Showing 123001 words to 126000 words out of 184118 words
Chapter 42 - Bakar Taada Hausa Novel Complete
ba ka'dan ba.
*Domin samun naku kayan gyara na mussaman, ko maganin sanyi sadidan.*
*SAIWOWINE da ake kawo su daga Chad da Sudan gangariya. Ku tuntu'be ni a kai-tsaye ta manhajar WhatsApp*
08032773332.
*KUN TUNA MAI GYARAN GUDUYO?*
*INA NUFIN FASEELAT BABBAR DILA TA G.H.T.*
*KO WANNE NAU'IN KAYAN GHT TANA SIYAR DA SU AKAN FARASHI MAI RANGWAME*
*KAWAI KU TUNTUBE TA A WANNAN LAMBAR DAN GANIN JERIN KAYAN DA TAKE DA SU*
*TUN DAGA KAN SUPPLEMENT, SABULAI DA LIPTON*.
*MASANIYA CE AKAN KAMFANIN DOMIN TA SAMU KARRAMA WA DAGA KAMFANIN A BANA, HANZARTA KI TUNTUBETA DAN SIYA DAI DAI KO SARI.*
*IDAN KUWA KINA SON YIN RIGISTA DAN FARA KASUWANCIN KAWAI KI TUNTUBETA DAN KUWA DA KYAKKWAR ZUCIYA ZATA MU'AMALANCE KI*
*07039269802*
*Annur food Delicious Nig*
*Da k'arfin zuciya da guiwa na ke muku shunen inda zaku samu kayan da na zano a kasa cikin saukakkan farashi.*
*Shaida nake yiwa kayan annur domin dadinsu da ingancinsu ya kai kurewa*
*HANZARTA ki nemi kayansu dan ki gasgata batuna*
*Garin kunun tsamiya garin danwake, garin borkono, yajin daddawa, man shanu, nikekkakiyar gyada ta kunu da ta miya*
*08039183880*
*Wannan page din tukuici ne ga masu comments akan littafin BAK'AR TA'ADA*
Kwana biyu da komawa ta Muna ta barzar amarci. Yaran kuwa tamkar almara basa kuka. Da sun yi ka'dan suka sha nono sai su yi kwanciyarsu sai an idar da sallar asuba zasu farka.
Yana dawowa kuwa zai d'ora mana ruwan wanka. Da aka sa zai juyo, ya taya ni mu yi musu wanka.
Ni da kaina na tabbatar zai yi wahalar gaske a samu miji irin Bulkachuwa. Domin duk aiyukan gida ba zai zame masa komai ya yi ba.
Ina jin dadin Supplement din FASEELAT. Sun taimake ni wajen gyara mini ruwan nono da sake hade ni. .G H.T duniya ne na yarda *07039269802*.
Rainon yaran nan kuwa ba abin da ba ya yi. Kafin na yi musu hidima d'aya ya yi musu biyar. Ko pampars suka bata, ba ya jin komai zai cire ya wanke musu ya saka musu wani. Idan sun yi barci, sai kuma ya dawo yana tiritiri da ni.
Tun tafiyar tamu bata yi nisa ba na fara fa'din madallah da aurensa a zuciyata. Ban dai furta a fili ba ne.
Kwana duk da kuwa yana da na'kasu, sai dai alherinsa yafi tsiyatakum yawa.
Kwana biyar da komawa. Baba Lami ta zo daga kangire. Wacce matsayin kaka ce a wajena. Tunda k'anwar mahaifiyar Gwaggo ce uwa daya uba daya.
Ranar da ta zo, a ranar ya koma Bauchi.
Cikin sau'ki da rangwame nake rainon yan biyu. Basu da fitina. Sannan Baba lami mace ce mai kazar kazar ainun. Abin da nake yi ka'dan ne. Watana biyu da haihuwa na koma kan sana'a ta.
A hankali kuma Tijjani yana samun rufin asiri a zamansa a baucy. Tunda abinci dai baya yanke mana. Iyakar kokarin jarfinsa yana yi. Duk sati zai taho musu da Pampers. Ni kuwa kayan shayi duk sati ne. Idan na ce "Basu kare ba".
Ya dinga fa'da akan me bazan dinga shan shayi mai kauri ba, alhalin ina shayar da yara har biyu. Ga su nan su sun yi girma ni kuma na sake zuke wa.
