Showing 162001 words to 165000 words out of 184118 words

Chapter 55 - Bakar Taada Hausa Novel Complete

na gari ya zama yana duba komai yana kuma kiyaye dukkan doka."
Ya rattaba hannu akan takardun tare da buga stamfi.
Gabadaya ahalinmu hankaliinmu ya yi mummunan tashi. Ni kam kuka na ke yi mai gunza. An daure shi shekaru bakwai babu tara?
Wacce irin bak'ar kaddara ce wannan?
A harabar kotun muka tsaya da shi tunda Yaya Ammar na cikin ma'aikatam gidan yarin. Na kalle shi sai kawai na fashe da kuka a dalilin raunin da na ga ni ya bayyana masa a dukkan jikinsa da zuciyarsa.
Muka zubawa juna ido ba tare da mun tuna daruruwan mutanen da suke wajen ba .
A sanyaye ya ce "Asiya shekaru bakwai da yawa. Tashin hankalina bai wuce ke ba. Ba zaki iya ba. Innalillahi wa inna ilaihir rajiun "
Sai kawai hawaye ya ya k'wace masa shabe shabe".
Na rik'e hannunsa na ce "Ko shekaru sha bakwai ne zan jira ka Baban 2. Idan har rayuwarmu ta kai zaka fito ka tarar da ni a dakin ka. Zan kiyaye maka amana, zan yi aiki tuk'uru na kular maka da y'aya'n ka. Jarumtar nan da ka ke fad'in na dinga yi, zan nin ka ta daga yau".
Baban Marina ya dauke idonsa amma bai iya tsayar da hawayensa ba. Tijjani ya matsa kusa da shi ya ce "Wallahi ban aikata laifin da aka jingina mini ba, rami aka haka mini na fad'a. Ka taimake ni, ba zullimin hukuncin ne ya zautar da ni ba. Fargabar yadda zan iya rasa Asiya ne. Shekaru hudu ne gejin da shari'a ta dibawa mace akan dakon mijinta. Ni kuwa shekaru bakwai aka zarge ni".
Hawaye ya cigaba da tsere babu kakkautawa.
Baba ya kasa ce wa komai. Su Yaya Salisu kowa hawaye. Cikin k'arfin zuciya na ce "Idan ni ce matsalar ka, to ka kaddara baka da damuwa. Zan jira ka. Ba ka ce ko ka mutu na zama jaruma dan na tallafi y'aya'n ka ba? Zan kiyaye mutuncin ka, zan kuma maye wa y'aya'n ka gurbin ka har zuwa lokacin da zaka dawo ka cigaba da kulawa da mu gabadaya. Ka sa a ranka ban yi kokwanto akan ka ba Tijjani. Na gasgata ka, na yarda da kai."
Ya saki ajiyar zuciya ya ce "Allah ya k'ara lafiya Baba. A sanya ni cikin addu'a. Ni kuma ya mini murmushi kad'an ya ce "Na gode".
Daga haka suka tafi da shi.
Fir na k'i yarda na koma Toro. Domin idan ina gida tashin hankalina yafi yawa a dalilin ina ganin tamkar Tijjani ya rasu ko mun rabu. Bayan haka karatun yara ya dakata.
Baban Marina bai matsa mini ba, jikinsa ya yi laushi ya kamu da mugun tausayinmu.
Yaya Indo ta zauna da ni na kwanaki biyu. Komai ita take yi, ta ji da hidimar yara ta kuma yi girki da kwantar mini da hankali. Tun sanadin auren Nasiba muka hade da su. Gabadaya yan k'ofarmu muka dinke, muka dunkule, duk wani tsegmi ya yi s'auki tunda dama manyan namu ne karkatattu.
Sai da Babah ta Bulkachuwa ta zo sannan ta tafi. Dada ce ta zartar da umarnin Babah ta zo ta zauna da ni. Cikin alhinin rashin Tijjani da kuma tausayi da kyautatawa muke zaune. Nasirun ta wanda shi Ihisan take bi a kai a kai yake zuwa mana domin dalibi ne a jami'ar Abubakar Tafawa Balewa da take cikjn Bauchi.

