Showing 177001 words to 180000 words out of 184118 words
Chapter 60 - Bakar Taada Hausa Novel Complete
su ya rufe da ce wa kada su fad'awa kowa sai abu ya kankama. Domin tafiya gabar kiran Allah ne.
A gurgurje na je gidan Nazira na dubo yaronmu.
Da yamma muka juyo da Yaya Aliyu akan gobe Baban zai zo BAUCHI don ayi masa passport.
Ba a fito da maganar tafiyarmu ba sai da komai ya kammala ya rage saura kwanaki hudu.
Baban Marina da kansa ya fad'awa y'an uwansa cewar zasu tafi Saudiya. Da Yabi da diyarta da Dada Tijjani ya biya musu. Aliyu ya biyawa Hauwa. Shi kuwa Yabi ce ta biya masa. Suka ka'du k'warai. Amma da yake dangantarsu ta yi tsami ainun kowa ya hadiye a ransa tunda yanzu so suke ace kowa yafi kusa da Baban Marina a tsakaninsu. Sannan basu gamsu Yabi ce ta biya ba. Duk da dai sun yi matukar sikewa da lamarinta tun auren Iklima. Zuwan tawagar matar gwamna Toro gidan Marina ba k'aramin cece kuce da girmama lamarin Yabi ya janyo ba.
Ranar talata da asuba muka nufi Kano tunda an ce shabiyun rana zamu tashi.
Karfe tara a airport din ta yi mana. Aliyu bai tafi ba sai da ya ga tashinmu. Sannan ya juya da twins da Ikilima da suka yo mana rakiya. Hamim sai kukan sharbe yake yi. Hanif sai hak'uri yake ba shi yana ce wa "Mun girma fa Hamim. Ammi ba dadewa zasu yi ba. Ba ta ce addu'a zasu je su yiwa Baban 2 ba? Husna zata raina ka fa". Suka bawa Aliyu tausayi. Haka kawai yaran suke ba shi tausayi ainun.
Bai bar Kano ba sai da ya siya musu kayayyakin wasa da na ciye ciye dan su warware gabadaya.
Kai tsaye a Madina muka sauka. Mun gaji likis. Dole muka kwanta. Dada sai addu'a take yi tana fad'in "Allah k'amshi ya cika hancina, haske ya cika idona, k'arfi ya yiwa gangar jikina k'awanya, farinciki da imani sun cika zuciyata. Allah ka karawa Annabi daraja. Allah ka karbi addu'ar da zamu yi, ka bamu k'arfin da zamu yi ibada ta gaskiya."
Sai ta zauna. Sai ta zabura ta je jikin windo tana leken asumayar masallaci ma'aiki. Tana kuka tana fad'in "Rabbani yadda ka sake yi mini gatan ganin koriyar gubba ta d'an Amina mai wuyar ga ni. Allah kasa zan gan shi da idona. Allah ka bani ikon rokon gafararka idan na shiga rauda. Allah ka shirya mini zuria, ka jefa soyayyya a tsakanin ahalina. Allah na yi tuba. Allah mai babban suna aiko ni ya yi takanas, Ubangiji a karba a sassauta a kubuto da shi albarkacin masoyinka Baban Nana".
Duk juyin da zan yi zan ga idonta biyu. Babah kuwa barci ta yi sosai domin bata runtsa ba a jirgi, ita take ta fama da Husna.
Daf da asuba muka tashi, muka yi alwallah muka nufi masallaci. A harabar hotel din muka had'u da Baban Marina shima ya fito zai tafi. Na kalle shi cikin sabuwar jallabiyar da na siya masa guda uku a Kano. Ya yi fes da shi. Garin Madina rahama ne.
Gabadaya zukatanmu cike suke da shauki da rauni. Duk juyin da muka yi da Dada ta saka silifas din ta. Ce wa ta yi "Wane mutum ta taka k'asar Madina da takalmi? Mu dai da muka ga zamu taka ba zata ce komai ba. Allah ya yafe mu kawai"
Kan dole muka k'yale ta. Domin har muka yi kwanaki biyar a a Madina bata yarda ta saka ba. Duk ranar da aka yi ranar juma'a ma haka ta tako. Sai da muka shiga motar tafiya Makkah sannan ta saka takalmi, tana hawaye tana fad'in "Allah ina son na sake dawowa. Idna ban samu damar ba, na yi godiya. Allah karbi addu'ar da muka yi."
