Showing 45001 words to 48000 words out of 184118 words
Chapter 16 - Bakar Taada Hausa Novel Complete
kwana, nake tashi, tare da zullumin kar'bar da zaka yiwa al'amarin.
Sai kuma na tuna ikon da shari'a ta bawa uwa ".
A sanyaye ya ce "Hakane".
To maganar auren Yabi da wannan ba'kin yaron ba shirayayya ba ce daga Allah.
Domin mai sunan manya za'a bawa ita."
Wani irin zullumi ya shige shi.
Murya a raunane ya ce "Dada ina ce Nasiba yake so?"
Nan da nan ta ce "Nasiba ai ubanta ne ya yi iko a kanta ya ce dan k'aninsa zai bawa."
Ya ce "Dada ina ro'kon arziki a ba shi wata cikin yaran Badamasi ko na Iliya tunda an riga an karbi komai na aurent a, akwai nauyi mai yawa a tsakaninmu da uban yaron nan ke ma shaida ce".
Ta kai kallon ta ga Baban Tsakiya ta ga ya murtuke fuska.
Nan da nan ta ce "Duk abin da yake tsakaninku da Tanimu ya kai da yar'uwar ka ne?"
Da sauri ya ce "Ba kai ba Dada! Sai dai haramun ne neman aure a cikin aure."
Baban kasuwa ya ce " Ai ba bisa son zuciya ba ne, biyayya ka yi, Allah kuma zai karrramaka tunda ka bi uwa. Idan ya so sai a bawa Nura Kaltume ba shike nan ba."
Baban Marina ya kalli kaninsa da wani irin duba.
Yana mamakin son zuciya irin tasa. Ya dauki y'arsa ya bawa Jabir yasan kuma saurayin Yabi ne. Yanzu kuma a kan idonsa yake fadin zai sake bawa Nura y'arsa tunda yasan akwai mamora a tare da yaron.
A hankali ya ce "To ko zaka lamince na bawa Tijjani Kaltumen kawai?"
Nan da nan ya ce "Ina! Ai ba ita Dada ta umarta ba, so ka ke na shiga fishin uwa?"
"Shike nan Allah ya amsa addu'ar ka, Allah ya sanya albarka a cikin wannan ha'din , ya amintar da lamarin. Na bawa Tijjani Yabi, da dukkan zuciyata"!
Baban Marina ya fa'da cikin wani irin yanayi mai ban tausayi.
Dada ta ce "Allah ya yi albarka".
Har ya yunkura zai tashi sai ya ce "Zan bawa shi Nuran kanwarta. Komai da suka kawo da sunan Yabi ya koma kan Ubaida".
Ya fita yana ha'da hanya.
A zaure suka yi kicibus da Bulkachuwa.
Baban Marina ya kalle shi cikin wani irin yanayi.
Kamar ba zai yi magana ba sai kuma ya ce "Dubi gashin kanka, kamar ba bahaushe ba, ka dubi wando jikinka, tamkar babu iyayenka a gidan, yaushe zaka zama cikakken mai kamala ne?"
Ya sunkuyar da kai ya ce "Za'a gyara Baba"
Domin kuwa da dukkan zuciyarsa yake ganin kimar Baban Marina fiye da su Baban Tsakiya.
A dakin Dada kuwa Baban Kasuwa ya dinga fa'din"Dada ai da kin ce a ba shi Kaltume kawai, ina ce ta fi Ubaidan a haife?"
A dan tsorace ta ce "Ga ni na yi zan takura da yawa, sannan dole hankalin mutane zai dawo kanmu".
Ba shakka ya ce "To ya dawo mana! Idan ka daka ta mutane ai ko sallah ba zaka yi ba, domin kana yi suna kallon ka, ba dan su gyara maka ba, sai dan su gano na'kasunka su yi zundenka
Bare kuma akan wani al'amarin duniya da bai zame komai a juya maka manufarka kyakkawa zuwa mummuna ba."
