Showing 99001 words to 102000 words out of 184118 words
Chapter 34 - Bakar Taada Hausa Novel Complete
yi cikin sanyin jiki.
Sai kuma matsalar Rafi'a. Wata guda da kammala karatunta na digiri ta tattaro ta dawo gida gaba'daya.
Kusan ko yaushe a k'ofata take. Idan ina k'unshi sai ta hakince a falo da sunan kallo. Ko Tijjani ne ya dawo ba zata tashi ba, sai ma ta yi ta jansa da zancen makaranta su yi ta hirarsu. Ko idan ta ga ya fita sai ita ma ta bi shi su fita tare.
Ranar da na yi masa k'orafi ya balbale ni da sababin wai na raina shi, ban yarda da shi ba.
Na kame baki na yi shiru, kuma sai da na ba shi hakuri akan hakan.
Tunda ya ja ya tsaya ba shine yake zuwa wajenta ba, ba shi yake kiranta ba, tunda bana so ta zo mini gida to na hanata zuwa kawai.
Na rasa ta yadda zan kore ta domin dai gaskiyar magana uwarta tana mini kirki da alheri mai yawa a matsayin ta na babba. Bayan haka ita kanta Rafi'a din kirki ne da ita. Bai zame mata komai ba ta yi mini gyaran gida ba. Kawai ni yadda take shige wa Tijjani ne bana so, domin na riga da nasan shi akan lutayen mata.
Wadannan matsaloli sai suke neman sauya zaman aurenmu. Domin ni a k'arancin shekaruna dauka na yi Tijjani ne ya ki yi mini cikin kawai. Sannan yana son Rafia.
A hankali na fara janye masa, abubuwa suka fara sauya wa a tsakaninmu.
Na daina sauraronsa ko na saurare shi ma to kuwa sau daya ne shima ba cikin da'din rai ba.
Ranar da na dawo daga sunan Nasiba kuwa. Kuka na zauna na yi masa mai d'aga hankali k'warai da gaske. Ina yi ina ce wa "Akan me zaka matsa mini sai ka ta'ba ni bayan bana so, na riga na gane ba cikin nan zaka yi mini ba, dan haka na gaji da nukurkusata da kake yi babu sassauci babu kuma wani abu da zan samu."
Ya zuba mata ido yana kallon yadda take kuka bilhakki. Ya tafi tunanin shekarunta. Watan da ya shud'e ta ciki shekaru sha bakwai.
Ke nan akwai k'uruciya mai yawa a tare da ita. Bai kamata kuma ya biye mata ba, domin ya fahimci da dukkan zuciyarta take ganin shine bai mata ciki ba.
Ya numfasa ya saki gauron numfashi kafin ya ce "Asiya Allah ne fa mai bayarwa, kuma ba mantawa ya yi damu ba. Kika san tanadin da yake yi mana?"
Cikin kuka na ce "Ba wani, ni kawai ciki nake so, ai ko wacce ta haihu saboda mazansu suna sonsu, sai ni ce kawai saboda baka sona, kowa wani gani gani yake yi mini ba'a yi mini ciki ba".
Dariya ta so subuce masa, amma ya maze ya ce "Asiya zai yi wahalar gaske a samu wacce ake takarta irin yadda nake yi miki a cikinsu. Kin san da yawan yi ne sanadin samun ciki da yanzu kin haihu sau uku.
Amma shi samuwar ciki ai ikon Allah ne."
Da rawar murya na ce"Ba wani kawai dai ni ce baka so na samu ba, ga Ubaida nan yarinya da ita jibi za'a ciro mata d'a ko y'arsu, kai ma da su Nasiba ka aura ai da tuni ka yi musu.
Ina goge idona na ce "Wallahi na baka nan da wata d'aya, idan ban samu ciki ba to ba zan zauna ba".
Ya sake zuba mini ido cikin mamaki mai yawa. Ni kuwa ko d'ar ban ji ba.
Ya ha'diye komai ya ce "Shike nan Allah ka taimaki Tijjani ya yiwa Asiya Toro cikin y'an-uku".
Na yi maza na ce y'an uku tashi guda? Y'an biyu ko daya ma ya isa."
Ya fara ta'ba ni, na bige hannun na ce "Ni fa yau na gaji Wallahi".
