Showing 180001 words to 183000 words out of 184118 words

Chapter 61 - Bakar Taada Hausa Novel Complete

arewa*.

Ya mik'e ya ce "Asiya rabon da na yi barci haka da safe har na manta. Wato mutum baya gane darajar y'anci sai ya rasa y'ancinsa. Gidan gyaran hali babu dad'i! Masifar da na gani ko makiyina bana fatan ya shiga wajen nan. Sannan babu abin da yake sake rikita ni irin Barnar da ta yi katutu a wannan wajen. A had'a masu k'ananun laifuka da manya. Sannan gwamnati bata yi tsarin yiwa masu laifin allurar kashe sha'awa na wani lokaci ba. Ko kinsan luwadi ya yi yawa a gudajen kurkuku?"
Cikin gigita na ce "Subhanallah! Ya rausayar da kai ya ce "Barna kan b'arna sai dai kawai Ubangiji ya yafe mana.
Abin tausayi wani abin da ya sata bai fi dubu biyar ba, amma rashin gata ya sanya an daure shi sherkaru sama da goma. Wani sharri ne irin nawa, wanni sawun barawo ya taka. Wani bisa kuskure ya aikata laifin. Amma duk an runtse ido an ki yiusu sassauci ta ya ya rayuwa ba zata tsananta mana ba? Addu'ar wadanda aka zalunce su babu hijabi. Sannan yanke hukunci babu hujja yana janyowa al'umma fishin Ubangiji.
Bakar Taada ta shiga ko ina a wannan duniyar Asiya."
A raunane na ce "ALLAH ya shiryemu ya kuma kawo mana fita.
Na yi matukar tsorata da yadda ake b'arna a gidan da ake masa lakabi da gidan gyaran hali.
Kwnanaki biyu da fitowarsa muka sami saukin zaryar jama'a. Takanas aka turo mota daga gidan gwamnati. Domin na yi waya da Hajiya akan ina son zu je mu yiwa first lady godiya. Domin na sani abubuwan da aka yiwa Tijjani na alheri har da arzikina da ya ci. Muna zube a gabanta, muna ta godiya. Mai girma gwamana ya ce "Tijjani kana ta sun gurbin aiki a ma'aikatu daban daban saboda a tayaka alhinin halin da ka shiga. Amma Hajiya ta ce "Wanda muka baka zaka yi. Domin ta dad'e da yiwa matarka al'kawarin zata fito da kai, bisa adalcinmu muka jinkirta sai azumi sai ka shiga sahun wadanda gwamnati zata yafe musu, duk da laifin ka mai girmane. Sai kuma gaskiya ta yi halinta. Hajiya ta roki arzikin na rik'e mata kai da kai da kyau dan matarka ta huce wahalar da ta sha ta rashinka. Dan haka zaka zauna a jihar me dan al'ummarka su amafana da kai."
Tijjani ya hau godiya da murna, yayin da kaina ke kasa nake taya shi godiya.
Cikin kasaita first lady ta ce "Sai a kula, a kuma rik'e mini diyata da kyau domin samun yarinya jaruma ikarama kamar Asiya za'a dad'e . Mace ce mai kamar maza. Na shiga zullimi akan sha'anin ka. Saboda soyayya da sadaukarwa da na ga ni a wajenta. Tana son ka. Ka rik'e a ranka ba zan laminci ka juya mata baya ba".
Ga mamakin Tijjani sai ya ji gwamna ya ce "Hajiya yo me yi miki shara ma ai ta wuce ta yi boranci bare y'ar boko irin wannan mai cike da kuruciya."
Tijjani ya ka'du k'warai da gaske. Domin ya fahimci tasirin da uwar dakin Yabi yake da shi a wajen mijinta. Sannan ya gane dukkan alfarmomim da gwamnati ta yi masa da iznin Hajiya ne. Ita kuwa saboda Yabi ta yi hakan. Da gaske nasararorin rayuwarsa na d'amfare da Yabi ne.
Ya sake yin kasa da kai ya shiga yi mata godiya tare da ce wa ", Za'a kiyaye Hajiya!.
Ni kuwa murya na rawa na ce "Na gode mamana. Na sani mahaifiya daya ce, amma idan mutum ya girmama mutane, ya sanyawa harshensa linzami akan sha'anin da ba nasa ba, sannan ya yi gaskiya da juriya sannu a hankali sai Ubangiji ya bashi uwaye masu yawa. Tabbas ina da mahaifiya. Amma ke din uwa ce a waje na. Allah ya kara miki lafiya. Ina fatan idan kin kammala shekarun biyar din data yi muku saura ki zama first lady din Nigerita ba iya ta jihar Bauchi ba."
Dad'i ya kama su daga ita har mijinta. Da barin baki ya ce "Ameen yarinya. Hajiya me za'a bata tukuicin wannan farin fatan da yi mana gabadaya?"
Da murmushin kasaita ta ce "A maye mijinta da gurbin Kwamishinan ma'aikatu da ya rasu satin da ya wuce mutane suke ta zawarcin kujerar."
Ya ce "Angama ranki ya dad'e Tijjani ka zama kwamsinan ma'aikatu na jaha gabadaya. Zan mika sunanka majalisar zartawa ka zama cikin shirin zasu gayyace ka domin tantace ka".
Gabadaya muka rikice da murna da godiya. Yayin da ta ce "Ita kuma a mayar mini da ita wata ma'aikata haka mai dama".
Take ya buga waya akan a kai ni college of education a matsayin non academic staff.".
Ta sake ce wa idan har na zama first lady din k'asa Asiya ki dinga jin ke ce magajiyata."
Na ce "Ina godiya k'warai mamana, alherinki mai yawa ne, ba kya fad'ar magana da zummar wake. Allah ya kai fata mizani".
Muka taho cikin rakiyar jami'an ican tsaro. Kafin kace miye har an sanar gwamna ya nada Tijjani Yusuf Bulkachuwa a matsayin kwaishinan aiyukan jihar.
Ta ko ina murna ake yi. Da kansa Tijjani ya sake gane al'amarin Yabi babba ne. Tabbas ita ce sababin arzikinsa. Sana'ar lallen dai da aka ce zata rike su itace sanadin zargo musu hamshakan matan da suka sada ta da mai dakin gwamna. Babu abin da zai ce da Yabi da sana'arta sai Hamdala. Zai cigaba da girmamata tare da kauce wa dukkan abin da zai had'a su. Domin ya ga ta k'ra wayo. Ta hadu da manyan mata da zasu yi masa fatafata idan ya ce zai taka ta. A ransa sai fad'i yake gwamna na tattala bacin ran Hajiya, bare ni?. Shi kad'ai ya yi dariya tare da kame bakinsa domin ya fahimci sha'anin babbane. Bayan haka Yabi ta yi hak'uri, ta yi juriya, ta yi masa komai. Shi ma zai yi dukkan iyawarsa ya saka mata da alheri kan alheri.