Watarana Baba lami ta ce masa ba rashin cin abinci ba ne, wasu matan idan suna shayarwa hakan suke yi. Sai sun ya ye sannan su yi kumari.
Baba Lami bata tafi ba sai da muka kwashe watanni kusan biyar a tare. Lokacin su Hanif na da watanni shida.
Muka ha'da mata alheri sosai. Sannan suka tafi da Gwaggo da Yaya Ummi bikin da za'a yi a can Kangire. Na so zuwa, amma ya yi mirsisi ya hana.
Sannu a hankali muke rayuwa, bamu cika samun matsala ba, tunda kwanakin da yake yi a Bauchi sun fi wanda yake yi a Toro.
Kullum idan ya dawo sai ya ce "ki tsananta yimini addu'a little. Mahassada sun kewaye ni a kasuwar nan. Ga shi an rasa gane inda matsalar take kullum Alhajin da muke wajensa sai karayar arziki ya ke samu.
Ina jin tsoro k'warai da gaske.
Cikin tausayi na ke kwantar masa da hankali da kalamai masu taushi.
Wani zuwa da ya yi, ya ce "mu
shirya zai kai mu Bulkachuwa mu yi sati.
Na dinga murna domin rabona da zuwa tun kafin na haihu. Ga shi yazu watannin su tara har sun fara tsayawa. A yanzu kam na gasgata kama suke yi da Bulkachuwa. Domin suma haka suke dogaye, masu gaba manya. Ba wanda zai ce ni ce uwarsu. Domin manya ne sosai, sannan ni yar tsurut ce sosai. Kawai faratuna suka diba, da kuma yan k'ananun kamanni. Amma kammanin ubansu yafi yawa a tare da su. Tun yanzun kuma halayyarsu ta banbanta. Haneef mai sanyi da hakuri ne. Sai ya yini baka ji kukansa ba. Kafin ya nemi nono sau daya Hamim ya nema sau uku.
Zai yi wahalar gaske ya damuki d'anuwansa yasa shi kuka. Amma Hamim kullum cikin nukurkusrsa yake.
Ga shi da shegiyar kiwa. Ko wajen Babansu sai ya akan dole yake zuwa. Ko idan ya ga ya dauki Hanif zasu fita.
Shi dai kullum yana jikina. Ko k'unshi zan yi, sai dai na ha'da masa kayan wasa a kusa da ni.
Ko ya ce ",sai na goye shi.
Sabanin Hanif da ba ya yin kiwa. Kowa ya mika masa hannu zuwa yake yi.
Shiyasa ma na fi kai shi gidan Yaya Ummi ya yini tunda yanzu ba ni da nisa da ita.
Kullum Bulkachuwa sai ya ce halina ya kwaso. Domin mafad'aci ne na gaske, ga kuka. Idan ina mita akan halinsa Gwaggo ma ce wa take yi hakan na yi mata. Haka ta sha fama a goyona. Bana yarda a dauke ni. Ko band'aki zata shiga sai an yi artabu da ni.
Da yammaci muka isa Bulkachuwa. Babah sai ina ka saka take yi da ni da yara. Komai ta mika hannu a kai sai ta dauko ta ajiye a gabana. Yara kuwa kayan wasa sabbi sun fi kala uku tamkar dama a wajenta suke. Na kasa ha'kuri na ce "Babah wadanda kayan wasan fa?". Domin ihisan ba a garin take ba. A cikin Bauchi take bari na yi zaton na yaranta ne.
Da walwala ta ce "Tunda ya ce zaku zo na siya musu, tunda na ga mai sunan yayan nawa rigimamme ne. Shi dai bai kwaso halin mai sunansa ba. Hanif ne ya kwaso halin mai sunansa."
Nasir da yake gefe ya ce "Su Babah ana yabon sunan masoyi".
Ya bani dariya na rufe fuskata na dinga yinta. Ta mike sabe da Hanif tana fa'din ja'iran yara bari na baku waje.
Shi dai Tijjani bai ce komai ba. Asalima matse wa ya yi ko dariyar bai yi ba.
Kwana biyu ya yi, ya barmu ya wuce Bauchi.
Bayan dakina da na Gwaggo ba inda nake samun natsuwa irin a dakin Babah. Domin wata irin mua'amala take yi da ni mai dadi da tattali. Bata taba nuna surukunta a tsakaninmu ba. Sai ni ce ma nake jin kunyar yin wasu abubuwan a gabanta. Ita kuwa da taga hakan zata balbale ni da fa'da tana fa'din bata son rashin kunya. Har yaushe na zama matar tasa da zan ture ta a uwa na mata kallon suruka. Na sake na yi komai yadda nake so kamar yadda nake yi tuntuni.