Ya ce "To shike nan Asiya Toro Allah ya kai mu gobe, tunda ciki kike so ki sani fa babu ke babu hutu, amma na yarda ki huta yau din".
*Annur food Delicious*
*Da k'arfin zuciya da guiwa na ke muku shunen inda zaku samu kayan da na zano a kasa cikin saukakkan farashi.*
*Shaida nake yiwa kayan annur domin dadinsu da ingancinsu ya kai kurewa*
*HANZARTA ki nemi kayansu dan ki gasgata batuna*
*Garin kunun tsamiya garin danwake, garin borkono, yajin daddawa, man shanu, nikekkakiyar gyada ta kunu da ta miya*
*08039183880*
✍️
*Akwai kaya masu kyau a cikin farashi mai sauki*
*Maganin sanyi*
*Saiwowin Tsumi*
*Saiwowin dahuwar kaza*
*Saiwowin dahuwar tattabaru*
*Gumba*
*Tsumin kwakwa*
*Y'aya'n gadali*
*Hadadden daka*.
*Tsugunno mai sa a matse*
*Goran tula*
*Goran tula syrup*
*Garin goran tula*.
*Maganin gyaran nono*.
*Zuma ta mussaman*.
*Tsumi*.
*Da sauran kayayyaki na mussaman da basu da illah*.
* Domin kuwa asalin Saiwowin ne da ake kawo su daga Chad*.
*Abu mai kyau shi ke siyar da kansa ku tuntube ni dan samun naku kayan cikin sauki da mututantawa. Ina aikawa ko ina a fad'in tarairaiyar Nijeriya*
*08032773332*
*KUN TUNA MAI GYARAN GUDUYO?*
*INA NUFIN FASEELAT BABBAR DILA TA G.H.T.*
*KO WANNE NAU'IN KAYAN GHT TANA SIYAR DA SU AKAN FARASHI MAI RANGWAME*
*KAWAI KU TUNTUBE TA A WANNAN LAMBAR DAN GANIN JERIN KAYAN DA TAKE DA SU*
*TUN DAGA KAN SUPPLEMENT, SABULAI DA LIPTON*.
*MASANIYA CE AKAN KAMFANIN DOMIN TA SAMU KARRAMA WA DAGA KAMFANIN A BANA, HANZARTA KI TUNTUBETA DAN SIYA DAI DAI KO SARI.*
*IDAN KUWA KINA SON YIN RIGISTA DAN FARA KASUWANCIN KAWAI KI TUNTUBETA DAN KUWA DA KYAKKWAR ZUCIYA ZATA MU'AMALANCE KI*
*07039269802*
59&60.
Haka al'amuran suka ci gaba da gudana.
Aka ciro wa Ubaida kyakkawar jaririyarsu mai cike da koshin lafiya. Ita kam gida aka tafi da ita. Tunda bata da lafiya.
Sai da aka yi sati biyu da haihuwar sannan aka yi taron suna.
Ranar sunan na ga dukkan y'anmata da muka taso har ma da k'anwata kowa da d'a ko y'a a hannunta amma ban da ni. Na shige d'akinmu na dinga kuka. Yaya Ummi ce kawai ta gano ni. Dan kuwa ita Gwaggo ma bata dauki hakan a matsala ba ne. Yaya Ummi ce ta dinga ba ni hakuri tare da cewa gaba'daya ma auren naku wata shad'aya ne fa Yabi. Sannan shekarunki shabakwai. Ban da an miki auren wuri ai har yanzu baki isa auren ba, bare aje ga zancen haihuwa. Wadanda suka zarce shekaru goma babu haihuwa fa sai su ce da Ubangiji me? Ki shiga a hankalin ki fa".
Sai da ta shawo kaina sannan muka fita cikin jama'a.
Watanni uku bayan haihuwar Ubaida mai gidan burodi da Tijjani yake zuwa ya rasu. Magada sun yi yawa a kai dan hakan suka siyar da shi. Wanda ya siya kuwa kabila ne dan haka ya sallami galibin ma'aikatan ya debo nasa y'anuwan ya zuba.