*INA KAWO MAGANIN MATA MASU KYAU DAGA CHAD DA SUDAN*
*MAGANIN SANYI SADIDAN*
*INA AIKAWA KO INA A K'ASAR NAN*
*BA ZAI YIWU NA TALLATA MUKU ABIN DA BA SHI DA KYAU KO INGANCI BA. DOMIN SOYAYYA DA AMINCI NE A TSAKANINA DA KU MASOYA RUBUTUNA*
*KU JARRABA SAIWOWIN DAHUWAR KAZA DA TATTABARU KU GA NI*

*KAZALIKA MAGANIN SANYI DA TSUMIN GORAN TULA BABU NA BIYUNSU*
*GA Y'AYA'N GADALI DA YAKE SHA YANZU MAGANI YANZU*
*ASALIN DAKA NA EMERGENCY*
*DA GUMBA DA KUMA TSUMIN KWAKWA DA ZUMA NA SHARHOLIYA*
*TUNTUBE NI KAWAI TA WHAT'S APP.DAN SAMUN BAYANI NA SOSAI*
*KU GYARA KANKU, KU GYARA Y'AYA'LNKU*
*MASU SHIRIN AURAR DA YARANSU KO KANNENSU A ZO A SAMA MASU KAYA MASU NAGARTA*
*08032773332*
*NA GODE


