Showing 153001 words to 156000 words out of 184118 words
Chapter 52 - Bakar Taada Hausa Novel Complete
Yabi. Ina samun nutsuwa saboda Ubangiji ya azurta ni da haihuwar ki. Da ikon Allah duk abin da kika saka a gaba na alheri sai kin ga fatahi a cikinsa. Allah ya shirya miki yaranki, Allah ya hore miki mijinki. Ya miki shamaki da dukkan abin da zai cutar da ke, ko ya gigita miki kwanciyar hankalinki".
Cikin jarumta na ce "Ameen na gode Baba".
**
Mafarkin maciji a randar Dada sai idan bata kwnata barci ba. Kan dole ta shirya ta tafi Toro, a lokacin sati biyu ya rage daurin aurensu Nasiba.
Sai didima ake yi tare da kambaba lamarin. Masu adawa da Yabi suna fad'in "Duk d'aya ne to wa za'a ki a tsakaninsu? Tare da fake wa da ce wa rabon aure ai kisa yake yi, gara a yi, kowa rabon ta zata samu".
A wannan tsukun na gasgata k'arfin jini domin hatta su Yaya Indo da suke mana yan'ubanci na gaske sun kaurace wa shiga shirgin auren ko taya masu adawa kanzagi da nuna kowa nasa ne a tsakaninmu. Kafatalin y'an k'ofarmu sun kame daga shiga cikin maganar auren gabadaya. Sun janye jikinsu sai isu isu. Ai kuwa mutanan gidan suka yi ca wajen sakin maganganun tare da ce wa "Kamar gaske. Su a tsakaninsu ma suke son ganin wani a uku shine yanzu zasu nuna mana an tab'asu? Suka dinga furzar da maganganun da su Yaya Indo suke fad'a akanmu a baya. Yaya Ummi kuwa ta k'i yarda da yadda ake son a sake gwara kansu. Tunda yawanci a kanta suke gulmar sai kuwa ni da na ke cikin rufin asiri. Suke taya masu yamididin duk abin da aka gani a jikina ni nake yiwa kaina. Da kuma ce wa duk k'afafar da nake yi bana gaban Tijjani domin har yau bai bar iskancin kule kulen mata ba.
Na ka'du k'warai da Nazira take mayar mini wadannan maganganun da ake ta fitowa da su tare da ce wa a bakin su Yaya Indo aka fara ji. Amma yanzu sun fitittke wai suna kishin kanwarsu sai ka ce gaske.
***
Babah sai dube dube take yi a tsakanin randunar Dada amma bata ga komai ba.
Ta kasa samun nutsuwa. Rashin ganin macijin, ga shi bata daina ganisa a mafarkinta ba. A yanzu al'amarin ma yafi ta'azzara ko barcin rana ta yi sai ta ga ni.
Tana zaune a gefen randar Aliyu ya k'ira ta a waya wanda a yanzu likita ne a F.M.C Azare.
Cikin rauni ya ce "Babah kina yawaita addu'a kuwa? Tunda kika fad'a mini auren Yaya Tijjani da yarinyar nan ban sake samun nutsuwa ba. Anya kuwa! Ke ce da kanki kika mara bayan irin wannan kwamacalar a zuria guda? Duk matan duniya a rasa wacce zai aura sai wannan abar da aka tozarta ki saboda ita?"
Ta kasa ce wa komai a dalilin yadda take jin an danne zuciyarta. Ga kuma sanyin da yake bin zuciyarta da gangar jikinta gabad'aya.
Ya numfasa ya ce "Ki tsananta addu'ar tsari. Ina yawan mafarkin wani abu kamar tulu ya danne ki. Sannan a k'ofar Dada nake ganin abun. Na kasa gane mene ne shi."
Jikinta ya sab'e da rawa. A rarrabe ta ce "ko randa ka ke ga ni?"
Kai tsaye ya ce "Abu dai da ake zuba ruwa. Amma ba randa ba ce".
Ta ce "Ai kuwa nima kullum sai na ga ni duk yadda aka yi akwsi wani abu a randar nan."
Ta katse wayar, ta zabura ta mike ta dauko tabarya.
Ta yi a'uziya, tare da ce wa "Innahu Sulaimanu wa Innahu Bismillahir rahamanin Rahim".
Ta kuwa fasa gindimemiyar randar da tashi ta yi ta ganta a wajen.
