Showing 132001 words to 135000 words out of 184118 words
Chapter 45 - Bakar Taada Hausa Novel Complete
ta, shi kenan magana ta k'are."
A sanyaye ya ce "Na gode na kuma yarda na yi kuskure. Amma me yasa ta zarge ni?"
Kai-tsaye Ummi ta ce "Kai ka bada k'ofar. Me yasa dan Nasiba zata zo gidanka sai ta hannunka zata biyo? Ba Yabi ce matar gidan ba? Me yasa sai da kanka zaka kai ta? Me yasa ka kausasa harshen ka akan zamanta?"
Ya ce "Yanzu dai Ummilolo Yabi ta yi dai-dai da ta fice ta bar gidan babu izinina?" Ta numfasa sannan ta ce "A fuskar shari'a bata kyauta ba. Amma tunda ni mace ce nasan yadda take jin zafi a zuciyarta bata yi laifi ba, tunda ka nuna wacce bata zama dolen ka ba sai ta zauna mata a gidan ko tana so, ko bata so, ba tare da rarrashi ba".
Ya saki ajiyar zuciya ya ce "Na gode sosai Ummi. Na kuma gamsu da wannan gaskiyar ta ki babu son kai a cikinta. Kuma yanzu hakan tun jiya na saka Nasiba a mota ta dawo Toro. Na sallame ta a kurarerren lokaci ko?"
Nan ma Ummi ta ce "Eh, baka girmama ra'ayin matarka ba, sai da ka bari ta yi maka tutsu, hakan kuma zai haifar muku da tazara da tsatsar zuciya mai yawa".
Cikin karaya ya ce "Na gode bari na shirya yaran nan, mu fita nemanta, ki taya ni addu'a, gaba'daya yarinyar nan ta gigita ni. Wato Yabi jidalinta mai girma ne."
Ummi ta kwashe da dariya ta ce ni fa ban ga laifinta ba Yaya Bulkachuwa. Haka kawai za'a lallaba a yi mata kutse mai dafa zuciya, da saka jinya a gangar jiki".
Ya numfasa ya ce "Allah ya sauwake, ni Wallahi babu tunanin komai a zuciyata akan hakan".
Ta ce "Kai kasan hakan, mu ina muka san zuciyar ka?"
Ya ce "Shi kenan bari na saka d'ambar neman ta."
Suka yi sallama, ya kashe wayar tare da zurfafa a tunanin ta inda zai fara nemanta.
A daddafe ya yi wanka saboda azabar kukan Hamim. Domin a bakin band'akin ya zauna yake kuka na tashin hankali. Hanif kuma sai ri'ke shi yake alamun wai ya yi shiru.
Dan haka ko da ya fito a rikice ya shirya, ya dauki yaran da yake ta gunjin kuka.
Yasan kukan neman Amminsu yake yi. Allah ya zuba masa k'ulafacin uwa. Ya gama shawo kan Hamim ya yi shiru, sai kawai Hanif ya fa'di ya dan bugu a goshinsa. Ya fara kuka shi ma.
Hamim da dama kukan ba daina shi ya yi gaba'daya ba, sai kawai ya bu'de baki yana taya Hanif. Suka rikice masa ainun.
Ya jima kafin ya samu su tsagaita. Shi da kansa ya fahimci d'a sai uwarsa. Duk da yadda ya iya raino. Amma rashin Yabi a tare da su sai komai ya k'wace musu daga shi har y'ay'an sa.
Har suka bar gidan bai yanke shawarar inda zai dosa ba.
Amma yana hawa titi zuciyarsa ta fi rinjayar masa ya je Bulkachuwa.
Dan haka gidan mai ya shiga ya sha mai. Ya siya wa yaran yoghurt da cake. Sannan suka dau hanya. Yana yi yana daukar fasinja dan ya samu sau'kin tsadar mai.
Da walwala Babah ta karb'e su. Tana ta tambayar ya aka yi suka baro Yabi a gida ita kad'ai?
Ya dan diririce, bayan ya ga rashin wasa a fuskarta. Murya babu karsashi ya ce "Bata jin da'di ne shi yasa bamu taho tare ba, nima kayan miya na kawo nan Dambam".
Ta ce "Ayyah me ya same ta? Ko zazzabin damina ne da ko ina yinsa ake yi".
A sanyaye ya ce "zazzabin cizon sauro ne, amma da sau'ki rashin k'warin jiki ne kawai."