Kwa aki uku kacal aka ba shi ya huta.
Gidan Marina ya kacame da murna kowa ya boye aibu da gilli aka dinga tseren yi mana murna. Baban Tsakiya da na Kasuwa washagari suka zo sai dai tafiyar kowa daban.
Dukansu maganganunsu suna nuni.tare da tuni sune suka had'a auremmu dan mu gane oron alherin da suka yi mana. Baban Tsakiya cikin rauni ya ce "Tijjani danuwanka dai yana zaune babu aiki. Jabiru naka. A duba, ga yaranmu nan ka yiwa Allah ka dubasu. Ka rage banbanci Tijjani. Allah ya shirya zuria."
Da zai tafi ya bude murya ya ce "Ina Hajiya Yabin?"
Gabana ya Fadi ni ce Hajiya Kuma?"
Na saka hijabi na fito na tsugunna na ce ga ni Baba".
Ya ce "To ku kula. Ki kuma dage da yiwa mijiki addu'a kinga dai fad'i tashin da muka yi har asirin da aka ta jifanku ya karye. Kada na ji, kada na ga ni. Ki dinga tunawa mijinki game da rashin aikin yayanki Jabiru. Ki kuma cigaba da hak'urin aure nasara tana gaba. Alhaji Babba mura yake shiyasa bamu taho tare ba".
Da mamaki na ce"wanene ke nan?"
Ya ce "Baban Marina mana"
A sanyaye na ce "Ai to, Allah ya bashi lafiya."
Ya ce "Ameen."
Yafi away da tafiya minda Tijjani bamu iya cewa komai ba. Domin ni tunanin fad'i tashin d Aya ambata sun yi nake yi. A hakan Baban Kasuwa ya iso shima ya gama kamun kafarsa da borin kunyarsa. Abin da yake bani mamaki yadda suka fi karkata akan ni naga farinsu fiye da Tijjani ya ga ni. Na fahimci sun riga sun yi nisa a wajen imani da ce wa sai ina son mutum da Tijjani ya taimake shi.
A wannan loakcin mun barji soyayya. Kusan salon gwamna Tijjani ya dauka na wajen ririta ni da mutunta lamarina.
Tuni ya canja wa twins makaranta ya kai su wacce ta amsa sunanta. Aikina kuwa bai hana ni ba. Haka nan na kan yi kunshi amma ba irin na da ba. Domin a yanzu mai kololuwar daraja nake yi. First lady da mukarrabanta kad'ai sai ko Hajiyar da ta yi mini sanadin zuwana gidan gwamnati.
Watanni uku kafin Tijjani ya gane kan ma'aikatar. Cikin sa'a ya samarwa Yaya J da Yaya Rabiu aiki. Ya daga darajar aikin Yaya Salisu. Hatta Yaya Musa da ya zama shasha ya samo masa aikin security a babban asibitin Bauchi. Ya biyawa Anas da k'aninsa Nasiru karatu suka tafi Sweden karatu. Anas digiri zai yi, Nasiru kuwa PhD.
Ba jimawa azumi ya zo, ya tisa ni a gaba da yara muka tafi Umrah da kuma Babah da abokiyar zamanta hadi da Aliyu da matarsa.
Fad'in irin jin dad'in da muka yi ma bata lokaci ne.
Babah Maryo ce ta kasa zuwa inda muke har yau. Hatta Nasiba ta zo yi mana murna. Ta Kuma ro'ke shi ya sama mata aiki duk da a Jos take. Ya mata alkawri zai saka a bata rubuta kati a asibiti.
Domin mijin nata babu. Na kuma san Tijjani zai yi mata wannan kokarin. Domin ma riga da na fahimci shi mutum ne mai saurin afuwa da sassauci. A yanzu haka ya yi amfani da kujerarsa ya fito da Alhji Auta. Ya gyara masa gidansa. Ya mayar da y'ayamsa makaranta. Ya kuma saka masa albashi duk wata.
Ya yiwa babbar y:arsa da take da hankali hanyar samun aiki in tunda ta yi karatu. Kuka ba irin wadda Alhaji Auta bai yi ba.
Lokacin aikin hajji na zuwa ya biya mini ni da shi, da Aliyu da Yaya Ummi. Da Kuma babbar yarsa da suke uba d'aya. Na so ace Ya biyawa Inna tunda itace babanmu bai samu sukunin kai ta ba.
Ya ce zata je amma sai ya kai Gwaggo Umrah ta dawo. Domin ya sani ta taka muhimmiyar rawa wajen dannata a loakcin da shaid'anu da mugaye suka so yin tasiri a rayuwar aurenmu.
Ummi kuwa mutumiyarsa ce. Kafin ya kai kowa Hajj sai ya kai ta a gidan Marina.
Haka muka dunguma ni da Yaya Ummi muka tafi tare da shi.
Duk da yanzu ba a iya cewa komai akanmu akan gidan Marina sai da aka yi yamididin yan dakinmu na ware masa ta kai. Da azumi ya kai Iklma an kasa gane ba dan ni ya kai ta ba,dabida Aliyu ne. Ko wata ce matar.kuwa zata je. Yaya Ummi kuwa ko ba ni ce matarsa ba zai kai ta. Cikin kankanin lokaci sunan Baban Marina ya koma Alhaji babba a wajen yan'uwansa. Ko yaransu ne zasu yi abu zasu ce basu da ta ce wa sai abin da Alhaji Babba ya zartar. Tun ana ganin abin daban har aka saba. Shekarar Bulkachuwa d'aya a matsayin kwaishina ya rushe gidan Marina. Ya yi gini na alfarma na zamani. Kowa part dinsa aka kawata shi, aka zamantar da shi. Kowa anmasa bene. Gefen Dada ne babu bene, gini mai suna hini aka yi. Hatta can ciki inda akace ya zauna da Yabi loakcin auren sai da ka rushe shi aka tamfatsa gini. Gidan Marina ya sake yin fice a Toro. Shi kuwa Juwad g.r.a yake nasa ginin na alfarma. Wanda ha siya da nufin ya saka Nasiba a ciki ya ce ya bawa Yabi halak malak.
Gidansu na Bulkachuwa ma ya sha gyara tunda gini ne mai kyau mai aminci. Gata na ban mamaki yake yiwa magaitda abokiyar zamanta. Koami tare yake kai musu sai abin da baaytasa ba. Haka nan sisters dinsa mata ko wacce ya sama mata abin yi,.ya dauki yaransu ya kaisu makarantu daban daban.
Ta bangarena hankalina ya kwnata domin na daina zullimi akan sha'anin Tijjani. Hatta saka masa idon da na yi akan sha'anin mata yanzu na janye domin aiyukan da suke gabansa bashi da sukunin wannan lamarin. Na murje na ciko. Na mallaki dukkan abubuwan k'awa na ado da kwalliya. Gwala gwalai manya suturu. Malaysia fabrics na Umm Nihla. Mota. Ga yarana suna karatunsu cikin nutsuwa. A yanzu haka cikine da ni na watanni biyar. Husna ta yi shekaru uka.
Ya dankara mana gida mun tare tun bara. Tun lokacin kuma ya dawo da Dada kusa da mu. Part dinta daban. Idan ta gaji sai ta tafi Toro. Haka idan ta gaji da Toro sai ta taho wajenmu.

