Showing 33001 words to 36000 words out of 184118 words
Chapter 12 - Bakar Taada Hausa Novel Complete
uku na tarar suna jirana.
Da yake a cikin nisha'di nake kafin ka ce kwabo duk na kitse musu.
Hatta Gwaggo sai da ta fahimci irin walwalar da nake ciki, rabon da ta ganni hakan tun komai bai tabarbare mini ba.
Ina idar da sallar isha na nufi wajen Dada.
Na tarar ta idar da sallar ita ma tana jan dogon carbinta.
Ni da Nasiba muke hirarmu, akan makaranta.
Dada ta shafa addu'a.
Muka gaishe ta ta amsa da walwala a dalilin yanzu shiri take yi da ni tunda tana samun alheri a dalilina.
A sanyaye Nasiba ta ce "Kin daina d'ora mana karatu dai Dada".
Ta murmusa ta ce "To kuwa yau zamu yi.
Zan d'ora muku addu'ar da idan kuka lazumce ta babu ku babu yunwa ila yaumil k'iyamati, ina nufin duk tsanani, Ubangiji zai yassare muku abin da zaku ci".
Nan da nan na nutsu domin idan na ji ingancinta na d'orawa Yaya Ummi domin ita kam tana wahala kafin ta k'oshi.
Ta gyara zama ta ce " *ALLAHUMMA RABBANA ANZIR ALAINA MA'IDATUN MINAS SAMA'I TAKULU LAANA IDDAL LI AUWALI WAL AKIRI...*"
Da sauri na ce "Ai mun haddace tuni, a cikin suratul ma'ida take Ashe haka take da falala Dada".
Ta washe baki ta ce "Ai wani bajimin Malami ya tabbatar mana matu'kar zaka biya wannan addu'a to haularka ba dai su rasa abinci ba bare kuma kai da kake bitar ta".
Na 'kyal-k'yale da dariya domin ni na dakatar da ita ne saboda kurakurai da na ji a ciki. Tunda ba yarda zata yi na gyara mata ba.
Ta ce to "Kun ga ni, ni da ku ne anan zan d'ora muku wata muhimmiyar addu'a, sadakar da zaku bayar ku yiwa Annabi salati, ku nema wa Shehu karin karama".
Cikin zakuwa muka ce "To".
Ta yi kasa da murya ta ce " ku dimanci *Ya ladifu*
Idan kun yi dari ba daya a cikon na dari ku rufe da fa'din *"Allahu ladifin bil ibadihi, yar-Razaku man ya shaa'u Wallahu Qawiyin Azim*".
Karon farko da Dada ta biya karatun da babu kuskure, da haka na dage nake ta biya wa a zuwan koyo nake yi, ita kuma sai fa'di take, tana sake gyara mini".
Muka kammala tana jaddada mu ri'ke adduoin nan falalarsu ta kai matu'kar shahara.Ya ladifu kundin sirri ne, gashi babu wahalar fa'da.
Na maze domin tsokanar ta zan yi, dan na ga reactions d'inta.
Na ce "Dada ki daina jan carbi fa, babu kyau Annabi ya ce mu yi da yatsun hannunmu domin su mana shaida ranar gobe".
Ta b'ata fuska kamar ba zata yi magana ba, sai kuma ta kufula ta ce "Asiya tun kafin a haifi Ubanki nake jan jarbi, duk wani sabon addini da kuke son kawo wa na raini Wallahi ba zai yi tasiri a wajenmu ba".
Nasiba ta fashe da dariya yayin da nake jira ta tara mini gayya irin wanda ta mini watannin baya, amma na ji muk'us.
Na jijjiga kai a raina sai fa'di nake "Allah ka sake bawa Yabi tsaron da ba za'a dinga tozarta ta ba." Ta ja robar maganinta da Honarabil ya kawo mata na warwarewar gajiyar tsufa da kara kuzari. Sai kuma na daidaita siga da bugawar zuciya duka daga kamfanin G.H.T. Na murmusa ina tuna a wajen FASEELAT ba zai kai kudin da na ga ni a manne a jikinsu ba. Na Santa a littafin Guduyo.
Nemi dukkan nau'in kayan ght daga gare ta cikin RANGWAME.
*07039269802*
Muna cikin haka sai ga Yaya J.
Ya sha kwalliya da wani farin yadi, d'inkin ya zauna masa sosai.
Ga kamshin turaren Dagmar ya baibayemu.
Cikin farin-ciki Dada take fadin maraba da Jabiru angon Maijidda".
Zuciyata ta buga da k'arfi, shi kuma ya dan diriri ce.
