Showing 150001 words to 153000 words out of 184118 words

Chapter 51 - Bakar Taada Hausa Novel Complete

shi ma ya sawa bakinsa linzami tamkar yadda na yi sai ya zarce da ce wa "Baban kasuwa ne kawai mai mace daya, shi ma nasan a dole yake zaune bai k'ara ba. Shi Baban Marina din da yake tunzuri irin haka ai uku ne da shi, shine ni zai nemi hana ni jin yadda a ke ji?"
Na kalle shi da fishi sosai na ce "Ya isa haka! Ina rantse maka da Allah Tijjani zamu kwashi y'an kallo. Komai kake ji da shi na wulakanci ya tsaya iya kaina. Amma ka yi kad'an ka tabo alfarmar ubana. Ya wuce hakan Wallahi".
Bansan ya aka yi ba jikinsa ya mutu. Ya kasa ce wa uffan.
Na ja tsaki mai tsananin gaske na tashi na bar masa wajen.
Muka k'ulla gaba sosai. Domin ya kullaci zuwan Baban Marina da kalamansa, dazu har da shaguben laifinsa ya shafi twins a wajen Baban Marina bai kula su ba. Yana wankin kayansu yana mini azanci. Ya kuma zabe iya nasu ya bar mini nawa. Ko kallo bai ishe ni ba. Domin sosai nake jin zafinsa.
Ranar da aka tabbatar mini su Baban Tsakiya sun kai masa kudin aure gidan iyayen Nasiba kwana na yi ina kuka. Sassafe na yi Bulkachuwa. Ina zuwa na sake tarar da wani abin alajabin. Fad'a kawai Babah take mini wanda babu rarrashi ko nuna soyayya a ciki. Cikin sanyi ainun ta ce "Haba kina da k'warzaba Yabi. A kanki aka fara yin kishiya ne? Tun yaushe kike jidali?. To ni bazan iya hana shi aure ba. Ni nan da kike ganina kan kishiya aka kawo ni. Mahaifiyar ki ma kan kishiyar ta zo, sannan bayan ita ma ya sake yin wata. Ina dalilin wannan kai komon da kike yi na azina?"
Na kafe ta da ido na ce "Har cikin zuciyata nasan ba haka siddan kika mini hakan ba. Allah Ubangiji ya kawo karshen wannanan al'amarin." Na fada ina kuka sosai. Ina kula da yadda kukan nawa ya raunanta amma ta kasa ce wa komai.
Haka na dawo Bauchi da kaina. Tare da hak'urin dole. Amma ni kad'ai nasan me nake ji a zuciyata.
*Toro*
Tunda a kai kudin auren Tijjani gabadaya lafiya ta yiwa Baban Marina karanci. Ba komai ke nukurkisar sa ba illah yadda babu wani mutum d'aya a gidan Marina da ya fito ya nuna rashin dacewar al'amarin. Ya kasa samun Hauwa uwar Tijjani a waya. Kowa murna yake yi da auren.
Tun jinyar na sand'arsa a hankali har ta kai ya kwanta. Ba'a samu wanda ya fito ya soki al'amarin a cikin yan'uwansa ba, balle a farga da yadda bakinciki ke sakatarsa. A wannan karon dukkan juriyarsa ta k'are. Ya yi amannar yan'uwansa basa son sa da gaske. Ban da haka mene ne za'a fifita Nasiba akan Yabi da take yar gidan?
A cikin wannan yanayin Babah ta Bulkachuwa ta zo garin.
A dakinsa ta tarar da shi. Kallon sa kawai ta yi hawaye ya tsinke mata. Domin a cikin sati kacal tsufa ya keto masa na ban mamaki. Tausayi ya kamata, ta sani bakin cikin yadda al'amarin ya juye ne yake neman kassara shi. Mussaman yadda kowa ya koma bangaren uwar Nasiba da ta take komai ta runtse idonta. Babban abin da yake damunta bata san me yasa take jin tamkar idan ba a yi auren Nasiba da Tijjani ba zata dauma a cikin kaico. So take ta bude baki ta barranta kanta daga lamarin amma ta kasa.
Murya na rawa ta ce "Sannu Yaya!