A sanyaye Dada ta ce "Hakane".
Suka tashi ba tare da sun so a bawa Nura Ubaida ba.
Washagari sassafe Baban Marina ya zaunar da matansa ya shaida musu juyin da aka sake yi, da kuma hukuncin da ya yanke akan yin madadi da Ubaida.
Daga Inna har Gwaggo abin bai musu da'di ba. Mussaman Gwaggo da take gani ita ce zata fi shiga cikin tashin hankali, domin matu'kar Yabi bata samu dacen aure ba, to komai ma zai kwace mata ne. Ga Ummi ita ma fama take a nata gidan.
Shike nan a hakan zasu kare ita da y'ay'anta?.
Shirun da suka yi gaba'daya shi ya sake sanyaya masa guiwa.
Ya ce "Kun yi mini zuru?"
Mama cikin walwala ta ce "To me zasu ce Alhaji? Y'ay'anka ne fa ka yi iko da su, sannan ba shawara ka nema ba, tunda an riga da an zartar to wace ce zata yi inkarin hukuncin Dada matu'kar tana son ka rabauta?".
Maganar Mama ita ta sanya wa Gwaggo k'warin guiwa domin ta sani so take ta ganta cikin rashin sukuni da tashin hankali.
Nan da nan ta ha'diye damuwarta, ta murmusa tare da ce wa"Allah ya sanya alheri da albarka, ina fatan Allah ya sa ace gara da aka yi".
Wata irin nutsuwa ta zo wa Baba domin dama uwar Yabi yake ji. Ya sani borin da Yabi zata yi ba zai yi tasiri ba tunda an yi sa'a ita din mai jin maganarsu ce mai kuma kishin kada su kunyata ne.
Ya dinga yaba mata tare da sanya mata albarka.
Ya juya ga amaryarsa Inna uwar Ubaida.
Ya ce "Ke kuma fa?"
Murya babu amo ta ce ", Allah ya sanya albarka".
Ya sake numfasa wa tare da cewa"Yadda kuka kwantar mini da hankali a lokacin da aka jefa ni cikin matsanancin hali, ina rokon Ubangiji ya kewaye y'ay'anku da farin ciki da kwanciyar hankali a wannan aure.
Allah ya sanya alheri mai yawa ya biyo baya. Allah ina rokon a azurtasu ta inda muka zata da
ta inda bamu zata ba".
Suka amsa da ameen cikin juriya. Amma Mama bata ce uffan ba.
Ha'din kai da ya samu daga wajen matansa ya taimaka kwarai wajen kwantar da hankalinsa.
Har dare muna namu yi, ban samu labarin komai ba. Sai dai na lura da rud'anin da Gwaggo take ciki, gaba'daya ta zama wata iri, ta yi zuruzuru.
Na tambaye ta ta ce mini gudawa take yi. Take na gasgata na tura Anas ya siyo mata filagil.
Da daddare bayan dare ya d'an fara tura wa Baba ya kiramu ni da Ubaida.
Na cika da mamakin ha'damu da ya yi.
Muna durkushe a gabansa, shi kuma yana kan kujerar ba'kin karfe irin ta da, da take dakinsa.
Ya kalle ni ya ce "ku zauna sosai. Ina bu'katar hankalinku da nutsuwarku".
"Muka nutsu kuwa, amma gaba'daya zuciyata ta shiga rud'ani sosai.
"Shi da kansa ya jima bai iya yin maganar ba. Ya jima yana juya maganar yana tunanin ta yadda zai iya fa'dawa Yabi a karo na biyu za'a bawa wata saurayinta. Babban damuwarsa irin yadda ya ga ta sanya Nura a ranta.
Ransa ya baci fiye da jiya. Ba'kin cikin y'anuwansa ya mamaye shi. Wai me ya tsare musu a wannan duniyar ne?
