Showing 84001 words to 87000 words out of 184118 words
Chapter 29 - Bakar Taada Hausa Novel Complete
fuska sosai.
Ganin hakan ya mik'e shima fursakarsa a d'aure ainun ya ce " Ban samu ku'di na siyo abin da zaki ci ba. Me kike son ci na dafa miki?"
Cikin son na wahalar da shi na ce "Faten doya da wake. Sannan da alaihu da kifi a ciki."
Ya nisa ya ce "Ba ni da kudin da zan sayi kifi yau. Zan dai je na siyo alaiyahun. Ya fara tafiya da nufin fita.
Na bu'de baki na ce "Zo ka kar'ba. Ni ina da kudin".
A zafafe ya juyo "Cikin kaushin harshe ya ce "Asiya Toro baki da kudin da zaki yi mini cefane matu'kar ina da lafiya, ina kuma kan k'afafuna. Ba zaki yi ku'din da zaki aike ni, na siyo abu sannan na zo na girka miki ba, har abada kuwa".
Ganin yadda ya rikice ya koma Bulkachuwan sa sai na yi maza na kame, domin na sani yana iya dauke ni da mari. Na laluba na kasa gane fishin me yake yi tun dare. To me na yi masa? Ni da ya ganawa azaba ma ban yi masa zafin kai ba sai shi zai dinga yi mini muzurai da hargagi?.
Ya yi k'wafa ya fice bayan ya jira na tanka, amma na yi muk'us.
Ina ta jin b'ab'atunsa a kicin. Ga mamakina sai ga shi ya kawo mini lafiyayen faten doya da wake a ciki. Ya ji alaiyahu da albasa mai lawashi.
Nabi bayansa da kallo. A dalilin bai zauna ba fice wa ya yi.
Ina jinsa a kan baranda ya zauna yake cin nasa.
Haka kawai sai na ji guiltiness na kama ni to me na yi masa?. Da ya gama bai lek'o ba. Daga inda yake ya ce "Sai anjima".
Na rasa gane manufar wannan abin da yake yi.
Da daddare ma da ya dawo bayan ya yi wanka. Ya dube ni ya ce "Zaki ci donot da tea ne, ko kuwa da abin da kike son ci?"
Cikin kuka na ce "Bazan ci komai ba Tijjani. Na hutar da kai" Na cigaba da gunjin kuka.
Da farko kamar ba zai tanka ba.
Sai kuma ya kasa jarumtar share ni. Ya ce "Wannan kukan fa? Ko dan na fa'da miki bana so shi yasa kike ta yi, tunda burinki ki kassara ni da ba'kin cikin ki".
*Annur food Delicious*
*Da k'arfin zuciya da guiwa na ke muku shunen inda zaku samu kayan da na zano a kasa cikin saukakkan farashi.*
*Shaida nake yiwa kayan annur domin dadinsu da ingancinsu ya kai kurewa*
*HANZARTA ki nemi kayansu dan ki gasgata batuna*
*Garin kunun tsamiya garin danwake, garin borkono, yajin daddawa, man shanu, nikekkakiyar gyada ta kunu da ta miya*
*08039183880*
"Na tsagaita da kukan na ce "Akan me zaka dinga yi mini fishi, alhalin ni ya kamata na yi".
Ya zuba mini ido yana yi mini kallo mai tsananin gaske.
Cikin b'acin rai ya ce "Idan a duniya akwai abin da na k'i to a jingina mini waccar Bak'ar TA'ADAR ne.
Ta yaya kina matar aurena zaki dinga kallon idona kina fa'da mini maganganun da suke neman sabauta ni. Ban da dai kin mayar da ni shasha marar mutunci kya fa'da mini na saba danne mata akan idona?"
Jikina ya yi sanyi ganin yadda yake cikin fishi sosai idonsa ya kad'a har k'walla ne kwance a cikinsu. Tabbacin ba karamin k'ona masa rai na yi da kalamun nawa ba.
Ban san ya aka yi ba na ce "Allah ya baka hakuri Tijjani".
Ina rufe baki ya matso jikina ya ce "Shike nan na yafe miki duniya da lahira. Na huce".
Na ce "Amma zan fa'da maka gaskiyar magana".
Ya ce "To ina sauraren ki."
Na kawar da fuskata na ce "Gaskiya baka iya wannan abin ba. Ba haka ake yi ba, sannan ba haka k'awayena da aka yi musu aure suke ji ba. Domin ni dai ko a littafi idan ina karantawa ba'a shan wannan azabar da kake gana mini. Na tabbatar da haka kowa yake ji da Adda Nazira ta fa'da mini. To ina ganin iyawa ne kawai baka yi ba gaskiya".