*Toro*.
Anas da yake bin Yabi. Yana bandakin k'ofar Dada yana simince shi a dalilin wanda aka yi mata da ta rubza ya farfashe, ba'a yi aikin aminci ba.
Gabadaya Baba Maryo ta shafa'a shaf yana k'ofar, kuma kusa da kicin din da take zaune ne.
Ta hau tonon murhun tana ce wa "Allah suturi buk'i da auren mazinaci kuma mai dilar k'waya. Wane mutum na had'a iri da shi cikin sanina?"
Kalaman ta suka ja hankalinsa ya ajiye abin aikin ya leko tunda bayin ba me k'yaure ne ba.
Ganin da ya yi tana tono ya sake jan hankalinsa k'warai da gaske, ya matso sosai. Yana kallonta k'yar. Ya jima yana zargin Yaya Bulkachuwa ba a bar shi haka siddan akan al'amarin Nasiba ba. Ashe kuwa hakane. Ya sandare cikin tu'aajjibi a lokacin da ya ga ta fito da laya a k'asan murhun ta kyasta mata ashana ta k'one.
Ta ja tsaki mai tsananin gaske tare da ce wa "Allah na gode da baka k'addara mini ganin auren ta da mai arzikin bogi ba. Ban da ma dai batan basira me za'a yi ne da wanda aka yiwa bulalar zina a bainar nasi? Lallai na yi mantuwa mai yawa. To na tone ramin da na hak'a tun ban rufta ba. Dama Yabi ce ta dace da shi a wannan duniyar."
Daidai lokacin Anas ya kasa jure wa ya yi gyaran murya. Ta waiwaya a ankare. Idanuwansu suka hadu, ta yi wura wura. Ta rasa inda zata tsoma ranta. Shi kuwa sai ya ce "A dinga yin sara ana duban bakin gatari Baba! Da Yaya Bulkachuwa, da Adda Yabi, da kuma Adda Nasiba kamata ya yi ki dauke su abu guda. Ba wai ki nemi rugurguza zaman lafiyarsu dan bukatar kan ki ba. Kin cutar da su duka. Ita kanta Adda Nasibar ai dan ba yadda zata yi ne, akan dole ta bi ra'ayin ki domin tana da darhamin imani a zuciyarta. Ya fara hawaye ya ce "Duk duniya ki rasa wanda zaki yiwa kulunboto ya so diyar ki sai mijin d'iyar Baban Marina! Kaico da
Bakar hassada, kaico da mutanan da suke da son zuciya, wacce irin BAK'AR TA'ADA ce haka? Asiri kika yi wa Yaya Bulkachuwa! Innalillahi wa inna ilaihir rajiun " Sai kawai ya fito daga bayin a gigice ya zunduma ihu da dukkan muryarsa tamkar mace ba jarumin namiji ba. Domin ya riga ya gigita da abin da ya ga ni k'warai da gaske.
Ta hau tafa hannu tana ce wa "Ashe a maza ma akwai makirai majununai? Zaka ga tsiya da tuggu kuwa! Zan nuna maka uban ka ma ya wuce ya tozarta ni, ya kwaye mini asirina. Zaka gasgata makircin mace aziman ne yau din nan".
Sai kawai ta takarkare ta zunduma ihu mai tsananin gaske. Da yake Dada barci take, a firgice ta farka tana fad'in "Waye ya mutu Maryamu? Jin shiru sai kukan Anas da na autarta ya cika mata kunnawan, ita ma sai kawai ta fashe da kukan daga dakinta. Tana fad'in "Allah kasa basu harbe mini "Mai sunan manya ba. Lah ha ilah ha ilallahu!
Mintina kalilan jama'a suka taru a k'ofar ta da Dada.
Baban Kasuwa da na Tsakiya suna gidan yayin da Baban Marina baya nan. Dan haka a sukwane suka bu sahun ahalin gidan da suke ta shigowa a gigice.
Kowa sai tambayar ba'asin kukansu yake yi. Anas sai hadiyar zuciya yake yi ya kasa bude baki ya yi magana.
Jikin kowa ya yi sanyi tare da sake shiga rudani mai yawa. Domin kowa yasan Anas ba mai hayaniya ba ne sannan yaro ne mai juriya da hak'uri na gaske. Sun tabbatar ba zai yi kuka irin haka ba tare da ya ga wata masifar, domin a lokacin da yake yaro ma ba mai fitina ko koke koken banza ba ne, bare kuma yanzu da yake da shekara ashirin da biyu, ya zama saurayi na sosai.
Baban Kasuwa ya ce "Maryo mene ne haka? Me ya faru ya tambaya zuciyarsa na rawa irin ta zullimi.