Da kanta ta dafa mini kazar da na tabbatar ta mata ce. Kunya ta kama ni. Ita kuwa fadi take ci ki sha romon. Tun lokacin haihuwar na siya na dauka zaku zo yawon arba'in. Tunda baku zo ba. Na ajiye nasan a can ma za'a gyara ki."
Na rasa yadda zan yi, ita kuwa ko a jikinta.
Ranar da Bulkachuwa ya dawo. Da daddare an hadu a falonta ana ta hira cikin walwala ya kutso da maganar yana son mu koma Bauchi gaba'daya.
Ta ce "ka dai kafe. Yanzu kam tunda yaranta sun yi k'wari ba zan hana ba. Allah ya bada sa'a.
Dama har da tunanin yadda sana'ar ta zata durk'ushe ne. Amma In sha Allah a can din ma sannu a hankali za'a santa."
Ni kuma sai kawo masa abinci abubuwa nake yi. Gaba'daya na kasa sukuni. Babah da kanta ta gane yanzu kam sonsa nake yi da dukkan zuciyata.
Washagari ana zaune bayan mun karya. Sai kawai ya kalle ni ya ce "A irin wannan ranar ta shekaru uku baya kika zo har nan kika ce ba kya sona Asiya".
Nan da nan na ji tamkar k'asa ta tsage na shige. Kunya ta rufar mini. Na rasa yadda zan yi. Sai kawai na fara kuka ina ce wa "Idan juninka tashin tashina ne, da son sai ka kunyata ni, to ni ba damuwa zan yi ba, kai ne zaka ji kunya Wallahi".
Nasiru ma cikin dariya ya ce "Ai kuwa nima na tuna yawun da kika kwalbana masa a fuskarsa. Yau kuwa sai faman girmama lamarinsa kike yi".
Na sake rushe wa da kuka ina ce wa "Ai kai dama baka fa'din gaskiya".
Babah ta ce "Yo ni ke kika fi ba ni haushi, to kukan na mene ne? Ware wa zaki yi ai ku yaga, suma ki nutsu ki fadi irin nasu al'amarin da baza su so a taso musu shi ba."
"Nasiru ya ce "Ni dai babu abin da zata fa'da a kaina, sai dai ko akan mijinta".
Tijjani dai tunda ya kunyata ni bai sake ce wa ba.
Jimawa ka'dan Babah ta mike ta shiga cikin gida.
Nasiru ma ya mike yana ce wa "Hajiya Yabi bari na fece tun Babah bata zo ta fa'da miki wani abu a kaina ba."
Ko kula shi ban yi ba.
Yana fita na kalli Tijjani na ce "Na gode sosai Baban 2"
Ya yi murmushi ya ce "wannan godiyar fa! Ta mece ce?"
Na matso hawaye na ce ",Na gode da kunyata ni da ka yi, na gode da wannan sakayyar".
Ya dara ka'dan ya ce ",Kin san na fa'da miki lokaci zai zo da zaki ji kunyar abin da kika yi".
A hassale na ce ",To mene ne zaka tayar a gabanta? Gaskiya kada ka sake yi mini irin haka. Idan kuwa ba hakan ba kasan kai ma ka mini laifin da ban ta'ba bude wa an ji ba".
Nan da nan ya shiga nutsuwarsa ya ce "Ai ni ba da bacin rai na fa'di hakan ba. Amma ba zan sake ba, mu rufe maganar haka nan.
Na girgiza kai na juyar da fuskata gefe. Ya shiga kiran sunana a hankali, na ki juyowa. Ya diririce. Ya ce "Asiya wasa fa nake yi miki. Me zai sa
mu yi fa'da a gaban Babah".
Na ce "Ai so kake ka bakanta ni a wajen ta, shi yasa ka dauko wannan maganar".
Ya marairaice ya ce "Billahillazi ba hakan ba ne. Gaba'daya ya rikice jin na lauya magana zan tado da tashin hankali.
Ya dinga lallaba ni da son sai na dawo da walwala ta.
Ni kuma ina sane na yi masa hakan.
Bamu bar garin Bulkachuwa ba sai da muka shafe sati biyu.