Ya waske da ce wa "Angon Dada dai, ai ke ce ta karfen".
Ta yi dariya ta ce "Yaudara ke nan."
Ya gaishe ta ta amsa da walwala tana tambayar amaryarsa.
Ya bata amsa da ce wa"Tana lafiya a gajar ce.
Ya shige cikin dakinta yana cewa "Zo mu yi sirri Dada".
Ta rarrafa ta bishi domin kuwa mutuminta ne baya rabuwa da kawo mata tsire da turare.
Ita kuwa duk wanda zai mata ungo tana mutunta shi.
Muka ci gaba da hirarmu wacce galibi Nasiba tana fa'da mini ciwon da take ji akan sharewar da Bulkachuwa ya yi mata.
Fa'di take "Dan Allah laifina ne?
Inda ya fahimce ni, da ya k'arfafa soyayyarmu ai komai za'a mini bazan kula kowa ba, amma daga maganar fatar baki ya d'ife, ya ce kada na kuma shiga sha'aninsa. Da yana sona ba zai yi irin wannan fishin ba."
Ta fa'da k'walla na zubo mata.
Jikina ya yi sanyi ainun domin kuwa Bulkachuwa ya riga ya yi rantsuwar ya yanke hulda da ita.
Kamar daga sama na ji muryar Dada cikin karadi tana cewa "Ina! Jabiru ka zo da *BAK'AR TA'ADAH* Mai wahalar tabbatuwa, ta ya ya zaka ha'da mini jikoki kishi? Dama kuma ba jituwa suke yi ba.
Ha'kuri zaka yi da Yabi domin tuni ta samu miji ita ma, dattijon arziki irin albarka."
A sanyaye na ji yo shi yana ce wa "Idan ban samu goyon bayan ki ba akwai matsala Dada.
Kin sani Yabi nake so tun fil'azal. Amma saboda na yi biyayya ya sanya na karbi auren Maijidda. Yanzu da nake son na cike wanccan burin nawa ba sai a taimake ni ba?".
Ya dinga magiya, tamkar zai fashe da kuka.
Cikin kad'uwa ta ce "Jabiru ka zo da babban al'amarin da yafi Dutsen dala nauyi.
Bana jin iyayenku ma zasu amince maka, ka bar maganar nan tun baka tono wani bacin ran ba".
Ba shakka ko nauyi ya ce "Ba zan barta ba Dada! Domin da zan iya barinta da ko ke baza ki ji ba.
Idan ba zaki taimake ni ba, to ki mini adalci kada ki b'ata al'amarin a gaban iyayenmu".
Ta ce "ita Yabi ta gamsu zata aure ka ka had'asu da Maijidda?"
Da sauri ya ce "Ina da tabbacin soyayyarmu ba zata yi zangwayenwar da babu alfarma ko fahimta ba, ban tuntu'beta ba, amma ina da yakinin ba zata juya mini baya ba".
Tsawon lokaci sun yi jigum jigum, muma da muka bar maganarmu muka kashe kunne muna jiyosu, jikinmu ya yi la'asar".
Nasiba ta ce "Tabbas soyayyar da take ta gaskiya kuma k'arfaffa ce ake yin afuwa da sassauci a cikinta."
Na kasa cewa komai domin hausa ta yi cikin hikima. Da Bulkachuwa take.
Bansan ya aka yi ba, kawai sai ganinsa na yi ya fito ya fice a hanzarce.
Sai ga Dada ma ta fito cikin rashin sukuni.
Ta zauna jiki a sanyaye.
Ta kasa jure wa ta kalle ni ta ce "Yabi Jabiru zai ballo wani irin tashin hankali, kada ki sake ki saurare shi.
Ki rike Alhaji nan yafi miki, ina tsoron abin da zai biyo baya."
Na yi k'uri ina kallonta a zahiri gaskiya ta fa'da tashin hankali zai iya biyo baya.
Amma kuma a zuciyata sai nake ganin son zuciya ne kawai yasa ba zata goya masa baya ba. Dan kawai Maijidda d'iyar shalelenta ne, kuma mawadacin gidanmu. Dan sai yanzu na fahimci ba fa wai ku'di ne da Baban Kasuwa ba, kawai a gidanmu ne yafi kowa wadata, saboda talakawa ne mu na sosai.
Me yasa a farko bata hana a bashi ita ba, tunda tasan ni yake so?
Me yasa a wanccan lokacin ba ta yi zaton hakan zai zama tashin hankali a dalilin gaba da kullaci da zai shiga zukatan y'an gidan gaba'daya ba?.
Duk yadda nake da ba'kin jinin a cikin ya'nuwana sai da suka yi kishin abin da aka yi mini, suka yarda ubanmu aka tozarta.
