Showing 168001 words to 171000 words out of 184118 words

Chapter 57 - Bakar Taada Hausa Novel Complete

tana zuwa makaranta ba iya sana'a take yi ba. Ashe ba yarinyace ainun yadda na zata ba, ban zaci ta cika sha biyar ba ma."
Ta ce kin yi karatu ne bayan na sakandire?"
A hankali na daga kaina na ce "Na yi N.C.E a nan college of education. Na karanta Home economics "
Ta fadada murmushin ta ta ce "Da kyau! Kina aiki ne?"
Na ce "A a takarda ta ta yi kyau amma Ubangiji bai kawo mini sababin samun aikin ba".
Ta ce "Ai kuwa kin samu yarinya".
Ta Kalli Hajiyar da ta kawo mu ta ce "A buga mata upper. A kai ta women center mafi kusa da ita ta dinga koyawa yaranmu sana'ar kitso da kunshi, hadi da tattalin gida."
Daga yau kuma na bata mukamin costume din first lady".
Cikin farin ciki Hajiyar take godiya a madadinmu. Ni kuma mamakin murnar da take yi ne ya sandarar da ni domin dai na jima ban ga mutanan da basu da Bakar Taadar kyashi da hassada kamar Hajiya mai magana da yawun matar gwamna ba.
Baba ta shiga godiya ita ma. Haka nima na shiga godiya mai yawa, kna hawayen farinciki. Na samu daukaka ta sanadin sana'a. Hatta aikin da na samu arzikin sana'a ne ya janyo mini. Alhamdulillah na dinga ambato babu sassautawa.


*Y'ar uwa, ya mukaji da bubukuwa?* *Daga nan fa har january kusan ko wanne sati akwai biki, in ba na kusa ba akwai na nesa, ban da tunanin gudunmuwa da ma kudin man da zakaje bikin ga tunanin abunda zaka saka.*
*Balle ace maaikaciya ce ko CEO ce kina business din ki, kinsan all eyes on you🧐, ke ba sayen atamfa ba komi tsadanta anyo copynta, shima lace haka, cabdi! To albishirinki yar uwa!*
*UMM NIHLA malaysianfabrics ta dauke miki damuwa, tana da fabrics kala kala masu sauki da inganci kuma babu inda zaki samesu in ba wurinta ba, kije taro ki haska kowa sai ya tambaye ki me kika saka ina kika samu💃 maza garzaya gurinta kusa labule.* https://wa.me/message/F3EWRSHQPQAAH1


*GUDUYO NA TALLATA MUKU INGANTATTUN SAIWOWI NA MUSSAMAN KUMA GANGANRIYA DAGA CHADI*
*IDAN KINA DA KANWA KI DIYAR DA ZAKI AURAR TO KI ZO KI JARRABA WADANNAN KAYAN DA BABU ASARA KO ALGUS A CIKINSU*.
*SANNAN KE MA DA KIKA KWANA BIYU A DAKI AKWAI BUKATAR KI SABUNTA KANKI*
*AKWIA SAIWOWIN SANYI*
AKWAI SAIWOWIN DAHUWAR KAZA*
*AKWAI SAIWOWIN DAHUWAR TATTABATU*
*AKWIA SAIWOWIN TSUMI*
*AKWAI PACKAGE DIN MAGANIN SANYI SADIDAN*
*AKWIA PACKAGE DIN AMARYA*
*AKWAI PACKAGE DIN MAIJEGO*
*AKWAI KAYAYYAKIN MASU INGANCI A FARASHI MAI RAHUSA*.
*AKWAI GORAN TULA SYRUP*
*AKWAI GORAN TULA FRUIT*
*INA AIKAWA KO WANNE GARI A FAD'IN TARAYYAR NIGERIA*
*MASU SO SU MINI MAGANA TA WANNAN LAMBAR 08032773332*
*DAN ALLAH SERIOUS BUYER'S ONLY*.