Da zamu tafi, tamkar wanda muka je fatauci saboda kayan da muka samu.
Lafiya k'alau muka isa Toro. Kwana biyu a tsakani ya koma Bauchi.
Kwatsam aka tashi da mutuwar mijin Nasiba. Wannan mutuwa ta bigemu, domin babu jinya sai mutuwa. Ashe kasurgumin dan shaye shaye ne. Can wajen sharholiyarsu rikici ya kaure tsakaninsa da abokinsa ai kuwa ya daba masa kwalbar a kahon zuci ya mutu a wajen nan take.
Gaba'daya maganar ta cika Toro da kewaye.
Na tausayawa Nasiba kwarai da gaske, duk da dama ba zaman dadi take yi da shi ba. Duk cikinmu ita ce bata samu sukuni a gidan aurenta ba. Yaranta biyu Muhsin, da kuma Maryam da bata fi watanni shida da haihuwa ba.
*Watanni bakwai a gaba*
Zuwa wannan lokacin mun koma Bauchi da zama. A satin nan kuma na yaye yara. Bulkachuwa aka kaiwa Babah su. Kwance nake ina fama da zazzabin da ciwon nono ya zuba mini. Ga kewar yara, abin sai ya hadu ya kwantar da ni. Nasan Hanif ba shi da matsala, amma Hamim kam sai Allah. Rashinsa ya fi takura ni.
Tijjani kuwa sai tsokana ta yake da fa'din Hanif ne kawai zai dawo, Hamim ya zama dan Bulkachuwa.
Bana ce wa komai amma na sani zolaya ta yake yi.
Sai da na sha allurai sannan na warware.
Sannu a hankali na shiga saboggina tunda anan Bauchi ma na fara sanuwa a wajen k'unshi da kitso, sai dai ba kaman Toro ba.
Matsakaicin gida ya kama, cikin madaidaiciyar unguwa.
Cikin nutsuwa da rufin asiri mukr rayuwarmu. Har yau din nan Bulkachuwa tattala ni yake yi. Baya kaunar abin da zai ha'damu rikici sai dole. Baya mini fishin da ya wuce na kwana d'aya. Ni ce dai nake jarumtar share shi na lokaci mai yawa.
Duk da ni din ma karfin hali nake yi.
Yanzu haka Tijjani yana da nasa teburin a cikin kasuwar ma'ana ba k'arkashin Alhaji yake ba. Watanni uku ya karbi ku'dina ya mallaki wajen flda zai ajiye teburinsa. Zobena daya muka siyar. Yanzu haka jiya ya kai ni na zabi wanda nake so ya siya mini a madadin nawa.
Na sani ba dan ya samu damar biyan ba ne, sai dan yana son ya biya ni ne.
Hakan kuma bai sa sun rabu da Alhaji Auta ba.
Ana cikin haka guda cikin kamfanin sadarwa ya nemi kafa turakan ayyuknasu cikin unguwar da filin Tijjani yake. Gaba'daya mutanan da suke da fili a wajen kowa fata yake a ce su karbi nasa, tunda haya zasu kar'ba.
Alhaji Auta har addu'a ya baza a yi masa ko ya samu ya d'an farfado.
Kamfani har yanzu zagaye yake tare da wakilinsu da suka san ilimin kimiyya suna ta auna inda zasu fi samun sabis.
Gaba'daya Tijjani bai sa hankalinsa a wajen ba. Gara ma jiya ya ce mini ku'din da mutum zai samu a shekara d'aya kacal ba k'ananu ba ne.
Ina bu'de baki na ce "Idan akwai alheri a cikin samun da za'a yi, Allah ya saukar a kan filinmu".
Ya ce "Kayya! Amma tunda Allah kika ce ai magana ta k'are. Ameen".
Muka bar magana a hakan.
A wannan tsukun auren su Yaya Ammar da na Yaya Rabiu da su Kaltume ya zo.
Muka shirya muka tafi tare. A can muka tarar da Babah da y'an yayenta. Hamim na ganina ya cakume ni, ya cukuikuiye hijabina wai bazan gudu na bar shi ba. Hanif kuwa kawai kwantar da kansa ya yi a jikina. Tijjani ya kalle shi ya ce "Kai ma ka bi bayan d'anuwan ka, baka ta tawa ko?" Ya kalle shi kawai. Ya yafice shi tare da ce wa "zo mana Babana".
