Showing 72001 words to 75000 words out of 184118 words
Chapter 25 - Bakar Taada Hausa Novel Complete
sai na kai ki?"
Ta yun'kura tana fa'din "Na gama, yinin ya isa, ba sai na kai almuru a waje ba."
Nima na bi bayan ta muka fito. Na kalle shi ya sanya jallabiya. Ko mai bai shafa ba, bare tuarare. Àllah ya sani ina son na dinga jin k'amshin na tashi a jikin mutum.
Na shiga daki, na d'auko ledar kayan da ya siyo. Na dauki dubu guda a cikin ku'din da na tara na lalle. Na saka mata a ciki. Na k'ulle. Na sake k'ara wata ledar.
Na tarar har sun kusa fita.
Na bu'de baki na ce "Dada mun yi sallama ne?"
Suka dakata na isa garesu. Na mika mata tare da ce wa "Ga shi Dadarmu na gode da ziyarar ki. Amma Wallahi bakin ki k'anin kafar ki akan sha'aninmu Dada. Idan kuwa kika fa'di wani abu, sai dai a neme ni a rasa."
Ta sassauta ta ce "Ayyah Asiya me na ga ni ma ban da alheri? Ai ko da na ce zan fa'di baku zauna lafiya ba. Dan ban fahimta ba ne. Yanzu da na fahimci shine da laifi, ai na fa'di gaskiya. Kawai da ke da shi ku yi kokarin d'abbaka sunna, kada auren naku ya b'aci ba'a ankara ba.
Kunya ta yi matu'kar kama ni. Na rasa yadda zan yi, sai kawai na juya da sauri na yi ciki na barsu.
Shi kuma ganin hakan ya sanya ya ce "Allah yasa dai ba sai yanzu kika yi mata wannan bitar ba Dada?
Domin a zaune zaki yi mata ba a kurarerren lokaci irin haka ba. Idan kuma zaki fasa tafiyar sai bayan Isha da na fi haka gode wa Dada".
Ta nuna shi da yatsa ta ce "Tabataccen marar ta ido. Oh ni Binta ina kallon shak'iyanci. Ai gara ma da Asiyan ce matar ka, ita ce maganin ka. Haba kana da fitina Wallahi".
Ya yi gum. Ta d'aga murya ta ce "Na tafi Yabi, na gode Allah ya yi albarka.
A ci gaba da hakuri."
Ina zaune ina kallonsu ta windo har suka fice.
Suna tafe a hankali yake jan mashin d'in gudun kada ta subuto tunda ba iya hawa ta yi ba.
A hankali take fa'din "Ashe haka zaka yi mana? Akan me zaka kawo wata har gidan auren ka?"
Ya ce ba ni na kawo ta ba. Wajenta take zuwa fa.
Kuma kunshi take yi, wai ni rage mata aiki nasa aka yi"
Ta hassala ta ce kaniyarka da rage mata aikin. To bata so. Kada ka kuma wannan d'anyen aikin."
Ya ce "To bazan sake ba, da gaske."
Suna isa ana kiran magariba. Dan haka da ya kafe mashin din a zaure bai shiga gidan ba, ya nufi masallaci.
Da nutsuwa ya isa kofar Baban Marina ya gaisa da su Gwaggo cikin kunya da girmama wa.
Kansa a k'asa ya ce "Gwaggo idan uniform din Asiya na nan wai a bata zata fara koyon dinki"
Da sauri ta shiga daki tana ce wa "Sabon yana nan. Tsohon dai Ikilima tana amfani da shi."
Jimawa ka'dan ta kawo masa a bak'ar leda.
Hannu biyu ya sanya yayin karba.
Ya yi godiya, ya yi musu sallama ya tafi.
A gurguje ya yiwa Dada sallama ya wuce gidansa. Yana Jin zumudi da d'okin zama kusa da Yabi.
Yana son yi mata ba zata. Yana son ya shawo kanta, ya d'ora mata girma ko zata rage tsiwa da zafin kai.
*MARUBUCIYA*
*BINTA UMAR ABBALE🍒*
*Tana farincikin sanar muku da sabon littafin ta mai suna YA ZA A YI? Wanda za ta sake shi ranar d'aya ga watan Oktoba (first October) wannan karon ma marubuciyar taku ta shirya sosai domin nishad'antar daku tare da fad'akarwa🥰 Ba sai na tsaya yi muku bayanin rubutunta ba domin da yawa daga cikin masu bibiyar litattafanta sun san cewa tana k'okari gurin ganin ta yi rubutu akan abubuwan da suke faruwa, mussaman a zamantakewar aure da tarbiyar yaranmu, Uwa uba kuma litattafanta akwai soyayya mai tsafta da nishadi da 'karuwa! Kada dai ku sake a baku labarin wannan littafin mai suna( YA ZA A YI)❓ Zaku iya yi mata magana ta Whatsapp da wannan numbers*
*08089965176*
*07084653262*
✍️.