"To Ubangiji ya bata lafiya". Ya amsa da Amin cikin damuwar to ina Yabi ta fantsama kenan?
Ya kasa ko da shan ruwan da yake gabansa bare kuma abinci. Yara dai suna ta cin abincinsu.
Ta zauna tana fa'da masa sati mai zuwa Aliyu zai je Ibadan yin jarabawar zama likita, tunda karatun likitanci yake yi a jami'ar Jos.
A gajarce ya yi murna da fatan alheri. Ta fahimci rudun da ya shiga amma ta matse ta yi kamar bata gane ba.
Ya sassauta murya ya ce "Tafiya zan yi, zan bar yaran a nan, zuwa jibi zan dawo".
Cikin nutsuwa ta ce "Haka kawai ka dauko su babu shirin zasu zauna ka bar mini su? Uwarsu ba zata ji dadi ba".
Ya basar ya ce "Ko ba wajen ki na kawo su ba, har ta yi mini inkarin inda na kai su bare kuma wajen ki ne".
Da azama ta ce "Wallahi ba zaka bar su ba, tunda kai ma ba da nufin su kwana ka taho da su ba. Kaya kala daya ka sako musu a leda. Nasan kuma idan sun bata na jikinsu a sauya musu ne iya yau. Ka bari idan ka shiryo su da kayansu sai su zo mini, amma ba haka kawai a shiga hakkin uwa da y'ay'an ta ba".
Ya rasa yadda zai yi, a kan dole ya kwashe su suka juya.
Ni da nake mak'ale a daki, zuciyata sai tsalle take yi a kan na ga yarana. Da k'yar na daure ban fito ba.
Da suka tafi kuwa sai na ji tamkar na ruga a guje na ce "Ga ni nan".
Na kwanta lamo. Ina kallon silin. Babah ta shigo yanayin da ta ganni a ciki sai ta yi turus. Ta iso ta zauna a gefen k'afafuwana. Ta sassauta murya ta ce "Nasan zaki so yaranki a tare da ke. Amma ki daure ba jimawa zaki yi ba. So nake ya rikice gaba'daya, ta yadda da kansa zai zo da bakinsa ya fa'da mini ba kya tare da su.
Har da ce mini wai kina gida zazzabi kike yi".
A hankali na ce "Idon Hamim ya yi ja?"
Ta galla mini harara ta mik'e ta na ce wa "Ban sani ba. Idan kuwa haka zaki mini, ki kuntata kanki sai ki zo ki bi bayansu kawai".
Ta fice tana ta sababin masifar son y'ay'a da iyayen yau suka mak'alawa zukatansu.
Da gaske dai mace tana saurin yin afuwa ga namiji a dalilin yaranta. Domin tun yanzu na fara kewarsu. So nake na bu'de ido na ga suna wasan hawa da sauka a jikina.
Na fesar da iskar damuwa. Na sani daga shi har yaran suna cikin kewata mai yawa. Barin ma sarkin kuka da k'ulafaci Hamim.
Haka na zauna, ina jin wani irin abu na bina.
**
Bulkachuwa kuwa da k'yar ya isa Bauchi domin ya shiga rudun inda zai ga Yabi. Ya kira wayarta yafi sau goma ana fa'da masa a kashe take. Amma ya kasa dainawa.
Suna isa gida, dakinta ya dire. Yaran da suka waiwaya basu ganta ba, suka dinga kuka a tare. Shi kansa ji yake tamkar ya bare baki ya tayasu. Gaba'daya azanjinsa ya k'are. Da k'yar ya shawo kansu suka yi shiru. Kwanaki biyu yana tiritiri da su. Sa'ar da ya yi ma ya riga ya saba da hidimarsu. Jiya a Toro suka yini, yana bulayin yiwa gidajen mutane dirar mikiya ko zai ga Yabi. Amma shiru tamkar Malam ya ci shirwa.
Komai ya tsaya masa cak. Kan dole ya sake komawa Bulkachuwa da su.
Ya rasa ta yadda zai fa'dawa Babah Yabi ta gudu ta barsu.
Ya gama kame kamensa ya fa'da mata gaskiya sun samu sabanin fahimta da Yabi ta yi yaji, ya kuma neme ta ya rasa tsawon kwanaki uku kenan.
Ta dauki salati mai tsananin gaske. Ta dake ta ce "Yarinyar da ubanta ya damka mini amanarta a hannuna ka yiwa sanadin da ta gudu ta fantsama duniya?"
