Showing 165001 words to 168000 words out of 184118 words

Chapter 56 - Bakar Taada Hausa Novel Complete

zurfafa karatu ba tare da aure ba a gidanmu. Sun kammala sakandire babu samarin aure. Hakan ya sanya Jabir samowa kannensa gurbin karatu a inda yake koyarwa. Gabadaya mun tafi a cewa iyayensa suka hana ya had'a da ita. Hakan da muka gani ya sanya ni da su Yaya Salisu muka yi kundubalar saka Iklima a Health Technology Azare.
A tsaye take cak, doguwa mai cukar halitta kuma fara tas. Na tabbatar ba zai tankwabe ta ba, amma ina jin tsoron na furta.
Dan haka sai na tsiri gayyato ta hutu a karshen watan da na tabbatar yana yi mana jele. Akai akai suke haduwa kuwa. Su yi ta cakar juna tunda shi ma mai zolaya ne. Ni kuwa na dinga fad'in "um um fa Yaya Aliyu kada fa reshe ya juye da mujiya."
Wani lokacin ya yi dariya ya waske, wani lokacin kuma ya ce "Ba Wani reshe da zai juye, yarinya kankanuwa, raini dai nake son jawo masa.
Baba kuwa idan ta ji ya ce haka sai ta ce "Saboda ka kallafawa ranka son ka auri sa'aninka. Ban da haka ai itacw daidai da kai ".
A duk sadda Babah ta fad'i hakan dad'i ne yake matukar kama ni. Ina ganin nasara a kudirina.
Matukar yana gidan ita zan saka ta yi masa girki, ta dafa masa zobo. Wani lokacin ya yi godiya ya kwashi girki. Wani lokacin ya ce "Tunda na zama matar yayansa na ture girme mini da ya yi, nake mu'amalantarsa a matsayin k'anina. Ban da haka me yake hana ni na yi masa hidima da kaina sai na saka yarinya ta yi masa."
Na yi dariya na ce "Yaya Aliyu ko a lahira wani na cin arzkin wani ai"
Ba'a d'auki lokaci mai yawa ba ya fara fad'awa tarkonmu. Domin idan ya zo bai ganta ba, ya dinga tambayar me ya hana ta zuwa. Ko ba hutu suke yi ba, da sauran tambayoyi. Da na fahimci hakan kuwa sai na dakatar da zuwan nata. Domin so nake ya taka ya neme ta a inda take ba wai sai ya ganta dan ya zo ba.
Ilai kuwa wanne tudu wanne gangare ya silala yake zuwa daga haka har suka had'a kansu.
Tunda aka garkame Tijjani ban yi farin ciki har zuciyata ba sai akan wannan al'amarin. Domin dai Na tabbatar Aliyu mutumin kirki ne. Sannan Babah uwace ta gari bayan haka Ikilima zata auri mai rufin asiri. Zamu sake zargowa k'ofarmu wani hasken.
Bugu da kari y'aya'nmu zasu kasance cikinsu guda. Tunda shi da Tijjani daya ne, haka ni da ita.
Da maganar ta fasu a gidan Marina a lokacin da iyayensa suka je nema amsa aurenta. Ba abin da ba'a ce ba. Bak'in ciki muraran har ce wa aka yi ai k'aramin likita ne, wasu kuwa cewa suka yi ba ma likita ba ne. Malamin tsafta ne. Shi dai Baban Marina ya ce ya basu. Mu kuma dukkanin y'aya'n sa muka goyi bayan al'amarin. Aka saka aure idan ta kammala makaratan da wata daya, watanni biyar masu zuwa.
**
Alhaji Auta yana zaune al'amarin duniya ya sake damalmale masa. Gabadaya kasuwa ta juya masa baya fiye da bara. Fatan da yake yi akan kamfani ya kyamaci filin Tijjani saboda an kama shi da laifi bai ci ba. Har asiri yake nema akan su saki filin amma shiru. Su kuwa kamfani sunce riba suke nema. A wajen suke samun gamsuwa, babu ruwansu da laifin Tijjani. Idna lokacin da zasu biya ya yi, zasu tuntubi iyalinsa.
Ya rasa inda zai saka ransa. Jiya aoa kama babban dansa a cikin sahun y'an kidnaffing.
Dazu kuma k'aramin dansa aka kama shi da yana yuwa yarinya yar shekaru uku lalata a cikin gidansa. Gabadaya kwanciyar hankali da nutsuwa ta yi masa tutsu. Ya rame, ya zama tamkar mai ciwon sida, tsufa ya keto masa na ban mamaki.
Yana kishingide amma damuwa ta yi masa k'awanya. Wai shine naira dubu take yi masa wahalar rik'e wa?. Zullimi ya kama shi, idan akwai Bakar Taadar da ya yi ta dame shi bata wuce had'a kai da aka yi da shi wajen yiwa dan amininsa kazafin da yake kulle tsawon shekara guda ba. Ya yi shiru yana tuna irin yadda Tijjani yake zuwa yana gaishe shi cikin girmamawa. Akai akai yake yi masa alheri a matsayinsa na aminin ubansa kuma ubangidansa a kasuwa. Amma shaid'an da hassada suka saka ya jagoranci zaluncin da aka yi masa.
Kuka shabe shabe da hawaye. Ya rasa ta inda zai warware wannan k'ullin da suka yi.
Kan dole ya kira diaya abokin sharrin nasa, wanda yaro ne a kansa dan ba zai girme wa Bulkachuwa ba. Ya dauka murya a shak'e ya ce "Alhaji kana mini waya da ta wuce kaidar hankali gaskiyar magana na ke fad'a maka. Nima nema nake idan zan samu, ka fitine ni da bani bani gaskiya".
Da zullimi ya ce "Ba rokon zan yi ba Haladu! Maganar Tijjani zan yi maka. Gaskiya na yi abin da ya sha mini kai. A harzuke ya ce "To ni me zan yi maka? Ina ce Kai ka kawo shawarar, Kai ka kitsa yadda za'a yi? Ni kawai na karba a hannunsa tare da bawa haro ya ba shi. Hatta lambar wayar da aka kira shi, kai ka siya tun kuma a ranar ka taune shi. Kai ka yiwa Yan sandar hanya shunensa tare da bada lambar motarsa. Kaine zaka yi dakon zunubin ka. Idan ka yi kuskuren saka ni a ciki kuwa Wallahi sai na bata maka suna a idon duniya. Sannan sai na lahanta ka."
Kuka wiwi ta k'wace wa Alhaji Auta tamkar mace.
Ta ya ya zai kubutar da Tijjani?