Da zamu tafi aka zuba mana leshina da atamfofi da kayan yara fall leda. Ga Kuma kayan ciye ciye da soyayyun nama. Sai da na nutsu sai na gane har da material din Malaysian Fabrics na umm Nihla.
Ta ce kuma Hajiyar ta sallame ni. Murya na rawa Babah ta ce "Baby wata sallama Kuma. Ai kin nuna mana ke din uwar kowa ce a wannan jahar. Allah ya kare ki, ya dora mijin ki akan magauta. Ya dauwamar da arziki ya shirya muku zuria "
Cikin Jin dad'i take fad'in Ameen amen".
Har gida Hajiyar ta kawo mu . Ta shigo ta huta. Kafin ta bar gidan Baba ta zayyane mata matsalar da mkue ciki akan lamarin Tijjani.
Ta ka'du k'warai da gaske. Sannan ta ce zata shigar da maganar gaban first lady da IZININ UBANGIJI.
Ta ajiye envelope tana ce wa "Ga albashin ki na farko costumes din matar gwamna. Kafin kuma ki fara karboa na gwamnati. Cikin satin nan zan kawo miki upper din ki har gida "
Na dinga yi mata addu'ar fatan alheri da godiya mai yawa. Ta karbi takarduna ta tafi da su.
Kwanaki uku ta dawo mini da upper kamar yadda ta yi alkawarin kawo mini har gida. Sannan women center din unguwarmu aka tura ni. Wnai abin burgewa a weekend ne aikin nawa. Ga albashina da tsoka babu laifi.
Sati na zagowa muka tafi wajen Tijjani muka yi masa bayanin halin da ake ciki. Ya yi murna, ya yi fatan alheri.
Ya sake jaddada mini bai yarda na dinga zuwa gidajen mutane ba. Gidan gwamnati ya amice Slshima sai tare da Babah zamu je. Da girmamawa nake ce wa to, domin ya samu nutsuwa. Nima kuma bana k'aunar abin da zai bata masa rai. Domin a yanzu na gasgata bayan iyayena ba abin da nake so a duniya irin Tijjani da y'aya'nsa. Hatta uwarsa da y'an uwansa ina jinsu daban a duniyata.
Ganin ya amince na ce wa Babah zamu je Toro na KAIWA su Baban Marina su ga upper ta."
Ta ce "hakan ya yi. Washagari kuwa muka tafi Toro.
Murna kan murna Baban Marina ya yi. Ya dafa kaina ya ce "Nasan zaki yi albarka Yabi. Na sani akwai babban al'amari a tare da ke. Na sani zaki daukaka. Alhamdulillah! Ubangiji ya fito mana da Tijjani. Allah ya shirya miki zuria. Allah yasa albarka a cikin komai na ki. Yadda kike tsaye a kaina da iyalina Ubangiji ya tsaya miki ke da ahalin ki fiye da haka. Asiya ke kad'ai gayya ce a gidan Marina".
Na yi k'asa da kaina ina hawaye. Ina Jin rashin Tijjani ne cikas dina.