A Makkah kuwa har tausayi suke bani tunda muka je dukkanmu a masallaci muke kwana. Mu yi sallah, mu yi dawafi. Duk shekarun Dada bata zama. Ko dan yar firit ce irina? Ban sake gasgata komai na Dada na kwaso a halitta ba. Sai a tafiyar nan da muka yi. Kamar da muke yi ta baci. Na tsinci kaina da addu'ar kada Allah yasa na yi halinta idan shekarun girma suka cimma ni. Tunda ta sha fad'ar hatta fad'an da na yi ina karama itama haka ta yi a lokacin kuruciyarta.
Baban Marina kullum sai ya ce "Dada yau ki kwanta ki huta, Hauwa ke ma ki huta, Ubangiji ya ji addu'ar mu da ikon Allah Tijjani zai fito. Idan kuwa har muka ga bai fito ba, to tabbas zamansa a can yafi alheri. Ku duba shekarun da Annabin Allah Yusuf. Da'n Annabin Allah Yakub, d'an Annabin Allah Ishaq, d'an Annabin Allah Ibrahim A.s. ya yi a kurkuku. An tambayi Annabin Rahma wanne mutum ne yafi kololuwar daraja da nasaba, sai ya ce D'an uwana Yusuf A.s. Amma ya yi shekaru masu nauyi a sijin. Hakan bai zame masa tawaya ba, sai ma k'ara masa kusanci da Ubangiji ya yi. Bayan ya fito kuma Ubangiji ya karrama shi daga bawa ya koma shugaban kasa, kuma babban d'an majalisar sarki."
Dada tana kuka ta ce "Hakane Alhaji amma tunda zan iya bari kawai na yi ibada tuk'uru. Na nemi gafarar Allah, na nemi soyayya da tausayi da afuwa ta wanzu a gidan Marina. Bar ni na yiwa Shehu addu'ar ya fito ya cigaba da walwala cikin iyalinsa. Yabi kad'ai idan na kalla sai na ji kuka, bare y'aya'nsa. Ni dai na yafe maka Alhaji. Kaima ka yafe mini". Sai ta kece da kuka. Ya rik'e ta a jikinsa ya ce "Sha'anin uwa ai mai girma ne Dada. Hakkin haihuwa kad'ai ya isa ayi mata biyayya, a girmama sha'anin ta. A kuma dauwama ana rokar mata alherin duniya da na kiyama. Ban kullaci kowa ba bare ke da aljannata take damafare da sawunki."
Cikin kuka ta ce "Albarkar d'aki ka rabauta duniya da lahira Alhaji".
**
Kwanakinmu goma a Saudiya. Saura kwanaki biyar mu koma gida. Addu'a kam mun yi ta sai fatan alheri ya biyo baya.
Imani ya sake cika mini zuciyata. Na ji sassauci mai yawa akan kullatar da na yiwa mutanan da suke gwada mana rashin kirki. Sai na fahimci afuwa da yafiya suna warkar da zuciya, suna sake girmama mutum a wajen jama'a da wajen Ubangiji.
Kwatsam na kunna wayata sai ganin status din danginmu nake babu kakkautawa dauke da hotunan Baban 2 babu kakkautawa
Jikina ya sab'e da rawa na kasa gane me suke rubutawa domin gabad'aya na rikice!
*Akwai kaya masu kyau a cikin farashi mai sauki*
*Saiwowin maganin sanyi*
*Saiwowin Tsumi*
*Saiwowin dahuwar kaza*
*Saiwowin dahuwar tattabaru*
*Gumba*
*Tsumin kwakwa*
*Y'aya'n gadali*
*Hadadden daka*.
*Tsugunno mai sa a matse*
*Goran tula*
*Goran tula syrup*
*Garin goran tula*.
*Maganin gyaran nono*.
*Zuma ta mussaman*.
*Tsumi*.
*Da sauran kayayyaki na mussaman da basu da illah*.
* Domin kuwa asalin Saiwowin ne da ake kawo su daga Chad*.
*Abu mai kyau shi ke siyar da kansa ku tuntube ni dan samun naku kayan cikin sauki da mututantawa. Ina aikawa ko ina a fad'in tarairaiyar Nijeriya*
*08032773332*
*Y'ar uwa, ya mukaji da bubukuwa?* *Daga nan fa har january kusan ko wanne sati akwai biki, in ba na kusa ba akwai na nesa, ban da tunanin gudunmuwa da ma kudin man da zakaje bikin ga tunanin abunda zaka saka.*
*Balle ace maaikaciya ce ko CEO ce kina business din ki, kinsan all eyes on you🧐, ke ba sayen atamfa ba komi tsadanta anyo copynta, shima lace haka, cabdi! To albishirinki yar uwa!*
*UMM NIHLA malaysianfabrics ta dauke miki damuwa, tana da fabrics kala kala masu sauki da inganci kuma babu inda zaki samesu in ba wurinta ba, kije taro ki haska kowa sai ya tambaye ki me kika saka ina kika samu💃 maza garzaya gurinta kusa labule.* https://wa.me/message/F3EWRSHQPQAAH1
*Kawata Janafty zata yi muku reposting din littafin Zaman Gidanmu*.