Ta kuwa karkace ta kara k'arfin kukanta ta ce "Ban san yana makewayi ba. Sai na afka bayin ba tare da na tambaya ko akwai mutum a ciki ba. Babu zato na ga Anas ya gogawa al'aurarsa sabulu yana wasa da ita! Na zauce na fito a sukwane ina hirji. Kunya tasa ya kasa fitowa. Sai yanzu ya yi jihadi ya fito, wai dan na yi masa matashiya akan haramcin hakan shine ya fasa mini ihu yana neman k'ulla mini sharri tunda dama dukkansu y'aya'n Alhaji sun tsananta mini akan Tijjani, mussaman y'aya'n Asma'u da ko gaisuwa sun yanke yi mini dan su nuna mini Yabi ta fini a wajensu. Amma ni ban ga laifinsu ba. Ubansu ne ya yarda
ta ni irin haka." Sai ta zarce da sabo n kuka.
Su Baban Kasuwa suka d'auki salati tare da ce wa "Muminin kare ne ashe kai. Kullum da kai ake kwatance a gidan nan da ma unguwar baki daya saboda nutsuwar ka da hamlnkalin ka ashe BAK'AR TA'ADAR da kake tafi ta yaranmu da ake yi musu kallon fitinannu ne! Duk yadda aka yi kai ne ka yiwa y'ar wajen Malam Kabiru fyade satin da ya wuce. Yarinya karama da ko magana bata iya ba, aka kasa gano mugun da ya aikata mata aika aikar ashe kai ne".
Kuka ya tsayawa Anas cak. Ya Kalli Baba Maryo ya kalli Baban Kasuwa. Yana ta kissima sune k'ananu a cikin iyayensu amma sune suke kan gaba wajen ruguza gidan Marina. Bai gama nazarinsu ba sai ya jiyo Baban Tsakiya ya ce "A a tunda ba mu ga ya haike mata ba, bai kamata mu jingina masa ba, shaidar zina babban al'amari ne. Sannan idan aka ji maganar a bakinmu ai muma mun kunyata domin baza mu ce ba daga gidan nan ya fito ba. Kawai shata masa layi zamu yi da y'aya'nmu kada ya dinga b'ata manaa su bamu ankare ba tunda ya jefa kansa a wannan BAK'AR TA'ADAR ta istimina'i".
Yara da manya kowa yabi Anas da kallon tsana da tuhuma. Duk Mama da kanta ta ce "Anas ba lallatacce ba ne. Na tabbatar bai aikata hakan ba Maryo".
Sai lokacin ya samu kuzarin Budeibaki ya ce "A a Mama kada ki ce mata komai. Na riga na kai alkalanci gaban Ubangiji. Idan ya tabbata na yi abin d at fada to ku nema mini gafarar Allah. Na kuma yafe mata tozarta ni da ta yi, tunda ai ba hakan ya kamata ta yi mini ba.
Idan kuwa ban aikata ba ta mini hakan to da ikon Allah ba zaki mutu da ido ba Baba Maryo ".
Ta zunduma ihu tana d'ura masa ashariya.
Bai rufe baki ba ya ce "Ganinta na yi ta tono mugun k'ullin da ta yiwa Yaya Bulkachuwa akan ya rikice akan Adda Nasiba. Tana fad'in ta fasa auren tunda dan k'waya ne kuma mazinaci. Ganin na ganta ta k'ona layar shine ta mini hakan. Ba zan zage ki ba, ko a lahira wani kan ci arzikin wani. Ban ci arzikin ubana a wajenki ba. Nima ba zaki ci nasa ba. Kin ci arzikin kasancewar ki uwar Yaya Ammar. Ba dan shi ba, ina rantse miki da girman Ubangiji sai na miki dukan da ko Dada sai ta yi gaske da ta shaida ki. Amma babu komai na barwa Allah komai."
Ya mik'e yana tangadi yayin da kowa ya yi tsit. Ya kalli Baban Kasuwa ya ce "D'a na kowa ne Baba".
Baban Kasuwa ya ce "Ni kad'ai zaka fad'awa hakan, shima Baban Tsakiya ai ya tofa nasa"
Anas ya ce "Ko ya tofa dai bai mini k'azafi ba, gaskiyar fahimtarsa ya fad'a.
Dada tana bakin k'ofarta tana kurshegen kuka tana fad'in "Dambarwa ta tsananta a cikin ahalina. Ubangiji na ci albarkacin sallah da salati, ka sassauta, yafe mini, ka shirya mini zuria gabadaya".
Har aka gama wannan cecekucen Baban Marina da Gwaggo basu tofa ba. Mama ce ta shiga lamarin ta yi kane kane tunda yanzu yar tsama ce mai tsananin gaske a tsakaninta da Maryo.
Baya ga hakan kowa yasan Anas ba zai yi abin da ta fad'a ba. An kuma gasgata shi,asirin da yaga ta tone.ne ya ya sanya ta yi wannan dibar albarkar.
Nasiba kuka ba wanda bata yi shi ba. Ammar da yake BAUCHI da ya ji labarin bai dauke shi da muhimmanci ba. Murnar yadda ta kunce k'ullin da ta yi yake yi. Domin yana matukar tausayin yadda Bulkachuwa yake damunsa ya kawo masa Nasiba ya ganta. Yanzu kuwa tunda an warware zai daina, zai samu nutsuwa, tunda wani lokacin har susuce wa yake zufa na karyo masa.