Ya yi tsumu ya rasa me zai ce. Ta ce "Sai ka fa'da mini abin da ka shuka mata har ta kasa ha'diye wa ta bar maka wadannan yaran da suka shiga ranta. Ta tafa hannu tana skae kambaba girman lamarin. Fadi take yi "Duk uwar da tafi ta bar k'ananun y'ay'anta ai ba'kin cikin da take ha'diye wa ba ka'dan ba ne. Tura ce ta kai bango".
Ya kasa ce wa komai. Illah zufa da take yanko masa tamkar mai hadiyar kunama.
Cikin bacin rai ta ce "Ya ya ina magana ka mini shiru sai zare ido ka ke yi irin na rashin gaskiya".
Murya babu amo ya ce "Wallahi ba komai na yi mata ba. Nasiba ce ta zo shike nan ta kwarzabi kanta."
"Ta kwarzabi kanta kamar ya ya?"
Ta tambaya cikin wani irin yanayi na bacin rai mai yawa.
Ya numfasa ya ce "Ce wa ta yi sai na kore ta. Ni kuma na ce bazan kore ta ba. Shi kenan na dawo na tarar ta bar gidan".
Ta rausayar da kai ta ce "To ai Yabi
ta yi adalci. Sai da ta fa'da maka bata son zamanta. Kai kuma ka nuna kana da bu'katar ta zauna a gidan tunda naka ne. To mene ne kuma dan ta fita ta bar muku gidan ku tabbata a ciki?".
Ransa ya baci ainun. Ita ma bata fahimce shi ba. Su duk haka mata su ke da kishi ne?. Basa fahimtar komai matu'kar akan kishi ne.
A hankali ya ce "Yanzu dan Nasiba ta zo shi kenan sai ya zama masifa? Ta ce sai ta bar gidan? Duk zamanmu da ita bata gasgata ni ba ke nan? Ni ba kula ta nake yi ba, bare ta ce ta fahimci wani abu a tsakaninmu. Wallahi saboda sababin Yabi ko kallon inda ta ke bana yi. Amma hakan bai yi mata. Shin Nasiba ba zata zo gidana ba, ba yar'uwa ta ba ce?".
Babah ta girgiza kai ta ce "K'warai yar'uwar ka ce ta gaske tunda har ka zabi fishin matarka akan ta. Madallah da Yabi bata za'bi zaman muzanci ba. Ta daga hannuwanta sama ta ce "Allah kasa yarinyar nan tana hannu na gari. Allah kasa tana Kangire ko kaduna gidan Jabir".
Nan da nan ya muzanta. Ya kasa yin shiru ya ce "Kaduna! Ya fa'da cikin takaici mai yawa.
Ya kasa yin shiru da rawar murya ya ce "Na rantse idan aka same ta a Kaduna duk masifarta sai ta ga ne bata iya komai ba".
Ta galla masa harara ta ce "To me zaka yi ne? K'arshe dai ka sake ta. Ni kuwa Wallahi tana gama idda zan bada aurenta ga saurayi ma, don bazan yarda ta fita daga ahalina ba."
Idonsa ya kad'a ya yi jawur. Da rawar murya ya ce "Babah a gabana kike nuna zaki bawa k'anina auren matata?"
Ta bu'de murya ta ce "Na fa'da na ji ruruf!".
A matu'kar ki'dime ya ce "Allah ya huci zuciyarki. Allah ya tsare ni aikata irin wannan BAK'AR TA'ADA din".
Ya bata tausayi ainun. Amma ta cije ta ce "Akan idona uwar Nasiba ba abin da bata fa'da akan ka ba. Ita ta hana a baka aurenta saboda suna ganin ka baka da mamora. Amma Yaya Sani ya juyawa dukkan nak'asunka ya tursasawa Yabi auren ka sai kuma dan ka fara samun dama, ka fara shiga sahun mutane sai a yi maka shunen ta har cikin gidan Yabi! Ta yi shiru. Saboda yadda zuciyarta take jin tsananin zafin yadda aka tado mata tsumin bacin rai na tsawon lokaci.
Ta zuba masa ido wanda rabon da ta yi masa haka ya manta.
A kaurare ta ce "Nasiba ba matarka ba ce, ko bayan raina ba zata zama matarka ba. Shari'a ta halasta ka aure ta babu aibu a cikin hakan. Amma kuma shariar da kanta ta ce "ku girmama ra'ayin iyayenku sama da naku. Matu'kar ina da hak'ki akan ka Wallahi na haramta maka ita. Soko marar tunani. Har ka manta tozarcin da uwarta ta yi mini akan maganarku?"