Dada ta fashe da kuka tana ce wa "Hauwa kika fasa mini randa ta. Kinsan ke ma kanki tare da aba ta kika gan ni. Kwanaki biyu tak a duniya Malam ya siyo mini ita tare da katangar wankan jegon ki. Amma yau kika fasa mini da gangan?".
Ita kuwa tunda ta fasa gumi yake yanko mata. Wani irin abu tamkar kiyashi take jin yana sauka daga kanta. Bakinta ya yi nauyi ainun. Daidai lokacin da Innarsu Ubaida ta shigo yiwa Dada sallama zata gidan suna.
Tana ganin ruwa ya jik'a tsakar gidan ga fasasshiyar randa ta hau jaje tana ce wa "Yanzu randar nan mai kafirin sanyi yau ta hadu da ajalinta?"
Da kuka Dada ta ce "Eh kuma kisan wulakanci da rainin wayo a hadu da shi. Ta ajiye ledar kayanta, ta shiga kwashe rugurguzun randar. A nan ta ga k'atuwar laya.
A tsorace ta ce "Dada a 'kona wannan ko ta tsari ce?"
Murya babu amo ta ce "Jefa ta a wuta bansan ko ta mece ce ba. Gidan nan kam ai tuni Malam ya kafe shi. Ba dai mugu ya ga kofar shigowa ba.
Ai kuwa ana kona layar Baba ta ji nauyin da zuciyarta ta yi ta ware. Sanyin da yake ratsa ta na tsoro da zullimin yin jayayaya ta ji duk ya gudu. Ta dinga Hamdala. A zuciyarta kuwa sai gasgata surkulle a ka yi mata ita kanta.
A haka Tijjani suka shigo tare da Nasiba asibiti suka je yin gwaji.
Bin su kawai take yi da ido. Bak'inta sai ambaton "Hasbunallahu wa ni'imal wakil yake yi.
Zufa kuma bata fasa feso mata ba. Gabadaya ta shiga alhinin BAK'AR TA'ADAR da y'ar uwarta shakikiya ta aikata a dalilin son kai da na zuciya.
Ta zuba ido tana nazarin Tijjani. Gabadaya ya kasa sukuni. Idonsa ya kad'a tamkar gauta. Shima sai zufar yake yi. Ya gaishe ta a sanyaye. Ta amsa masa murya babu amo domin gabad'aya ta duniyata ta yi mata tsanani.
Jira take ta ji ya yi sallama ko ta fita. Amma yana zaune, duk da bai sake Bude baki ya yi magana ba.
Duk takalarsa da magana da Dada take yi.
*Annur food Delicious*
*Da k'arfin zuciya da guiwa na ke muku shunen inda zaku samu kayan da na zano a kasa cikin saukakkan farashi.*
*Shaida nake yiwa kayan annur domin dadinsu da ingancinsu ya kai kurewa*
*HANZARTA ki nemi kayansu dan ki gasgata batuna*
*Garin kunun tsamiya garin danwake, garin borkono, yajin daddawa, man shanu, nikekkakiyar gyada ta kunu da ta miya*
*08039183880*
Ya dai gaishe ta a gajarce.
Tsawon lokaci yana zaune. Rigarsa ta jike ta gaba saboda yadda zurlfa take keto masa tamkar mai hadiyar kunama.
Fiye da shudewar mintina talatin yana zaune ba ya um ba ya um um. Gabadaya Babah ta shafa'a da miyar da take yi wa Dada.
Sai tashin kauri suka ji a hancinansu. Da azama ta yunkura ta sauke. Sannan ta janye wutar ta kashe.
A tausashe ta ce "Dada me za'a d'ora kuma?"
Cikin bagararwa Dadan ta ce "Kashe kawai."
Domin bata sakar mata fuska a dalilin tana taya autarta Maryo fishin cin mutuncin da suke k'irarin ta yi mata da ta je wajenta takanas.
Ta fito da garwashin. Ta kashe sannan ta yayyafa ruwa a murhun ta kashe shi gabad'aya.
Ta dawo ta zauna. Sannu a hankali Tijjani ya fara dawowa cikin nutsuwarsa. Gumin da yake yi, ya fara tsane wa. Mintina kad'an ya mik'e ya ce "Zan tafi. Babah yaushe zaki koma?"
Da mamaki ta ce "Tukunna."
Da hanzari ta fice yana fad'in ",Na tafi Dada".
Bai ko bi takan Nasiba ba, bare ya yi mata sallama.
