Showing 135001 words to 138000 words out of 184118 words

Chapter 46 - Bakar Taada Hausa Novel Complete

fishi na yi ba. Tunda laifin kaina zai juye to kawai ki bisu. Duk tsamin ran da nake taya ki, baki yaba ba, bare ki bani hadin kai mu yi maganinsa da kyau".
Murya na rawa na ce "To ai da sai ki karbi yaran Babah".
Ta bude murya ta ce "Na ki karbar tasu. Ina ce ke kika barsu a gidansu? Kuma ba a hannun ubansu suke ba tabbatacciyar marar ta ido!"
Na yi shiru amma dai fuskata a daure.
Kafin ta yi magana sai kukan Hamim muka jiyo tabbacin sun dawo. Kafin Baba ta fita har sun shigo falo.
Da azama ta fita tana mini kashedin kada na fito da hannu.
**
Turus ta yi ganin Hamim na rike da riga da hijabin Yabi a hannunsa, ya kuma sassauta kukan da yake yi. Sai ajiyar zuciya yake faman saki.
Kafin ta ce komai Hanif ya ruga ya dauko takalman Yabi da suke gefen falon. Shi ma ya rik'e.
Tijjani ya samu nutsuwa domin ya tabbatar tana gidan.
Yayin da Babah ta kasa ce wa komai.
Cikin nutsuwa Tijjani ya ce "Ashe ba shaid'anu ya ke nuna mana ba. Kayan ta ya ga ni. Har mun fita ya tsananta kuka, ya kuma k'i yarda ya shiga motar. Sai hannuna yake ja. Na yarda na biyo shi muka dawo, sai kawai ya kai ni baya wajen kayan. Anan na fahimci kayan Yabi ya ga ni. Dan Allah Babah ki yi hakuri, ki ji tausayinsu ki basu uwarsu."
Ta yi kicin kicin ta ce "Idan ka ganta ba sai ka daukar musu ita ba. Ai tunda har zaka wulakanta Yabi irin haka, tabbas nima zaka wulakanta ni. Dan haka ba zan zuba ido ka fara mata cin kashi bayan ta gama shanye wahalar ka ba".
Ta rik'e hannun yaran ta tura su cikin dakin. Domin sun bata tausayin yadda suka rik'e kayanta gamgam. Kayan da shafa'a ne ya sanya aka barsu har yaran suka ankarar da ubansu.