*Yajin Annur duniya ne Hajiya domin na jarraba shi, akwai na garlic, akwai marar garlic, akwai na daddawa, tana yi ga masu jego*.
*Akwai man shanu, akwai garin danwake*.
*08039183880*

A yanzu kowa Hajiya yake ce mini. Burina ya cika. Na kai Gwaggo Umrah, na kaita hajji. Nazira ta je, da su Yaya Salamatu. Mama ta je Umrah. Inna kuwa aikin hajji ta je bara.
Baban Kasuwa da na Tsakiya suma sun je Umrah da azumi. Shi kuwa Alhaji babba ta bakinsu duk azumin duniya tunda muka samu dama a can yake yi. Sau uku ke nan. Duk shekara idan zai tafi, zai tafi da matarsa daya. Haka Babah da abokiyar zamanta.
Kowa ya yi hakuri da sake saken zuciyarsa, ya yarda da hukuncin Allah baya canjawa zai ga alheri mai yawa. Babah Maryo da kanmu muka kai mata ziyara bisa umarnin Babah. Ta saka ya gyara mata gidanta. Aka sanya y'aya'n ta a makaranta. Tunda Yaya Ammar ne kawai ya yi karatu mai zurfi. Nasiba kuwa tuni ta samu aikinta tana cikin rufin asiri. Haka nan Tijjani ya yi k'ok'ari an daga darajar Ammar a wajen aiki.
Amma kunya gabad'aya ta hana Baba Maryo sakewa. Umrar bana ma tare Babah ta ce zasu tafi. Hakan kuwa aka yi.
Babah da Bulkachuwa da Baban Marina sun fahimtar da ni yadda saka alheri idan an yi maka sharri na matukar tasiri a dukkan mu'amala mussaman ma a harkar zumunci.
Duk yadda lokaci ya yiwa Tijjani karanci, ina da lokaci na mussaman a wajensa. Da zarar ya shigo gidan zai kashe wayoyinsa ya tisa ni a gaba da y'aya'nsa. Soyayyar nan da nake so bai fasa shayar da ni ba. Haka nan a shimfi'da sai ya tsiyayar mini da ruwan kai tas. Da kaina nasan an yiwa Baban 2 baiwar lafiya da kuzari.
**
Zaune muke a babban falona ni da dukkan yan'uwana da muka taso tare domin a yanzu kowa so yake ace yana kusa da ni. Hatta Maijidda da Nasiba kuwa. A dalilin na haihu sati hudu baya, sai yau na shirya walima tunda c.s aka yi mini. Na Kalli Nazira na ce Adda Nazira dan Allah ki sam mini kiba. Kin ga yadda kika tara teba kuwa?"
Ta ce baki ga Maijidda da Nasiba ba sai ni? Ni maganin rabge tumbi ma nake nema. Na ce "zansa a kawo miki daga Kano."