*BAKAR TA'ADA*
*45&46*
*WANNAN LITTAFIN NA KUDI NE BIYA KUDIN KARATUN KI TA WANNAN ASUSUN DAN GUJE WA BAKAR TA'ADA!*
*REGULAR 500*
*VIP 1K*
*VIA*
*2384876855*
*SURAYYA IBRAHIM DAHIRU*
*ZENITH BANK*
*KO*
*7061488065*
*SURAYYA DAHIRU IBRAHIM*
*OPAY DIGITAL SERVICES.*
*TURA SHAIDAR BIYA TA WADANNAN LAMBABOBIN*
*08032773332*
*09069067488*.
*Tallah Tallah Tallah*
Shaharriryar marubuciyar nan wacce tanishaɗantar ku a littafin ta mai sunan
SAMHA```!
```Ta sake sabon shirin ta, wajan ƙara faranta maku rai' tazo maku da sabon book ɗin ta Wato KECE SANADIN [rayuwa]```
```Masoyana kufito ku nunamin ƙaunar da kuke cewa, kuna min```
```farashin KECE SANADIN ₦500 0nly```
```wacce bata shirya ba kada tamin magana```
```masu san fara pyarment da wuri gashi, 810353370 kimin screen shot ki turo ta wannan no 08138012334```
```masu kati kuturo ta wannan layin 08108353370```
*UMM NIHLA COLLECTIONS*
*Ta k'ware wajen kawo yadina masu kyau da sauki, cotton da silk, embroidered, Batik*
*A Malaysia take daga can kuma take turo su Kano direct. Dan haka kayanta akan farashi sari take bayarwa, daga guda daya har zuwa dari zaku samu*
*Kayan ta masu aminci da rahusa ne, ku tuntube ta Whatsapp dan ganin JERIN gwanon yadinanta da basa kode wa ko jeme wa*.
*07020695644*
*What's app only*.
45&46.
Ya shiga da kuzari. A falo ya tarar da ita tana kallon tashar Bollywood.
Yana wahalar gaske ya ga tana kallon tashoshinmu. Har gara tana kai wa Sunna TV sa'i zuwa sa'i.
Ya manta da uniform a cikin but din mashin din.
Ya zauna kusa da ita.
Ya sassauta ya ce "Asiya Toro babu magana, babu yi mini barka da zuwa?"
Na galla masa harara na ce "To ni ina ruwana da kai da zan yi maka magana? Ba gaba mu ke yi ba?"
Ya ce "mun shirya ai. Na baki hakuri, kakarmu ta baki, mene ne kuma ya yi saura?"
Na ja tsaki mai tsananin gaske na ce "Da wa din ka shirya? Ai ni duk mutumin da zai tozarta ni, ya kuma ta'ba lafiyata da sunan duka to babu ni, babu shi har gaban abada".
Na fa'da cikin matsanancin fishi.
Jikinsa ya fara mutuwa. Ya numfasa ya ce "Ashe duk maganganun Dada basu shige ki ba? Daga tafiyar ta Asiya zaki fara d'aga mini hankali, mene ne nak'asuna ne da kika washe ni har hakan?"
Yana rufe baki na ce"nak'asunka ai birjik ne. Mafi muni baka da kamun kai.".
Ya zuba mini ido ya ce "sai me kuma Asiya?"
Kai tsaye na ce "Baka burge ni ko kadan. Domin bana jin k'amshi a tare da kai. Baka iya kwalliya ba. Kullum kayan ka babu guga. Kalli faratan hannun ka.
Kullum na kalle ka ba'kin ciki ne yake kama ni maimakon farin-ciki."
Jikinsa ya yi sanyi kwarai da gaske. Idanuwansa suka canja launi sosai.
Murya a dashe ya ce "Sai me kuma?"
Na ce "Idan na tuna, na fa'da maka".
Ya numfasa ya ce "Duk zan gyara indai sune cikas dina a wajen ki. Idan na sauya din shi ke nan zaki daina tsananta mini?"
Na sake shan kunu ban tanka ba.
Ya ce "To nima ina da damar da zan fa'di abubuwan da kike yi mini da bana sonsu?".
Kamar bazan kula ba.