Suna shiga ta janyo k'ofar ta zauna akan kujera, ta tsare gida ainun.
Ya rasa ta yadda zai fara yi mata magana.
Tsawon lokaci kafin ya tausasa harshe. Ya ce "Ina sake baki hakuri. Tunda wannan ne karon farko da ta kawo miki karata a zamanmu da ita. To ki yi mini uzziri a wannan karon . Ni kuma na miki alkawarin ba zata sake kawo miki karata akan wannan matsalar ba. Ki yi hakuri dan Allah".
Jikinta ya yi sanyi. Mussaman da ta zuba masa ido ta ga ya fada ya kuma birkice gabadaya.
Ya dinga magiya. Da ban baki tamkar zai rushe da kuka tsabar tsananta rokon da ya yi.
Rauni irin ma uwa ya shige ta. Ta furzar da iskar takaici. Ta ce "Ba dan ta yi hankalin tahowa nan ba. Da an yi ta yamididi da murnar ka yi kudi ka fara wulakanta ta. Da wanne idon zamu Kalli iyayenta da suka yi alkunya da kawaicin baka auren ta? Ta dinga yi masa fada da togaciya tamkar zata bige shi. Yayin da shi kuma yake fad'in "Ki yi hakuri zan Kiya ye da ikon Allah".
Ta tashi ta nufi daki. Ya yi maza ya mik'e ya bi bayan ta a d'arare tare da fargabar kada ta dakatar da shi.
Tana tsakiyar gadon. Yayin da Hamim yake kwance kan cinyarta. Hanif kuwa sarkin hakuri filo kawai ya yi da cinyar jikinsa na kan gadon. Daga ita har yaran kowa ya yi shiru tabbacin suna cikin alhini.
Baba ta sassauta murya ta ce "Yabi ga shi nan ku sasanta. Idan kin ga zaki yi hakuri ki bisu to, idan kuwa kin ga ba zaki bisu ba. Ba zan matsa miki ba. Ban san me kike hadiye wa ba".
Ya rasa inda zai tsoma ransa. Murya babu amo ya ce "Amma na baki hakuri fa".
"Dan ka bani hakuri sai na tirsasa ta?"
Ta jijjiga kai tabbacin ba zata mini dole ba.
Ya sassauta murya ya kalle ni ya ce "Asiya ki yi hakuri da abin ya faru. Na yi kuskure duk da dai fahimta ta ne baki yi ba".
Yana rufe baki na ce "Ba zan fahimta ba."
Babah ta yi shiru tana kallonmu. Watak'ila kuma mamakina ta yi na yadda na kame kamar ban gan shi ba tamkar ba yanzu na gama yin tijarar na huce ba ".
Ya munfasa ya ce "shi kenan ki yi hakuri." Ya furta a hankali.
Babah ta zame ta fice.
Yana ganin hakan ya matso kusa da ni ya zauna. Ya rage murya ainun ya ce "Saboda Allah little ya kamata ki bar dakin ki babu iznina?"
Na galla masa harara na dauke kai ban ce komai ba.
Ya sake tausasa harshe ya ce "Tashi mu tafi, idan mun je gida sai ki yi mini ko wanne irin darun ni kuma zan yi ta rarrashin ki, da kalolin soyayya masu tsayawa a rai."
Na ja tsaki tare da fad'in "Na bi soyayya da gudu. Ni yanzu bana son ka, kai ko ganin ka bana kaunar na bude ido na yi".
Ya saki ajiyar zuciya ya ce "Tom shi kenan, ki dawo dakinki dan yaran ki, ko ban ci arzikin komai ba ki dawo dan y'aya'n ki".
Na dauke kai na ce "Idan na mutu zasu fasa rayuwa ne?".
Ya rik'e kafata da tafi kusa da shi. Na goce da sauri. A tunzure na ce "Kada ka kuma tab'a ni. Ka je ka cigaba da damukar wadanda suke da daraja a wajen ka".
A zafafe ya ce "Na cigaba Asiya?".
Na dauke kai na ce "Eh".
Murya na rawa ya ce "Kin ga na damuk'e ta ne? Me yasa kike son jifa na da wannan mummunar maganar ne?"
Ba ja in ja na kalle shi na ce "Saboda ina da hujjoji na gaskiya. Sannan idan ba hakan ba, me yasa zaka kawo mini wannan suntumemiyar cikin gida? Har kuma kana kumfar bakin ba zaka ce ta tafi ba, saboda ta yi maka alkhairai. Fada mini alherorin da ta yi maka dan kuwa ban sansu ba".
Ya kafe ni da ido. Cikin matsanancin bacin rai ya ce "saboda kin fahimce ni a baibai shi yasa kika taho babu izinina, sannan kike kallon idona kike jifana da alamarin da kika san na tsani a jingina mini. Me yasa kike son ki dinga tayar mini da hankali ne Asiya?"
A tunzure na ce "Saboda ba ni da alheri a wajen ka sai sharri. Yanzu ba sai ka sakawa Nasiba da kalar naka alherin ba. Ni kuma ka bini da irin nawa sharrin ba".

*Akwai kaya masu kyau a cikin farashi mai sauki*
*Saiwowin maganin sanyi*
*Saiwowin Tsumi*
*Saiwowin dahuwar kaza*
*Saiwowin dahuwar tattabaru*
*Gumba*
*Tsumin kwakwa*
*Y'aya'n gadali*
*Hadadden daka*.
*Tsugunno mai sa a matse*
*Goran tula*
*Goran tula syrup*
*Garin goran tula*.
*Maganin gyaran nono*.
*Zuma ta mussaman*.
*Tsumi*.
*Da sauran kayayyaki na mussaman da basu da illah*.
* Domin kuwa asalin Saiwowin ne da ake kawo su daga Chad*.
*Abu mai kyau shi ke siyar da kansa ku tuntube ni dan samun naku kayan cikin sauki da mututantawa. Ina aikawa ko ina a fad'in tarairaiyar Nijeriya*
*08032773332*

