Showing 138001 words to 141000 words out of 184118 words
Chapter 47 - Bakar Taada Hausa Novel Complete
ne ace anji kanki?"
Ya saki ajiyar zuciyar samun nutsuwa. Ya ce *Tsautsayi ne. Zan kuma kiyaye.
Muka gama sannan muka yi haramar tafiya.
Har kofar gida ta rako mu tana sake ba ni hakuri.
A hanya kuwa shi da su Hanif suke ta hirarsu, yana ta amsa musu gwarmcin maganarsu.
Muka isa gidan. Kaca-kaca yake tabbacin bai samu nutsuwar da yake gyara shi ba.
Ya tafi masallaci sallar laasar. Ina idarwa na hau aikin gyara gidan. Ya dawo ya shiga taya ni. Cikin lokaci k'ank'ani muka kammala.
Na yi wanka, na shiga kicin na fara hidimar had'a abincin dare.
Ya fito sanye da jallabiya sai kamshi yake yi tabbacin shi ma wankan ya yi . Sannan ya yiwa yaran.
Ya shigo kicin din ya ja turmi ya zauna.
Ya zuba mini ido. Ya ce "Little ba ki huce ba ne?
Ban kalle shi ba. Na ce "Me ka ga ni?"
Murya babu amo ya ce "Ba ki dawo da walwalar ki ".
Na yi k'asa da kaina tare da ce wa "Na huce mana. Kawai zuciyata ce take ta yin wasiwasi mai yawa".
Ya mik'e da azama ya rungume ni ta bayana.
*GUDUYO NA TALLATA MUKU INGANTATTUN SAIWOWI NA MUSSAMAN KUMA GANGANRIYA DAGA CHADI*
*IDAN KINA DA KANWA KI DIYAR DA ZAKI AURAR TO KI ZO KI JARRABA WADANNAN KAYAN DA BABU ASARA KO ALGUS A CIKINSU*.
*SANNAN KE MA DA KIKA KWANA BIYU A DAKI AKWAI BUKATAR KI SABUNTA KANKI*
*AKWIA SAIWOWIN SANYI*
AKWAI SAIWOWIN DAHUWAR KAZA*
*AKWAI SAIWOWIN DAHUWAR TATTABATU*
*AKWIA SAIWOWIN TSUMI*
*AKWAI PACKAGE DIN MAGANIN SANYI SADIDAN*
*AKWIA PACKAGE DIN AMARYA*
*AKWAI PACKAGE DIN MAIJEGO*
*AKWAI KAYAYYAKIN MASU INGANCI A FARASHI MAI RAHUSA*.
*AKWAI GORAN TULA SYRUP*
*AKWAI GORAN TULA FRUIT*
*INA AIKAWA KO WANNE GARI A FAD'IN TARAYYAR NIGERIA*
*, SO SU MINI MAGANA TA WANNAN LAMBAR 08032773332*
*DAN ALLAH SERIOUS BUYER'S*.
Ya rankwafo sosai in ya dora kansa a wuyana ya sassauta murya ya ce "Bai kamata ki yi wasiwasi a kaina ba Little. Kuskure ne wanda ajizanci yake sababa shi. Ki manta wannan al'amarin. Ina cikin matsanancin damuwa da fishin ki. Pls my little angel double sorry ".
Na saki ajiyar zuciya tare da ce wa "Allah ya kiyaye na gaba"
Ya amsa da "Ameen dear. Allah ya yi miki albarka."
Ya dinga kissing d'in kunnena da wuyana da duk inda ya yi masa.
Tamkar ya jani daki. Amma kusantawor magariba ya sanya ya hakura a dole.
Da daddare yara na yin barci, ya fito da maitarsa a fili. Bai sarara mini ba sai da ya samu nutsuwar da yake so. Kalaman soyayya da na rarrashi ya dinga amayarwa. Wasu ma ni ban tab'a jinsi ba sai a ranar.
Ya jadda mini ce wa "Dukkan nasarar da ya samu tana d'amfare da irin gudunmawar da na ba shi a zamanmu. Ya sani bai manta ba, ba kuma zai mance ba.
Ni kuma na yi lamo a jikinsa na shige ya rufe ni ruf. Ina jin kalamansa suna warware dukkan damuwata.
Ina sake gasgata yana sona, so na hakika. Domin ya shayar da ni kalolin kauna masu tsayawa a rai da gangar jiki gabadaya.