Ya kalle ta da idanuwansa da suka kad'a. Murya babu amo ya ce "Hauwa Tijjani zai yi aure nan da kwanaki kad'an. Bana inkarin k'arin aurensa domin kuwa yana da sukunin da zai ajiye mace hudu ma. Amma ki sani Wallahi ba zai had'a mini y'aya'na guda biyu kishi ba. Idan har dukkan ku babu mai fitowa ya yi magana to ni na yi. Bazan yarda na mutu na bar Yabi a cikin wannan taskun ba. Domin na san kafatalin ahalin gidannan ba zata samu wanda zai mata adalci irin na uba ba. Ke nake da garantin zaki tsaya mata. To ga shi ke ma an juya miki tunani. Shin kina ganin ya dace na zuba ido ana jifanmu ni da ahalina da sihiri bayan na jure dukkan k'iyayya da warakin da na shafe lokaci mai yawa ana mini ni da zugata?"
Kamar a tsaorace ta ce "A a Yaya! Ni kaina ina tambayar kaina me yasa na kasa yin magana? Me yasa nake jin tsoron yin magana? Me yasa tashi d'aya na ji soyayyar al'amarin ta shige ni fiye da komai a yanzu?"
Ya jijjiga kai ya ce "Na barwa Allah ya kawo mini dauki. Abin da nake so da ke yanzu. Yau din nan ki shiga mota ki dauko mini Yabi. Saboda ke na bawa Tijjani ita. Kin sani a wanccan lokacin ba shi da rigar da za'a bashi aure, asalima hana shi ake yi gida da dawa. Ke na bawa amanarta, ke na damkawa ita a hannunki. A yau kuma ina son ki dawo mini da ita salin alin yadda na baki ita cikin girma da arziki".
Ta fara kuka mai tsananin gaske. Tana fad'in "kada ka yi hakan Yaya. Daure mu bi al'amarin a nutse. Tunda har ka gano sihiri ne, ka taimake ni mu lalubo bakin zaren mana!"
Ya yi shiru yana sauraren kukanta. Ya numfasa ya ce "Bayan sihiri ai kin san yadda ni da y'aya'na muka zama saniyar ware. Lokacin da Jabir yake hakilon zai had'a Yabi da Maijidda gabad'aya kowa tofin Allah tsine aka yiwa lamarin. Bansan adadin kashedin da Dada ta yi mini akan na jawa Yabi kunne ba. A gabana Badamasi yake fad'in Jabiru ba zai auri Yabi ba. Iliya kuwa shi ma ya sha fad'in "Daga ranar da aka ce Jabiru zai auri Yabi to a lokacin zai sako masa Maijidda. Amma kuma an zuba ido tare da bada goyon baya a kwace wa Yabi mijin da ba'a yarda aka bata shi ba, sai da aka tabbatar ba shi da mamora. Yanzu kuma da ya samu madogara sai aka ga yafi k'arfin ta. Tunda abin hakane sai ta fito ta basu waje. Adalcin Ubangiji ya ishi kowa.
Kuka kawai take yi tana jin yadda tsoro da sanyi yake d'ada girma a zuciyarta.
Murya babu amo ta ce "Dan Allah Yaya ka janye umarnin na dauko maka ita. Kasan dai yadda Ubangiji ya mutunta sha'anin aure. Ka yi hak'uri mana har muga karshen wannan waki'ar".
Ya yi shiru kamar ya yarda sai kawai ta ji ya ce "Wallahi ba zai had'a su ba. P bi mini kadina. Bare ina fatan na yi tsawon rai dan kawai ran Yabi kad'ai ".
Kukanta ya karu. Tana yi tana ce wa "Allah ka warware wannan dambarwar. Ubangiji ka taimaki zumuncin ka fahimtar da ni abin da yake boye. Allah na tuba astagafirillah. Ta mike ta tafi babu waiwaye. Ya bi ta da ido yana gasgata surkullen dabaibaye zuciyarta aka yi.
Hawaye mai ciwo ya dinga gangarowa ta kwarmin idonsa.
Gwaggo ta shiga ta tarar da shi a hakan. Ta zauna ta ce "Alhaji ba zaka karanta wa kanka damuwa ba? Ina jin tsoron kada ka hadu da ciwon nan mai shanye barin jiki".