*Kada a manta da littafan marubutan Dab'i*
*Hajiya SALIHA ABUBAKAR ZARIA*
*Hajiya Hafsat C SODANGI*
*Hajiya Maryam Kabir Mashi*
*Hajiya HANNE ADO ABDULLAHI*
*INA KAWO MAGANIN GYARA MASU KYAU DAGA CHAD DA SUDAN*
*MAGANIN SANYI SADIDAN*
*INA AIKAWA KO INA A K'ASAR NAN*
*BA ZAI YIWU NA TALLATA MUKU ABIN DA BA SHI DA KYAU KO INGANCI BA. DOMIN SOYAYYA DA AMINCI NE A TSAKANINA DA KU MASOYA RUBUTUNA*
*KU JARRABA SAIWOWIN DAHUWAR KAZA DA TATTABARU KU GA NI*
*KAZALIKA MAGANIN SANYI DA TSUMIN GORAN TULA BABU NA BIYUNSU*
*GA Y'AYA'N GADALI DA YAKE SHA YANZU MAGANI YANZU*
*ASALIN DAKA NA EMERGENCY*
*DA GUMBA DA KUMA TSUMIN KWAKWA DA ZUMA NA SHARHOLIYA*
*TUNTUBE NI KAWAI TA WHAT'S APP.DAN SAMUN BAYANI NA SOSAI*
*KU GYARA KANKU, KU GYARA Y'AYA'LNKU*
*MASU SHIRIN AURAR DA YARANSU KO KANNENSU A ZO A SAMA MASU KAYA MASU NAGARTA*
*08032773332*
*NA GODE*
*Alhamdulillah! Alhamdulillah!*
*Nasararorin da na samu a wannan labarin tabbas daga Allah ne*
*Na gode masa da ya bani lafiya da azanci*.
*Na gode masa da ya bani ikon sauke nauyinku, na gode da ban ja muku rai ba*.
*Idan rayuwa da lafiya sun cigaba da wanzuwa mini zamu sake haduwa a wani sabon littafina*.
*Idan kuwa ba'a samu damar hakan ba, to na gode muku gabad'aya da soyayyarku ga rubutuna*
*Allah ya shiryemu ya shirya zuria.*
*Wallahi ina matukar alfahari da duk wacce ta saka kudinta ta siyi wannan labari*.
*Ubangiji ya fini yabawa, ya rufa muku asiri duniya da lahira*.
*Lokaci ba zai bani na kama sunan kowa ba*.
*Domin shafin ya yi kad'an na zayyano sunayen mutanen da suka yi mini karamci ta sanadin rubutu*.
*Labarin Bakar Taada ya janyo mini mutanen da basu san komai ba sai alheri*.
*Mahaifina a lokacin da yake raye yana yawan ce mini ke y'ar gata ce Surayya*
*Na gasgata shi, domin kullum Ubangiji cikin kewaye ni yake da rufin asiri mai yawa, yana ta had'a ni da mutanan arziki da suke ta mayar da ni gayya a cikin jama'a*
*Na gode sosai Allah ya kewaye y'aya'nku da rufin asiri mai yawa*.
*Zan yi KEWARKU Wallahi!*.
Na nutsu na lalubo na Aliyu sai na ga hoton Bulkachuwa sannan ya rubuta Barka da samun yanci Yaya. Allah yasa wannan al'amarin ya zame maka tsanin shahararka a duniya."
Na bude murya sosai na ce "jama'a Tijjani ya fito, an sake shi. Gabadaya na rikice, na rikita su. Da k'yar na nutsu na musu bayani. Dada aka fad'i aka yi sujjuda. Ni da Baba muka yi maza muka but bayanta muma muka yagi sukjadar. Ta zabura ta ce "Haramin zan koma. Duk da dare ne bamu hanata ba, muma muka bi bayan ta. Bayan mun je dakin Baba baya nan tabbacin yana masallaci a can zai kwana.
Duk son mun gan shi bamu samu zarafin hakan ba. Sai da gari ya waye muka dawo masauki. Ai kuwa gabadaya muka kutsa dakin da yake ciki. Muka hau rigen yi masa albishir. Muna tare a dakin Aliyu ya kira ni vedio call. Aka gaisa aka yi murna, ya nuno mana fuskar Tijjani da ya kare da hannu. Da k'yar ya ce "Ina gaishe ku gabadaya. Na gode sosai. A kuma sake yiwa Ubangiji godiya.