Ya kuwa isa gare shi ya kwanta. Yayin da Hamim ya rikice sai ya sha nono. Da k'yar Tijjani ya yane shi suka fice.
Babah ta ce "Ai ban yi zaton darun d'anuwana ya kai haka ba sai yanzu".
Na ce "Ai ba shi da sau'ki Babah. Hanif ya fi sassauci". Ta ce "Babu hadi ma. Allah ya musu albarka ya tsare su. Ki yawaita yi musu addu'ar tsari da kuma kambun baka".
Cikin na ce "To".
Duk inda na shiga sai an kalle ni. Da na juya baya za a hau zancena. Haka Ikilima ta jiyo mini gulmar da sa'anina da muka taso tare su Saratu su Maijida. Suna fa'din ",Ai gaba'daya Bulkachuwa tsorona yake ji saboda ina da ku'di. Duk kafafar da nake yi da burgar kwalliya da yadikan yan gayu na Umm Nihla collection. Ni nake yiwa kaina ba shi ba ne. Su kuwa sun gode Allah mazajensu ne suke dawainiya da su yadda Allah ya hukunta. Barin Maijidda da a yanzu suke Kaduna. A dalilin Yaya J ya samu aiki a kwalejin kimiyya ta kaduna(Kad-poly).
Gaskiya ne duk ta fimu d'aukar ido. Amma kuma ba wai ta fi kowa kwanciyar hankali ba ne. Ko wacce ita tasan yadda take zaune a gidanta.
Nasiba tuni ta sake dawowa gidanmu gaban Dada. A yanzu da bata da aure ma tafi walwala da kwanciyar hankali. Tunda yayanta Ammar na kula da ita daidai gwagwado. Sannan iyayen mijinta suna ri'ke da Muhsin cikin kulawa, Maryam din da take shan nono ma sukan yi mata aike lokaci zuwa lokaci. Gaba'daya ta murmure ta dawo da jikinta da ta rasa a baya. Sai daga baya aka gane komai na d'akinta ashe ya siyar tunda mashayi ne kuma dan caca. Da ace wata a k'ofarmu hakan ta same ta da anyi yamididin halin d atake ciki. Amma wannan shiru ake ji.
Tallafin da take samu ya sanya take figa take yin y'an sitturu da kayan kwalliya dan haka fes take bata da makusa.
Na yi tsuka na ce "Basu da abin yi ne, koma a ya ya na ke rayuwa ai babu ruwansu, tagayyara da ake mana fata kuwa ba zamu shige ta ba in sha Allah."
Amma a tunzure nake kwarai da Maijidda. Na kuma ku'dire indai ta sake ta mini maganganun banza yadda ta saba yi mini, idan mun hadu a taro, to a wannan karon zamu sake gwada yar kwanji dan na tuna mata baya.
Ta fitine ni da yawa. Nazira da take gefe ta ce "Sanin kina da daraja ne a wajen mijinta ya sanya ta washe ki, ban da haka kina matar wani, ta shafa miki lafiya mana, tunda tasan a musulunci mace bata auren miji biyu. Da a ce Nasiba ce ke, ai da tuni Maijidda ta kusa zama gawa, domin ba abin da zai hana mijinta fitowa neman auren ki, tunda har gobe yana son ki".
Da hanzari na ce "Allah suturi bukui. Ai sai yanzu na fahimci tun asali ba wani sonsa na yi ba, shak'uwa ce da soyayyar k'uruciya. Yanzu da na saba mua'amalantar barden namiji irin Baban 2, mai zan yi da dan karamin sauron mijinta? Su je can su k'arata har abada ba zai sake burge ni ba."
Dadi ya kama Adda Nazira ta fashe da dariya ta ce "Ina komawa zan fa'dawa Baban su Abid tun yanzu Yabi ta fara fa'din madallah da auren Yaya Bulkachuwa".
Kunya ta dan rufar mini na ce "eh ki fa'da masa".
Haka aka yi bikin aka gama lafiya. Baba Maryo da kanta wani gani gani take yi mini da ban san dalilinsa ba. Ba dama ta ga Babah ta yi mini wani abu sai ta ce "Ba hakan aka barki ba, da aka tashi kame mata Tijjani har da uwarsa aka ha'da ban da hakan irin wannan gudun zuciyrta da kike yi har ina? Yara na son zuwa wajen uwarsu kin kanekane kin rikesu kina fa'din ta je ta yi hidimar