Da labari ya zo mana Babah ta ce mini "Tare ta hada ta mana ai, ni tun kwanaki na kubuta. Nawa a kasan randa aka yi mini ta yadda zan zama mai sanyi akan sha'anin. Sannan aka danne mini zuciyata.
Shi kuwa a k'asan murhun. Matukar aka hura wuta a murhun ba shi ba sukuni idan bai ganta ba. Kai wacce irin BAK'AR TA'ADA ce haka?
Ta fara hawaye. Na taya ta muka yi kukanmu sosai domin ta ba ni tausayi. Da ciwo kwarai ace d'an-uwanka ne zai musguna maka irin haka.
A raina kuwa na yafe dukkan musgunawar da Tijjani ya yi mini akan Nasiba. Na sake gasgata ba yin kansa ba ne. Na kuma sake kudire a raina matukar ba Babah ba, wani mahaluki ba zai ji halin da nake ciki da shi ba.
Zan jira shi har ya kammala WA'ADIN da zai yi, zan kuma yi gwagwarmaya har komai ya daidaita mana.
Karshe na yi jarumtar ce wa "Mu yi hak'uri Babah ai ba kuka zamu yi ba. Alhamdulillah zamu tsananta fad'a, mu kuma sake dage wa da addu'a."
Murya babu amo ta ce "Allh ya yi miki albarka, ya kara miki hak'uri, da ikon Allah Ubangiji zai miki sakamakklon alheri na gode sosai"
Nafi wata biyu ban warware na fara sabgogina ba. Duk karshen wata zamu je mu gano shi. Aliyu kuwa daidai gwargwado idan karshen wata ya zo zai siyo mana kayan abinci, ya kawo da kansa ya kuma damkawa Babah kudin da zamu rik'e. Ya tisa yara a gaba su fita, ya yo musu siyayya sai ya dawo da su. Shirin aurensa ake yi wannan al'amarin ne ya dakatar da komai.
Haka su Yaya Salisu akai akai suke mana aika. Yaya Ammar kuwa duk sadda muka je prison sai ya bawa Yara kudi masu auki, kuma babu jami'in da yake tsaya mana a kai saboda Yaya Ammar.
Ba laifi kuma yana leko mu jifa, jifa shi da iyalinsa.
Yaya J ma duk watan duniya yana aikowa yara kudi amma bata hannuna ba, ta hannun Yaya Rabiu. Shi kuwa yana turo mini ta asusuna. Idan na yi masa text din godiya sai ya ce ba sai an ji ba. Bamu da wata matsala gagaruma. Amma da tafiya ta fara nisa sai na fahimci dukkan masu tallafa mini kama daga kan mahaifana, Aliyu kanin Tijjani, su Yaya Salisu da J hadi da tsirarrarun dangi masu bamu sabulai kowa yana da nauyi a kansa baza su tabbata suna mana hidima ba . Mussaman da kullum rayuwar take sake tsefe wa. Ina kwnace ni kad'ai a daki yara sun tafi makaranta yayin da Baba take dakinta tana lazimi. Tunani nake yi tare da nazarin kaalaman da Tijjani ya yi ta yi mini a lokacin da nake bacin ran shiga makaranta. Ba abin da yafi tsaya mini a rai fiye da yadda yake ta nanata ni kad'ai ce yake da tabbacin bazan gaza da hidimar y'aya'nsa ba.
A lissafi watanninsa tara a tsare. Har lokacin kuma bana aikin komai, ban dogara da komai ba sai wanda dangi suke mana. Tunda na riga na gajiya na kasa yin kitso bare lalle.
Na numfasa a fili na furta "Ya kamata na yi hobbasa na taimaki kaina.
Na hakurkurtar da zuciyata na fita na siyo kayan kunshi. Na fara posting na fara lalle.
Ba'a dauki lokaci ba mutane suka fara dawo mini.
Da yake bamu da wasu matsalar sosia, sai na ninka aiken da nake yiwa Babanmu. Tunda aka rufe Tijjani ahalin Baban Marina suka gane Tijjani ke hidimar k'ofar da kaso bakwai cikin goma. Wanda ko ni ban gane hakan ba sai yanzu.
Dan haka na dage nake tallafawa Yaya Salisu da Yaya Rabiu rik'e gidan.
Gefe ina ajiye dan ajiye wani abu a banki, dan tsaron lalurar da zata zo mini b'akatatan. Na shafe tunanin siyan gidan da nake burin yi. Domin tunda muka yi fad'an da Baban 2 ya ce mini gidansa ne ba nawa ba nake tunanin ya kamata na siyi gidan kaina. Idan na had'a zobuna na da dankunne na na sani ciko zan yi tunda manya ne sosai kowa yasan yadda gold ya tsefe. Zan siya zuwa gaba idan na warware matsalar Tijjani.
Sannu a hankali nake samun k'arfin zuciyar rungumar kaddarar da afko mana bakatatan. Mussaman da Baban 2 ya kwantar da hankalinsa ya yi imani da kaddarar da ta same shi.