Da k'yar ya yi k'arfin halin cewa "Yabi kinsan ce wa a duniya ba wanda zai so ki, ya so cigaban ki irin ni da gyatumarki ko?"
Ba haufi na ce " "Eh Baba".
Ya ce "Madallah! Sannan kuma ba wani abin kaico da zai dunfaro d'a mahaifi ya zuba ido ya cimmasa, sai idan abin ya gagare shi.
Ina son ki fahimce ni, ki mini adalci, ki kuma ninka biyayyar da zaki mini a wannan karon.".
Jikina ya fara tsuma, zuciyata ta shiga zullumi, idanuwa suka cika da ruwa.
Na kasa bu'de baki na ce komai dan tsananin bugun da zuciyata take yi.
Ya numfasa sosai ya ce "Ina son na fa'da miki auren ki da Nura ba zai yiwu ba, ba kuma na son ki kalli hakan a matsayin shirina ko shirin wani, ki yarda shirin Allah ne, shi kuwa idan Ubangiji ya jarrabe ka, ka yi ha'kuri a farkon al'amarin kana da lada da sakamako mai girma".
Take ruwan da ya cika a gurbin idona ya tumbatsa ya fara zuba.
Ina jin nauyin da zuciyata ta yi ba zai kwatantu ba.
Wacce irin Bak'ar kaddara ce nake gudu take bina da gudu shigen na fanfalaki?
Na kasa bu'de baki na ce uffan domin sai na fara hasashen mafarkin da nake yawan yi ne akan aurena da Nura zai iya ruguje wa.
Jin shiruna ya sanya ya ce "Na sani kina sona, son da yake sanya ki son duk abin dana haifa, ko nake so.
Ina ro'ko ki taimake ni, na yiwa mahaifiyata biyayya, ni kuma zan dauwama ina miki addu'ar wanye wa lafiya da kuma rufin asirin duniya."
Cikin rishin kuka na ce "To Babanmu".
Ganin irin rudin data shiga sai wata dabara ta zo masa.
Sai ya ce "Babanku Iliya ya bu'kaci na bawa Nura Kaltume a madadinki".
Na d'ago a matu'kar birkice na ce "Wai me na yi muku ne Baba?
Yan'uwanka suna azabtar da ni, kai kuma ka zuba ido kana kallo, ka kasa kare mini darajata! Ko dai da gaske karayar arzikinka tana damfare da zuwana duniyar nan mai cike da ba'kin ciki mai tsanani?"
Na fa'da ina kuka sosai.
*Auzubillahi! Na yafe miki Yabi! Na sani kina cikin ki'dima ne, ni kaina da na haife ki kiris ya rage ban zautu ba a dalilin wannan al'amarin.
Allah ka sassauta, Allah ka kawo mafita. Allah kada ka jarribi Yabi da jarrabawar da zata bijire mini. Bare ta haifi wanda zai bijire mata."
Na yi kasa da kaina ina kuka kasa kasa.
*UMM NIHLA COLLECTIONS*
*Ta k'ware wajen kawo yadina masu kyau da sauki, cotton da silk, embroidered, Batik*
*A Malaysia take daga can kuma take turo su Kano direct. Dan haka kayanta akan farashi sari take bayarwa, daga guda daya har zuwa dari zaku samu*
*Kayan ta masu aminci da rahusa ne, ku tuntube ta Whatsapp dan ganin JERIN gwanon yadinanta da basa kode wa ko jeme wa*.
*07020695644*
*What's app only*.
Tsawon lokaci kafin na ce "Na ha'kura da shi Baba. Amma Wallahi indai aka ba shi Kaltume to zan roki Ubangiji ya matso mini da ajalina kusa, domin na sani bazan sake farin ciki ba.
Indai kunyar Babansa kake ji, to ka bashi Ubaida tunda dama saboda kai ya turo d'ansa ya neme ni, ka bashi ita, zai fi mini sauki a maimakon ka rasa suruki nagari irinsa".