Hankalinsa a matu'kar tashe ya ce ", Wallahi Tallahi ba ni da manufar komai akan ta. Dan Allah ku fahimce ni mana"
"An k'i a fahimce kan. Ban da sakarci me ya kai ka taho da ita tunda ga Toro har Bauchi ku ka'dai ka kawo ta gidan ka. Ai sai a rasa gane wace ce matar gidan tunda sai ta goyi Yabi da zani tsab. A kan wanne dalilin da ta ce ba zata zauna mata a gida ba, ka kafe sai ta zauna d'in? Ban da munafunci irin na ku na maza. Na gode wa Yabi da ta fahimci bata da daraja a wajen ka. Ta fice ta bar maka gidan".
Da rawar murya ya ce "Allah ya huci zuciyar ki. Na yi kuskure a yafe ni dan Allah. Tun ranar kuma Nasiba ta tafi, da kaina na ce tafi din"
Ta ja tsaki mai tsananin gaske tare da fad'in "Ta baya ta rago".
Akwai kaya masu kyau a cikin farashi mai sauki*
*Maganin sanyi*
*Saiwowin Tsumi*
*Saiwowin dahuwar kaza*
*Saiwowin dahuwar tattabaru*
*Gumba*
*Tsumin kwakwa*
*Y'aya'n gadali*
*Hadadden daka*.
*Tsugunno mai sa a matse*
*Goran tula*
*Goran tula syrup*
*Garin goran tula*.
*Maganin gyaran nono*.
*Zuma ta mussaman*.
*Tsumi*.
*Da sauran kayayyaki na mussaman da basu da illah*.
* Domin kuwa asalin Saiwowin ne da ake kawo su daga Chad*.
*Abu mai kyau shi ke siyar da kansa ku tuntube ni dan samun naku kayan cikin sauki da mututantawa. Ina aikawa ko ina a fad'in tarairaiyar Nijeriya*
*08032773332*
✍️
*WANNAN LITTAFIN NA KUDI NE BIYA KUDIN KARATUN KI TA WANNAN ASUSUN DAN GUJE WA BAKAR TA'ADA!*
*REGULAR 500*
*VIP 1K*
*VIA*
*2384876855*
*SURAYYA IBRAHIM DAHIRU*
*ZENITH BANK*
*KO*
*7061488065*
*SURAYYA DAHIRU IBRAHIM*
*OPAY DIGITAL SERVICES.*
*TURA SHAIDAR BIYA TA WADANNAN LAMBABOBIN*
*08032773332*
*09069067488*.
*UMM NIHLA COLLECTIONS*
*Ta k'ware wajen kawo yadina masu kyau da sauki, cotton da silk, embroidered, Batik*
*A Malaysia take daga can kuma take turo su Kano direct. Dan haka kayanta akan farashi sari take bayarwa, daga guda daya har zuwa dari zaku samu*
*Kayan ta masu aminci da rahusa ne, ku tuntube ta Whatsapp dan ganin JERIN gwanon yadinanta da basa kode wa ko jeme wa*.
*07020695644*
*What's app only*.
Ya yi shiru ya kasa ce wa komai. Haka ita ma. Yara ne kawai su ke ta wasa a tsakaninsu. Sai iskar fanka da take kadawa da karfi sosai. Amma hakan bai sa zufa ta daina yanko masa ba. Gaba daya ya shiga rudani mai yawa. Ya rasa inda Yabi ta gudu. Ga magaganun Babah masu tsauri. Wanda hakan yake alamta masa yana cikin fishinta.
A sanyaye ya sake bata hak'uri tare da matsar da jakar kayan yaran gabanta. Ya mik'e ya faki kallon yaran da suke wasan tsere a tsakaninsu. Ya ce "Zuwa gobe zan dawo".
Galala ta kalle shi ta ce "Dauki jaka da y'aya'nka. Ai ba zai yiwu ka kori uwarsu da baki cikinka ba. Sannan ka saka rai zan maka wahalarsu. Wato na zama shasha ma!
Ya koma ya zauna ya sassauta murya ya ce "Haba mana, dan Allah ki ji tausayi na. Gabadaya nutsuwa ta yi mini tutsu. Idan na barsu ma ba wai hutawa zan yi ba. Neman ta zan cigaba da yi. Gobe Kaduna zan tafi".