Ya kaurara murya ya ce "Ki mini alkawarin baza ki sake barin gidan nan babu izinina ba. Ki mini alkawarin komin runtsi ba zaki juya mini baya, Asiya ki mini alkawarin zaki gasgata ni ko da kowa bai yarda da ni ba. Idan har kin tsaya mini zan yi ta samun cigaba a rayuwata. Amma idan kika juya mini baya ina tabbatar miki komai zai lalace mini ya cakalkale watak'ila ma na shiga rayuwar da tafi wanda na yi a baya muni!"
Ya karasa cikin matsanancin damuwa da karaya.
Tausayin sa ya baibaye ni. Na nisa na ce "Idan har ka mini alkawarin zaka kame daga kule kulen mata, zaka kiyaye dukkan iyakokin shari'a to mene ne ba zan yi maka ba Baban 2?"
Ya sake tsanta rungumar da ya yi mini.
Yana fad'in "Na gode sosai Asiyata".
Sai kawai na ji hawayensa na sauka a kan goshina.
Na shiga rudani mai yawa domin a tsawon lokacin da na shafe tare da shi ban tab'a ganin kukansa ba hana rantsuwa lokacin rikicin Rafi'a. Na ga k'walla a idonsa amma hawaye bai zuba ba . Murya na rawa na ce "mene ne?"
Shi ma da rawar murya ya ce "Haka kawai nake ganin kamar duniyata ta zo karshe. Karbar filina da kamfani ya yi, yana neman zame mini fitina. To idan ke ma zaki dinga yi mini irin wannan fishin akan sabanin ra'ayi, ki dinga zargina akan abin da baki ga ni ba. Na tabbatar wata rana za'a wayi gari ne bakin cikin duniya ya mayar da ni gawa".
Murya babu amo na ce "Da ikon Ubangiji hakan ba zata faru ba. Ba zan sake yi maka irin haka ba. Ka yi hakuri ".
Ya saki ajiyar zuciyar samun nutsuwa, domin shi din mai son na ba shi hak'uri ne ainun.
Ya sake ce wa "na sake rokon ki?"
Zuciyata na bugawa ainun na ce "Ina jin ka."
Ya ce "Dan Allah ki yi dukkan iyawar ki, kada ki bari yaran nan su tagayyara idan har mutuwa ta yi gaggawa ta sure ni".
Ai bansan yadda aka yi ba, kuka ya goce mini mai tayar da hankali domin k'warai ya gigita ni.
Maimakon ya kwantar mini da hankali sai ya sake ce wa "Na sani idan na mutu dole zaki yi aure Asiya. Domin a yanzu ne ma kika yi shekaru ashirin. Amma dan Allah, dan darajar ma'aiki ban da Jabir, ban da shi little!".
Ya fada da wani irin yanayi na tashin hankali sosai.
Kukan da na ke yi ya tsaya cak a dalilin tashin hankalin da ya jefa ni ya wuce kukan hawaye ko na baki. Sai kukan zuci da na gangar jiki. Zufa ta dinga yanko mini tamkar na yi tsere.
Na kasa ko da motsi. Tsawon lokaci muna ta fama da sake saken zuciya da fargaba.
Murya babu amo na ce "wannan ne tukuicin dawowar da na yi ko Baban 2? Haka kawai ka tayar mini da hankali. Kana nufin mutuwa zaka yi ka bar ni da k'ananun y'aya'n ka Tijjani?"
Ya ce "Jikina da zuciyata ke raya mini hakan, amma ai bani da tabbacin hakan domin gaibu ne. Fatana dai ki cigaba da zama jajirtacciya ko bayan babu ni. Akwai mata da yawa da suka sadaukar da kuruciyarsu da jin dadinsu dan inganta goben y'aya'nsu. Ki kula da su, ki saka idon a kan tarbiyarsu, idan Ubangiji ya baki tsawon rai sai suma su raine ki, su ji kan ki".
Na sake kece wa da kuka tare da ce wa "Kada ka mini haka Baban 2. Dan Allah ina son na rayu da kai. Ina son twins su girma a tsakanin uwa da uba, bana son na rasa ka. Kai nake fatan ya zame mini miji har a aljanna. Idan mutuwar zata dauke ni, to kawai ta hada ta dauke mu tare."
Da sauri ya ce "A a In sha Allah ke zaki rayu, ki zame wa y'aya'nmu bangon jingina. Me yasa ba ki gano girman kalubalen da zasu fuskanta a dalilin rashin uwa da uba ba?."
Cikin kuka sosai na ce "Allah ka jinkirta mana rayuwarmu gabadaya".