Tashin hankali tuni an shige shi ai, kawai sa'ar da aka yi Baban Marina mai sassauci ne, shi yake ta tsawatarwa dan kada mu kullaci y'anuwansa ko muce zamu rainasu.
Amma iyakacin wula'kanci da kaskanci an yi mana.
Ba kuma wanda ya k'alubalanci hakan sai Baba ta Bulkachuwa ita ma kuma bata da power kamar Babanmu. Duk da a cikin rufin asiri take, dai-dai gwargwado tana dan tagazawa wajen yiwa Dada hidima. Haka nan ita ka'daice kafatalin yan'uwan Babanmu zata aiko da wani abu da sallah ta ce a bawa y'ay'ansa.
Wani lokacin sark'a da yan kunne, ko hijabai, ko y'an takalma masu sau'ki haka.
Dan ko sallar da ta wuce da hijabanta muka je sallar idi ni da Nazira.
Amma Baba Maryo uwarsu Nasiba da bata iya tsinana komai har a Dadan ma ita take zuba mulki, haka nan komai aka yiwa Dada na dangin sutura ko wani abu mai k'yau karshe sai ya zama nata ko na y'ay'anta, ita kuma saboda auta ce da ta shiga rai.
*BAK'AK'EN TA'ADODI* masu yawa na faruwa a gidanmu da dole duk kawaicinka sai zuciyarka ta motsa sa'i da lokaci.
✍️
*Ina tallata muku kayan gyara na mussaman na mutanan Sudan da chadi*.
*Saiwowin dahuwar tattabaru*
*Saiwowin dahuwar kaza*
*Saiwowin Tsumi da Zaki dafa da kanki, ki ajiye ki sha sosai ya ratsa miki jiki*
*Y'aya'n gadali na mussaman*
*Hadadden daka emergency*
*Tsumin kwakwa da zuma*
*Turaren matsi na tsugunno*
*Maganin sanyi sadidan na mara har ma da gabobi*
*Gumba*
*Goran tula syrup and fruits*
*Tsumin Goran tula na asali*
*Duk zaku same su da RANGWAME kuma na asali me ba karabiti ba.*
*Ina aikawa ko ina a fad'in tarairaiyar Nijeriya*.
*Tuntube ni a wannan lambar*
*08032773332*
✍️
*BAKAR TA'ADA*
*NA*
*SURAYYA DAHIRU GWARAM*
*(MRS M.I.NASHE)*
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.}``` ✏️
____________(✪)______________
https://www.facebook.com/profile.php?id=100069755834980
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*Annur food Delicious*
*Da k'arfin zuciya da guiwa na ke muku shunen inda zaku samu kayan da na zano a kasa cikin saukakkan farashi.*
*Shaida nake yiwa kayan annur domin dadinsu da ingancinsu ya kai kurewa*
*HANZARTA ki nemi kayansu dan ki gasgata batuna*
*Garin kunun tsamiya garin danwake, garin borkono, yajin daddawa, man shanu, nikekkakiyar gyada ta kunu da ta miya*
*08039183880*
*Last free page*
*500regular page*
*VIP 1k twice pages*
*2384876855*
*Surayya Ibrahim Dahiru*
*Zenith Bank*.
*Ko*
*7061488065*
*Surayya Dahiru Ibrahim.*
*Opay Bank.*
*08032773332*.
19&20.
Jin na yi shiru tsawon lokaci a dalilin tunanin da nake ta yi.
Ya sanya Dada ta ce "Yabi da alama zaki bawa Jabiru ha'din kai".
Na yi murmushi na ce "A a sai dai na yi imani Ubangiji ne yake shirya komai, dan haka shi na barwa al'amurana ya yi mini zab'i.
Dama kuma ban k'ullace shi ba domin ba shine ya mini laifi ba, sannan Dada idan har auren Maijidda da aka sanya ya yi ya bar ni, bai zama abin kaico da rikici ba, ashe kuwa nawa auren da yake hak'ilon yi a yanzu adalci ne da tsantsar gaskiya".
Jikin Dada ya yi tub'us tabbacin tasan gaskiya na fad'a.
Da k'yar ta ce "Ana barin halak dan kunya Yabi".
Are yi murmushin da yake nuna ba wananan maganar.
Ta sake ce wa "Kuma yanzu wannan dattijon arzikin sai ki bar shi, duk dawainyar da yake faman yi dake da dukkan dangin ki?"
Na sake murmushi na ce "To ai aure gaibu ne, sannan Allah ne ya gadar wa maza su yi ta hidima da macen da suke so dan su ja ra'ayinta. Abin farin cikin ba rok'arsa nake yi ba, haka nan wani nawa bai ta'ba rok'arsa ba."
