Showing 129001 words to 132000 words out of 184118 words
Chapter 44 - Bakar Taada Hausa Novel Complete
k'wace mini kai?"
Na fa'da hawaye na ziraro mini. Ya tsananta rik'on da ya yi mini ya tausasa harshe ya ce "me yasa kika karaya haka Asiya? Ban ji akwai wata mace da zata firgita ki ai. Ni naki ne, a hannunki na ke. Ki daina damuwa da abin da yake gaibu ne. Al'kawarin da zan miki d'aya ne. Har abada kin wuce wula'kancina. Kina da alfarmomi masu yawa da babu wata macen da zata samu irin alfarmomin ki a waje na."
Bai bar ni ba. Sai da na samu nutsuwa. Can kuma ya ke ce da dariya ya ce "Ubangiji yana ta kama mini Asiyata. Kamar yau take fa'din me zata yi da Basamude irina. Kin tuna amsar da na baki a ranar?"
Na k'yale shi domin yanzu ya riga da ya lakanci tuno mini abubuwan da suke kunyata ni.
Bai bar maganar kamar yadda na barta ba sai da ya ce "A lokacin na ce miki akwai ranar da zaki yi kuka akan son basamuden nan. Sannu a hankali komai na fa'da a kanki Ubangiji yana zartarwa. Na share ban yarda na tanka shi ba.
Cikin Ikon Allah Tijjani ya fara safarar kai kayan miya kasuwanni daban daban na cikin jahar Bauchi da makwabtanta irin su Jigawa.
Da wuri yake fita. Ya je ya kai. Idan zai dawo kuma sai ya lodo mutane. Gaba'daya ya ajiye girman kai, da tunanin yana da kwalin digiri.
Ba'a dauki lokaci mai yawa ba, muka rabu da matsalar babu. Domin sosai yake samun ku'di tunda ba balance yake kai wa ba. Ni ce ma na koya masa dabarar ya dinga ajiye wani abu a banki saboda ko watarana motar zata bukaci gyara. Ko wata lalurar zata gitto bakatatan. Ba ja in ja ya yarda da shawara ta. Akai akai yake yiwa mahaifiyarsa da Baban Marina sako. Dada ma bai barta a baya ba. Wani lokacin idan ya je Jos sai ya tsaya ya musu alheri, sannan ya taho. Hatta su Baban Tsakiya yakan yi musu alheri kai musu kayan miya ko doya.
Ku'di ne dai baya basu.
Wannan rufin asirin da ya samu ya sanya masu yi masa kallon banza suka shiga nan nan da shi. Akai akai ake bugo masa waya, sabanin lokacin baya da ba'a saka shi cikin mutane bare a tuna da shi.
Rannan kwatsam sai ga shi ya dawo da Nasiba tare da akwatinta shake da kayan da suke nuni zata jima tare da mu.
Na gama nazarinta. Gaba'daya ta goge ta yi fes da ita. Ta cika ko ina dam tabbacin yanzu tafi samun nutsuwa.
Ni ce shaida muka akan son da take yiwa Baban 2.
Na ha'diye komai na yi mata uzziri tunda shi so Ubangiji ne yake kitsa shi a zukatan bayinsa. Sannan a lokacin da aka zartar da aurena da shi bata yi mini koamai ba, sai fatan alheri duk da kuwa yadda al'amarin ya buge ta. Dan haka nima a yanzu zan mata kawaici ka'dan. Amma ban da aurensa. Wannan kam bazan iya ba. Na kuma tabbatar da niyyar hakan aka turo ta. Uwarta zata yi komai dan ganin Tijjani ya aure ta ba tare da ta jin kunyar ubana ba. Ta manta yadda ta ture komai ta yi sanadin datse soyayyarsu. A yanzu kuma da ake ganin ya samu mamora shine za'a lika masa ita. Ko kunyar ha'damu kishi bata yi. Kiri-kiri take nuna mini tsana tamkar wadda agola ce ni a gidan haka take yi mini.
Da daddare muna kwance gaba'daya na kasa sakin raina. Har shi ma na ji haushinsa ya turnik'e ni, akan wanne dalilin zai dauko ta tunda ga Toro su taho Bauchi?
Ya kasa ha'kuri ya ce "Little wai mene ne?"
Na yi masa banza. Ya tunzura ya ce "Amma dai kin san na tsani na miki magana ki share ni ko?"