Cikin rashin nutsuwa ta ce "To ka tafi da su, ko ka fara kai su Toro wajen Nasibar sai ka wuce. Amma Wallahi ko gwaggonsu ka kai wa yaran nan, ni da kai ne".
Ya yi shiru, idon sa ya kad'a ainun, ya koma ya zauna. Murya babu amo ya ce "Ki yi hakuri dan Allah Babah."
Ta jijjiga kai ta ce "A kan Yabi Bilhillazi zan yi matukar saba maka. Zan fita a sha'anin ka gabad'aya."
Ya yi shiru. Amma ransa suya yake tamkar ya fad'o kasa.
Me ya yiwa Yabi da zata janyo masa irin wannan jidalin?
Ya dinga bata hak'uri. Da k'yar ta ce sai ya gano Yabi idan ta huce, sannan ita ma zata hakura." Ya mik'e da sauri yana fad'in "Na gode sosai. Bari na tafi neman ta da ikon Allah zan nemo ta".
Daidai lokacin Hamim ya fasa kuka yana nuna windo. Tare suka isa gare shi, suna fad'in mene ne?"
Shi dai Hanif yana tsaye, yayin da Hamim yake kuka tare da nuni da saitin windo. Nan da nan zuciyar Baba ta tsinke domin ta gano kayan Yabi yake nuna wa akan igiya. Ma'ana ya gane kayan uwarsu, a ba shi ya rik'e mata.
Nan da nan ta dauke kai, ta shiritar da Tijjani da ce wa "Tofa masa addu'a mana, watak'ila shaid'anu ke son bude masa ido. Allah ya tsaremu daga sharrin abin da bama kallonsu".
A gigice ya hau tofa masa falaki da nasi. Yaro kuwa sai zabura yake akan zai je ya dauko abin da yake ganin na uwarsa ne. Yayin da Babah take ta hirji tare da addu'ar kada Yabi ta kasa jure kukan Hamim da yake d'ada canyarwa tamkar gyare ta fito. Ita da kanta ta gane irin kukan da Yabin ta yi tana yarinya ya gado.
Ta ce "Dauke shi ku tafi. Idan ya ga kun shiga mota zai yi shiru."
A raunana ne ya ce "Yadda ya razana hakan zan tafi da shi? Ki yi hakuri na bar su a nan, gobe ko jibi da ikon Allah zan dawo na dauke su. Ko ban ganta ba.
Ta ce "A a ba fa zan rike su ba. Ai idan kasan zan rik'e maka yara ka dinga shagulatin bangaro da auren ka kenan. Ina ce lokacin da suke hannuna ka fi uwarsu nuna zalamar na baku su? Yanzu kuwa ba zan karbe su ba."
Kamar zai rushe da kuka ya ce "Gobe Kaduna zan je Baba."
A gajar ce ta ce "Tafi da su ka kai wa Ihisan. Idan ka dawo ka je ka dauke su".
A kan dole ya sunkuya ya dauki Hamim. Ya rike hannun Hanif. Bayan ya saba jakar kayansu. Yadda ya d'ebi yaran da jakarsu sai tausayinsu duka ya kama ta.
Suka fita, sai da suka jima da fita. Sannan ta bude dakin da Yabi ta ke. Ta tarar da ita zaune akan gado tana faman goge idonta tabbaccin kuka take yi.
Ta k'arisa kusa da ita. Ta ce "Yabi kuka kike dan ina kokarin ya fahimci muhimmancin ki a rayuwar sa da ta y'aya'nsa?"
Da wata irin tab'ara da kuka na ce "Ai da sai ki karbe su. Kukan Hamim kad'ai abin dubawa ne".
Ta yi galala ta zuba mini ido ta kasa ce wa uffan.
Na kuwa matse na ce "To ni dai na huce tunda haka ne. Ai ya yi ta zuwa, na kuma san yana cikin tasku, sai ki zaunar da mu, a mayar da zan ce, ki yi masa fada, mu tafi."
Ta jijjiga kai tare da ce wa "Ban yi hakan ba Yabi. Ba kuma zan yi ba".
Na kuwa juya na kwanta ina kunkunin bazan sake yin yaji na zo nan ba, tunda ba sulhu zata yi ba".
Ta dinga salati tana tafa hannu. Tare da ce wa "Ban ga laifinki ba. Amma zaki ga karshen iyashege. Dauko hijabin ki, ki bisu. Na bata rai tare da daure fuska ainun. Ta sassauta ta ce "Ba