Amma babu abinda ban samu ba na rufin asiri a duniyar nan ba.
Kafin ka ce miye wannan sai na fara Tara kudade masu nauyi. Domin dai ban fasa yin lalle a gida ba. Duk wata albashi biyu nake ja. Ga wanda gwamnati zata ba ni. Ga wanda ake ba ni a envelope idan na je gidan gwamnati na yiwa Madam da iyalin ta kunshi da kitso.
Bana tab'a su tunda har yau Yaya Aliyu bai tab'a yin lako lako da abincinmu da kuma kula da yara ba. Iya na lalle dai da shi nake hidimar da nake yi. Domin so nake na yiwa Baban Marina ba zata ta ban mamaki.
A hankali alherin da ya same ni ya fara shiga kunnuwan mutanan gidan Marina.
Nan da nan aka fara cece kuce. Ko a biki aka taru saa'anninmu da na yi musu zarrra zasu yi ta sakin baki a gaban Nazira suna ce wa "Ai yanzu na zama y'ar siyasa ba kuma siyasar ce abin kaico ba. Manyan mata ne suke dauka ta muke sheke ayarmu. Ta ya ya za'a ce wai matar gwamna nake yiwa kunshi. Wace ce ni? A wanne karatun da bai fi cikin cokali ba. Tun Nazira na hak'uri, tana tankawa cikin dad'in rai tana fahimtar da su, har ta shiga yin tashin hankali da duk wanda zai soke ni. Hatta yaran dakin inna k'ananunmu ke nan da a yanzu suke y'anmata matukar suka ji wani ya soke ni sai dai aji na gwabza fad'a. Tunda ce wa suke hi karuwanci nake yi. Gabadaya y'an k'ofarmu ba yadda za'a yi a tab'asu su kyale a yanzu. Ganin hakan sai aka koma fad'in ni ce nake musu huduba tunda nima hakan na yi , sannan na mayar da dukkan ahalin Babanmu agwagi sai abin da na ce tunda na fisu kudi. Dan ma sunsan kudin nawa da ake famkama na kazanta ne. Sannan mugun k'ullin da yake raina ne ya sanya aka gane mijina dilar k'waya ne.
Dana zauna na nutsu sai na gane tabbas wata k'iyayyar bata da dalilin yin ta. Mafi yawa hassada ne da kyashi. Ba kuma zai yiwu kowa ya so ka ba. Babbar godiyar da nake tsananta yi ban tab'a zuwa gidan Marina na tsugunna a gaban wani na ce a taimake ni ba. Duk yadda aka yi mini aure dan a kassara ni, sai Ubangiji ya yi kishina. Wahala kam na sha ta, amma ba mai yawa ba ce. Sannan Ubangiji ya yi mini rufin asiri irin wanda ko y'aya' mazan gidanmu basu same shi ba.
Mafi girman Niimar da Ubangiji ya yi mini, itace ta lafiya da kuma sana'ar hannu, ya kuma ba ni haihuwa, ya sake ba ni mijin da yake tsananin sona. Bugu da kari ina cikin wadanda Ubangiji ya yi musu gata irin na gam da katar na girma da iyayena guda biyu. Wannan kad'ai babbar niimace a wajen bawa. Domin ko da ban san zafin rashin iyaye ba. Allah ya sani ina matukar tausayin wanda iyayen sa suka rasu domin al'amarin da suke fuskanta mai tsananin gaske ne. Ka ga masu iyaye suna samun TAGOMASHIN addu'a, suna samun tallafi, suna zuwa su yi hira da su, domin sun san zasu boye damuwarsu, sabanin wadanda basu dasu a raye sun dinga tiri tiri da matsalar da ta dame su saboda gudun za'a fantsama matsalarsu a duniya.
Da na tattara wadannan ni'imomin sai na ga ba zai yiwu kuma a ce kowa ya so ni ba. Ba zai yiwa kuma na ga yadda nake so ba. Tunda sunnar rayuwa ce kowa da irin k'alubalen da zai fuskanta a duniyarsa. Sai na gamsu kalubalena rufe Tijjani da aka yi. Ina rayuwa babu miji tsawon shekara guda. Sai kuma rashin soyayya daga dangi, da rashin hadin kai a tsakaninmu.
Na numfasa na ce Alhamdulillah. Ubangiji ka yi mini komai. Allah ka fito mini da Mijina. Ubangiji a sanya soyayya da tausayi a zukatan ahalin gidan Marina gabad'aya. Domin na riga da na gaji da gutsiri tsoma Wallahi.

A haka bikin su Ikilima ya matso. Ta ko ina ba ni da sukuni. Domin da na fad'awa mai dakin gwamna za'a yi auren kanwata. Tana bude baki sai ce wa ta yi mu je da Hajiya na zaba gado da kujeru da kayan dakin koami da koami zata yi.
Allah ya dora mata sona da tausayina, mussaman yadda na bata labarin tabbas Tijjani sharri aka yi masa ba halinsa ba ne. Ta yi mini alkawarin za'a fito da shi amma ba tashi guda ba. Na saurare ta.
Dan haka komai na garari aka siyawa Iklima. Har Toro kuma ta tura Hajiya ta kai kayan abinci gidanmu ta ce a yi hidimar biki.
Ganin yanayin gidan namu ya sanya Hajiya ta sake buda mini a dalilin ta yadda gidan yake na masu k'aramim k'arfi ne ainun.
Idan na zauna sai na yi ta ambton Ubangiji domin ya yi mini komai. Mafi Jin dad'i ta yadda ni ce sanadin hadin kan y'an k'ofarmu.
A haka aka yi bikin cikin rufin asiri. A cikin BAUCHI ya yi gidansa ba nisa da ganeral hospital din da yake aiki.
Ba'a jima ba aka kawo Baban 2 asibiti ba shi da lafiya. Kwanaki biyu na fahimci dan yana da hanya ne har aka fito da shi, ban da hakan ai za'a ba shi magani a sickbay din kurkun. Yaya Aliyu kuwa ya saka aka bashi daki a aminity. Yayin da Yaya Ammar ya yi kane kane shine jami'in da zai zauna da shi a madadin ma'aikatan gidan yarin. Dan haka da rana anan muke yini. Da yamma mu tafi da su Babah. Da daddare kuwa Yaya Aliyu zai zo da kansa ya dauke ni da abinci mu tafi. Ba zan dawo ba sai da safe. Tun ina jin kunyarta har na matse na cigaba da harkar gabana tunda bata taba ce mini komai ko bin ba'asin kwanan da nake yi a asibiti ba.
Ragowar saiwowin da aka yiwa Iklima da garin daka na yi ta sha. A gefe kuma Ina hadiyar zabbabun supplement na GHT da FASEELAT ta zaba mini su.
Muna kwance akan bargon da na shimfi'da akan tabarma tunda gadon ya yi mana kad'an.