Na kasa bu'de baki na ce mass komai a dalilin kuka nake yi irin na sharbe.
Jin shesshekar kukana ya sanya ya shiga rud'u.
Ya dinga tambayar ba'asin kukan nawa. Sai da na tabbatar na rikita shi matu'ka da gaske sannan na ce masa "A kan me za'a sa ya kawo mini Nasiba gida ba tare da yarda ta ba?"
A hankali ya ce "Dada ta ce na taho da ita ta mana kwana biyu. Ita ma kuma ta da'de tana fa'da mini tana son zuwa ta ga sabon gidanmu. Shine yau da ta ce zata biyo ni na ce to".
Na tashi na zauna na ce "Hakan ya yi. Wato har waya kuke yi ko Tijjani?"
Ya zuba mini ido sosai domin yasan tunda na gatsa sunasa gatsal to zan iya yin komai na rikici a tsakaninmu.
Ya sassauta ya ce "Dan ta zo mana bakunta mene ne a ciki?"
A tunzure na ce "akwai komai ma. Bana son bakuntar ta, ba kuma zata zauna mini a gida ba".
Ga mamakina sai ce mini ya yi "Wai gidan na ki ne?"
Na kad'u matu'ka da gaske. A matu'kar sanyaye na ce "A a naka ne mantawa na yi, amma ka tabbatar ba zan yarda da kai alhalin ina ganinku a gida daya ba." Na koma na kwanta, shi ma ya kwanta bayan ya juya mini baya da alamu ya yi matu'kar fusata da na ce Ban yarda da shi ba. Ya sani kuma ina da hujjar da zan guji zamansu a gida daya, mussaman karamin gida irin namu.
Washagari muka tashi kowa na ganin laifin d'anuwan sa. Na yi matu'kar boye wa Nasiba halin da muke ciki. Tare da ita muka karya a kwano daya. Tunda shi ya fice bai saurari abincin ba.
Da daddare ma hakan muka sake kwana babu jituwa. Domin nasan jira yake na ba shi hakuri, na kuma rarrashe shi. Ni kuwa al'amarin da yake cina ba k'arami ba ne.
Ko magana bama yi ni da shi.
Ba dan bana son ta fahimci akwai matsala a tsakaninmu ba da ko dakinsa ba zan je ba.
Amma ina zuwa bayan mun sha hira ni da ita.
Ranar da ta yi kwanaki biyu da daddare mun kwanta. Na bu'de baki na ce "Tijjani gobe bakuwarka zata yi kwanaki uku a gidanka. A ka'idar shari'a kuma bakunta ta kwanaki uku ce. To kasan yadda zaka yi ta bar maka gidan a gobe, ko kuma ka ga abin da baka so".
A tunzure ya ce ",Tun yaushe na ga abin da bana so Asiya? Ai tunda babu yarda a tsakaninmu magana ta k'are. Ba kuma zan kore ta a gidana ba. Ni da kika gan ni bana manta alheri komin tarin kalubale da rashin kirkin mutane. Dan haka komai zaki yi Bismillah".
Na ce "Hakane. Madallah da Tijjani".
Kasan zuciyata kuwa tamkar na tashi na cinnawa gidan wuta haka nake ji.
Washa gari ya saka kai ya fice bayan ya amsa gaisuwar ta a tsaitsaye ba tare ma da ya kalle ta ba. Haka kuma yake yi mata tunda ta zo.
Mun gama karyawa na kalle ta na ce "Nasiba zan je Kangire dubiya. Wata'kila na kwana, wata'kila kuma na dawo. Na tafi da yaran nan ko na bar miki su?"
Zucyarta daya ta ce "Ki barsu mana indai baza su yi rikici ba. Idan suna ganin Babansu baza su yi kuka ba ai babu damuwa".
Na ce "Hakane.
Na shirya kayana set uku a dan k'aramin akwatina, na yi sallama bayan na yi dabarar tura tagwaye kwaso shanya a baya. Na fice a hankali, bayan na ce mata na bar ki da wahalarsu kuma".
Ina jin ta tana fa'din 'yayanki ba nawa ba nawa ba ne ke nan Yabi?"
Ban tsaya bata amsa ba gudun kada su fito, su ga tafiya ta.
Da azahar ya koma gidan a dalilin ya dawo daga Dass.