Cikin wadanda aka sallama kuwa har da Tijjani. Ban gane aikin da burodin da yake yi rufin asiri ne mai yawa ba, sai bayan an rasa shi. Domin ba'a dauki kwanankin sati ba sai da muka ga gurbinsa. A da bamu da matsalar abin karya wa tunda burodi har yawa yake yi mana. Ga kuma donougt da ita ma bata yanke mana. Ko baki na yi zan basu. Sannan da daddare ba kasafai muke cin abinci ba, sai kawai muci da shayi mu yi kwanciyarmu.
Sannu a hankali rashin samun ku'di ya dabaibaye shi k'warai da gaske. Tunda aikin saka tiles sai an samu. Haka na satellite shima hab'o ne.
Tsawon wata biyu muna cikin wannan yanayin. Ga shi ya k'i yarda na taimake shi, tunda ni kullum kasuwancina tamkar ba iya mutane ne suke zuwa mini kitso da lalle ba. Saboda yadda Ubangiji ya ba ni jama'a.
Tunda kayan abincinmu suka k'are kullum cikin dirka mana garin rogo ko wainar fulawa yake.
Tausayi yake ba ni saboda gaba'daya ya zama desperate kullum cikin yawon neman abin da zai yi yake. Wani lokacin na ga ya fita da takardunsa, wani lokacin idan ya fita tun safe sai azahar zai dawo, haka kuma yake dawowa sai dai na gan shi da garin rogo da siga a leda. Ni kuwa sai ya bani filawa a farar leda ya ce ki yi abin da zai samu da ita, ki mini hakuri dan Allah"
Rannan na gaji da bin ra'ayinsa muna kwana da yini cikin yunwa.
Na ha'da kan ku'din da na samu na kwanaki biyu na rubuta koamai da nake bu'kata a takarda na bawa almaajirina na ce ya je ya ce nawa ne kudinsu. Jimawa ka'dan ya dawo ya ce "Wai dubu sha bakwai da dari shida".
Na kirga na ga har da canjn dubu uku ya rage mini.
Dan haka na cire canjin na ba shi ya tafi ya karbo mini.
Na duba na ga komai ya cika. Na kinkima na kai kicin na shiryasu.
Na ba shi gudar dubu akan ya siyo mini gawayi rabin buhu, da kuma danyar kubewa. Domin na tsani siyan abu dan tsurut a leda kullum. Ina da gas amma na bar shi sai iya da safe zamu dinga amfani da shi.
Ya siyo mini bushasshe kuma manya dan jos haka ma kubewar. Na ce "To je ka dawo anjima ka'dan."
A lokacin kuwa yammaci ne sosai. Dan haka na ha'da wuta na dora tuwon garin masara wanda yana cikin siyayyar da na yi d'azun.
Na gama na kwashe na mayar da miya. Magariba tana yi ina kammala wa.
Sai da na yi sallah, na yi wanka sannan almajirin ya dawo. Na zuba masa ya tafi. Sai ga Tijjani ya dawo. Ya kalle ni na ci kwalliya ko'ina kamshi ke tashi. Ya kalle ni da alamun tausayi ya ce "Sannu da gida. Ya mik'o mini ledar hannunsa wacce awara ce. Na kar'ba tare da godiya.
Na tashi na gabatar mana da abinci, na zuba mana a plate guda.
Na ce "Bismillah".
Ya girgiza kai ya ce "Na gode".
Na zuba masa ido murya na rawa na ce "Ba zaka ci ba, bayan na tabbatar da yunwa a tare da kai!
Da rauni sosai ya ce "Ni ni ne mai ciyar da ke, ba wai na zauna ki ciyar da mu ba".
Na tashi na koma kusa da shi na ru'ko dukkan hannuwansa na sassauta murya na ce "Ba ciyar da mu zan yi ba. Ubangiji zai buda maka k'ofofin da zaka samu ka sauke nauyin rik'on iyali tunda shi ya wajaba maka. Kana kuma da niyyar yi d'in. Abin da nake so ka fahimta ko aure bai ha'da mu ba, ai jini ya ha'damu. Ko ina wani gidan idan ina da ikon kula wa da iyalinka ai zan yi, bare kuma ni ce iyalin naka, to mene ne amfanin sana'ar da ka bar ni nake yi alhalin ba zata yi maka rana ba?"
Ya yi shiru bai ce komai ba, na sake sassauta murya na ce "Dan Allah ka yarje mini na yi iya abin da zan iya yi".