Ina rufe baki kawai Babanmu ya fara hawayen da ya daskarar damu.
Wanda na tabbatar na zallar ba'kin ciki da kuma farin cikin yadda nake tsananin son y'anuwana.
Ai ko murya na rawa ya ce "Irin yadda kike son yan'uwanki haka nake son nawa, amma shaidan da son zuciya sun shiga cikin al'amarinmu sun yi kane kane."
Ya daga kai ya ce "Allah kada ka jarrabi ya'yana da rugujewar zumunta".
Jikinmu ya sake yin mugun sanyi ya ce "Ubaida kin ji me yayarki ta ce shin zaki bi bayanta wajen sadaukar da burinki, ki mini biyayyar da ke ma zan dauwama ina yi miki farar addu'a?"
A sanyaye ta ce "Zan yi Baba! Na amince, da ikon Ubangiji ba zan kunyataku ba, komai zan zama kuma a duniya a sanadin auren nan, na sani arzikin Adda Yabi na ci, ba kuma zan juya wa al'amarinta baya ba".
Zan yi zumunci da ita a cikin ko wanne hali da rayuwa zata wullamu".
Daga hakan kuma ta fashe da kuka sosai.
Wanda ita kanta bata san dalilinsa ba, amma dai tana jin na tausayin Yabi ne.
Da ya rasa yadda zai fadi Tijjani ne mijin da aka zaba mata sai ya ce "Yabi ki tsananta addu'ar shiriya ga Tijjani! Ki kuma rage tsananta al'amarinsa ta yadda zaki fahimce shi da kyau, Annabi ya ce "Addu'ar miji akan matarsa karbabbiya ce, haka addu'ar mata akan mijinta karbabbiya ce.
Dan haka ki tsananta yi masa addu'ar shiriya, da kuma a cika kirjjnsa da soyayyar ki da tausayin ki, sannan a buda masa kofofin arziki"
A ki'dime na ce "Baba dan Allah warware mini wannan curarren bayanin, d'an yi mini gwari gwari".
Da matu'kar rauni ya ce "Tijjani zan aura wa ke".
Ai kuwa na dage na zunduma ihu ina birgima, ina fa'din "Wayyo Allah mutuwar tsaye ta samu Yabi! Wayyo Allah nakasa ta zo mini. Yabi zata zama iyalin mai *BAK'AR TA'ADAH*
*Akwai kaya masu kyau a cikin farashi mai sauki*
*Maganin sanyi*
*Saiwowin Tsumi*
*Saiwowin dahuwar kaza*
*Saiwowin dahuwar tattabaru*
*Gumba*
*Tsumin kwakwa*
*Y'aya'n gadali*
*Hadadden daka*.
*Tsugunno mai sa a matse*
*Goran tula*
*Goran tula syrup*
*Garin goran tula*.
*Maganin gyaran nono*.
*Zuma ta mussaman*.
*Tsumi*.
*Da sauran kayayyaki na mussaman da basu da illah*. Domin kuwa asalin *Saiwowin ne da ake kawo su daga Chad*.
*Abu mai kyau shi ke siyar da kansa ku tuntubi marubuciyar Halin yau dan samun naku kayan cikin sauki da mututantawa*.
*08032773332*
*WANNAN LITTAFIN NA KUDI NE BIYA KUDIN KARATUNKI TA WANNAN ASUSUN DAN GUJE WA BAKAR TA'ADA!*
*REGULAR 500*
*VIP 1K*
*VIA*
*2384876855*
*SURAYYA IBRAHIM DAHIRU*
*ZENITH BANK*
*KO*
*7061488065*
*SURAYYA DAHIRU IBRAHIM*
*OPAY DIGITAL SERVICES*
*TURA SHAIDAR BIYA TA WADANNAN LAMBABOBIN*
*08032773332*
*09069067488*.