Ya tarar da yara na kukan neman Amminsu. Ya fahimci Yabi ta fice ta bar gidan babu izininsa. Hankalinsa ya kai k'ololuwar tashi, ransa ya baci ainun.
Cikin hikima ya ce "Da nasan da wuri zan dawo ai bazan bari ta fita ba.".
Nasiba da take kicin ta ce "Nima da ta ce mini zata iya kwana a can na shiga zullumi."
Ya mik'e ya ri'ke hannun yaran suka fita, ya rasa inda zai tsoma ransa da wannan tashin hankalin da ya kewaye shi.
"Sha'anin mata yana da gigitarwa. Mene ne abin tafiya ki bar dakinki idan ba kalen masifa ba little?" Ya furta a fili a kuma ki'dime.
*Annur food Delicious*
*Da k'arfin zuciya da guiwa na ke muku shunen inda zaku samu kayan da na zano a kasa cikin saukakkan farashi.*
*Shaida nake yiwa kayan annur domin dadinsu da ingancinsu ya kai kurewa*
*HANZARTA ki nemi kayansu dan ki gasgata batuna*
*Garin kunun tsamiya garin danwake, garin borkono, yajin daddawa, man shanu, nikekkakiyar gyada ta kunu da ta miya*
*08039183880*
✍️
*Oriflame products*
*Daga make up artist din Guduyo*
*Idan kina bukatar Oriflame products ko wanne irin ne, ko Kuma kina sha'awar yin register da su*. *Ki tuntubemi babbar dealer din su Aisha lame*
*Ina kuma fad'a muku akwai da daddan ganyen shayi na Lame Tea*
*Akwai pop corn*
*07036662633*
*JAN HANKALI*
*BAN YARDA A HADA MINI DOCUMENT BA! BAN AMINCE BA.*
*DUK WACCE TA YI HAKAN YANZU, KO BAYAN NA KAMMALA LABARIN NAN, WALLAHI NA KAI TA K'ARA WAJEN UBANGIJI.*
*FATAN ALHERI GA*
*Aunty Umma Kulsum Muhd Kumo*
*Aunty Maryam Saminu Sulaimanu*
*Gaisuwa da fatan alheri, na gode sosai da alherinku a gare ni*.
*Yabo da godiya ga*
*Mamana*
*Hajiya Zahra Shehu*
*Fatan alheri mai yawa a gare ki da ahalin ki*
Tsawon lokaci yana tunanin abin yi. Ya rasa inda zai dosa meman ta. Ya tabbatar ba zata nufi Toro ba.
Ya tambayi kansa to ina zata tafi har tana fa'din idan dare ya yi zata kwana?.
Kukan Hamim na sake rib'anya tashin hankalin da yake ciki.
Ga haushinta, ga zullumin fishinta gaba'daya sun ha'du sun yi masa rubdugu.
Ya mike ya shiga gidan, ya tarar ta kammala abincin da take yi. Ransa ya sake b'aci da abin da Yabi ta yi, wato manufarta ta bar musu gidan su yi komai ma.
Cikin rashin sukuni ya ce "Ha'da kayan ki zan kai ki tasha ki koma gida. Tafiya ta same ni zuwa gadar mewa. Ba zai yiwu kuma na bar ki ke ka'dai a gidan ba."
Cikin nutsuwa ta ce "To". Amma yaran fa?"
Cikin rashin sukuni ya ce "Zan kai su wajenta daga can, tunda hanya ce".
A hankali ta ce "To ko zamu tafi gaba'daya ina ajiye mu a wajenta sai mu dawo gobe da ita".
Da rawar ya ce "A a, mu je dai na kai ki tashar, ba zai yiwu na yi ta yawon kasuwa da ke ba."
Tunda ya ajiye ta a tasha yake gararanba a titunan Bauchi. Gaba'daya ya rasa ta inda zai fara nemanta.
Nasiba kuwa da ta Isa Toro a gidan Marina ta tarar da gyatumarta tare da Dada.
Cikin mamaki Dada ta ce "Ke da kika ce sai an gan ki kuma sai ki dawo, duka duka yaushe kika tafi ne?"
Cikin nutsuwa ta ce "Yabin ce ta tafi Kangire dubiya. Shi kuma ya ce na taho tunda kwana zata yi".
Dada ta ce "Ikon Allah. Ga kuma uwatata bata fadi wani abu ya samu ba, bare mu yi mata ja je".