Ganin hankalina ya tashi ainun, sai ya kawar da maganar ya shiga rarrashina da tarairaya ta. Amma gabadaya hankalina bai kwanta ba. Na riga da na ankara matuka da gaske.
Washagari haka na tashi sukuku babu kuzari bare walwala. Ya yi shirin tafiya kasuwar Ilela. Zuciyata ta dinga ayyana mini na hana shi fita domin sai nake ganin tamkar ba zai dawo ba.
Ai kuwa na fasa masa kukan ba zai fita ba. Duk yadda dinga rarrashina amma ban yarda na amince zai fita ba. Kan dole ya zauna ya fasa fitar.
Ya sassauta murya ya ce "Idan Ubangiji ya so ikon sa sai na mutu a kan katifata lafiya lau ba tare da ciwon komai ba."
Ina hawaye na ce "Masifa da jafa'in kake jawo mini Tijjani Allah ya yafe maka kawai. Allah yasa kai ne zaka ga gawa ta. In kuwa ba haka ba tabbas sai ka yi mini sababin hawan jinin da zai nannad'e ni na kasa moruwa".
Ya numfasa bai ce komai ba, fitar da bai yi ba ke nan. Yaranmu suna ta kai komon farincikin ganina a tare da su. Mu kuma muna cikin wani irin yanayi mai wahalar wa.
Kwanaki biyu na rik'e Tijjani a gida. Masallaci kawai nake barinsa ya je. Mukullin motar na boye na hana shi. Na kafe sai ya canja sana'a. Da wa'azi da nasiha da lallashi ya shawo kaina ta hanyar cusa mini tauhidi tare da gasgata hukuncin Ubangiji baya sauyawa. Kawai na dinga fahimtar maganganunsa tare da zama jaruma, mai fuskantar dukkan kalubalen rayuwa da k'arfin zuciya, sai kuma na dage da addu'ar duk runtsi Ubangiji ya tsare mini imani ya kuma shirya mini zuria.
Na yarda da nasiharsa. Na ba shi mukullin motar sa.
Ranar da ya fara fita, na k'ira wayarsa tafi sau goma, ina tambayar sa inda yake.
Kwanaki suka yi ta shud'e wa ba abin da ya samu Tijjani. Sai na fara warware wa. Zullimin da nake ciki ya yi sauki. Yayin da shi kuma yake ta samun nasibi. Domin a yanzu ya bar kasuwa. Amma yana sarar kayan miya ya kai kasuwannin k'auyuka. Idan zai juyo sai ya saro abin da yake sauki a garin ya zo ya siyar a cikin gari. Kafin azahar ya dawo gida. Sai ya sake fito da dabarar kai da karbo sako(Delivery). Sosai yake samun alheri da harkar.
Ya fara tafiya Jos ya kai kayan miya da sakonnin jama'a, idan zai dawo ya sake karbo sakonni ya kuma saro dankalin turawa da su atile. Nan da nan sai al'amarin ya karbe shi. Muka canja mu da y'aya'nmu a dalilin wadatar da yake samu. Na fara murje wa, ina haske, suturu suka yawaita mini. Mussaman material din Umm Nihla mazauniyar Malaysia. Bana gajiya da siyan yadinka ta. Saboda rashin nauyinsu da kuma yadda suke shan ruwa babu kode wa. Shi kansa Tijjani yana matukar son na yi masa kwalliya da su....
Yawan fataucin da yake yi tsakanin Bauchi zuwa Jos ya sanya akai akai yake zuwa Toro. Ganin wadatar da yake ciki sai aka fara yi mana sintiri da sunan ziyara ko hutu. Wanda kafin ya shiga wannan rufin asirin ba'a cika tunawa da shi ba. Bare a taimake shi.
Nasiba ce dai bai sake yarda ta zo ba, ya yanke dukkan hulda da ita.
A wannan tsukun na fahimci al'amarin da yake zuciyar Tijjani, domin yadda yake yiwa Baban Marina hidima ko su Yaya Salisu basa yi masa hakan. Yanzu a gidanmu ana iya soya dankali ko doya. Shi da su Yaya Salisu da Yaya Rabiu suka kwaskware kofar tamu ta farfado. Baban Marina da kansa ya fada mini a waya ce wa Duk satin duniya sai Tijjani ya tura masa kudi. Ban da kayan miya da su dankali da yake kai masa babu gajiya.
Haka kuma yake yiwa mahaifiyarsa. Dada kuwa kayan shayi ne da sabulai da turare baya rabata da su.