Ya ce "Kina shan maganin kuwa?"
Na ce "Na kai wata ina sha, da yake an dora ni kan maganin da zai taimaka mini wajen conceiving. Ya saki ajiyar zuciya ya ce "Allah yasa satin da na yi addu'armu ta cika. Gobe zan koma kin sani. Wato albarkacin Ammar na yafe wa Baba Maryo! Asiya Ammar mutum ne. Kullum sai ya kai mini abinci. Wanccan satin na nuna masa ina son ya mini alfarmar ganin iyalina na kwana d'aya. Ina rufe baki ya ce "Na fara zazzabi, zai yi kokarin a kai ni asibitin waje daga nan sai ki zo."
Ki ga irin hadarin da ya runguma saboda ya faranta mini. Tunda idan aka gane shi za'a iya sallamarsa daga aikin ace ya ci Amanar aikinsa. Ki ga yadda ya bamu sati a maimakon kwana d'aya ko biyu."
Na numfasa na ce "Ni ma na yafe mata Allah ya shirye mu gabadaya."

Ya ce "Ameen! Allah yasa kin harbu little."
Na rufe fuskata a kirijinsa.
Ya dinga Shafa fatar jikina ya ce man nan na Oriflame ya karbe ki. Jikar Dada dai ta iya zabarwa mutum man da ya dace da shi."
Na murmusa cikin jin dadin yabawarsa na ce Aisha lame ai ta k'ware, wajen mayar da mace zama y'ar gayu ta gaske".
Ya ce "Na gasgata ki".
Washa gari kuwa aka sallame shi. Ina kallon yadda aka tafi da shi. Sai kawia kuka ya kwace mini a dalilin Babah tana gida saboda yara.
Aliyu ya dinga ba ni hakuri yana ce wa "To da ba ki samu damar ganinsa ba fa?
Sati guda fa ya zo ya yi miki haba dai Yabi. Ki yi hak'uri komai zai wuce.