Babah ta kasa gane al'amarin domin tamkar mai jinnu haka yake canjawa. Ta hakura ta kudiri aniyar tsananta addu'a domin ta yi imanin Ubangiji ba zai juyar da addu'ar ta ba.
Sannu a hankali kwanaki suna ta shude wa har ya zama saura kwanaki goma auren da ake ta cece kuce a kansa.
Lefe ne kawai ba a kai ba, an yanke shawarar idan ta je gidansa ya bata domin zuciyoyi sun kai kololuwa wajen fusata.
*
Da safe bayan ya tafi da yara makaranta, shi kuma ya wuce Dass. Ina zaune a falo ni kad'ai, kuka kawai nake yi, irin kukan nan da yake zuwa ko da baka so ba. Gabad'aya duniyar ta mini zafi. Idan na tuna saura kwanaki 'kalilan na fara raba Bulkachuwa da Nasiba sai na ji ina fatan mutuwa ta dauke ni kawai.
Na kifa kai a hannun kujera ina kuka tamkar mai wake, domin bilhakki na Bude baki nake yi.
Ba zato waya ta hau kuwwa. Na mika hannu a dalilin Gwaggo kawai na saka taken da yake tashi.
Sai da na yi jarumtar shanye kukan sannan na dauka.
Murya ta kawai ta ji. Ta tausasa harshe ta ce "Kuka kike yi ne Yabi?"
Haka kawai ta fad'a na rushe da kuka mai tsananin gaske.
Cikin kuka sosai na ce "Gwoggo ba zan iya ba, zuciyata na mini ciwo, tana zafi mai radadi."
Ta numfasa ta ce ",Zaki iya mana. Ai ba a kanki aka fara yin kishiya ba, ba kuma za'a kare a kanki ba".
Da rawar murya na ce "Amma dai kishiya irin tawa Gwaggo zan zama cikin mutane kad'an da aka yiwa irin ta. Mena yiwa Tijjani da zai mini irin wannan cin mutuncin a rayuwata?"
Da taushi sosai ta ce "Nutsu ki ji ni! Shawara zan ba ki, ba umarni ba, kinsan umarni wajibi ne ki mini biyayya. Ita kuwa shawara sai kin so za ki bi. Amma idan kika bi zai fi miki alheri fiye da barin."
Ta nisa tare da ce wa "Duk runtsi kada ki ce mijinki ya sake ki matukar bai keta haddi da alfarmar shari'a ko ta aure ba. Sannan ki yi dukkan iyawar ki, kada ki nuna damuwa ko gazawarki a gaban mahaifin ki Yabi. Ya damu da halin da kike ciki. Ki daure, ba abin da ba zai wuce ba, sai ikon Allah".
Na yi shiru illah kukan da nake yi mata tamkar zan shid'e. Cikin jarumta ainun ta ce "Allah ya sassauta miki, ba komai kin ji. To ban da ma kin saka damuwa a ranki ai bai kamata al'amarin duniya ya susuta ki irin haka ba Yabi. Kinsan kalubalen da yake gaban ki kuwa?
Kwanciyar kabari kad'ai da muna saka ta a gabanmu da bamu bari kalubalen duniya ya kidima mu ya shagaltar da mu yiwa kanmu tanadin kwanciyar da Ubangiji kad'ai yasan adadin tsayin ta ba.
Me yasa kishi ya ke sawa mu manta Annabi ya ce mu yawaita sadaka, sallah da istigifari. Domin ya hango mataye da yawa yan'wuta ne. Kuma tsananta kishi alamu ne, na mace ta barranta kanta daga ayar da Ubangiji ya saukar. Wacce kuwa ta barranta daga imani da ayar Allah. La budda tana cikin hatsarin kafirta matukar bata gaggauta tuba tare da yin hak'uri cikin hukuncin da Ubangiji ya halasta ba."
Tsikar jikina ta zuba k'warai da gaske. Na sassauta kukan da nake yi. Ta sake sassauta wa ta ce "Ki yawaita karatun kura'ani domin karanta shi kad'ai yana wanke tsatsar zuciya. Ki yawaita sallah. Ki rungumi y'aya'nki da sana'ar ki. Miji kuwa kada ki zalunce shi, kada ki tauye shi, kada ki hana shi samun nutsuwa da ke ko a gidansa. Illah iyaka ki sassauta zazzafar soyayyar da zata saka ki halaka, ki kuma halaka shi".