Ya sake kallona, ba tare ya ce uffan ba, na tabbatar ya rasa me zai ce mini ne.
✍️
*UMM NIHLA COLLECTIONS*
*Ta k'ware wajen kawo yadina masu kyau da sauki, cotton da silk, embroidered, Batik*
*A Malaysia take daga can kuma take turo su Kano direct. Dan haka kayanta akan farashi sari take bayarwa, daga guda daya har zuwa dari zaku samu*
*Kayan ta masu aminci da rahusa ne, ku tuntube ta Whatsapp dan ganin JERIN gwanon yadinanta da basa kode wa ko jeme wa*.
*07020695644*
*What's app only*.
*Oriflame products*
*Daga make up artist din Guduyo*
*Idan kina bukatar Oriflame products ko wanne irin ne, ko Kuma kina sha'awar yin register da su*. *Ki tuntubemi babbar dealer din su Aisha lame*
*Ina kuma fad'a muku akwai da daddan ganyen shayi na Lame Tea*
*Akwai pop corn*
*07036662633*
*BAKAR TA'ADA*
51&52.
Me ya tuna oho. Na ga dai ya ha'diye dukkan fishinsa da mamamkinsa ya ce "Nasan ke ma baki iya ba, bare na kwantar da kai ki koya mini."
Na dauke kai na ce "Mu y'an kananu ba'a d'aukar lokaci mai yawa tare da mu."
Ya murmusa ya ce "Shike nan next time zan kiyaye."
Na sake dauke kai na ce "Ni fa ba zan sake yarda ba".
Ya murmusa ya ce "Ai hakan ma na gode".
Bai sake tayar da maganar ba. Ya dinga ririta ni.
Muka kwana lafiya lau.
Washagari zai fita bayan mun karya tunda babu zuwa gidan burodi.
Na kalle shi na ce "Ina son zuwa gidan Adda Nazira".
Ya girgiza kai ya ce"Ba yanzu ba Asiya".
Na bata rai na ce "To sai yaushe?"
"Ta kusa haihuwa ai, sai Allah ya sauke ta lafiya. Kya je ganin abin da ta haifa miki".
Na tsuke fuska na ce "Gaskiyar magana fa Tijjani ba irin wannan rayuwar nake harin samu ba.".
Ya girgiza kai ya ce "Ki gode Allah dai".
Na zum'bura baki na ce "Kullum cikin godiyar na ke. Amma yanzu an daina irin wannan takurar fa".
Ya kalle ni ya yi murmushi tare da cewa "Asiya Toro manyan mata".
Daga haka ya tafi ya bar ni.
Kwana hudu a tsakani na warware na cigaba da harkokina har da sana'ata.
Shi kuma ya daure bai sake takura ni ba.
A haka muka sake kwashe sati. Har lokacin kuma ban sake yarda mun ha'du ba, duk jarabarsa kuwa.
Ya rasa yadda zai yi da ni. Domin duk dare sai na sanya panties uku, sannan na saka dogayen wanduna biyu. Na sake saka riga a kai.
Duk hilarsa ya kasa cimma ni.
Ya gaji da rara-gefe ya koma rarrashi.
Amma fir na k'i domin gaba'daya na tsora ta. Da gaske rad'ad'in da nake ji ya wuce misali.
Rannan da daddare ya kasa barci.
Ya tashe ni, a marairaice yake lallaba ni.
Murya a raunane ya ce "Ina jiye miki tsoron tsinuwar mala'iku Asiya."
Rai a bace na ce "Ni gaskiya bazan yarda ba, haka kawai ba komai a ciki sai azaba. Daga gunka ne matsalar, tunda ai ba haka ake ji ba, ni ce nake jin hakan."
Ya ru'ko ni a diriri ce ya ce "Allah zai taimake ni. In sha Allah yau ba zaki ji zafi ba. Ki yi ha'kuri kin ji. Da ace kin bu'de mini zuciyarki ba zaki ji zafin har haka ba".
Duk yadda ya ki'dime da son na aminta da shi fir na bijire, da na ga zai saka mini k'arfi ma. Kuka na dinga yi masa mai tsananin gaske.
Ya k'yale ni.
Amma barcin da bai yi ba ke nan.
Washagari ya tashi da azumi. Amma me?
