Showing 87001 words to 90000 words out of 184118 words

Chapter 30 - Bakar Taada Hausa Novel Complete

me ya same ki Yabi?"
Na kasa bu'de baki na ce mata uffan, illah kukan da nake yi mai cin rai, mai kuma sauti sosai. A lokacin kuma dare ne sannan yana gidan.
Ya ji ni sarai, tunda a lokacin yana falo. Amma ya yi kamar bai ji ba.
Washagari da asuba sai ga Yaya Ummi ta diro mana gidan.
Tausayinta ya kama ni. Yargale yargale da ita. Da alamun ma kukana bai barta ta yi barcin kirki ba.
Ta same ni kad'ai a dalilin bai dawo masslaci ba.
A gigice take tambayar me yake damuna?
Murya a dashe tsabar kuka na ce "Tijjani yana shirin kashe ni da raina ne. Haka siddan ina zamana ya saka mini rai zai mayar da ni makaranta na samu shaidar kammala sakandire.
Yanzu ya zo ya ce ya fasa. Hakan bai ishe shi ba sai ya ha'da har da soke sana'ata. Sannan dan yasan Baban Marina ba zai saurare ni ba, sai yake amfani da hakan yake musguna mini. Fiye sati yana gaba da ni. Sannan kulllum dare sai ya sheka wanka sannan ya fice ya bar ni a gida sai dare ya raba zai dawo. Ni nasan Bak'ar TA'ADAR sa ya koma. An cuce ni Yaya Ummi."
Na fa'da ina rushe wa da kuka sosai.
Daidai lokacin kuma ya dawo, amma kukan da Yabi take yi tamkar na mutuwa shi ya hanasu jin motsinsa. Ya zauna a barandar yana son fahimtar abin da yake faruwa.
Jikin Yaya Ummi ya yi sanyi. Ta ru'ko hannuna ta ce "Yabi nutsu ki ji ni. Shin me kike masa yake yi miki hakan?".
Cikin kuka na ce "Bana yi masa komai".
Ta numfasa ta ce "Me yasa kike gaba da shi? Da kina gaishe shi, na tabbatar Yaya Bulkachuwa zai masa miki."
Na yi shiru dan kuwa gaskiya ta fa'da.
Ta sake ce wa "Da kin ja shi a jikin ki, da ba zai iya fitar da yake yi ba. To me zai yi a wajen bayan yana da d'anyar amarya mai cike da shiriritar kuruciya?"
Na bata rai na ce "Kawai saboda ke da shi akwai amana da yarda shi yasa kike shaidar sa a bayan idonsa ni kuma kike bani laifi a kan idona ko?"
Na fa'da hawaye na ziraro mini.
Ta tsananta ri'ke mini hannu ta ce "Gaskiya ai bata bu'katar ado Yabi. Babu ruwan alk'alami akan kina so ko ba ky so. Kawai girman hakkinsa da ya rataya a kan ki za'a duba. Idan baki sau'ke ba Wallahi halaka zaki yi Yabi. Ni yanzu son nawa mijin nake yi? Amma na yarda kaddara shi ta zaba mini. Dan haka na yi hakuri nake yi masa biyayya, duk da shi din ba duka yake sauke hakkin da shari'a ta gindaya masa ba. Amma na sani ina rabo mai girma a wajen Azza wa jallah".
Na tsananta kallonta domin gaskiya ta fa'da. Har zuwa yanzu da ta zarce shekaru goma da aure bata son mijinta, ni shaida ce akan hakan, amma kuma ha'kuri da biyayyar da take yi akan sha'aninsa mai yawa ne.
Ta numfasa ta ce "Yabi ba kya yarda da Tijja
Yaya Bulkachuwa. Su kuma maza da kike ganinsu komai zaki yi musu na kyautata wa matu'kar ba kya mutunta shinfidarsu, to fa komin kokarin ki a banza ne a idonsu. Saboda haka ki d'auki matakin gyara a tsakaninku."
Na nisa na ce "Baya gamawa da wuri Yaya Ummi. Ni gaskiya bazan iya ba."
Ta ce "Ahab dama da labarin neman auren da yake yi ya riske ni, sai da na ce na tabbatar ke ce silar k'arin auren sa. Ai sai ki yi tunda al'amarin kishiyata bai saka kin k'yamaci kishiya ba".