Sai lokacin Baba Maryo ta ce "Hmm Wallahi ba abin da ya faru, kawai zamanta ne bata so a gidan. Shi kuma da yake salallamamme ne shine ya ce ki taho. Yarinya k'ank'anuwa sai azabar iya barikanci. To duk shure shuren kaza baya hana a dirza mata wuka. Yabi akwai tuggu Wallahi shi yasa na washe ta, bata da kunya ko kad'an bare mutunci".
***
Da azahar na dira a Bulkachuwa. Babah sai ganina ta yi kwatsam. A sanyaye ta shiga yi mini barka da zuwa. Sai da na yi sallah ta bani abinci da ruwa, na ta'ba ka'dan na rufe. Ta zuba mini ido ainun. Ta ce "Wai mene ne damuwar ki ne Yabi? Maimakon tunda yanzu ba shayarwa kike yi ba, ki murje ki cike, amma kullum sai fige wa kike yi tamkar wacce ake tsakurarki?."
Na yi k'asa da kaina, ba tare da na ce komai ba. A tausashe ta ce "Yanzu me yasa kika taho ba shiri ba komài?"
Na fara hawaye, ba tare da na bu'de baki na ce komai ba.
Ta ri'ke hannuna ta ce "Da ke da Ihisan daya nake jinku. Dan haka zan fa'da miki gaskiya. Gaba'daya aure hakuri ne. Ba yadda ake so ake ga ni ba. Idan Ubangiji yasa farin yafi ba'kin yawa a cikin zamantakewar sai a yi ta gode wa Allah. A kuma yi hakuri da inda aka kuskure. Idan kuwa ba hakan ba sai ki ga gidan aure ya zama tamkar kurku dan tsanani. Adadin mutuwar aure ya yi ta tunbatsa. Yin sassauci da kawaici babban jigo ne da yake rike da gidajen aure.
Cikin kuka na ce "Wallahi ina yi."
Ta ce "Na sani. Yanzu fa'da mini abin da ya yi miki har kika kasa hadiye wa"
Cikin kuka na tsara mata yadda muka yi da shi, ban yiwa al'amarin kwaskwarima ba. Da kuma kafewar da ya yi sai ta zauna da mu saboda tana da alkairai masu yawa a idonsa. Cikin kuka na ce "Ni kuma Wallahi bazan yarda na zauna da ita ba".
Ta yi shiru, na tsawon lokaci kafin ta ce "Tashi ki je d'aki ki yi kwanciyar ki. Kar kisa wannan maganar a ranki. Kina da gaskiya dan hakan zan tsaya miki, da kuwa baki da gaskiya da a yau zan mayar da ke dakinki".
Dad'i ya kama ni. Babah ta fahimci irin rad'ad'in da nake ji. Ina kwance ta shigo ta ce "Kuma sai kika bar mata yaran?"
Fuska ba walwala na ce "Eh". Ta ce "Da kin taho mini da su, ina cikin kewarsu ainun. Amma bar masa din da kika yi akwai hikima mai yawa tunda ba sha suke yi ba. Kukan Hamim kadai ya ishe su ai. Ki yi zamanki ba wanda zai san kina nan tunda Umman gidan nan tana garinsu tafi wata a can. Ko Nasiru ma baya gari. Aliyu ne ya ce zai zo yau, to kuma ya fasa sai satin sama, saboda zasu je Ibadan".
Ta dauki abin da zata dauka ta fice. Tana fa'din "Da ni yake zancen".
Sai da dare ya fara ja sannan ya koma gida. Bayan Nasiba ta masa text din ta sauka lafiya. Tunda ta kira shi ya fi sau biyar yana gani amma bai dauka ba.
Da asuba ya kira wayar Yaya Ummi.
A d'an tsorace ta ce "Yaya Bulkachuwa barka da asuba"
Murya na amo ya ce "Ummilolo taimake ni ki bani lambar mijinki na nemi izinin aikenki yanzu zuwa gidan Marina".
Ta ce yana jinka ma yanzu haka, na saka ta a sifika ka tambaye shi."
Ya bu'de murya cikin ladabi ya gaishe shi. Ya kuma roki alfarmar zai aiki Ummi zuwa gidan akan wani al'amari da tayar masa da hankali.
Nan da nan ya ce "Babu komai na amince ta je. Ya mika wayar ga Ummi.