Da ya dawo daga gidan burodi sai gani na yi, ya fito mini da tarkacen filillinkan lallena da na saka aka kawo mini su daga gida. Hatta robar da nake k'wabin sai da ya fito mini da ita.
Ya shigo d'akina ya kwashi wasu daga cikin kayansa.
Ya mayar can.
Ina kallonsa ban ce komai ba. Amma dai kam na shiga damuwa. Domin an jarrabe ni da son sana'a tun ina k'aramata. Ina samun nisha'di a cikin yin lalle da kitso.
Na sani kuma ba zai yiwu na mayar da falona wajen dabdalar yin k'unshi da kitso ba.
Ya gama uzzirinsa ya yi shirin fita. Ya same ni har cikin falon da nake zaune.
Fuskarsa babu walwala ya ce "Asiya kada ki shigar mini daki, ina bu'katarsa. Domin kwanan cikinsa zai fiye mini masalaha ga lafiya ta".
Na kalle shi. Yadda ya tsare gida ya sanya na kasa sakar masa bakaken maganganu.
Na tsuke fuskata na ce "Al'kawarin ke nan? Ni ba Tijjani ne ya ce ya bar mini d'akin na yi yadda nake so ba?"
Ya girgiza kai ya ce "Tijjani ne ya fa'da, yanzu kuma ya fasa sai ya ya?"
A kufule na ce "Sai hukuncin mai sab'a al'kawari ya hau kansa".
Ya ce "Ya hau din. Tunda dai ba tsinuwar mala'iku zata hau kaina ba ai da sau'ki".
Na sake hassala na ce "Wai na tambaye ka mana?".
Ya ce "Kunne na jin ki".
Babu tsinkaye na ce "Ni a siffofin munafiki ai har da sab'a al'kawari ko?"
Da budaddiyar murya ya ce "Eh" , sai kawai ya shammace ni ya dauke ni da mari".
Na zunduma ihu ina ce wa "Manzallazi ya saka mini akan wannan zaluncin da kake yi mini".
Ya ce "Idan zaki zage ni sau dubu. Ni kuwa zan d'aga miki hannu sau dubu. Shege ka fasa a tsakaninmu. Kuma idan kin cika marar kunya ce ke, to ki shiga mini d'aki da nufin yin k'unshi, ki ga kalar tawa rashin kunyar".
Na kasa ce wa komai illah kuka sosai da nake yi.
Bai damu da kukan ba, ya saka kai ya fice.
Asarar da na yi, a yinin wannan ranar ba ka'dan ba ce.
Domin kuwa mutane sun fi goma da suka zo k'unshi ina sallamarsu.
Gara ma na yiwa yara uku kitso a falo.
Sau uku yana kewayo wa ko zai tarar na shiga, ya wula'kanta ni. Sai kuma ya ga duk zuwan da zai yi bai ga kowa a ciki ba.
Kwana biyu muna wannan takun sak'ar.
Ga shi na ji a bakin Rafi'a ana ta tumfirint din Neco.
Kwana na uku na same shi a d'akinsa da daddare na zauna na sassauta murya na ce "Tijjani ka ce "Zan yi Neco ga shi ana fa'din an kusa rufe yin rigista da tumfirint din".
Kai-tsaye ya ce "Na fasa fas. Dama ai ba wai karatun ya dame ki ba ne. Ni ne a kokarin na sanya farin ciki a zuciyar ki ya sanya na ce zaki yi. Ina kuma da sha'awar mace mai ilimi. Yanzu kuma na fasa tunda baki da abin wula'kantawa, sai ni".
A sanyaye na ce "Dan Allah Tijjani tunda ka saka mini rai ka bar ni."
Ya ja tsaki ya juya ya cigaba da kwanciyarsa. Na tsura masa ido ina jin zuciyata tamkar ta fa'do. Wato ko wanne namiji ya iya tsiyataku masu k'ona rai. Na dinga mamakin me zai sa wula'kancinsa ya yi mini ciwo ne?".
Na tashi na bar shi, zuciyata tamkar ta fa'do k'asa.
Kullum fishin nasa gaba yake yi ba baya ba.
Gaba'daya ya fitittike ya koma wanccan Bulkachuwan da yake dauke kai ga mace in ta nemi yaga shi. Magana ma da k'yar yake yi mini. Tsakaninmu ya shigo mini da cefane. Idan ya samu sararin siyo kayan masarufi kuwa, sai dai na ga yawansu ya k'aru. Ya daina sauraron abincina. Ya kuma daina tambayar me zan ci. Da ya gama uzzirinsa zai sa kai ya fice, nasan dai bai ta'ba fashin kawo mini cefane ba. Sannan bai damu sai na ba shi idan na girka ba.