Maimakon a yaba masa sai gabadaya gidan aka hau cece kucen ni na hana shi ya kyautata wa su Baban Tsakiyar da Baban kasuwa sosai. Tunda ai duk daya suke da Baban Marina a wajen sa. Amma suna gani za'a yi ta shiga da kayayyaki kofarsa akai akai. Amma su a leda ne kuma sai jifa jifa. Shin dan yana surukinsa ne, ko kuwa akwai wata alak'a ce da tafi tasu?"
Nazira ke tsegunta mini. Tare da bani labarin yadda Baba Maryo take cusa masa Nasiba da fad'in ai ba komai ba ne dan ya hadamu ya aura. Rabon y'aya'n da ta haifa ne ya sanya ba a yi da shi ba. Haka kuma ga rabon y'an biyu a jikin Yabi.
Dada dai bata ce wa komai a dalilin tana gudun bacin ran autarta. Yayin da Nasiba bata zafafa ba. Tabbas tana son Bulkachuwa. Idan ya nuna yana sonta a radin kansa zata amince domin ba zata zalunci kanta saboda Yabi ba. Amma ta karaya a dalilin ta fahimci shi kansa a hannun Yabin ya ke. Tunda ta dawo daga gidansa ta zauna ta yi nazari da kyau ta fahimci Yabi ta bar masa gidan ne saboda ya kai ta. Tun daga lokacin kuma bata sake ganin walwalarsa ba. Idan ta gaishe shi zai amsa. Amma ko kallon inda take baya yi, bare ya fahimci me take ciki. Ta kuma tabbatar fishin Yabi yake gudu na gaske. Ita da kanta mamakin yadda yake shiga nutsuwar sa yake idan yana gabanta. Idan kuwa ya zo Toro ta bugo masa waya gabadaya nutsuwa wa yake tamkar uwarsa ce ta masa waya. Ya dinga b'are b'are yana tambayar lafiyarta da ta tagwaye. Sannan ya bawa Dada wayar dan ya tabbatar mata a inda yake.
A kasan ranta bata ganin aibun matsananciyar soyayya da gudun zuciyar Yabi da yake yi. Domin ta tabbatar Yabi ta cancanci ya mata irin wannan soyayyar domin ta sadaukar da abubuwa da yawa saboda shi. Ta jure a lokacin da kowa yake gudunsa duk da tirsasata aka yi. Ta rufa masa asiri da sana'arta. Kenan a yanzu da ya fara samun dama, dan ya kyautata mata ba abin birge wa ya yi ba. Abin da ya kamata yake yi.
Ta sake yarda ko ya aure ta, ba zata iya da jidalin Yabi ba. Tunda a bayyane yake a hannunta yake. Kawai zaman hak'uri zata yi.
Abin da ya dame ta daya ne. Yadda mahaifiyarta ta fantsama nemo mata maganin da za'a karkato da hankalinsa kanta. Kullum a cikin bata rubutu take wanda ta tabbatar sunansa ake rubuce wa.
Tana kwance ita kad'ai a daki tana ta nazari tare da alkalancin bai kamata ta aure shi ba. Mafi muni ma ta hanyar asiri. Ta tabbatar mahaifiyarta ce ta yi sanadin raba ta da shi a dalilin ba shi da komai, kuma ba a kintse yake ba. "Yanzu kuma da ya zama mai daraja sai ki cusa masa ni a kan dole?"
Ta furta a fili ba tare da ta shirya yin hakan ba.
Kunya ta kama Nasiba. Ta ya ya mahaifiyarta zata runtse ido daga yin alkunya ga d'iyar wanta uwa daya uba daya? Ta san zumuncin zamani ya shiga tasgado mai yawa, mussaman na gidansu. Amma tana matukar kaduwa da son kai irin na gyatumarta. Har kunya ta taya ta ji a sadda ta karbo mata taimakon da aka rubuce sunan Tijjani da na uwarsa. Alhalin a sadda yake sonta akan idon uwar tasa ta wulakantasu ta hanyar ce wa d'anta bai kai a ba shi aurenta ba. Amma yanzu wai ba wanda take so ya zama surikinta sai Tijjani, mijin Yabin Baban Marina. Ta sake ce wa "wacce irin BAK'AR TA'ADA ce wannan? Wanne irin son zuciya ne ya yiwa mutanan yau katutu a zuciya?"
✍️
*Akwai kaya masu kyau a cikin farashi mai sauki*
*Saiwowin maganin sanyi*
*Saiwowin Tsumi*
*Saiwowin dahuwar kaza*
*Saiwowin dahuwar tattabaru*
*Gumba*
*Tsumin kwakwa*
*Y'aya'n gadali*
*Hadadden daka*.