Wani irin abu ya soki k'irjina, ban san mene ne ba. Amma gaba'daya ji na yi tamkar zan shid'e.
Na rushe da kuka mai tsananin gaske.
Ta ce "Ai indai kika cigaba da tafiyar da shi a hakan, tabbaskuka na gaba. Ba ki ga Bilkin da yake zuwa wajenta ba, gansamemiya ta yi biyu da rabin ki."
Da rawar murya na ce "Me za'a yi da mai BAK'AR TA'ADAH irin ta Tijjani. Aure ko rufa wata biyu ba'a yi ba har ka fara neman wani auren. Na rantse Yaya Ummi sai dai a tsine mini. Amma bazan taba zama da wata macen a k'arkashin ikon Tijjani ba".
Ta sake ru'ko hannuna ta ce "Idan kina son ki zauna lafiya, ki yi sana'arki, ki cigaba da tallafa mana. To ki zauna lafiya da mijin ki, ki daina gudunsa, ki yi hakuri da shi watarana sai ki ga kun kai ga babban bigire. Ni fa na dauka ma ciki ne da ke. Jiya nan na je gidan Ubaida na tarar tana ta kwarara amai. Da kaina na rakata asibiti aka tabbatar ciki ne da ita. Kin ga kuma ai kanwar ki ce duk k'uruciyar ki ai kin fita a haife. Jabir din da kike ta kulafacinsa matarsa wata tara ta haihu. Sai ke ce zaki zama shasha wacce bata san me yake mata ciwo ba. Da ace kin kwantar da hankalinki da wata'kila ke ma da na ki cikin a jikinki".
Kunya ta rufe ni, na ce "To yanzu dai ki fa'da masa ya bar ni na yi sana'a ta."
Ta ce "A yanzu bazan yi masa magana ba. Idan kin canja kin daina gudunsa, bai bar ki ba, sai na yi masa magana. Amma yanzu ai ke ce zaki fara zuwa da gyara".
A sanyaye na ce "To".
Amma k'irjina tamkar ya fa'do a dalilin nauyin da yayi akan batun tsohuwar budurwar Bulkachuwa wacce aka kai masa ku'din aurenta aka k'i karb'a. Tun lokacin ya fita a harkarta amma ita take ta nacin ya yi hakuri.
Tijjani da ya yi bakam yana sauraronsu. Ya saki gauron numfashi yana k'ara ganin hankalin Ummi. Sai dai mamakin da ta bashi a ina ta ji yana zuwa wajen Bilki?
Shi yasan tunda aka yiwa su Baban Marina wula'kanci bai sake taka gidansu ba har yau. Idan Ummi ta fa'di hakan da nufin yiwa Yabi barazana. Ya tabbatar liki ta b'allo masa.
Duk yadda Yabi take kirarin bata son sa amma kuma kishi take yi akan lamarin sa ba ka'dan ba. Duk da dai ya yi amanna kishi dabi'arta ce.
Amma ya tabbatar wannan maganar sai ta ri'ke ta a ranta.
Ya saki gauron numfashi yana fatan a sami dai-daito a tsakaninsu.
Tsawon lokaci yana sauraronsu, yana jin irin yadda Ummi take ta wasa shi tare da ban baki a madadinsa. Wanda hakan ba k'aramin kaunarta ya k'ara ji ba.
Jin tana haramar tafiya ya sanya shi mike wa ya maze tamkar bai ji me suke fa'da ba.
Da murmushi ya ce "Ummilolona ke ce da sassafen nan?"
Ita ma da walwala ta ce "Eh Yaya Bulkachuwa barka na je nan gabanku ka'dan, shine na biyo na gaisheku ko na yi laifi?"
Da sauri ya hau girgiza kai tare da fa'din"kin yi daidai Ummi. Allah ya bada ladan zumunci".
Ta ce "Ameen."
Ya bita suka fita da kafarsu. Wata'kila har gidanta ya rakata domin ya jima bai shigo ba.
Hadari ya hadu mai k'arfin gaske. Daidai lokacin ya dawo tamkar jifa.
Sai da ya rufe k'ofar d'akin da yake yi mini isa, ya rufe tagogin falo.
Sannan ya shigo d'akina. Na kalle shi na dauke fuska domin haushinsa ya sake kama ni sosai.