Ta ce "Ya ya ne Yaya Bulkachuwa?".
Cikin zullumi ya ce "Asiya ce ta yi mini yaji Ummi! Tun jiya ta fice ta bar mini gidan da yara."
A zabure ta ce "Subhanallah a kan me Yaya Bulkachuwa?"
A sanyaye ya ce "Hmm! Kawai mu bar maganar tattauna wa ki tashi yanzu ki je gidan, ki duba ko ina. Idan kin ganta kada ki nuna komai kawai ki dawo gidanki. Ki fa'da mini sai na taho".
Yana rufe baki Ummi ta ce "Gaskiyar magana ban jin Yabi zata iya zuwa gidanmu da sunan yaji. Ta tsani yamididi, tana kuma matu'kar tsoron bacin ran Baban Marina".
Ya fesar da iskar damuwa ya ce "To saboda Allah ba kisan inda take ba Ummilolo?"
"Wallahi ban sani ba, ko waya bamu yi da ita ba. Amma bari na je sumame gidan Nazira".
Da sauri ya ce ",Yauwa Ummilolo, na gode, hanzarta dan Allah".
Ta ce "Zan sallami mutanan gidan da abin karyawa tukun".
Akan dole ya ce "To."
A hanzarce ta gama dumame ta sallami kowa.
Kusan da sanda ta shiga gidan Nazira domin ta tabbatar mijinta baya nan. Amma bata ga wata alama mai kama da rashin gaskiya ba. Suka gaisa ta tambayi yara.
Ta ce "Daga ina Yaya Ummi?"
Ta ce "Mafarkin ki na yi Nazira shi ne na taho dan na ganki, na ga lafiyarki".
Da'di ya kama Nazira. Ta ce "Madallah da Yaya Ummi. Kin kuma tarar da ni lafiya, har na karya na yi hidimar gida".
Ta mike tana fa'din "Alhamdulillah! Tunda na ganki lafiya bari na tafi".
Ta hanzari Nazira ta yi kicin dinta ta juyo mata dafadukan macaroni mai dan dama a madaidaicin filas. Ta ce ga shi ki kaiwa yaran nawa. Na maigidan ne bai tsaya karyawa ba. Ana ta jiransa zasu je Lame. Ya dai sha kunu a tsaitsaye."
Ta karba da godiya ta tafi. Maimakon ta zarce gidan ta, gidan Marina ta yiwa tsinke. Duk wani bin kwakkwafinta bata ga ko ganin wata alama da take nuna sun san Yabi bata gidanta ba. Dan haka suma ta yi musu sallama ta tafi ba tare da ta bu'de musu komai ba.
Sai da ta isa gidanta sannan ta kira Bulkachuwa ta tabbatar masa Yabi bata zo Toro ba. Ya lalube ta anan Bauchin.
A rikice ya ce "Yanzu Ummi abin da Asiya ta yi mini dai-dai ne?"
Kai tsaye ta ce "To ai bansan me ya faru ba Yaya Bulkachuwa".
Ya ce tsaya ki ji, ki fa'da mini inda nake da laifi, ki kuma fa'di shin ta kyauta mini kenan?"
Ta ce "To zan fa'di gaskiya tsakanina da Allah kuwa".
Ya numfasa ya shiga koro mata bayani tiryan tiryan na gaskiya.
Bata katse shi ba sai da ya gama tsaf ya ce "kin ji abin da ya faru".
Ta numfasa ta ce "Ka yarda gaskiyar magana zan fa'da?"
Da sauri ya ce na gasgata ki Ummi. Komin tasirin jini na sani zaki yi adalci domin ke din mai kauna ta ce na shaida."
Ta ce "Na gode sosai. Amma gaskiyar magana kai ne baka kyauta ba. Kasan Yabi tasan akwai tsohuwar soyayya tsakaninka da Nasiba. Yanzu Kuma bata da aure. Akan wanne dalilin zaka dauke ta da kanka ka kai ta gidanka da sunan ta zauna, ba zama irin na bakunta ba.? Me yasa da Yabi ta ce bakuntar kwanaki uku ta amince ta yi muku baka yarda kun fahimci juna ba? Me yasa ka ankarata ta hanyar ce wa Nasiba tana da darajar da ba zaka kore ta a gidan ka ba?. Tsakanina da Allah wannan maganar ta yi nauyi a zuciya. Ai da sai ka ce mata ita ta kore