Murya a karye ya ce "Ban da darajar sallah da salati Asama'u ai da tuni zuciyata ta buga ma gabad'aya. A ce haka zan kare cikin bak'inciki da tashin hankalin cikin yan'uwana? Yanzu na rasa mutum daya da zai yuwa Yabi kara da alkunya duk cikin dangina? Tausayin yarana gabad'aya ne yake neman kassara ni. Idan na mutu haka zasu yi ta tashi fad'i babu mai tsaya musu, yanzu shi ke nan bani da wanda zai kula mini da alamarinsu ko wanda zan damk'asu a hannunsa?"

*Akwai kaya masu kyau a cikin farashi mai sauki*
*Saiwowin maganin sanyi*
*Saiwowin Tsumi*
*Saiwowin dahuwar kaza*
*Saiwowin dahuwar tattabaru*
*Gumba*
*Tsumin kwakwa*
*Y'aya'n gadali*
*Hadadden daka*.
*Tsugunno mai sa a matse*
*Goran tula*
*Goran tula syrup*
*Garin goran tula*.
*Maganin gyaran nono*.
*Zuma ta mussaman*.
*Tsumi*.
*Da sauran kayayyaki na mussaman da basu da illah*.
* Domin kuwa asalin Saiwowin ne da ake kawo su daga Chad*.
*Abu mai kyau shi ke siyar da kansa ku tuntube ni dan samun naku kayan cikin sauki da mututantawa. Ina aikawa ko ina a fad'in tarairaiyar Nijeriya*
*08032773332*
Idonta ya ciko sosai amma ta sanya jarumta ta hadiye. Ta ce "To Alhaji ban da abin ka, duk wanda ka damkasu gare shi ai shima zai mace wata rana. Kawai yi dabarar damkasu a hannun Ubangiji domin shi ne rayayye wanzazze. Ina kuma son ka yiwa Hauwa adalci. Al'amarin ne yafi k'arfinta. Shi kansa Tijjani ai ba'a hayyacinsa yake ba. Idan muka daure muka yi hakuri. Muka taushi Yabi ta yi hak'uri komai zai wuce. Duk abin da aka gina shi da son zuciya baya k'arko".
Ya saki ajiyar zuciyar samun nutsuwa. Ya ce "Kina nufin na sake tirsasa Yabi ta zauna da Tijjani ko da bata son hakan?"
Da sauri ta ce "Eh. Domin babu abin da hak'uri ba zai bayar ba idan aka nutsu."
Ido cikin ido ya ce "To a yau kam bazan d'auki shawarar ki ba. Sassauci d'aya zan yi, idan ta ga zata zauna shi ke nan sai na bita da addu'a. Idan kuwa ta ga ba zata zauna ba, to kuwa ko menene zai faru sai dai ya faru amma zan fanshi y'ata."
Ta kasa ce wa komai domin ta san da dukkan zuciyarsa yake magana.

*Bauchi*.
Ina falo kan sallaya na idar da la'asar ina jan tasbaha. Hawaye kuma sai sintiri suke yi. Yayin da Tijjani yake zaune babu sukuni a tare da shi. Yara kuma suna islamiya.
Na daga hannuwana sama a fili na ce "Allah kai ne mai sarrafa zuciya, Ubangiji ka sarrafa mini ita ta zama mai hak'uri, Allah ka mini baiwa da juriyar shanye ko wacce irin damuwa ba tare da hakan ya tab'a imanina da lafiyata ba. Ina rokon a cire mini damuwa akan wannan al'amarin domin na zama cikin masu imani da abin da ka hukunta. Allah ka warware mini dukkan abin da zai tunkare ni na sharri. Allah ka bawa Mijina lafiya, ka k'ara masa arziki, ka kare shi daga dukkan mummunar kaddara. Ina rokon a shirya zuriata, a tsare mini su, a kuma sanya su a cikin bayi na gari. Allah ka jik'an iyayena ka musu tukuici da aljanna."
Na sake yin salatai da istigifati sannan na shafa.
Na jingina da bango ina ta sakin ajiyar zuciya domin gabad'aya ji nake tamkar na ciro ta, ko na huta da azababben ciwon da nake ji.
Ya sassauta murya ya ce "Asiya na gode miki. Ki cigaba da yi mini addu'a dan Allah. Ina ji a jikina bani da lafiya. Na kasa gane kaina, ki yi hakuri da ikon Ubangiji komai zai faru bazan bar ki ba Asiya".