Sai kuma na ce "Baka da damar domin ni ba so nake sai na burge ka ba. Ba kuma so nake ka zauna da ni akan dole ba.
Ya saki ajiyar zuciya ya ce "Shike nan! Amma ina ro'kon ki kada ki sake shiga mini da mata dakina".
Na tunzura! Na tashi zaune sosai na galla masa harara na ce "Sannu mai d'aki. Komai dakinka, dakinka. To sai na shiga d'in.
Shima ya hassala ainun ya nuna ni da yatsa ya ce "Kada ki fasa Asiya. Ai tunda na gane ba kya son sulhu da sassauci, to mu zuba tsiyatakun mu ga wa zai janye wa wani".
Na ja tsaki na ce "Ai ka k'oshi shi yasa ka samu kuzarin yin musayar yawu da ni".
Ya juyo a tunzure, ni kuma na zabura na yi shirin kai masa naushi.
Dariya ta kama shi ya ce "Wai dambe zaki yi da ni? Ko da yake ai mai hali baya fasa wa."
Na ce "oho dai."
Ya fita ban sake jin sa ba, sai da asuba ya tashe ni.
Da safe ba yadda bai yi ba akan na tafasa masa wani abu, duk da ya shigo da burodi a safiyar, kawai bai dame shi ba ne. Na yi tsallen bad'ake na ce bansan zancen girki ba, gara mu cigaba da zaman doya da manja kawai.
Ya shiga ya tafasa farar taliya ya zuba yajin *Annur food* da manja. Ya ci ya fice bai bi ta kaina ba.
Sai da na gama komai sannan na d'ora shayi.
Na karya na yi wanka. Ina zaune babu wuta, kuma babu kowa.
Sai da azahar sai ga y'anmata uku sun zo k'unshi.
Muka shiga d'akin da ake ta mini kashedin kada na shiga na fara yi musu.
Na gama wa mutum d'aya sai ga Hajiya babbar mace sosai. Dan zata haife ni. Mun saba tuntuni, wani lokacin har gidanta ina zuwa na yi mata, sanadin haka suka saba da Gwaggona.
Na marabce ta da murna.
Na kammala saka musu. Na kammala yiwa Hajiya a hannu.
Sai ga shi ya dawo. Ban san me yasa ba, na ji faduwar gaba ainun. Wata'kila ko dan ya yi ta jaddada mini kada na shigar masa d'akin da nufin yin kunshi ne?
Ya lek'o ya tabbatar ban ji maganar sa ba.
Ya juya ko gaisuwarsu bai amsa ba.
Ya dauko bokiti ya janyo ruwa.
Hajiyar ta ce "tashi ki je ki masa sannu".
Na ce To" ba dan ina so ba, na yun'kura na fita. Na gan shi ya gama cika bokitin, ya dauko na tsaya ban ce masa kanzil ba.
Zuciyata ta tsinke a dalilin yanayinsa ya koma na Bulkachuwa na asali, ba na yanzu da ya koyi sassauci ba. Ya shige ni bai ko kalli inda nake ba. Ya kai ruwansa band'aki. Nima na koma na cigaba da lallena.
Mintina biyar sai ga shi ya shigo d'akin babu sallamah. Y'anmatan suka fara gyare gyaren jikinsu yayin da Hajiyar ta rasa yadda zata yi a dalilin duk na yiwa hannuwanta k'unshin.
Ba zato ya cire rigarsa ya mak'ale. Zuciyata ta tsinke. Wani irin abu ya tokare ni. Kafin na wartsake sai kawai ya zame dogon wandonsa, ya yi saura daga shi sai singileti da gajeran wando. Hankalina ya kai k'ololuwar tashi lokacin da ya cire singletin.
Ya dauki tawul din da yake rataye ya daura a kugunsa. Ban san me ya hana shi zame gajeran wando ba. Yasa kai ya fice zuwa band'aki.
Na yi kasa da kaina hawaye ya b'alle mini.
*KUN TUNA MAI GYARAN GUDUYO?*
*INA NUFIN FASEELAT BABBAR DILA TA G.H.T.*
*KO WANNE NAU'IN KAYAN GHT TANA SIYAR DA SU AKAN FARASHI MAI RANGWAME*
*KAWAI KU TUNTUBE TA A WANNAN LAMBAR DAN GANIN JERIN KAYAN DA TAKE DA SU*
*TUN DAGA KAN SUPPLEMENT, SABULAI DA LIPTON*.