*Tsugunno mai sa a matse*
*Goran tula*
*Goran tula syrup*
*Garin goran tula*.
*Maganin gyaran nono*.
*Zuma ta mussaman*.
*Tsumi*.
*Da sauran kayayyaki na mussaman da basu da illah*.
* Domin kuwa asalin Saiwowin ne da ake kawo su daga Chad*.
*Abu mai kyau shi ke siyar da kansa ku tuntube ni dan samun naku kayan cikin sauki da mututantawa. Ina aikawa ko ina a fad'in tarairaiyar Nijeriya*
*08032773332*
83&84.
Zaune nake ina duba kayan gyara da na siya a wajen Surayya Halin yau. Domin lokacin haihuwar twins a wajen ta Yaya Ummi ta siya mini kayan da suka gyara ni matuka da gaske har Baban 2 ya dinga tambabar ni na haife su kuwa?.
Tsumin kwakwa ya tayar mini da kwadayinsa da na jima ina yi. Domin dad'i gare shi. Na dauka na sha. Na tashi na je kicin na dauko gwangwanin Madara ta ruwa na fasa. Domin tunda Tijjani ya fara samun sukuni kullum sai na sha gwangwanin Madara. Ban da sauran abubuwan da suke inganta lafiyar jiki.
Na fasa na juye a kofi. Na dawo falo na bude robar koren maganin da na tabbatar da kyaunsa. Na zuba na juya na shanye. Ina hasasho subadin da zan sha yau a wajensa.
Na tattara sauran na kulle dan kada na yi over dose.
Na dauki waya na k'ira shi. Ya amsa na ce "ka taho ne?"
"Eh kina son wani abu ne?"
"Ka taho mini da dabino ko kwakwa ".
Da azama ya ce "Done my little, ban ji hayaniyar 2 ba". Na ce "gasu nan barci suka yi".
Ya ce "Da yammacin nan? Tashe su dan Allah. Bazan yarda da daddare su tisamu a gaba su hana ni hutawa ba".
Na kyalkyale da dariya. Domin nasan nufinsa.
Na mayar da robar y'aya'n gadali domin sai gobe zan ci tunda bani da kwakwa ko dabino a hannuna.
*Akwai kayan Chad masu kyau a cikin farashi mai sauki*
*Maganin sanyi*
*Saiwowin Tsumi*
*Saiwowin dahuwar kaza*
*Gumba*
*Tsumin kwakwa*
*Y'aya'n gadali*
*Hadadden daka*.
*Tsugunno mai sa a matse*
*Goran tula*
*Goran tula syrup*
*Garin goran tula*.
*Maganin gyaran nono*.
*Zuma ta mussaman*.
*Tsumi*.
*Da sauran kayayyaki na mussaman da basu da illah*. Domin kuwa asalin Saiwowin ne da ake kawo su daga Chad*.
*Abu mai kyau shi ke siyar da kansa ku tuntubi marubuciyar Halin yau dan samun naku kayan cikin sauki da mututantawa*.
*08032773332*.
Sosai muke zamana lafiya da taka tsantsan kan abin da zai janyo mana rikici. Na fahimci yajin da na yi, ya sake sawa Tijjani tsoron mu yi fada. Duk da hakan kuma wani loakcin zai fitittke ya yi mini sababin na raina shi, ko akan abu kad'an sai ya tsiri fishi yana fad'in "Tunda Babah ta bani lasisin na dinga yi masa yaji shi ke nan nake yi masa abin da nake so. Dan na ga ba shi da yadda zai yi. Idan yana irin wannan fishin, wani zubin ya bani dariya. Wani lokacin ya bani mamaki. Idan na so sai na rarrashe shi tunda shi haka yake kamar su Hanif wajen son a ritata shi, a tarairaye shi. Wanii lokacin kuwa na share shi, na fi shi fishi. Idan ya lura da hakan sai ya yi maza ya hadiye nasa fishin ya hau lallaba ni.
*Shekara daya a gaba*
Kwanci tashi tagwaye suka yi shekaru uku. Haka muke gurgura rayuwa yadda ta zo. Wataran fari, wataran baki. Zuwa lokacin sosai harkokokin Bulkachuwa suka sake mike wa. Ni kaina ina siyar da dankalin turawa da su karas da atile a cikin gida. Ba kuma k'aramin alheri nake samu ba. Tunda shine yake siyo mini babu maganar kudin kawowa. Idan na siyar na cire riba na ba shi kudin sai ya sake siyo mini wasu. A hakan har na tara jarina ba tare da