Ranar da babu gidan burodi kuma bai samu aikin da zai yi ba. Zai dawo ya ce mini ki yi wake da shinkafa ko ki dafa taliya da manja.
Shi kuwa sai ya jika garin rogonsa ya sha, ya sake fice wa. Wani lokacin tausayinsa ya hana ni sukuni. Na rasa yadda zan yi da shi, ya k'ulla gaba mai yawa a tsakaninmu.
Rannan ya ce mini "Ya tafi Bauchi. Da'di ya ratsa ni, domin zan samu na dan yi k'unshi kafin ya dawo garin. K'warai na takura a halin da nake ciki.
Ai kuwa mutum uku suka zo, na kai su dakin bayan na kintsa masa kayansa gefe guda.
Na dauko bedsheet na rufesu.
Na gama yiwa mutum biyu, ina cikin sakawa ta uku. Tamkar jifa sai buga k'ofa na ji. Ban kawo shine ba. Tunda ya ce ya tafi Bauchi. Nasan kuma sai wajen dare zan gan shi.
Na fita da sauri ina zaton ko Anas ne.
Ina bu'de kofa kawai na ga mutum a tsaye.
A gigice na ce "Tijjani ba ka tafi Bauchin ba?"
Fuska a daure ya ce "Allah bai yi ba".
Na tare hanyar shigowar. Ya ce "menene haka, ba ni hanya band'aki zan shiga".
Na diririce. Baki na rawa na ce "Dan Allah, dan darajar Annabi Tijjani ka rufa mini asiri, ka yi hakuri kada ka shiga d'akin lalle.
Ya galla mini harara ya ce "Yau munafurci ya tabbata a kan ki, kuma zaki ga k'arshen rashin mutunci Wallahi".
Na zabura na ri'ke shi sosai. Murya na rawa na ce "Ka yiwa Àllah da Manzonsa kada ka yi mini haka. Na yarda komai ka ke so zan yi, amma kada ka sake tozarta ni Tijjani".
Ya zuba mini ido yana kallon yadda hawaye yake tsere akan fuskata.
Ya jijjiga kai ya ce "Shike nan".
Sanin bai iya yaudara ba, ya sanya na sake shi ya shiga, ina bin sa a baya. Domin da zai shiga d'akin, ba zai nuna mini ba zai shiga ba.
Kai-tsaye falo ya dosa. Na samu nutsuwa a zuciyata.
Tsabar nutsuwar da na samu har ruwa na dauko masa.
Na kawo masa abincin da na dafa zan ci.
Ya hakince tamkar wani basarake. Yana cin magani, komai isa isa yake yinsa.
Haka dai na lallaba shi, ya koma harkokinsa.
Yana fita na saki gauron numfashi. A fili na ce "Oh Allah. Menene damuwata ne akan abin da zai yi a d'akin da nake shiga zullumi idan zai shiga din?"
Na kasa bawa kaina amsa.
Na kalli mashin dinsa da yake gefe wanda bai fita da shi ba.
Yana fita wasu zugar suka zo. Dan haka har kusan magariba sannan na gama saka musu.
A gurguje na yi wanka.
An fara kiran isha wacce na saka wa a karshe ta cire ta tafi. Na dinga jin da'din ku'din da na tara. Da na nutsu sai na gane, idan ban dauki matakin dai-dai to a tsakanina da Bulkachuwa ba. Asarar da zan dinga yi a kullum ba ka'dan ba ce.
Ba'kin cikin rashin bishiya ko rumfa yana cina.
*GUDUYO NA TALLATA MUKU INGANTATTUN SAIWOWI NA MUSSAMAN KUMA GANGANRIYA DAGA CHADI*
*IDAN KINA DA KANWA KI DIYAR DA ZAKI AURAR TO KI ZO KI JARRABA WADANNAN KAYAN DA BABU ASARA KO ALGUS A CIKINSU*.
*SANNAN KE MA DA KIKA KWANA BIYU A DAKI AKWAI BUKATAR KI SABUNTA KANKI*
*AKWIA SAIWOWIN SANYI*
AKWAI SAIWOWIN DAHUWAR KAZA*
*AKWAI SAIWOWIN DAHUWAR TATTABATU*
*AKWIA SAIWOWIN TSUMI*
*AKWAI PACKAGE DIN MAGANIN SANYI SADIDAN*
*AKWIA PACKAGE DIN AMARYA*
*AKWAI PACKAGE DIN MAIJEGO*
*AKWAI KAYAYYAKIN MASU INGANCI A FARASHI MAI RAHUSA*.