Ta yi shiru ta rasa me zata ce kuma.
Sai ta hau addu'a da kamun k'afa a wajen Shehu kada zuri'arta ta rikice a dalilin wannan al'amarin.
Har k'asan raina da al'amarin zai yiwu ba wani nauyin da zan ji, domin nawa ne aka k'wace mini saboda kawai zuciyar ahalin gidanmu a cike take da gilli da ba'kin ciki mai yawa.
Kwanaki biyu kullum sai na ga Yaya J ya zo gidanmu, kusan a nan yake yini, ba shi k'ofarsu ba shi a wajen Dada.
Rashin sukunin da nake ga ni a tare da shi, ya tabbatar mini kasafin ya cud'e fiye da zatonsa.
Bai kuma neme ni ba.
Kwanaki suka yi ta shud'e wa har aka samu kwanaki bakwai babu tartibiyar maganar Yaya J.
Dama na sani mawuyacin abu ne su amince, sai dai dan ya ce zai iya ha'diye gatari ne, shi yasa na sakar masa k'ota ko zai dace ya ha'diye, bayan ya sha kakarin tagwaitakar riskar ajali.
Ina cikin wannan yanayin sai ga wani b'acin ran, gidan da Bulkachuwa ya tura su Baba akai masa ku'din aure suka shafa wa idonsu toka suka ce basu san wannan maganar ba, ba zasu dauki y'arsu su bawa wanda aka bulale a bainar nasi bisa k'azamin laifi irin wannan ba, kuma marar tartibiyar sana'a.
A sanyaye su Baba suka dawo babu kuzari.
Dukkan iyayenmu ukun nan sun ji ciwon abin da aka yi musu. Amma ba wanda ya hango irin wannan tozarcin mai ciwo suka yiwa Babanmu ta hanyar hana Yaya J aure na.
Shi kuma Baban Kasuwa ya dauki tasa y'ar ya ba shi.
A gabana Baban Marina yake yiwa Bulkachuwa bayanin halin da ake ciki, cikin alhini da bacin rai.
Ba wata damuwa mai yawa ya ce "Babu damuwa Baba! Ban damu ba, domin an hana ni aure a cikin gidan nan ma. Dan haka dan waje sun hana ni ba zai zama abin kaico ko tashin hankali a gare ni ba.
Ciwon da nake ji daya ne! Da na yarda da hukuncin Allah. Na amince aka mini bulala sai kuma na zama abin k'yama a idon al'umma.
A wauta ta imani na yi, domin na yi biyayya ga abin da Allah ya zartar ba tare da bin ra'ayin turawa na yiwa hukuncin Ubangiji tawili ba.
Na sani na yi laifin da ku kanku na zubar da darajar gidanku, amma ina yiwa Allah kyakkawan zato zai katange ni daga sake aikata wa tunda na yarda da hukuncinsa, na zabi tereren duniya akan na lahira.
Matu'kar kuwa mutane zasu ci gaba da nuna irin wannan *BAK'AR TA'ADAR* Akan mai laifin da ya d'aura d'amarar taubatun nasuha ba shakka zasu dauwamar da mutum cikin b'ata, tunda idan ya dawo kan sahihiyar turba, ba zasu karbe shi ba, ba zai tsira daga yamididinsu ba."
Baba ya kasa ce masa k'ala domin jikinsa ya yi sanyi da kalaman na Bulkachuwa.
Ni kaina da nake gefensu ina wa Baban Marina wanki ba k'aramin sanyaya jikina kalamunsa suka yi ba.
Na sani gaskiya ya fa'da, hana shi aure da ake yi kuma ba shine mafita ba, illah bashi lasisin sake dulmiya cikin zunubin da ake k'yamarsa.
Baya ga hakan basu taimaki y'ay'ansu ba, tunda dukkan y'anmata nasa da aka hana shi auren su sonsa suke tamkar su bashi kyautar kansu, ashe kuwa idan ya so lalata rayuwar yaran nasu cikin ruwan sanyi zai yi hakan, tunda Ubangiji ya kyautata masa halittarsa k'warai da gaske .
Dan haka zai iya amfani da son da suke masa ya lalatasu a banza, idan kuma hakan ta faru zai yi wahalar gaske ya karbi aurensu domin komin lalace war namiji baya son lalatacciya. Cigaba aka samu ko tabarbare wa?
A wannan rana na fahimci ashe cikakken mutum ne mai nutsuwa, kawai sharholiyar ce ta yi masa k'awanya.