Ya jima bai iya ce wa komai ba. Da alamu kokawa yake da zuciyarsa. Domin fishin da ya ke shimfide a fuskarsa ya kai intaha.
Tsawon lokaci mun yi shiru. Yaran kuwa duk sun yi barci.
Ya munfasa ya ce "Ki yi hakuri. Na baki hakuri. Tashi mu tafi, na yafe miki".
Na sake hade rai na ce "Ba na son ka yafe mini, domin ban maka komai ba. Ban zalunce ka ba. Kai ne ka ke shirin zalunta ta. Shi yasa na saukaka maka hanyar rabuwa da ni. Kawai ka sallame ni, ba zan iya zaman zullimi da fargaba ba. Tunda ka fara samun kudi ka ke canjawa. Nan gaba bansan yadda zamu kwashe ba. Gara tun wuri na barka tun baka gama barina ba ".
Murya babu amo ya ce "me nake yi miki Asiya?"
Baka yi mini komai. Son ka ne ba na yi! Ko dole ne?"
Ya mik'e tsaye ya ce "Babu dole, to ba ni yarana".
Na rungume Hamim da yake ta barci yana sakin ajiyar zuciya. Na ce "Ba zan bayar ba, dauki Hanif shi kenan an raba."
Nan da nan ya hau rantsuwar ba zai bar shi ba. Ba zai raba su ba. Na dage tamkar har cikin zuciyata da gaske nake yi. Sosai muke yin takaddama.
Sai da na gama famfa shi. Ya sakankan ce bazan iya yarda ya tafi da su ba.
Sai kawai na ce "Dauke su ku tafi, Allah ya shiga al-amarinsu."
Nan da nan ya yi turus. Jikinsa ya yi sanyi ainun. Ya zuba mini ido tsawon lokaci, ni kuma na yi kamar ban ga ni ba.
Ya koma ya zauna a maimakon mikewar da ya yi, yana kumfar bakin sai na ba shi y'aya'nsa.
Ya sassauta murya ya ce "Na baki hak'uri fa little. Ki mini uzziri mana".
Murya na rawa na ce "Sau nawa ka ke yi mini laifi ina share wa?"
Da sauri ya ce "Da yawa. Ina kuma gode miki. Na kuma dha fad'a miki kina da alfarmomi masu yawa a waje na. Yanzu ki mini hakuri dan Allah. Bazan sake yin hakan ba."
Na hirgiza kai tabbacin ban karbi ban bakinsa ba.
Ya marairaice ya ce "Haba mana my little angel. Ki huce, kin san fishin ki kassara ni yake yi".
Sai lokacin na ji kuka ya zo mini. Na dinga yinsa bilhakki. Tsawon lokaci sannan na daina. Ya saki gauron numfashi ya ce "very sorry little. Nasan kin huce, tashi mu tafi dan Allah".
Na girgiza kai na ce "Ni kam bazan koma ba fa. Ai tunda har waya ka ke yi da ita, nasan akwai abin da zai biyo baya. Dan haka ka je na bar mata kawai."
Ya diririce ainun. Ya fara musun basa waya.
Na zuba masa ido na ce "Waye ya ce mini Nasiba ta ce da Dada za'a zo ganin gida?"
Ya ce "Ni ne".
"Me yasa ni bata fada mini a wayar ba? Me yasa kullum sai ta kira ka? Me yasa sai kai Tijjani? Tunda bata kirana, bata kiran Yaya Salisu da ragowar. Na tsani rashin kame wa".
Ya kasa magana tsawon lokaci. A sanyaye ya ce "Ba ni da bakin magana , am speechless. Abin da zan iya ce wa biyu ne. Ki mini uzziri, ki yi hakuri."
Na yi shiru. Cikin rarrashin ya ce "Wallahi duk hasashen da kuke yi ni ban tab'a d'arsa shi a raina ba. Amma na gamsu kin fini gaskiya. Idan kika yarda muka tafi yanzu kuma. Na miki alkawarin har kasa ta rufe idona babu magana mai tsayi a tsakanina da ita bare soyayya ko aure, In sha Allah ".
Na yi k'asa da kaina, ban ce komai ba, amma kuma k'ullin zuciyata ya hau warware wa".
Ganin rarrashin ya fara tasiri. Ya sake tausasa harshe ya ce "Ai ni na dauka babu abin da zan yi miki, ki yi mini yaji. Tunda baki kai hakan ba ma, na miki babban laifi, kika rufa mini asiri kika yafe mini. Amma yanzu kuma a kan zato da zargi kika tozarta ni. Me yasa zaki munana zato a kaina? Me yasa kika zabi ki janyo mini fishin Babah?"
Yana rufe baki na ce "saboda ka fahimci ban dauki alamarin da wasa ba, ka kuma gane yanzu hankali ya fara ratsa ni. Ba komai zan lamunta ba".
"A karo na ba adadi ina sake baki hakuri. Allah ya huci zuciyar ki. Dan Allah mu rufe wannan matsalar. Wallahi bazan sake yi miki hakan ba, babu ruwana da ita, ko kallon inda take bazan sake yi ba. Ko na ganta a wajen Dada idan ta gaishe ni, zan amsa ne ba tare da na kalle ta ba, bare na gane me take ciki".