*AKWAI GORAN TULA SYRUP*
*AKWAI GORAN TULA FRUIT*
*INA AIKAWA KO WANNE GARI A FAD'IN TARAYYAR NIGERIA*
*, SO SU MINI MAGANA TA WANNAN LAMBAR 08032773332*
*DAN ALLAH SERIOUS BUYER'S*.
Ga shi yanzu yanayin damina ne. Idan ruwa bai zuba ba rana ake yi, idan kuma an yi ruwan ba damar zama a waje.
Ya shigo na ha'diye haushinsa na yi masa sannu. Na kawo donot da flask din shayi. Sai da muka kammala. Na dauko dukkan cinikin da na yi a ranar. Na tura gabansa.
Na sassauta murya na ce "Tijjani ka ga cinikin da na yi yau ka'dai. Na ro'ke ka daina hana ni. Na yarda kullum kana da kaso a cikin ku'din da zan samu".
Ya fusata irin sosai din nan.
Ya nuna ni da hannu.
Ya ce "Ke ce kike mutunta ku'di irin haka. Na kuma sha fa'da miki ce wa baki da kudin da zan sa ido akansu bare har ki yi mini iyashege saboda su. Ya jijjiga kai ya mike tsaye bayan ya dangwarar da kofin shayin.
"Da nasan zaki kalli idona ki yi mini irin wannan tayin na raini Billahillazi da dazu ban yarda na karbi ban hakurin ki ba. Amma shike nan. Daga yau din nan bana bu'katar ayi mini lalle da kitso a gidan nan gaba'daya ma".
Ina jin hakan na takarkare na ce "Bilhiillazi ba zai yiwu ba, komai kake ji da shi Tijjani, baka isa ka hana ni sana'ar da ka gan ni da ita ba! Duk masifar ka kuwa".
Ya murmusa ya ce "Lokacin da aka dauke ki aka ba ni babu shawarata ai ba a ce mini mata zasu dinga yi mini zarya a gida ba. Dan haka yanzu da na ga bazan iya d'auka ba, na dakatar da su".
Na sake hassala na ce "To wai dole aka yi maka ka zauna da ni?
Na ce ba na sonka, kai ma baka sona, to mu rabu mana. Mugunta ce kawai ta sanya ka ri'ke ni, kake musguna mini."
Ya ce "Shike nan bar shi a muguntar ne kawai. Sai dai ki sani na riga na samo wa kaina mafita. Ki saurari abin da zai biyo ba. Ban karbi auren ki ba sai da na kudire wa zuciyata komin rintsi bazan bari mugun halinki ya sanya na kunyata Baban Marina da Babah ba.
Ki je ki karaci diban albarkar ki. Ai Ubangijin adalci ya riga ya samar mini mafita a cikin wula'kanta ni da kike yi tun kafin a halicce ni".
Daga haka ya fice.
Gaba'daya na kasa gane manufar maganganunsa. To wacce manufar ya samo?
Na kwana ina tauna maganganun Tijjani. Zuciyata ta yi nauyi a wajen son na fahimci inda ya dosa.
Ko dokar da ya sanya mini ta hana ni sana'ata bata tokare mini wuya ba. Irin son na gane mafitar da ya samo.
Kwanaki biyun da suka biyo baya, zaman namu ya sake yin tsami bisa dalilai guda biyu. Na farko ya tire kan ra'ayinsa na kada a ayi masa lalle a cikin gidansa. Sannan ya tsiri ya yi wanka ya sheka kwalliyar da ni na koya masa yin ta. Da daddare zai dauki wankakken kaya kuma gogagge ya fesa turaren da duka gidan sai ya amsa tsabar bulbulawar da yake yi, sannan ya fice ko kallon inda nake ba zai yi ba bare ya yi mini sallama.
Ba zai dawo ba sai goman dare ta shud'e.
Wannan al'amarin ba k'aramin ci mini kwarya yake yi ba.
Na rasa inda zan tsoma raina da ba'kin cikin da Tijjani yake guma mini. Mussaman na barina a gida da daddare ni ka'dai kamar mayya.
Ranar da muka yi sati a cikin wannan halin. Na bugawa Yaya Ummi waya, ji na babu kuzari ya sanya ta dinga fa'din "Mene ne,