*MARUBUCIYA*
*BINTA UMAR ABBALE🍒*
*Tana farincikin sanar muku da sabon littafin ta mai suna YA ZA A YI? Wanda za ta sake shi ranar d'aya ga watan Oktoba (first October) wannan karon ma marubuciyar taku ta shirya sosai domin nishad'antar daku tare da fad'akarwa🥰 Ba sai na tsaya yi muku bayanin rubutunta ba domin da yawa daga cikin masu bibiyar litattafanta sun san cewa tana k'okari gurin ganin ta yi rubutu akan abubuwan da suke faruwa, mussaman a zamantakewar aure da tarbiyar yaranmu, Uwa uba kuma litattafanta akwai soyayya mai tsafta da nishadi da 'karuwa! Kada dai ku sake a baku labarin wannan littafin mai suna( YA ZA A YI)❓ Zaku iya yi mata magana ta Whatsapp da wannan numbers*
*08089965176*
*07084653262*
*Annur food Delicious*
*Da k'arfin zuciya da guiwa na ke muku shunen inda zaku samu kayan da na zano a kasa cikin saukakkan farashi.*
*Shaida nake yiwa kayan annur domin dadinsu da ingancinsu ya kai kurewa*
*HANZARTA ki nemi kayansu dan ki gasgata batuna*
*Garin kunun tsamiya garin danwake, garin borkono, yajin daddawa, man shanu, nikekkakiyar gyada ta kunu da ta miya*
*08039183880*
Ina alwallah ina kuka. Ba abin da ya sake karya mini zuciya irin yadda na jiyo Baban Marina yana cewa Baba "Ni fa ki daina ro'ko na Hauwa! Tuni na yafe mata, amma walwalata ce ba zata ga ni ba, har sai ta kwantar da hankalinta an yi hidimar nan lafiya lafiya. Sannan kuma ta zauna lafiya da mijinta kamar yadda y'anuwanta suke zaune lafiya.
Ina ce Ummi gidan mai iyali aka kai ta? Ga kuma mijin ya d'orawa ransa masifar son abin duniya. Ba ya sauke hakkin da shari'a ta wajabta masa.
Duk k'uncin da take ciki yau shekaru kusan takwas da aurenta, bata ta'ba zuwa gabana da nufin wata matsala ko da zummar na taimake ta ba.
Na sani kuma tana bu'katar a taimake ta, amma da yake ta dauko ha'kurin uwarsu ta shanye komai tana zaune da y'ay'anta, sai kuma ta yi tabarar koyon sana'a cikin cire girman kai da buri.
Shiyasa ni kuma ban ta'ba yin sallah ban roka mata sassauci a wajen Ubangiji ba.
Duk kuma wanda Allah ya ba shi nisan kwana zai ga yadda Allah zai albarka ci zuri'arta. Allah sai ya yi mata tukuicin hakuri da biyayyar da ta yi da ikon Allah".
Da k'yar na tokara na tashi zuwa daki na tarar da Gwaggo tana share hawaye.
A sanyaye na ce "Gwaggo baki huce da ni ba ne?"
Ta girgiza kai sai kuma ta ce "Ina mamakin duk alherin da mace zata yiwa namiji na ha'kuri da juriya akan al'amarinsa ko na ahalinsa. Amma idan d'anta ya yi laifin da ita kanta bata sani ba sai ya shafeta.
Ko sai yaushe uwa zata kubuta daga irin wannan kalubalen a k'asar hausa?
Duk lalacewar uwa ba zata so d'anta ya zama marar tarbiya ba. Na sani akwai uwayen da basa son laifin ya'yansu, amma me yasa aka fi yiwa masu hakuri da kawaici raddi?
Yanzu duk laifinki a kaina ya k'are. Yana wahalar gaske Babanku ya yaba ha'kurin da nake yi a gabana sai dai a bayan idona. Shikenan ita mace ba za'a yabe ta a kurzanta ta ba?
Ba za'a yayata alherinta ba, amma kuskuren da ba ita ta yi shi ba ma sai an yi mata tuya a kai".