Na numfasa tare da ajiyar zuciya mai nauyi na ce "To"
Ta shiga jero mini albarka. Ta ce "Idan akwai abin da yafi albarka da yafiyar uwa na roki Ubangiji ya yi miki da ke da zuriarki. Idan har Ubangiji baya juyar da addu'ar uwa akan d'anta , to alafamar ma'aiki ba zaki wulakanta a wannan duniyar ba. Duk inda rayuwa zata kai ki, komin tsanani zaki zama cikin rufin asiri mai yawa. Da ikon Allah wani mahaluki ba zai ga gazawar ki ba Yabi".
Da rawar murya na ce "Na gode Gwaggo! Allah ya kara miki lafiya da nisan kwana mai albarka".
Na jiyo ajiyar zuciyarra alamun ta samu nutsuwa da yadda na karbi ban hak'uriinta. Ta ce "Ameen, ina tagwaye?"
Na ce "suna makaranta".
"To ke me kike yi yanzu?"
Ta tambayar cike da soyayya mai yawa.
A hankali na ce "A zaune kawai nake Gwaggo ".
"Tashi ki yi nafila, ki daina bari wannan lokacin mai tsada na wuce ki, baki yi salatul duha ba. Kinsan duk abin da Ubangiji ya rantse da shi mai falala ne, mai daraja ne. Allah ya ce "Wad Duha!
Lalle ki yawaita neman gafara da rahamar Allah a wannan lokacin, Ubangiji baya juyar da addu'ar da aka yi ta a wannan sa'ar sai dai jinkiri, ko ya mussnya maka fiye da abin da ka roka alheri".
Na ce "To!Da budaddiyar murya.
Ina jin soyayyar Gwaggo na sake tunbatsa a dukkan sassan jikina. Kwalla ta zubo mini wacce bata ciwo ba ce, ta tausayinta ne, tare da tausayin wacce duk bata girma da uwa mahaifiya ba. Tabbas soyayyar uwa ita ce mafi kololuwa a wannan duniyar. Muka yi sallama na tashi na dauro alwallah, na yi walaha. Akan sallayar barci ya sure ni, irin wanda na jima ban samu yin sa ba.
Akai Babah take yi mini waya, tana tambayar lafiyata da lafiyar yara. Na dinga mamakin yadda ta sauko. Na sani tana sona. Amma a kwanakin baya gabadaya ta canja mini. Yanzu kuma ta dawo mini Babah tawa Mai kaunata. Na dinga mamakin haka, da na ga kaina zai dauki caji Sau kawai nayi Hamdala a raiana tare da rok'on Ubangiji ya sake tsare mu daga sharrin masu tofi a cikin kulle kulle.
Da daddare muna kwance a dakinsa yara suna dakinsu da yake cikin falona sun yi barci.
Dukkanmu kowa tunanin zuci yake yi.
Ba abin da nake so irin na fice na bar gidan Tijjani. Tufka da warwara kawai nake yi. Maganganun Gwaggo sun yi matukar karya lagona. Domin a da na kudire wa raina daga ranar da ya shiga dakin Nasiba ya kwana da ita. Tabbas washegari zan bar shi, bari na har abada tunda nasan Baban Marina zai bani masauki tare da kyakkwar mu'amala a tsakaninmu.
Amma yanzu Gwaggo ta mini tilas din cigaba da zama ta hanyar rarrashi da dabara.
Na nisa na saki ajiyar zuciya.
Daidai lokacin ya ce "Sannu Asiya!
Ban kula shi ba, ya ruko ni, na yi bakam tamkar mai barci.
A sanyaye ya ce "Zullimi ne yake kama ni from no where! Samar mini da nutsuwa pls. Dan Allah bude baki ki fad'a mini wata kalma da zan samu sassauci a zuciyata. Ina daf da tarwatse wa Asiya".
Na ja tsaki mai tsananin gaske tare da ce wa "Tsuntsun da ya ja ruwa".
Ya sake rik'e ni ainun. Ya kasa ce wa kanzil. Ajiyar zuciya kawai yake yi. Murya babu amo ya ce "Idan na mutu Asiya dan Allah kada laifina ya shafi twins. Ni kaina bana gane kaina a wasu lokuta, kin ga da hantsi ko yamma sai na ji tamkar ana hura mini huta a kirjina.
Da zarar wani aka jima kuma sai na ji duk yadda aka azalzale ni na je Toro sai kuma na ji ke nake son na dawo ma ga ni. Ko dai na haukace ne Asiya?"