Cikin kuka na ce "Bari na nawa Tijjani? Sau nawa zaka ga ina kuka ka banzantar da ni, sau nawa kake sanadin sa ni kuka? A da na dauka duk lalacewar giwa ta fi k'arfin kiyashi ya ja ta. Ashe sannu a hankali idan suka yi taron dangi sai su jata su kacaccalata. Amma babu komai na barwa Allah ya zame mini garkuwa."
Ya tsugunna a gabana ya ruko hannuna a tausashe ya ce "Ba dan ki gamsu ba, ina rantse miki da Ubangijin Al-arshi bana jin so ko wacce mace da sunan soyayya ko sha'awa a zuciyata sai ke Asiya. Amma bansan me yasa nake jin zuciyata na tafarfasa a dalilin Nasiba ba. Ina jin idan ban aure ta ba bazan samu nutsuwa ba har abada. Ki yi hak'uri kada ki juya mini baya a cikin wannan halin da nake ciki. Masifu sun dabaibaye ni, ikon Allah kad'ai yake rik'e da tunanina. Amma gabadaya bani da sukuni.
A gida babu nutsuwa a tsakaninmu, a wajen sana'a ta jifana ake yi. Ga shi an kulle mini zuciya da tunanina. Babban tashin hankalina yadda Baban Marina ya shirya kwace mini ke. Dan Allah little kada ki barmu ni da twins. Ya ya ake son mu yi, k'arfin hali kawai nake yi, amma ni yanzu har na fara fatan mutuwa ta dauke ni na huta da wannan dambarwar".
Na kasa kwace hannuna. Wani irin abu ya dinga taso mini. Na gasgata ina son Tijjani k'warai da gaske. Domin saukowar da ya yi, ya mini magana ta rarrashi da tausayawa sai na ji k'ullin zuciyata ya fara kunce wa.
Na fara kuka na ce "Ta ya ya zan yarda kana sona Tijjani alhalin kullum sai ka mini abin da zai sa ni kuka? Yaushe rabon da ka zauna ka ji damuwata, hatta yaran nan sun san ka canja mini. A gabansu kake rufe ido ka tsigale ni haka siddan. Kullum a cikin yi musu karyar baka da lafiya na ke dan kada su kullace ka. Yaushe rabon ka da nemi wani abu a tare da ni, me kake so na fahimta tunda nasan baka da hak'uri a wannan fagen?".
Ya tsananta rikon da ya yi mini ya ce Na gode da kike rufa mini asiri a idon y'aya'na. Allah ya yi miki albarka. Sannan Allah ne shaidar furucin Baban Marina da yake nuni zai k'wace mini ke ya sanya na rasa k'arfi a tare da ni. Wallahi bana aikata komai na b'arna Asiya".
Ban ce komai ba ya sake sassauta murya ya ce "Kin tab'a mini alkawarin ba zaki sake fita daga gidan nan ba sai da izinina, ina son ki samar mini da nutsuwa ta hanyar tabbatar mini har yanzu ma ba zaki fita babu yardata ba. Wallahi Asiya ke ce Tijjani. Ke ce nutsuwata, ke ce rufin asirina idan har kika bar ni, ina tabbatar miki komai zai kwace mini. Masu son nawa ma sai sun guje ni, saboda zan rasa abin da suke so a tare da ni."
Na kalle shi hawaye na sintiri akan fuskarsa. Ya jani jikinsa ya rungume yana fad'in "Dan Allah ki yafe mini, ki fahimce ni, ki mini uzziri, ki tsananta yi mini addu'a ".
Muka dinga kuka babu mai rarrashin wani. Dukkan jarumtar Tijjani ta k'are gabad'aya. Na kuma gasgata ba a haiyacinsa yake yi mini wani wulakancin ba. A haka yaran suka dawo suka tarar da mu.
Hamim ya zuba mana ido. A hankali Tijjani ya sake ni tare da dabarar dauke hawayen sa. Yayin da nawa ya kasa tsayuwa.
Hanif ya ce "Ammi Baban 2 yau ma ba shi da lafiyar ne, ya sake yi miki wani abu ne?"
Kafin mu amsa masa Hamim ya ce "Lafiyarsa k'alau fa. Ammi ce take ce mana ba shi da lafiya, marar lafiya yana yin fad'a ne?"