Ta fa'da hawaye na sake k'wace mata.
Na taya ta kukan da take yi domin na sani sanadin tafiyar da na yi ne.
Da rawar murya na ce "Ki k'ara hakuri Gwaggo! Idan kika yi sa'a Ubangiji ya yabi ha'kurinki shikenan kin gama dace wa."
Ta zuba mini ido sosai ta ce "Kema na hore ki, ki yi hakuri, ki yi juriya, ko bana raye shine tsanin da zaki ri'ke, ki tsallake dukkan k'alubale a wannan duniyar".
Jikina ya sake sanyi. Domin kalmar ko bata raye ta yi matu'kar dukana.
Na ha'diye kukan na tayar da sallah.
Sai dai hawaye bai yanke mini ba, na idar da sallar ina zaune ina lazimin Ya ladifu da fatan na samu sau'kin halin da nake ciki.
Washagari sassafe Babah ta koma Bulkachuwa.
Ala dole na ha'kura na zuba ido aka cigaba da shirin aure, wanda yake sake k'arantowa.
Duk da na ha'kura amma wata irin rama nake yi mai tayar da hakankalin masu kallona.
Na sake zama wata yar sumoli da ni.
Ba annuri a fuskata.
Na kasa yiwa jama'a kitso bare kuma lalle.
Idan ba k'ure wa ta yi ba yana wahalar gaske na yi magana. Na zama very silent.
Makarantar boko ma na daina zuwa duk da a shekarar k'arshe muke.
Kwatsam sai ga Yaya J ya dawo daga Bauchi.
Bai samu labarin aurena da Bulkachuwa ba sai a jiya.
A ki'dime ya iso gidan Marina. Ya gurfana gabana Dada yana fa'din "Dada wanne irin abu ne haka?
Ta ya ya za'a dauki Yabi a bawa Bulkachuwa! Saboda Allah Dada wannan daidai ne?
Me yasa aka hana shi Nasiba baki tsawatar ba?
Me yasa aka tirsasa ni na auri Maijidda?
Akan me ita kuma za'a yi mata hakan? Ciwon abin ba shi ya yana sonta ba.
Idan saboda kada na sameta ne kuka k'ulla wannan al'amarin, na sadaukar da soyayyar da nake yi mata, na janye, bazan sake furta sonta, ko a bani aurenta ba. Amma ki yiwa Àllah Dada kada ki kassara mata rayuwarta.
Waye bai san BAK'AK'EN TA'ADODIN da yake yi ba?
Ta ko ina basu dace da juna ba.
Yabi mai son sana'a ce, yayin da Tijjani bai damu da ya gina kansa ba, irin mazan da suke barwa mace hidimar da shari'a bata dora musu ba ne.
Tijjani manemin mata ne, yayin da Yabi ta kasance mai tsananin kishin gaske.
Tijjani fari ne, Yabi bak'i take so.
Tijjani mai zafi ne. Yabi mai tsiwa ce.
Ta ina zasu ji da'din zama?
Ta ina suka dace?"
Kafin Dada ta ce wani abu Bulkachuwa da yake tsaye a bakin k'ofar Dada ya ce "Bamu dace da juna ba Jabir. Sai dai ka sani Ubangiji ne yake jujjuya al'amura, yake kuma k'addara afkuwar komai ko da bamu tsara faruwarsa ba.
Maganganunka sun yi matu'kar ta'ba zuciyata. Tabbas gaskiya ka fa'da, duk da na ji na muzanta. Da a ce son Yabi bai yi mini kamun kazar kuku ba.
Dana tirje wa aurenta. Sai dai an jarrabe ni akan ta cikin kankanin lokaci."
Ya numfasa ya sake fa'din " Na gode da ka ankarar da ni, duk inda sana'ar da zan gina kaina take zan nemota zan kuma yi duk wahalar ta.
Laifin da ka jingina mini kuma na neman mata wannan kai da Allah!