Da k'arfi sosai na ce "Tunda har kana banbance wasu alamuran da hamkalinka sarai. Kuma ina nan akan bakana, ba zan zauna da kai ba Bulkachuwa. Ana kawo maka Nasiba ka tabbatar na hak'ura da kai".
Jikinsa ya dauki rawa. Ya ce "Bazan iya rabuwa da ke ba. Haka kuma idan ban aure ta ba, bazan tab'a samun nutsuwa ba. Ki taimake ni mana".
Na ce "zaka ga taimako ganin idon ka. Na rantse maka duk wani sababin duniya ka shiryawa ganinsa. Hala dai ka manta Yabin marina ne Tijjani?".
Ga mamakina bai iya taso mini da masifar sa ba. Gabadaya jikinsa ya sake sosai.
Washagari na tashi da bala'i ko kallon inda yake ban yi ba. Na yarda da zancen Gwoggo. Amma bazan iya samar masa da nutsuwar da ake so ba.
Ya je can ya k'arata da dibar albarkar sa, shi da masu goya masa baya.
A wannan safiyar ya mini magana yafi sau goma ban kula shi ba. Na ki yin girki. Shi kuma ba shi da kuzarin da zai yi. Gabadaya ya koma Tijjanin farkon aurenmu. Ba na yanzu da yake masife ni a dalilin ina adawa da k'arin aurensa.
Ya kai ya kawo a tsakanin dakinsa da nawa. Ya kasa fita bare na samu na d'an sarara. Tunda gabadaya haushinnsa nake ji mai kama da tsana.
Sallah kawai yake fita. Da k'yar ya lallaba ya tafi dauko su Hanif.
Da gudu suka shigo. Na yi maza na hadiye damuwar da nake ciki na shiga yi musu oyoyo tare da murmushin yak'e.
Na dora musu indomie, bayan na juye musu ruwan wanka. Na kammala yi musu wanka, suka yi sallah.
Sannan na juyo mana indomie muka fara ci da su.
Hanif ya ce "Baban 2 sauko mu ci".
Hamim ya ce "Ba shi da lafiya ai marar lafiya ba ya cin abinci"
Takaici ya shake Bulkachuwa.
Ya daidai ta zamansa ya ce "Hamim baka tausayina ko kad'an?. Zaka ga tsiya, daga yau Hanif zan dinga siyo wa abina tunda kai uwarka kake so kawai".
Da yake mai kwadayi ne sai ya marairaice ya ce "Na daina Baban 2 sauko mu ci to."
Bai sauko ba, ya koma ya zauna. Ba tare da ya sake ce wa komai ba.
Muka kammala da kansa ya saka musu yunifom din islmamiya ya rakasu waje ya dawo.
Ya zauna daf da ni ya ce "Asiya Tsakanin ki da mai rumfa me ya hana ki daukar ciki?"
Na hassalo na ce "Saboda na gama haihuwar da kai, sai da wani".
Ai kuwa ina rufe baki ya cakume ni yana kokarin murde mini baki.
Na dinga zille wa, ina ture shi. Maimakon ya bar ni tunda ya ga kuka nake yi sosai, duk da bai mini komai ba, kuka nake na takaicinsa da na aurensa.
Amma bawan Allah bai yarda ya kyale ni ba. Ya sure ni ya yi dakina da ni. Sai da ya yi abin da yake so. Ya tara mini gajiya ya ce "Ya kika ji? Kin hana ni abinci, amma kin dafa muku ke da y'aya'n ki, kun ci. Sai kuma na zarta ki k'arfi da kuzari."
Na ja tsaki na juya masa baya, bayan na ja mayafi na lullube jikina.
Da daddare ya fita ya siyo tsire mai yawa. Ya dafa shayi ya kawo falo.
Ya juye naman a plate ya ce mu sauko mu ci.
Shi da yaran suka ci. Ni kuwa ko sha'awar ci ban ji ba, duk da yadda k'amshin ya cika wajen gabad'aya.
Washagari har wajen tara yana gida kamar ba zai fita ba. Kamar zan masa magana a dalilin yadda ya bani tausayi, amma da zarar na tuna ba janye wa zai yi ya fasa auren Nasiba ba, sai na ji tsanarsa na sake darsuwa mini.
Yana zaune sai waya ake yi masa babu kakkautawa. Kan dole ya