da isa ,da kamar bazai tsaya ba sai yayi wani tunani ya tsaya bata tsaya akoina ba sai a gabansa ido cikin ido take kallonsa tana masa murmushin gefen baki mai nuna alamun sunyi nasara daman da biyu suka shirya zuwa dan su aiwatar da nufinsu uncle jay ne kawai tafiyarsa dabam “ya kaji umarni da baba qarami ya zarta nasan baka ji dadin haka ba ko? amman dai aikin gama ya rigama ya gama ko kana so ko baka so kamar yadda ya fad’a sultana sai tayi aiki kuma a duk inda take so koda kuwa acikin office dinka ne baka isa ka tsaidaita ba, tunda ka kasa bata aiki wanda yake da iko akanka da kuma kamfani ya bata dama yanzu sai kayi duk abinda zaka..”ai bata kai ga qarasa maganarta ba taji saukar wasu lafiyayyun mari ji kake tass tass !! har guda biyu ajere akan kuncinta “enough..!ya fad’a a matukar tsawace gbdy mutanen da ke zaune a parlour’n babu wanda hankalinsa bai tashi ba cikin tsananin tsoro da tashin hankali aunty abida ta tsaya cak dafe da kuncinta tana dubansa fuskarta da bayyanan ne mamaki “Adam ka mareni ? “kad’an kika gani muddin bazaki daina shiga rayuwata ba “
ya fad’a a matukar tsawace .”
Hankalin aunty shahida a tashe ta qaraso inda yake tsaye jikinsa na wani irin tsuma ta dafa kafad’ansa
tare da fad’in “kana da hankali kuwa ?”ka kusan wacce ka mara ?matar aure ce kuma matar shakikinka tana magana tana nuna masa aunty abida da hannunta “.iskar bakinsa ya fesar yace “nasan ko wacece kuma nasan matsayinta kuma itama tasan ko waye ni bana cikin irin wadan mutanen da zuciyarsu Ke jurar raini wallahi idan bata daina enter dinta ba wata rana dukan mutuwa zan mata zaro ido aunty shahida tayi jikinta na wani rawa kamar yadda na mami ke rawa kana hauka ne adamcy ?”I don’t know but I fell like na haukace “wai meke damunka ne da kake abubuwa haka ?”dan Allah shahida ki barni kin cika min kunne abinda ya kamata kiyi ki ja mata kunne ta fita hanyata ta daina shiga lamarina that’s all yana gama fad’ar haka ya haye sama da sauri sauri yake taka step .”
gabad’ayansu da kwayar idanu suka bisa dashi har suka daina ganinsa .”aunty shahida ta soma taku zata bisa mami tayi saurin riko mata tana girgiza mata kai”karki bisa shahida kinsan halinsa “an san halinsa mami amman shikenan sai a zuba masa ido ya dinga abinda yaga dama .”?ai daman ita ke daure masa gindin yin iskanci da wulakanci da taka duk wanda yaso dadin abun itama bai barta ba shegen yaro mara tarbiya kawai “inna lillahi wa inna ilaihi rajiun abinda aunty shahida ta furta kenan alokacin da taji abinda baba qarami ya fad’a tayi data sanin yin maganarta, da kuma tasan kalmar da zai fad’a kenan da wallahi bazatace komai ba jiki a sanyaye mami ta nufi hanyar bangarenta aunty shahida ta juyo ta kalli baba qarami dake qoqarin mikewa tsaye zuciyarta na wani irin tafasa taso kwarai ta furta koda kalma daya ce akan kalmar shegen daya furta ga adamcy amman sai zuciyarta ta gargadeta domin a yanzu ma kuskurenta ne ya janyo ya fad’a abinda ya fad’a bazata so ta sake aikata wani kuskuren ba ranta a ‘bace ta juya tabi bayan mami .”
Zaune ta isketa mami a baki gadonta tayi shiru idanunta na kallon sama d’akinta ta samu waje kusa da qafafunta ta zauna cike da girmamawa ta kira sunanta “mami ! mami ta sauke idanunta tana kallon aunty shahida fuskarta da alamun damuwa aunty shahida tayi kasa da kanta kana ta soma magana cike da biyayya “dan allah mami kiyi hakuri bisa kuskurena sam ban ji dadin abinda baba qarami ya fad’a ba domin idan mutun yace wa d’anka bashi da tarbiya to kai yake