***
*Watanni biyu*
Ana cikin haka kwatsam gwamnatin tarayya ta rage lakcarori cikin ikon Ubangiji har da Yaya Jabir aka sallama.
Gabadaya mun ji ba dad'i mussaman da yake ya tara iyali. Tunda amaryarsa ma yaranta biyu, Maijidda na da biyar domin haihuwa take akai akai tamkar da gayya.
Zaman Kaduna ya gagara tunda dama a quayers yake. Kan dole ya tattaro ya dawo Toro.
Na tausaya, na ji babu dad'i dole a aka hak'ura tare da fatan Allah ya kawo wata damar.
Baban Tsakiya ya dinga fad'in sa hannu ne. Kuma a cikin wadanda yake zargi har da Baban Kasuwa. Domin ya ce ai tunda Jabir ya kara aure yake ta tsiyace wa. Tabbas hannu aka saka masa. Yayin da Baban Kasuwa da ahalinsa suke murnanr hakan da ya samu Yaya J. Tunda sun tafi a cewar Jabir yana fifita amaryarsa akan Maijidda da take yar'uwasa kuma uwar y'aya'nsa. To yanzu sai ya yi rashin mutuncin su ga ni.
Daga Baban Tsakiya har Baban Kasuwa kowa so yake a ce Baban Marina a bayansa yake. Har yau din nan sun fishi kudi. Amma ya fisu gata da rufin asiri . Domin a yanzu yana fita wajen sana'arsa saboda sabo da kuma mike kafa. Amma duk watan duniya sai mun ajiye abincin da za'a ci a kofarsa da kudin cefane. Hatta sabulun wanki da na wanka da zai bawa iyalinsa mun dauke shi. Hadawa muke yi gwagwadon k'arfin mutum. Ni ce sha kundum.
Hakan da suke gani kuma sai kowa a cikinsu yake son ya shige masa, ya soki d'an-uwansa a gabansa. Shi kuwa baya biye wani a cikinsu suyi hirar wani. Amma ya karbe su da fuskar afuwa da sassauci yake mauaamala da su. Tunda ba abin da Ubangiji bai masa ba. Jahilci ne ka ce zaka rama sharri da sharri. Bakar Taada ce ka ce zaka maimaitawa wani irin kuskuren da aka yi maka. Mussaman akan zumunci, matukar ana son gyara, matukar ana son cigaba. To a bar BAK'AR TA'ADAR riko da kullaci. Afuwa da yafiya yana kawo soyayya da masalaha a tsakanin jini guda. Tashin tashina kuwa yana dawo da gaba da k'iyayyar juna. Allah ya yafe mu gabadaya.
Zaune nake kusa da Babah yayin da Anas yake kan kujera su Hanif suna ta dabdala a jikinsa. Babah ta kalle shi ta ce "Kai bana son iskanci ka ji. Da wasa kake ko kuwa da gaske kake wannan maganar?"
Da murmushi ya ce "Wallahi ta makance Babah!
Ga mamakinmu sai Babah ta fashe da kuka tana fad'in"Allah mun tuba. Allah ka yafe mana. Ni dai ka shaida na yafe mata.
Anas ina rokon arzikin ka, ka yafe mata. Addu'ar da ka yi mata cikin fishi ne Ubangiji ya karba. Ka yi hak'uri. Yau na sake gasgata A guji addu'ar wanda aka zalunta, mussaman idan ya yi ta cikin fishi da neman agajin Allah".
Nan da nan ya ce "Na yafe mata. Ko yanzu idonta ya bude zan yi murna, idan bai bude ba kuwa Allah yasa ya zame mata kaffara. Amma ai ko yanzu ta ga karshen sharri. Tsofe tsofe da ita ta yi mini bakin sharri irin wannn. Haba wannan duniyar cike take da rudani. Ace wai jinin ka bai k'i ka tozarta ka yi bak'in ciki ba?"
Ta share hawaye tana fad'in "Babu wanda zai mori zumunci sai wanda ya yi hak'uri ya hadiye komai, ya yi sassauci ya kuma yi afuwa. Zumunci da kansa ya roki Zati ya ce "Ubangiji ka jefa wanda ya yanke ni cikin wuta. Ubangiji ka tsananta wa wanda ya tsananta mini. Allah kuma take ya karbi addu'ar zumuncin. Shi yasa Annabi ya yi ta jan kunnenmu akan zumunci. Hatta makoci da aminin iyaye sai da Annabi ya yi ta jan kunnenmu a kansu bare kuma wadda nasabarku guda. Akwai bukatar mu ninka hak'uri da kawaici, hadi da yafiya idan kuwa ba hakan ba, gaisuwa ma sai ta gagara a tsakanin jini guda."
Ya saki ajiyar zuciya ya ce "Da dukkan zuciyata na yafe mata. Na yafe wa kowa. Allah ya cigaba da dafa mana."
Ta ce "Ameen na gode Anas. Na gode da ka yarda da maganata Ubangiji ya yi maka albarka".
*Ya ce "Ameem Hajiya Babah tamu".
**
Jumaa da yamma muka yi Toro. Muka tarar da baba Maryo a zaune a dakinta jikinta ras. Ido kuma gwaragwara amma bata ga ni. Fadi take yi "Na rantse bakin Anas ne ya kama ni. A yiwa ma'aiki a kira mini shi. Wallahi ya fini gaskiya. Hauwa ki yafe mini. Ki roka mini afuwa a wajen Yabi da Tijjani."
Ta kece da kuka. Na matsa kusa da ita na ce "Baba ki yi hakuri. Ban kullace ki ba. Na kuma yafe miki. Na Ari bakin Tijjani shi ma ya yafe miki. Allah ha baki lafiya."
Babah ma tana kuka ta rik'e hannunta ta ce "Sannu da ibada Maryo! Tuni na yafe miki babu komai a zuciyata game da sha'anin ki. Sai alheri. Allah ya yafe mu gabadaya ya kuma gajarta miki wahala. Sannan Anas ya yafe miki tuni, zan kuma k'ira miki shi ki ji da kunnen ki.
A take Babah ta kira Yaya Aliyu ta ce ya bar komai gobe ya zo ya dauke su zuwa asibiti a duba ta da kyau.
A Toro Babah ta barmu suka nufi asibitin Jos tare da Yaya Aliyu

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login