Na yi shiru. Ban tanka ba. Ya ce "Haba mana Little"!
Na cuna baki na ce "To kuma wayar da kuke yi fa?"
Da hanzari ya miko mini wayar yana fad'in duba ki ga ni. Na share lambarta. Na kuma jefe lambar a black list ta yadda ita ma ba zata same ni ba".
Na yi shiru ya ce "please mana Little ki ce kin huce, ki ce komai ya wuce".
Na dauke kai na ce "To kuma iyakar da ka nuna mini fa? Da ka ce gidan ka ne ba nawa ba?"
Da rawar murya ya ce "Kinsan An nadamu ala ma fata? To hakan maganar ta ke. To ni me ma zan yi da gidan da babu ke a cikinsa? Idan wannan maganar ne ta sake b'ata miki rai to ki huce. Na baki gidan ma gabadaya. Ki yi yadda ki ke so a cikinsa. Shi kenan?"
Na ce shi kenan, amma bazan koma yau ba".
Da hanzari ya ce "A a kada mu yi hakan, yanzu zamu tafi idan ba so kike hankalina yafi hakan tashi ba."
A hankali na ce "To kawai sai Babah ta ga zamu tafi? Ka bari idan na fada mata jibi sai ka dawo mu tafi".
Da azama ya ce "Wallahi bazan iya ba, kada ki zalunce ni, kin sani bazan iya ba. Tunda mun shirya ina ruwanta da mu?"
Ya mik'e yana ce wa "bari na je na fada mata zamu tafi".
Na bi bayan sa da kallo. Ina jin fishin da na yi da shi yana warware wa.
Na zuba wa yaran ido. Ina rasa ga ne wa nafi so a cikinsu. Dukkansu Abu guda nake ji a kansu. Amma na fi jin tausayin Hamim haka siddan duk da shine fitinanne kuma marar hak'uri.
A fili na furta "Allah ka rayamu tare da yaranmu, ka tsare mana su, ka yiwa rayuwarsu albarka".
Ina kallon Hanif da yake barcinsa akan gado illah kansa da yake jikina. Ina ayyana mutane masu karamci da sadaukarwa tun suna kananu ake fahimtarsu. Yana wahalar gaske ya ture d'an-uwansa a jikina. Ko abu ya dauka da Hamim ya fara kuka zai ba shi. Haka nan baya damuwa idan na goyi Hamim shi na rik'e hannunsa.
A raina sai nake ganin shine yafi dace wa ya amsa sunan Baban Marina. Ko da yake bansan ko Baban Bulkachuwan shi ma haka yake mai hak'urin gaske ne.
Na shafa kansa ina ce wa "Allah yasa ka zarce da hak'uri da yakanar ka. Allah ya saukaka muku rayuwarku gabadaya".
Na yi shiru ina jin wani irin abu na tsirga mini da bansan ko mene ne ba.
A hakan Babah ta shigo, Tijjani na biye da ita a baya.
Ta kalle ni ta ce "Wai har kin hakura kin ce zaki bi shi Yabi?"
Yadda ta yi maganar sai na kasa amsawa.
Nan da nan ya ce "Ta hakura mana Babah. Dan Allah kada ki sauya mata shawara. Na bata hak'uri, ke ma ina sake baki hak'uri."
Ta ce "Idan ta ce zata koma ai shike nan. Amma idan ta ni ne ko zata koma sai na kira maza sun taya ni kafa maka hujja".
Ya marairaice ya ce "Harshe da hakori ma ana samun sab'ani. Mun fahimci juna yanzu. Na yi alkawarin bazan kuma yi mata hakan ba. Mu rufe wannan matsalar a tsakaninmu dan Allah".
Ta kalle ni ta ce "Zaki koma, ko sai mun zauna da iyayensa na nan na fada musu BAK'AR TA'ADAR da yake neman tsiro da ita, kada nan gaba su ce na kashe masa aure".
Na kasa magana. Shi kuma fadi yake "Babah mun fa shirya ta fahimce ni, na bata hak'uri."
Ta ce "Kasan Allah sai na ji da kunnena sannan zan bari ku tafi. Ai kai yanzu maganar ka ba abin dubawa ce ba".
Ya rasa inda zai sa ransa. A kidime ya ce "Asiya taimake ni ki fada mata, kin huce, daure ki ce komai ya wuce. Kalli yadda yaran nan suke barcin nutsuwa a jikin ki. Ko baki hakura dan ni ba, huce saboda su".
Dakin ya dauki shiru. Kallon Tijjani kawai za'a yi a gane yana cikin zullimi sosai.
Ta sassauta ta ce "me kika ce, zaki koma, ko kuwa?"
Na yi k'asa da kaina na ce "Tunda ya gane kurensa, ya janye kalamansa, ya kuma bada hakuri, to ba sai an tara masa jama'a ba. Ai mun ba shi assignment ".
Ya yi maza ya ce "Wallahi exam ma kuka ba ni."