Ya zauna a gefen gadon ya sanyaya murya ya ce "Albarkacin zuwan Ummi na ajiye fishina. Na huce, komai ya wuce".
Na yi kamar ban ji ba. Ya matso jikina sosai ya ru'ko ni, na fizge a fusace na ce "Bana son ka huce Tijjani. Domin dai ni bana ha'da sabgata da marar imani bare kuma tausayi."
Ya sassauta ya ce "me na yi na rashin tsoron Allah Asiya?"
Murya na rawa ina shirin kece wa kuka na ce "Ban da ka tabbata baka da tausayi mene ne zai sa ka jajibo aure alhalin ko wata biyu baka rufa da yin auren ba. Mene ne hakan inba rashin tsoron Allah da rashin imani ba?."
Ya sake matsowa jikina ta yadda bayansa na shafar cikina.
Ya yi k'asa da murya ya ce.
"Wallahi Asiya Toro tsoron Allah nake ji sosai. Shine shaidar hakan. Asalima saboda ina tsoronsa ya sanya na fara neman auren. Ya zan yi? A d'an zaman da muka yi ya kamata ki fahimci bazan iya ri'ke kaina alhalin ina ganin ki, muna kwana gida d'aya ba.
Ke kuma gaba'daya kin bijire , kin k'i saurara ta, tunda ba sona kike yi ba. Sanin zan iya fa'dawa halaka ya sanya na samu wata bazawara mai gajeran buri muke tattauna wa. Idan Allah ya yi zan aure ta. Kin ga shike nan na magance tashin hankalin da yake tsakaninmu, sannan na samu mafita daga hatsarin fa'dawa zina da aurena".
Yana rufe baki ba zato na mik'a hannuna na d'auko wata doguwar robar mai ta kokobota. Na kwad'a masa a goshi. Ina kwada masa tare da ce wa "Allah ka yi mini tsari da mugun k'ullin da yake zuciyar wannan bawan naka. Bilhiillazi kana da fitina Tijjani."

✍️

*UMM NIHLA COLLECTIONS*
*Ta k'ware wajen kawo yadina masu kyau da sauki, cotton da silk, embroidered, Batik*
*A Malaysia take daga can kuma take turo su Kano direct. Dan haka kayanta akan farashi sari take bayarwa, daga guda daya har zuwa dari zaku samu*
*Kayan ta masu aminci da rahusa ne, ku tuntube ta Whatsapp dan ganin JERIN gwanon yadinanta da basa kode wa ko jeme wa*.
*07020695644*
*What's app only*.

*Assalamu alaikum Bayin ALLAH, kun san ce wa FREE PAGES na littafin ƘALUBALEN RAYUWA ya ƙare? Wanda cigaban littafin KUSKUREN SO na? Kun san dai yadda na nishaɗantar daku a labarin Nafeesar Sufyan? Kuma dai kun san yadda na nishaɗantar DAKU a littafin ISHARA labarin Zainabun Sameer? Littafin ƘWAƊAYI fa? Labarin Zainabun alamaramma? Na san baku manta RAHEELA MAI ƊAN BUJE ta cikin littafin RUGUNTSUMI? Jamaa na rubuta kun karanta kuma kun shaida, alƙalami ne da babu tantama a cikin shi, Jamaa yanzu ma tafe da nake da ɗaya tankar dubu, salon na daban ne? Ba zan so ya wuce ku ba, shiyasa na maku promo ku biya 300 madadin 400 kacal ta wannan hanya 9994468172 Access bank fiddausi musa tare da shaidar biya ta 08036953516 ko 07042277401, domin mu tafi tare, na maku alƙawari, labari ne da zai tsaya zukatan..*

53&54.
Ta ko ina nake jifan sa, gaba'daya na hargitse dakin.
Da k'yar ya samu ya ri'ke ni ya dauke ni caraf ya d'ora a cinyar sa ya rungume ni tsam tsam.
Gaba'daya na shige jikin na yi luf, sai kukana kawai yake tashi, wanda na shagwaba da kishi ne.
Cikin rad'a yake ce wa "So ki ke ki illa ta ni ne?"
Da k'arfi na ce "Eh. Wata'kila dan ka ga kana da kyau ne ya sanya kake ganin ko wacce mace ka ce kana so, ba zata tankwabar da kai ba. To gara na rugurguza ka. Tunda ni kyaun naka bai rud'e ni na makance akan ka ba"
Ya sakar mini wani irin nishi a kunne, sannan ya dan cizar mini shi ka'dan. Yar na ji jikina ya amsa. Na fara fizge fizgen bazan yarda ba, sai nima na cije shi a nasa kunnen.