*MASANIYA CE AKAN KAMFANIN DOMIN TA SAMU KARRAMA WA DAGA KAMFANIN A BANA, HANZARTA KI TUNTUBETA DAN SIYA DAI DAI KO SARI.*
*IDAN KUWA KINA SON YIN RIGISTA DAN FARA KASUWANCIN KAWAI KI TUNTUBE TA DAN KUWA DA KYAKKWAR ZUCIYA ZATA MU'AMALANCE KI*
*07039269802*
Gaba'daya y'anmatan suka bi shi da kallo. Wani irin mak'aki ya tokare ni. Na sani zai burgesu tunda Ubangiji ya masa kyakkawar sifa kwarai da gaske. Motsa jikinsa da yake yi, ya sanya jikinsa ya ginu sosai.
Wanne irin wula'kanci Tijjani ya yi mini yau? Na fa'da a zuciyata.
Matar ta ce "Cire mini lallen nan. Ai bansan maigidan baya so ba. Na tabbatar ba da izininsa kike wannan sana'ar ba. Shiyasa ya dauki wannan k'azamin matakin.
Innalillahi wa inna ilaihir rajiun. Yau na ga lukutar tsiya ni Hadiza."
Ta fa'da cikin kad'uwa.
Na fara kuka sosai, ina yi, ina cire mata. Ai kuwa ina gamawa ta ja ni jikinta ta mak'ure ta rufe ni da duka tana cewa "wanne irin shak'iyanci kike yi masa da ya janyo miki wannan d'anyen hukuncin. Shin baki da makusanta da suke fa'da miki gaskiya ne? Kowa ya kalle shi yasan yana tsananin son ki. Me kike yi masa?"
Dama so nake na yi kukan sosai, ko na samu sau'kin zugin da kirjina yake yi mini.
Dan hakan na bu'de baki na dinga canyara ihu. Ita kuwa sai dukana take tamkar ita din Gwaggo ce.
Sai kuma ya fito a bazame. Dan ya ga me ya sani irin wannan kukan. Ganina a hannun Hajiyar ta matse ni tana ta mintsini na ya sanya shi ce wa "Na ha'da ki da Allah ki bar ta haka nan Hajiya, k'yale ta"
Ai kuwa ta k'yale ni. Ya tsaya daga ba'kin k'ofar ya mika hannu ya d'auko jallabiyarsa da take rataye. Ya yi baya, ya sanya.
Ya dawo ba'kin kofar ya ce "Darajar wannan baiwar Allah kika ci, tana gidan. Na rantse miki da yau kin ga k'arshe taurin kai da tsiya."
Ya kalli Hajiya ya ce "Na gode sosai, amma dan Allah kada ki sake ta'ba ta. Ki yi ha'kuri".
Yasa kai ya bar gidan gaba'daya.
Y'anmatan nan suka kasa ce wa komai amma dai gaba'daya sun shiga rud'anin al'amarin da ya faru.
Ta tashi, ta fita tana fa'din "Zan je har gidanku na sanar wa Gwaggonki baki shirya zaman aure ba. Gara ta sani kada rana daya ta gan ki kamar jifa kin koma gabanta. Ke ko tunanin halin da take ciki ba kya yi? Tare da kanwar ki aka aurar da ku. Tana zaune k'alau, amma ke kin fitini kanki kin fitine shi."
Na dinga kuka ina bata hakuri akan kada ta fa'da wa Gwaggo fishi zata yi da ni.
Da k'yar ta yarda ba zata fa'da ba.
Bayan ta ce na kira mata shi a waya.
Akan dole na kira shi. Na danna speaker.
Yana dauka sai ce wa ya yi "Bebina kin daina kukan? Ki yi ha'kuri kin ji. Ai da nasan mutumiyar kirki ce irin haka da bazan yi hakan a gabanta ba".
Ba'kin cikinsa ya nemi kassara ni. Na mika mata wayar cikin b'acin rai.
Jin muryarta ya sanya ya shiga cikin nutsuwa sosai.
Bai bari ta ce komai ya fara bata ha'kurin abin da ya yi.
Ta ce "Tambayar ka zan yi. Baka son ta yi k'unshin ne?"
Da sauri ya ce "Ina so. Ai bazan hana ta sana'ar da ta kafu da ita ba. Amma dai dole ta bar abin da na ce mata. Na ce kada ta kuma yi mini lalle a d'akina, ta je ta yi a nata d'akin. Shine kawai rikicina da ita".
Ta ce "To shike nan. Magana ta k'are."
Ta kashe wayar ta murd'e mini kunne tare da ce wa "Dama can dakinsa ne, amma kike masa k'unshi a ciki?
Saboda ke tabbataciyar marar kunya ce?