*Anti Rabi how far?*

✍️
*UMM NIHLA COLLECTIONS*
*Ta k'ware wajen kawo yadina masu kyau da sauki, cotton da silk, embroidered, Batik*
*A Malaysia take daga can kuma take turo su Kano direct. Dan haka kayanta akan farashi sari take bayarwa, daga guda daya har zuwa dari zaku samu*
*Kayan ta masu aminci da rahusa ne, ku tuntube ta Whatsapp dan ganin JERIN gwanon yadinanta da basa kode wa ko jeme wa*.
*07020695644*
*What's app only*.


*Oriflame products*
*Daga make up artist din Guduyo*
*Idan kina bukatar Oriflame products ko wanne irin ne, ko Kuma kina sha'awar yin register da su*. *Ki tuntubemi babbar dealer din su Aisha lame*
*Ina kuma fad'a muku akwai da daddan ganyen shayi na Lame Tea*
*Akwai pop corn*
*07036662633


Ya juya ga Babah ya ce "To ga shi nan ta fada miki ta hak'ura".
Ta fita tana fad'in "Y'aya'nta dai sun raunana ta. Ni kam ban so hakan ba."
Gabadaya ya yi sanyi da kalamanta. Yana ganin zasu sa na sake botsare wa. Da sanyin murya ya ce "Mu tafi yanzu ko sai anjima little?"
Na dauke kai ban amsa ba. Ya diririce. Ya ce "Mun gama magana fa Asiya".
"Sai na shirya kayana". Na fada ba tare da na juyo ba. Ya ce "To bari idan an yi azahar sai mu tafi ko?"
Ya fada da sigar da tambaya. Ni kuma na yi bakam.
Ya yi shiru yana kallona. Ya saki gauron numfashi ya ce "Ina kayan na ki suke na hada miki?"
Ban juyo ba na ce "Suna cikin wadirof din".
Ya bude ya fito da jakar kayan nawa. Ya gyara su. Ya ninke wanda Hamim ya dauko a igiya ya saka, sannan ya zuge.
Ya zauna yana ta yin mini maganganu da nufin mu yi hira. Ni kuwa sai basarwa na ke yi. Amma bai daina ba.
Ya dawo daga masallaci ya tarar yara sun tashi muna falo duka muna cin abinci.
Ya zauna shi ma ya zuba nasa.
Babah ta sake yi masa fada sosai. Sannan ta hadamu gabadaya ta ja kunnenmu akan mu kara hak'uri da junanmu. Sannan ta gode mini da har yau ban canja mata matsayin da na bata ba.
Ta rufe da ce wa "Dama idan kin ga kin gaji to wajena ne mafarki matukar ina raye".
Na amsa mata da ce wa "In sha Allah Babah".
Ya kasa hak'uri ya ce "Kin bata lasisin ta yiwa zaman aure tustu kawai Babah".
Ta girgiza kai ta ce "Matukar za'a tozarta ba. Amma idan akan son zuciya zata yi, ai ba yarda zan yi ba. Kai ba abin kunya ba

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login