Shi kuma ya dinga dariya yana cakuma ta son ransa.
Babu zato ruwa mai k'arfi ya goce.
D'akin ya yi duhu saboda ko ina rufe yake gudun kada ruwa ya shigo.
Wannan yanayin ya sake susuta Tijjani. Ni kuma na dinga koke-koken jan rai. A ki'dime yake rarrashina.
Fa'di yake "ki yi ha'kuri I will be soft and gentle."
Ni kuwa sai botsare wa nake yi. Tare da ce wa "Ni dai ba da'de wa zaka yi ba."
Da rawar murya ya ce "Nà yarda amma idan kika cije ni, ko kika yi mini fallashasshen kuka. Ki tabbatar kina cikin komar mala'iku".
Na yi shiru. Amma zuciyata sai harbawa take yi. Domin har zuciyata nake jin tsoron al'amarin.
Ina ji ina ga ni, ya shiga yin yadda ya ga dama da ni.
A farkon tafiyar gaba'daya na kankame jikina ina sauraron jin matsanancin zafi.
Amma ga mamakina sai ban ji ba. Har na sakankace na saki jikina. Wanda hakan ba k'aramin dadi ya yi masa ba. Ya k'ara haifar masa da kuzari mai yawa.
Dan haka lokacin da ya shafe yana abu daya, bai dame ni ba.
Bayan ya nutsu. Ya rungume ni yana ta faman sakin kalaman yabo da soyayya.
"Asiya da hakan kike yi mini, to me zai sa ma na yi fishi da ke? Bare har na yi tunanin k'arin aure. Na gode sosai, Ubangiji ya sanya albarka a rayuwar ki gaba'daya."
Na yi shiru. Amma zuciyata sai kai kawo take yi akan abin da nake son amayar wa.
Na kasa jarumtar ha'diyewar murya babu amo na ce "Yo ni ai tunda wula'kanci ka shiryo mini daga yin aure za'a ka fara neman wani dan kawai ka nuna wa duniya bani da wata kima a idonka. Wallahi ba zama zan yi ba. Zaka wayi gari ne ka ga na bace maka."
A diririce ya sake ru'ko ni sosai tare da ce wa "Kar ki tayar mini da hankali dan Allah.
Na fasa, dama dan na rasa yadda zan yi ne. Amma yanzu indai kin daina yi mini abubuwan da kike yi. Wallahi bazan sake tayar da maganar ba. Ke ko hanyar da ta bi, bazan sake bi ba".
Cikin kuka na ce "Daga baya ke nan. Wadanda suka ganka kana zuwa tadi ai tuni sun san baka son Yabi. Dan haka kuwa ba yarda zan yi ba. Ka je ka cigaba da abin da kake yi, ni ma zan samu mafita Wallahi".
A raunane ya ce "Bana son kukan ki Asiya! Amma sai ki ta yi mini, dan kawai ki gigita ni. Ban iya yaudara ba. Na ce miki, na fasa, na janye, to ba shikenan ba?"
A zabure na ce "Ba shike nan ba".
"Da azama ya ce "To fa'da mini yadda za'a yi, me kike so na yi dan ki gamsu?"
Na dinga gunjin kuka da na tabbatar yana jijjiga shi.
Ya dinga shafa kaina, yana fa'din " Sorry Asiyata! Na ce bazan sake ba, ki yi ha'kuri da gaske na fasa. Dan Allah mu rufe maganar nan haka. Me kike son ci na dafa miki?"
Na fara kokarin fizgewa daga rugumar da ya yi mini, amma na kasa.
Cikin tab'ara na ce "Bazan ci ba. Yau kwana nawa rabon ma da ka tsaya ka saurare ni akan maganar abinci. Ko na ci, ko kada na ci ai babu ruwan ka".
Ya sake sassauta murya ya ce "Wula'kanta ni fa kike yi. Ta ya ya zuciyata zata ji da'din kyautata miki? Yanzu kuwa ai komai yi miki zan yi da kaina".