Ya saki gauron numfashi ya ce "Idan na amince ya tabbata dai da aka ce ke ce zaki ciyar da mu Asiya. Shike nan zan rasa yancina na mai gida, shike nan zan zama mata, ke ki zama mijin".
Ya fa'da murya na rawa ainun.
Na durk'ushe a gabansa na ce "Wallahi ba zaka zama ba. Yadda muke hakan zamu cigaba da tafiya kai ne miji. Ni ce mata, zan dinga karban umarni daga gare ka, abin da kake so hakan za'a yi.".
Ya yi shiru yana nazari bai ce komai ba.
Na matse hannunsa na ce "Pls mana" cikin sigar shagwaba.
Ya zuba mini idonsa da ya kad'a sosai ya ce "Asiya zuciyata ba zata nutsu ace kina siya mini abinci a gidan nan ba. Gara dai ki bari na dinga baki abin da aka yassare mini, idan ma zaki kara da abin da kike so to bazan hana ki ba, tunda ban wadatar da ke ba. Amma ni kada ki yi da ni. In sha Allah ko da bashi ne dai bazan kasa baki abin da zaki saka wa ba'kin salatinki ba. Sai idan kin raina".
Na kalle shi na gane da gaske yake yi.
Na yi k'asa da murya na ce "Anya kasan kalubalen da yake tare da cin bashi kuwa mussaman a waje? Kawai ka yi hakuri tunda dai Ubangiji ya baka matar da ya bata sana'ar hannu mai k'arfi. Ina fatan Ubangiji ya kawo maka aiki ko sana'ar da zaka dogara da ita."
Ya girgiza kai tabbacin bai gamsu ba.
Na ce "To shike nan ka dinga karban bashin a wajena."
Ya gyara zama ya ce "Nawa kika kashe a hidimar tuwon?"
Na ce "mu je kicin a lissafa.
Ya mike muka je. Na nuna masa komai da aka siyo wanda a k'alla zamu kai wata muna ci a talau ce.
"Nawa kika kashe a wannan siyayyar?
Na ce dubu sha bakwai da dari shida na. Sai gawayi na dubu daya."
Ya ce "To kub'ewar fa?"
Na ce "A bar wannan".
Ya girgiza kai.
Da sauri na ce "Ta naira dari ce."
Ya ce "Sha takwas da dari bakwai ke nan ko?"
Na ce "Eh" ya ce "In sha Allah zan biya ki, matu'kar ina shakar numfashi."
Muka koma falon muka ci abinci ina ta yi masa hira dan ya ware sosai.
Wannan kayan abincin da muke da shi sai ya rage masa damuwa mai yawa. Duk da hakan kuma bai yarda ya zauna a gida ba. Kullum sai ya fita. Rannan ya yi sa'a ya samu hada saltelite har gida uku. Da k'arfinsa ya dawo ya mik'o mini dubu biyar ya ce "Ga shi, na rage miki bashin ki. Ya fita ya dawo da leda mai d'auke da soyayyen kifi.
Na kar'ba tare da addu'ar Allah ya kara budi.
A wannan tsukun gaba'daya a takure nake domin maimakon na samu ninkin tattalin da yake yi mini kafin mu shiga tsananin da muke ciki. Sai ya zamana ni ce nafi rawar kai a kansa domin dai na samar masa nutsuwar shine mijin. Tunda na lura yana kame wa ne dan kada na samu dama a kansa. Na dinga mamakinsa domin gaba'daya ban yi zaton zai mini kallon zan raina shi dan ya shiga halin babu ba.
Ya takura kansa sosai, komai kaffa kaffa yake yi.
Idan na yi kamar zan yi masa magana sai na ha'diye.
Na dinga hakuri ina lallabawa ina binsa a hankali.
Hidimar da ta karu a kaina sai ya zama ina ta kokarin fa'dada kasuwancina. A dalilin an kawo wa Tijjani takardar biyan ku'din gida tun kwanakin baya.
Na fara tunanin yin Home service domin na samu na tara masa ku'din kafin lokacin da suka diba mana ya cika.
Na kalli yatsun hannuna guda biyu gold ne. Daya na wajen kwamishina ne, dayan kuwa da sana'ar tawa na siya.
Jiya na bashi daya na ce ya siyar ya biya ku'din ya ce "Ba ya so, kada na sake na siyar da kadarata akan al'amarin da ba hakkina ba ne. Idan kuma na siyar to ba zai karba ba.