Amma yanzu ai kin ga 'karshen tsageranci."
Ta saki kunnena ta tashi ta bud'e wadrof d'ina ta ga dukka kayana ne babu nasa ko daya. Ta sake kai kallo ga d'akin ta ga babu alamun hula ko wani abu na miji a ciki.
Ta daure fuska ta ce "kwanta na duba ki, wato har yanzu ke budurwa ce ko?"
Na rushe da kuka wiwi. Ina fa'din Dan Allah ki yi ha'kuri sanin da na yi ita din mai zafi ce. Sannan ba mai wargi ba ce, y'ay'anta ma shakkarta suke yi ainun.
Ta cije ta ce "Kin san Allah sai na ga ni. Ko kuma yanzu na saka Salisu ya dauko mini Gwaggonki tunda ni ba ni da mutunci a wajen ki."
Na sake tsananta kukana ina fa'din "Dan Allah Hajiya ki rufa mini asiri. Dama fushi suke yi da ni. Mussaman Babanmu, ki yi hakuri. Kuma ni akan wannan ba laifina ba ne. Na yarda na yi kuskure akan maganar d'akinsa, ba kuma zan sake maimaita wa ba.".
Ta saki ajiyar zuciya ta ce "Shikenan na hakura. Amma na baki daga nan zuwa kwanaki uku ki kwaso kayansa ki dawo masa da su nan.
Sannan ki kwantar da kai, ki roke shi ya baki iznin zama a d'akin tunda gidan naku babu bishiya ko rumfa.
Ba sai na fa'da miki muhimmanci sana'ar ki ba. Komin wadatar miji neman na kai da'di ne da shi. Zaka yi harkokinka kai-tsaye ba sai ka jira an yi maka ba. Bare ke da kika saba yiwa iyayenki hidima a cikin sana'arki".
Ina kuka na ce"To. Domin dai na gamsu da maganganunta.
Ta sake ce wa "Ki ajiye komai ki rungumi auren ki, kowa da kaddararsa Yabi. Ke taki ma da kyua. Tunda mijin na ki yana son ki da alama kuma yasan me yake yi tunda soyayyar bata rufe masa ido ya sarayar da yancinsa na miji ba. Ki shiga taitayinki. Wadanccan y'anmatan zarata kallon so da fatan ace nasu ne suke binsa da shi. Ki ribaci damarki. Ki rike darajarki tun baki tankwabar da ita ba. Idan a yanzu da yake neman zaman lafiya da ke, kika yarda kuka zauna, to har tsufanku ya dinga kaffa kaffa da ke. Ban ce ba zai bata miki ba, ban ce ba zai kuntata miki ba. Amma dai zaki samu sau'ki, zai kuma din ga shakkar ki botsare masa. Kada ki yarda ki koya masa jure wa fishin ki Yabi".
Cikin kuka na sake ce wa "To" Wanda ban san dalilin da ya sanya na kasa daina wa ba.
Ta nisa ta sake ce wa "Ban da ma ke din sakarya ce ai cikin hikima zaki gaje can din. Da kin nuna masa nan ne dakinsa ai shike nan. Yanzu kuwa can din da kika raina sai ki ga ya samu wacce zata yarda ta zauna a cikinsa. Sai dai ki ji an kawo masa amarya."
Ba k'aramin dukana wannan maganar ta yi ba. Na k'ara sautin kukan da nake yi. Ta ce "Sha sha a haka kamar wayayyiya amma bagidajiya ce. Baki iya komai ba sai kishi. To wai wannan kishin na mene ne tunda ba sonsa kike yi ba? Ya auro uku mana me zai dame ki? Na so bana gidan yau, ya tub'e ya zauna cikin mata na ga yadda zaki yi. Kin san kuma duk masu hankali baza su sake zuwa miki ba. Marasa tunani kuwa sun dinga zuwa, dan su k'ulla alaka da shi".
Bata bar gidan ba sai yamma lis, bayan y'an matan sun cire nasu sun tafi.
Sai bayan Isha ya dawo. Ya same ni a dakina ina kan abin sallah duk na takura tsabar takaicinsa da yake dafa ni.
Ya zauna a kasa kusa da ni. Ya ce "Barka da gida Asiya Toro".
Na kasa bu'de baki na ce masa uffan.
Domin yadda zuciyata take tafasa sai na ji tamkar na yi ta k'unduma masa ashariya.
Yasa dukkan hannunsa ya ru'ko ni yana fa'din "Ba kya gajiya da kuka ne Asiyata?"
Ai kuwa ba zato na fara