*Akwai kaya masu kyau a cikin farashi mai sauki*
*Saiwowin maganin sanyi*
*Saiwowin Tsumi*
*Saiwowin dahuwar kaza*
*Saiwowin dahuwar tattabaru*
*Gumba*
*Tsumin kwakwa*
*Y'aya'n gadali*
*Hadadden daka*.
*Tsugunno mai sa a matse*
*Goran tula*
*Goran tula syrup*
*Garin goran tula*.
*Maganin gyaran nono*.
*Zuma ta mussaman*.
*Tsumi*.
*Da sauran kayayyaki na mussaman da basu da illah*.
* Domin kuwa asalin Saiwowin ne da ake kawo su daga Chad*.
*Abu mai kyau shi ke siyar da kansa ku tuntube ni dan samun naku kayan cikin sauki da mututantawa. Ina aikawa ko ina a fad'in tarairaiyar Nijeriya*
*08032773332*


95&96.


*HAJIYA HANNE ADO ABDULLAHI?*
*MARUBUCIYAR WANKA DA GARI DA KUMA WACE CE UWA?*
*KUN TUNA IRIN BAJINTAR TA AKAN RUBUTUN ADABI DA TARBIYA?*
*TO ITA MA TAKANAS NA SAMO MUKU LITTAFANTA DOMIN KUN SANI TA YI RUBUTU MASU MA'ANA*.
*LITTAFAN DA YAWA, AMMA AKWAI DISCOUNT DOMIN SO NAKE KU YI TA SIYAWA Y'AYA'NKU DA KANNENKU LITTAFAI MASU DARASI DA MA'ANA*.


*INA MUKU ALBISHIR AKWAI DUKKAN TSOFAFFIN LITTAFAN MARUBUCIYA HAJIYA SALIHA ABUBAKAR ZARIA*
*ZAKU SAME SU SOFT COPIES, A HANNUNA*
*SANNAN SABO DAL NA KAN HANYA*

*HAKA NAN AKWAI WASU DAGA CIKIN LITTAFAN MARUBUCIYA HAJIYA HAFSAT C SODANGI, SUMA SOFT COPIES KAZALIKA ITAMA SABON LITTAFIN TA MA KAN HANYA*

*BA DA JIMAWA BA ZAN ZO MUKU DA SU*.
*08032773332*


*INA MATUKAR GODIYA BISA ADDU'ARKU DA KUMA KAUNARKU GA RUBUTUNA*
*WANNAN SHAFIN SADAUKARWA NE TARE DA GODIYA GA DUKKAN WADANDA SUKA SAKA KUDINSU SUKA SIYI WANNAN LABARIN DON JADDADA MINI SOYAYYA DA KUMA KARFAFA GUIWA*
*NA GODE, NA GODE*.


Auren Aliyu ya samu tasgado. Ba akan komai ba sai akan an kai suka gidansu amaryar cewar d'an-uwansa dan safarar kwaya me gwamnati ta rufe shi Shima ana kyautara zaton yana da BAK'AR TA'ADA. Muna ji muna ga ni aka hana Yaya Aliyu aure ba a akan laifinsa ba. Dama Kuma Babaiba son inda ya dauko auren ba, yar babban attajirice. A raina na Jin ciwon yadda mutanan yau suke yiwa mutane hukunci da laifin yan'uwansu ko na dangunsu alhalin Allah da kansa baya bawa da laifin mahaifansa bare kuma laifin d'an-uwansa. A zuciyata tamkar na ce masa ya nemi Iklima da a yanzu take kwalejin koyon aikin jinya da ke Azare, tana shekarar karshe. A kansu a aka

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login