✍️
*Y'ar uwa, ya mukaji da bubukuwa?* *Daga nan fa har january kusan ko wanne sati akwai biki, in ba na kusa ba akwai na nesa, ban da tunanin gudunmuwa da ma kudin man da zakaje bikin ga tunanin abunda zaka saka.*
*Balle ace maaikaciya ce ko CEO ce kina business din ki, kinsan all eyes on you🧐, ke ba sayen atamfa ba komi tsadanta anyo copynta, shima lace haka, cabdi! To albishirinki yar uwa!*
*UMM NIHLA malaysianfabrics ta dauke miki damuwa, tana da fabrics kala kala masu sauki da inganci kuma babu inda zaki samesu in ba wurinta ba, kije taro ki haska kowa sai ya tambaye ki me kika saka ina kika samu💃 maza garzaya gurinta kusa labule.* https://wa.me/message/F3EWRSHQPQAAH1




*Oriflame products*
*Daga make up artist din Guduyo*
*Idan kina bukatar Oriflame products ko wanne irin ne, ko Kuma kina sha'awar yin register da su*. *Ki tuntubemi babbar dealer din su Aisha lame*
*Ina kuma fad'a muku akwai da daddan ganyen shayi na Lame Tea*
*Akwai pop corn*
*07036662633*.



Bamu yi mamakin furucinsa ba domin tamkar dan kama haka Hamim ya ke da magana. Ga kafirin wayo tamkar ya shekara goma.
A sanyaye Tijjani ya jasu jikinsa dukkansu. Yana gode wa Yabi a zuciyarsa da ta rufe masa k'ofar da y'aya'nsa zasu tsane shi. Domin ya riga ya gane Hamim, ba abin da yake so a duniya sama da Yabi. Hanif ne ba shi da alkibla, bai san wa ya fi so a tsakaninsa da ita ba.
Sosai ya tisa mu gaba a da tarairaiya. Rabon da ya yi mini hakan na manta. Gara yara yana ta tasu ni ce dai babu dad'i a tsananinmu. Da wuri ya sa suka kwanta. Suna yin barci kuwa ya ja ni dakinsa. Bamu samu kanmu ba sai tsakiyar dare. Mun tabbatar mun yi kewar junanmu. Haduwar kuma ta yi awon gaba da wani kason bacin ran da ke zukatanmu.
Barci na shirin daukemu ya yi azama ya ce "Mu tashi mu kai kukanmu gun Allah. Ya taimake mu ya kawo mana mafita ya kuma yi mana maganin duk abin da zai farrak'amu". Duk yadda na gaji tikis. Haka na daure na yi wanka, na bishi sallar da ya tayar muka dinga yi har sai da lokacin asuba ya yi.
Kwanakin da suka biyo baya na samu sassauci domin ya yi matukar rage kyara ta. Sannan ya daina fita ya shafe lokaci yna waya a waje. Watak'ila yana yi ne kafin ya shigo.
**
Tunda Babah ta koma Bulkachuwa ta shiga damuwar halin da ta baro d'an uwanta, mahaifin Yabi. Sannan ta shiga alhinin yadda ake ta shirin bikin Tijjani da a Nasiba babu nadamar komai a gidan Marina.
Ta kasa gane kanta sai kawai ta durfafi addu'a tare da fatan Ubangiji ya warware dukkan abin da babu alheri.
Kwanaki biyu kullum sai ta yi mafarkin wai randar Dada ta sanyi akwai maciji mai dafi a ciki.
Kwanaki biyu a jere tana wannan farkin babu tsagaitawa. Tun bata tunawa har ya fara shiga ranta mussaman da take ganin macijin na yunkurin fitowa ya hallaka Dada.
Ta kasa katabus ta fara kokwanto akan lamarin.
Yayin da ya rage saura sati uku biki. Baban Marina ya mik'e ya fara samun sauki a dalilin yadda Yabi ta kwantar da hankalinta. Takanas ta zo har Toro ta bashi tabbacin zata jure matukar ba Tijjani ne ya sake ta ba, to zata yi dukkan iyawarta ta tsallake dukkan kalubalen da yake gabanta. Murya na rawa ta ce ",Ya kamata ka huta Baba. Ya kamata ka samu nutsuwa, sannan mune zamu yi gwagwarmaya mu tsaywa kanmu. Ranar da babu kai kuma waye zai tare mini fad'a ko ya tsaya mini? Bini da addu'a kawai, na karbi wannan kaddarar da dukkan zuciyata, Allah yasa abokiyar arziki ce".
Ya d'ora hannunsa a kaina ya ce "Ina alfahari da haihuwar ki

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login