Na cuna baki na ce "Abar maganar abinci. Ka tashi tunda ruwan ya tsaya, ka kwaso kayanka da ka kai mini wanccan d'akin dan kawai kana nema na da jidali".
Ya zabura ya tashi. Ya lalubo jallabiyarsa ya d'ora akan gajeran wandon bai ce komai ba ya fice.
Ya kwaso su tsab. Ya mayar dasu inda suke.
Ya juyo ya ce "Na kwaso, shike nan?"
Na bata rai na ce "Ba shike nan ba. Kada mu samu sabani ka sake yi mini hakan. Tijjani ba ruwanka da d'akin can. Nan ne dakinka. Idan kuma zaka dinga fitina ta akan dakin to ka sani zan tattara kayan gadon na mayar maka can din. Tunda nan d'akina ne da shari'a ta ce ka bani shi tilas. Idan anan nake sana'ata ban shiga cikin dakin ba, ai na tsira ko?"
Ya yi wani irin murmushin da na fahimci mai harshen damo ne.
Ya numfasa ya ce "Namiji ai ba yi masa shamaki a gidansa. Dan haka mu zauna lafiya mu mutuntata juna shine kawai. Amma bazan yarda ina tattala ki, ke kuma ki ce zaki dinga wula'kanta ni, sannan kuma na yi miki yadda kike so." Ya girgiza kai ya ce "Ba haka Tijjani yake ba. Ba kuma zai zama hakan ba".
Na kura masa ido na tabbatar iyakacin gaskiyar sa ya fa'da. Na rasa me zance masa domin na tabbatar duk bala'ina. Idan ya kunsa mini ba'kin ciki daya tak kwana zan yi na yini cikin ba'kin ciki mai tsanani.
Dan haka sai kawai na buge da sake fashe wa da kukan.
Daga inda yake tsaye, ya ce "Allah dai ya taimake ni ki hau ko na samu sau'kin wannan rikicewar da gangan. Idan kina ganin baby a hannunki wata'kila kya daina yi irin wannan sakalcin."
Yana rufe baki na fara nuna kaina cikin kuka ina ce wa "Tijjani ni ce sakaliya?"
Kafin ya amsa mini na rausayar da kai na ce shike nan na gode da wannan tukuicin".
Ya taho da sauri yana kuma dariya. Ya rike k'afafuna ya ce "Ina nufin sakaliyata fa".
Na yi tsuka na juya.
A sanyaye ya ce "Bana son tsuka Asiya. Amma na yafe miki, ban yi fishi ba".
Daga hakan ya koma ya fita. Na tabbatar kuma kicin zai shiga. Ni dai daga nan barci ya sure ni.
Sai bu'de ido na yi na ganshi ya yi wanka ya shiraya tsab. D'akin ma ya cika da kamshin turaren nasa.
Yana daga jikin sif din yana saka links ya ce "Yanzu dama zan tashe ki, na kai miki ruwan wanka".
Ban ce komai ba, na tashi, na daura zani a kirji sannan na saki zanin gadon na sauko.
Ya kalle ni babu riga a jikina. Ya ce "Asiya Toro a gabana babu riga. Sai na sake ganin ki wata yar kwaila, a hakan tamkar ba zaki iya komai ba. Nan kuwa al'amarin da yake tare da ke azimin ne".
Na cuna baki na ce "Ai ni na gode Allah ma da aka baka yar mitsil din. Kai da rusa rusan mata sai kallo daga nesa. In juninka cusawa mutum takaici ne. Har abada kai da zunduma zunduman mata".
Ya murmusa duk da dai yana kokarin shanye dariyarsa.
Ya ce "Wato baki ji da'din yabon da na yi ba, sai kika dauki abin da bai yi miki da'di ba, kika yi raddi?"
Na share, na dauki tawul na fice abina.
Na dawo na tarar da shi ya gyara gadon tsab. Ya share dakin. Na kasa hakuri na ce "Tijjani wai a ina ka iya gyaran gado ne, tunda kullum dakinka na gida a hargitse yake, sai asarrariyar can ta gyara maka shi yake yin fasali".
Ya dauko mai yana murmushi ya tarar da ni a bakin gadon. Na yi kamar na hana shi shafa mini mai din sai na fasa kuma.
Domin a dan zamanmu na fahimci yana matu'kar son ya shafa mini mai, kafin na sanya komai a jikina.
Ina ji ina ga ni ya dinga shafe ni da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login