Da zai fita na tambaye shi zan fita, zan je bayan layinmu. Bai hana ba.
Tunda na fita da hantsi ban dawo ba sai yamma lis tunda asabar ce ban cika samun k'unshi a ranar ba sai kitso.
Na dawo na tarar da shi a gida. Ya gyara ko ina.
A falo na tarar da shi yana kallo. Na yi masa murmushi ya mayar mini a gajarce. Ya kalle ni ya ce "Daga ina kike na ji sai k'amshin muhallibiya kike yi"
Zuciyata daya na ce "Wallahi lalle na yiwa wata babbar mace da ahalinta zasu je biki Abuja.
Na fito da kudina dubu sha biyar na ajiye masa na ce "Idan Allah ya yarda a satin nan zamu ha'da ku'din da zaka biya gidan".
Ya zuba mini ido galala sai kuma ya kad'a kansa ya ce "Babu laifi".
Ni ban kawo komai ba. Na tashi na yi kicin da nufin dora girki. Sai na tarar da ya girka ya juye a flask. Ga shi ya mayar da ruwan wanka kan gawayin. Na bu'de na ga ya yi zafi ainun. Na dauko babban flask din da nake zuba ruwan zafi na cika shi. Na ajiye sannan na juye ragowar na shiga wankan.
Sai da na shirya na ha'da Mana abincin na kai ina cewa "Yau dai ka zama Yabi, na dawo na tarar ka yi komai sannu da kokari".
Ya sake yi mini wani irin kallon da ban gane ma'anarsa ba.
Duk da dai yanzu ya canja amma ba musguna mini yake ba, kawai walwala da sukuninsa ne suka ragu, sannan yana yawan yi mini abubuwan da suke kona mini rai ta hanyar shata layi da abin hannuna.
Na kalle shi na ce "Sauko mu ci to".
Ya girgiza kai ya ce"ci, ni ba yanzu zan ci ba".
Na marairaice na ce"To zo ka dinga bani a baki na gaji sosai Wallahi".
Ya sake kafe ni da kallon da yafi wadanda ya yi mini. Bai kuma ce komai ba. Na rasa gane manufar hakan sai kawai na fashe masa da kuka mai tsananin gaske.
Ya taso ya zauna kusa da ni ya ce "Me na yi miki zaki yi mini irin wannan kukan?"
Da kuka sosai na ce "To akan me zaka dinga yi mini kallon tuhuma? Akan me ba zaka zo mu ci abinci tare ba? Na riga da na gane ka tunda ka fahimci na fara sonka shikenan ka nade kafar wando fara yi mini wula'kanci kala kala".
Ya matso jikina sosai ya kwantar da ni a kirjinsa ya ce "Da gaske kina sona Asiya?"
Na ture shi na zum'bura baki na juyar da fuska gefe.
Na kasa bu'de baki na ce uffan.
Ya saki gauron numfashi ya ce "Shikenan na daina yi miki wula'kanci, duk da nasan ba na yi din".
Da kansa ya zuba mana abincin. Lokaci zuwa lokaci kuma zai debo ya bani a baki. Ko ruwa da ya bula ledar bai sha ba, bakina ya nufa da shi. Na zuke tas na bar masa leda a hannu. Sai wani ya bu'de.
Da yake ina siyar da pure water, saboda masu zuwa lalle kawia na tsiri siyar wa kuma sai nake yin ciniki sosai.
Na yi gyatsa "Na yi hamdala. Gaba'daya sai jikina ya mutu murus gajiya ta taso mini, ba abin da nake so irin na kwanta na yi barci. Ga shi maghariba ta kawo kai.
Na kalli agogo na ga za'a kai minitina arba'in da biyar kafin a kira sallah.
Na mik'e na kwashe kwanukan, na hau zaga tsakar gida dan abincin da na ci ya dai-daita. Na koma falon na kwanta a kujera na yi daidai iskar fanka na kad'a ni. Ya taso ya fara bin gabbobina yana dannawa sannu a hankali nake jin da'di a jikina.
Ban ankara ba sai kawai ya sure ni yana cewa "mu je daki na wartsake miki gajiyar gaba'daya. Na fara shure shure shi kuma ya ri'ke ni gam. Fadi nake yi "No bazan yarda ka dora mini wata