*Bada jimawa ba zan zo muku da littafan Hanne Ado Abdullahi*
*Marubuciyar Wanka da gari da Kuma wacece uwa?*.

Maijidda ta ce ni kuma na sanyi".
Na ce "Tom gangariya ne kuwa maganin sanyin".
Iklima da Ubaida suka ce mu dai a kawo mana na gyara kawai".
Na ce "kowa zan siya masa wadda yake so. Kayan surayya masu kyau ne na yarda da su. Sannan albarkacin Anti Kulsum free delivery ne ga duk wcce ta ta siya take zaune a jihar Bauchi. Suka ce Hajiya kina da yawan jama'a".
Na yi murmushi na ce sana'ata ta had'a ni da mutane masu karamci da kyautatawa dan adam. Ba abin da zance da Allah sai godiya."
Daidai lokacin jariri ya tashi wanda ya ci sunan gwamna. Muke kiransa da Halifa.
Na Kalli kaina a cikin yan'uwana na ga nice zarra. Mafi yawansu kuma sun sake samun rufin asiri ne ta sanadina. Mahaifiinmu da mahaifiyata sun sake samun daukaka ta sanadina. Matan gidan da ada suka hade mata kai, aka mayar da ita banza yanzu kowa so yake ya hlga dariyarta. Ko wacce so take ta samu shiga a wajenta.
A sanadina da Tijjani an samu s'aukiin bak'ak'en taadodin da suka yiwa gidan Marina katutu.
Ba'a dinke an zama abu d'aya ba. Amma hassada da jahilci da suka samu gindin zama a gidan yanzu ya yi k'aura.
Dada tana nan gar da ita. Umrah duk shekara. Tijjani ya tsaya mata. Ta kuma rungumi istigifari. Komai na ce mata na gyara zata karba babu inkari. Idan na so nishadi ma a wajen ta nake yini tana d'ora mini karatukan ta masu sanya ni dariya da tuna baya.
Hatta kangire alherina na isarsu. Har yau din nan da Tijjani ya zama attajiri Ina matukar Jin dadin aikina da kuma sana'a ta domin idan a na je na yiwa first lady kunshi makuden kudade take zuba mini a jaka. Idan zan yiwa dangin uwata alheri bana jiran Tijjani. Duk da shima yana iyakacin kokarinsa. Haka nan yadda nake son ganin dakin Gwaggo da kayan ciye ciye haka nake gani, domin bayan siyayyar kayan abinci na duka gida da Tijjani yake yi. Ina warewa na yiwa uwata hidimar da dace da ita. Suma matan gidan na kan yi musu amma ba kamar ita ba. Tunda dukkan y'aya'n k'ofarmu sai da nasan yadda aka yi aka bawa kowa upper aiki. Duk dai k'ananun ma'aikata ne . Amma dai duk wata zasu ji albashinsu. Hatta Yaya Ummi ta samu aiki a woman center tana koyawa dinki tunda ta iya. Sannan Tijjani ya dauki nauyin karatun y'ayanta biyu maza da suka kammala sakandire a jami'ar Ahamadu Bello da take Zaria. Suna Karantar manyan kwasa kwasai domin sosai suke da hazaka.
Har su Maijidda da su Saratu.
Nazira kuwa koyarwa take yi tunda ta cigaba da karatunta tunda mijinta dan boko ne.
Amaryar Yaya J a gidan radiom Toro ta samu aiki.
Tuni ya farfado. Maijidda ce a BAUCHI a amaryar na Toro saboda aikinta.

***
Waya muke da Nazira akan maganin rage tumbin ya ya isa gareta. Maimakon ta yi mini godiya sai sababi take yi mini tana ce wa "Yabi ban ga Malaysian Fabrics a ciki ba. Ban ga mayukan Oriflame da maclen da kika mini alkawari ba. Ban ga supplement din GHT

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login