Duk yadda nake jin dad'i a Makkah amma sai na ji kwnanaki hudun da suka rage gabad'aya sun mini tsauri. Ji nake tamkar na bude ido na gan ni a BAUCHI.
**
*Yadda al'amarin ya kasance*
Rundunar ta gurfanar da Alhaji Auta a gaban kotu domin da kansa ya kai karar kansa ofishin y'an sanda ya tabbatar musu laifinsa akan abin da ya yiwa Tijjani. Cikin kuka ya ce "Na aikata BAK'AR TA'ADA, na bari sharrin zuciya da shaidan sun janyo mini wahala. Tunda aka rufe yaron nan. Al'amarina ya sake kacame mini, kullum masifu sake yi mini k'awanya suke yi. Dan haka na zabi na kubuta daga azabar lahira. Tiryan tiryan ya yiwa y'an sanda bayani yadda ya shirya komai.
Take aka k'ira yan jaridu na radio da talabijin ya maimata a gabansu.
Nan da nan abu ya watsu a
BAUCHI da kewaye ko ina maganar ake yi. Sai Allah wadai ake yi da halin Alh Auta. Wasu kuwa su ce ya yi sa'a ma da ya zabi ya fadi gaskiya ya samu sassaucin kwanciyar kabari. Wasu kuwa su ce Yasin aka yi ta buga masa da alkunut shiyasa ya kasa gaba ya kasa baya har sai da ya fito ya lashe amansa.
Mai dakin gwamna na zaune a katafaren falonta tare da mai girma gwamana suna kallon N.T.A BAUCHI. Suna kallon yadda kae nuna Alh Auta kai tsaye (live) yana bayanin tuggun da ya had'a. Take ta tuna labarin da Yabi mai lalle ta yi mata. Nan da nan ta ce "Yallabai ka yi magana a gaggauta sako yaron d aka yiwa kaAmzfin nan babu dogon turanci. Ina sake rokon gwamyta bashi Wani abu na diyya bisa samaye shi da aka yi babu laifinsa. Sannan a gaggauta gurfanar da wannan tsohon banzan a gaban kuliya. Idan ka gaggauta sakinsa tare da yi masa wani alheri jama'a zasu sake son ka su tabbatar adali ne. Tunda a yanzu babu abin da zai dauki hankalin al'ummar BAUCHI irin wannan al'amarin ".
Take kuwa ya dauki waya ya yi magana da mahukunta. Kasa da awa daya aka.gata ganin Tijjani a talabijin, tare da jajanta masa. Gwamnati kuma ya bashi kyautar milyan ashirin bisa bata masa lokaci da suna da aka yi. Bayan haka take gwamna ya bashi S.A. wato mai bashi shawara akan gidajen gyaran hali.
Ba a jima ba sai ga hukumar kare hakkin dan Adam sun dauke shi aiki. Haka ta costom da kuma hukumar kula da kiyaye safarar k'waya da tu'ammali da ita. N.D.LA.
Cikin yini daya tak sai da aka yiwa Tijjani aiki tayin aiki a ma'aikatu biyar.
*KAWATA JANAFTY ZATA SAKE REPOSTING DIN ZAMAN GIDANMU, za Kuma ta kai shi AREWA*.
Ganin hakan gwamna ya sake ce wa ya bashi aiki a a ma'aikaar aikin Hajj. Da albashi mai tsoka. Wajen da aka bawa Tijjani duk shekara sai ya samu gurbin kujerar aikin hajji d'aya ko biyu. Ga shi babban mai bawa gwamna shawara.
Ga milyoyin kudi. An sha wahala, an yi bak'in ciki, amma a karshe sai alheri da daukaka ya biyo ba.
Yanzu da aka gurfanar da Alhaji Auta a gaban shari'a sai aka yanke masa kwantankwacin shekarun da Tijjani zai yi. Bisa kama shi da zambo cikin aminci, da kuma yiwa k'asa da jihar BAUCHI zagon kasa. Ga mamakin alkali sai Tijjani ya mike ya ce "Ni dai laifin ya yi mini na yafe masa. Allah shine shaida na yafe masa, ubana ne, sharrin zuciya ne d azal ya hau kansa. Tare suka yi gwagwarmaya da mahaifunay. A saddna naje gabansa da nufin ya taimake ni ya bani sana'a bai ki, ba asalima ya daukake ni a cikin yaransa. Maganar filina d aka karaba ba nasa ba , shaidan ne ya shafi kirijinsa. Da yawa mutane basa iya tsallake tarkon kyashi da hassada. Dan haka na yafe masa. Allah ne shaidar hakan".