Ya katse shirun da Baba ya yi ta hanyar ce wa "Baba na gode sosai, zan cigaba da istigifari, idan al'amura suka sake daidaita mini zan fara sana'a, zan je Bulkachuwa na nemi aure ina da tabbacin a dangin mahaifina ko nafi hakan lalace wa zan samu mai k'arfin halin da zai bani aure tare da fatan auren ya zame mini sanadin shiriya da bud'ewar arziki."
Ya mike ya tafi yana sake godiya sosai.
Ajiyar zuciya kawai Baban Marina yake yi, na lura ba k'aramin ki'dima ya shiga akan al'amarin ba.
Murya babu amo ya ce "Yabi idan kina son Alhaji ki ce masa ya turo wakilansa, idan kuma ba kya sonsa to ki fa'da mini zan sallame shi".
Na yi k'asa da kaina na kasa amsa masa, daga haka kuma sai ya fita, na bishi da ido amma tunanin a yadda jikin Baba ya mutu murus akan al'amarin Bulkachuwa da ace Adda Nazira ba ta yi aure ba, Babanmu na iya juya wa nak'asunsa baya, ya bashi auren ta.
A fili na furta "Alhamdulillah da Allah ya sanya ta yi auren ta ta barranta da auren tantiri ma'abocin *BAKAKEN TA'ADODI*.
Haka kawai sai zuciyata ta buga da tsananin gaske, a dalilin ayyana wa da na yi, wata'kila fa idan ban tsayar da miji ba, Baba yana iya cewa ya bashi ni.
Nan da nan na tsirtar da yawu saboda kyankyaminsa da ya taso mini.
Gashi dai zabgegen saurayi ne dogo cak mai murdadden jiki tamkar ya fito cikin Kyawawan Tirkawa(Turkish).
Amma kwata kwata baya burge ni duk da farar fatarsa da bak'ar sumarsa, da suke rudar y'anmata.
Asalima Y'ar tsama muke yi, sassaucin rikicinmu a dalilin kwamshina ne, domin sosai yake yi masa alheri.
Ya karbi takardunsa, samun aikin ne dai shiru, amma ana saka rai tunda kwamshina baya wasa kuma mutuminsa ne. Tuni Yaya Salisu ya samu aiki a asibitin Toro a matsayin accountant na asibitin tunda dama bangaren ya karanta.
Yaya Rabi'u da Bulkachuwa ne shiru amma akwai kyakkawan zaton suma zai samo musu.
Wananan dalilin ne ya sanya ya daina tsokanata ta hanyar muzanta ni.
*Idan kina bukatar Oriflame products ko wanne irin ne, ko Kuma kina sha'awar yin register da su*. *Ki tuntubemi babbar dealer din su Aisha lame*
*Ina kuma fad'a muku akwai da daddan ganyen shayi na Lame Tea*
*Akwai pop corn*
*07036662633*
A fili na furta "dutse a tsakanina da Bulkachuwa ya Rabb".
Ina wankin ina jaddada wa kaina matu'kar Yaya J bai yi yun'kuri mai k'arfi ba, to nan da lokaci kankani zan bawa kwamishina dama ya fito tun zuciyar Baba bata ayyana masa wani al'amarin da zai iya kassara ni, ya dauwamar da ni a cikin ba'kin ciki mai tsananin gaske ba.
Na kammala wankina.
Mama ta fito ta ce "Yabi anjima zan aike ki gidan Nazira".
A ladafce cikin murna na ce "To"
Domin kuwa ha'din baki muka yi da Naziran, saboda na yi ta tambayar Baba zani gidanta yana hana wa, basan me yasa yake hana ni zuwa ba, amma bai ta'ba yin k'orafin zuwa koyon sana'ar da nake fita ba kullum.
Duk kuwa da ce wa ake yi shargalle nake yi da sunan koyon sana'a.
Shiyasa Nazira ta ce wa Mama ta bani kwanuka na kai mata kar aba wa marar wayo ya yi b'arinsu su yi lamba.
Tunda idan ita ce ta aike ni Baban ba zai hana ba, ba kuma zai tambayi aiken menene ba.
Dan haka a gurguje na shirya na tafi.
Muna zaune ina bata labarin yadda muka yi da J.
Ta galla mini harara ta ce "um um uhum. Ashe dai Yabin bata san ciwon kanta ba. Har wane ne Jabir kuma?
Idonta ya ciko ta ce "Allah ka sanya sai bayan raina zaki zama matarsa!.
Jikina ya sabe da rawa na ce " Addda Nazi!
Cikin gigita domin ban ta'ba ganin fishi mai yawa a tare da ita irin