Mafi yawan mutanan sai da suka yi kuka. Suna ayyana da ace mutane irin su Tijjani ne suka fi yawa a duniyar da ba a shiga tsananin da ake ciki ba. Abin da ya yi ya sake zaburar da jama'a girman afuwa da sassauci. Take kotu ta zabtare shekaru biyar a cikin bakwai aka mayar masa shekaru biyu, wanda wannan hakkin cin amanar gwamnati ne bata yafe ba. Sannan ya zama gargadi ga masu son k'ulla sharri haka siddan.
Gabadaya kafafen sadarwa labarin da ake tattunawa akai.
Cikin rakiyar jami'an tsaro aka ki shi gidansa.
Aliyu ne da su Yaya Salisu da Yaya Ammar suka tarbe shi. A ransa kuwa so ya yi ace ya tarar da Babah da Yabi da kuma Dada. Ya tabbatar ukun nan suna gaba da komai a rayuwarsa. Domin ya sani Dada ta so shi hakikanin soyayya.
A daddafe kwanakin suka cika muka tattaro muka dawo cikin tsananin farinciki da murna.
Aliyu bai samu sukunin zuwa daukarmu ba. Muna dira ya kira Baban Marina tamkar mai auna lokaci. Ya ce mu dauko shatar mota ta kawomu. Da yake karfe takwas muka sauka a Kano na safiya. Hakan kuwa muka yi. Ban tab'a ganin nisan tazarar Kano zuwa BAUCHI na sai yaiy. Jin na yi gabad'aya na kosa.
Haka muka isa Lafiya muka tarar da gida cike da mutanan Toro da na Bulkachuwa. Ana murna tare da dawowa lafiya. Na kalle shi yana kan kujera ya yi wanka yana sanye da k'ananun kayansa. Ya rame kam. Amma ya yi kyau. Ya yi aski saisaye. Ya yi fes, twins suna gefen hagu da damansa ma'ana sum sanya shi a tsakiya. Sai satar kallon juna muke muna murmusshi. Gabadaya mutanan da suka cika gidan sun gundure ni. So nake kawai su kauce su bamu waje.
Sai la'asar suka dunguma suka tafi Toro tare da Dada da Baban Marina.
Yayin da Aliyu ya tafi da Baba da twins gidansa. Kafin ta koma Bulkachuwa tunda Tijjani ya fito.
Bamu samu sararin marabtar juna ba sai da ya dawo daga sallar Isha, ya rufe gidan. Ko da mutanan Toro suka tafi, jama'ar unguwar sai shige dagice suke mana da sunan murna da kuma yi mini sannu da dawowa.
Da kansa ya yiwa Husna wanka yana ta tsala kukan kiwa. Daga karshe sai na fahimci da ruwan zafi sosao ya yi mata. Dan haka kukan har da dalili. Ya shafe ya da mantaleta, ya Sha nono. Ba'a jima da yin wankan ba kuwa barci ya sure ta irin mai nauyin nan.
Daga haka ya tisa ni a gaba da rawar jiki. Bamu iya ce wa komai ba illa barin da jikinmu yake yi. A matukar matse muke da juna. Abubuwan da suka biyo baya masu nauyi ne.
Sai dai bai yarda min yi barci ba, wanka muka yi muka dinga sallar godiya. Dukkanmu kuka muke yi. Domin al'amuran da muka tsallake taimakonsa ne kawai. Ba dan ikon Allah ba da tuni aurenmu ya dad'e da daidaicewa. Muna cikin bala'in asiri sai kuma k'azafi da hassada ya sake gigitamu. Amma cikin hucewar Ubangiji komai ya wuce.
Da asuba ma da ya dawo rufe gidan ya sake yi. Dai-dai loakcin Husna ta farka. Na canja mata pampers da ta cika shi da fitsari. Na d'ora ta kan fo. Na gyata ta sha nono sai ta sake komawa barcinta. Na kwantar da ita a gadonta tunda Hajiya mai magana da yawun first lady har gado ta kawo mata na garari lokacin haihuwar ta. Na lallaba na shige jikin Tijjani domin barci da gajiya ne a jikina ainun. Tara muka tashi shima kukan Husna ya tayar da mu.
Ya bude ido ya ga na yi mata wanka na ina shirya ta.
*Ba da jimawa ba zan kai Sabo da kaza da Kuma Halin Yau