***
Yini na yi ina yiwa wata hamshakiyar Hajiya kunshi ita da mukarrabanta. Da zata tafi ta ajiye mini kudi a envelope. Ga mamakina da na bude dubu hamsin na gani a ciki. Duk da sunzo da yawa sosai. Amma tabbas kudina bai kai haka ba. Rub'anya mini ta yi. Ban sani ba ko dan na yi jarumtar yi musu jollof din taliya mai dad'i ne. Na kuma baibaye su da pure water mai sayi tunda Ina siyarwa.
Na lura ta ji dad'in yadda na yi musu, sannan ta yaba da kunshin da na yarfawa kakkaurar k'afarta fara tas.
Cikin hira nake fad'a mata na iya kwalliya ma sai dai nafi bada k'arfi a lalle da kitso.
Kwanaki biyu da tafiyar ta sai ga waya ta k'ira ni akan wani satin zan je gidan gwamnati na yiwa mai dakin gwamna kunshi zata je bikin d'iyar gwamnan Jigawa.
Jikina ya sab'e da rawa. Ni Yabi zan je government house a sanadin sana'a ta?
A fili na ce "Alhamdulillah! Ubangiji ka bani damar da zan yi amafani da ita na fito da Baban 2. Allah ka yi alkawarin taimakon wanda aka zalunce shi. Ubangiji ka shiga lamarin Tijjani."
Na zauna kusa da Babah ina fad'a mata. Ta yi farinciki sosai.
Na ce "Idan mun je ganinsa zan fad'a masa, idan bai amince ba zan hak'ura, tunda nasan baya son na dinga zuwa gidajen mutane".
Ta zuba mini ido ta ce "Allah ya yi miki albarka, Ubangiji ya kawo mana karshen ibtilain nan. Allah ya dawo da mijin ki, zaman zai yi miki yawa babu miji a tare da ke."
Sai kawai ta fashe da kuka sosai. Da rawar murya nake bata hak'uri. Ina ce wa "Zan iya Babah! Zan jira shi, da ikon Allah zai dawo a kusa ma".
**
Muna ta shirin tafiya dubo Baban 2 a dalilin a irin wannan ranar ta asabar din k'arshen ko wanne wata muke zuwa duba shi, tare da kai masa kayan shopping tamkar na dan makarantar kwana.
Ni nake had'a masa wannan kayan. Kudin lallena da kitso suna tafiya ne a hidimarsa da ta gidanmu domin Yaya Aliyu ne yake rik'e da mu. Daidai da pencir ban san na siyawa su Hanif ba. A yadda na taso a irin gidanmu da babu tausayi da tallafawa na k'asa ban yi zaton Aliyu zai yiwa Bulkachuwa irin wannan zumuncin ba. Na sani hidimar kayan abincinmu da baya mantawa akwai alfarmar mahaifiyarsu a tare da mu. Amma yadda baya mance wa da y'aya'n Tijjani na gamsu ko Babah bata tare da mu zai yi iyakacin kokarinsa.
Da na fahimci basu mayar da hankali wajen kai wa Tijjani kayan ciye ciye ba. Ni kuwa sai na mayar da hankali, domin shopping nake yi masa mai sunan shopping. Hatta kifin gwangwani ina siya masa fiye da dozin guda duk wata. Kayan shayi da su conflakes kam ba'a maganarsu. Babah har fad'i take wai kayan suna yin yawa. Biskit irin masu dadin nan kullum na yi lalle sai na siya, kafin lokacin da zamu je, sai na yara masu yawan gaske. Sannan bana raba shi da cincin da cake. Kullum fes muke ganinsa. Illa duhu da ya yi. Amma da dukkan zuciyarsa ya karbi kaddarar da ta fad'o masa. Da wuri muke tafiya, da k'atuwar tabarmarmu. Tunda Yaya Ammar yana cikin manyan gandorurobobin kurkun bamu da matsalar komai. Domin yini muke sai yamma lis muke dawowa.
Muna zaune mun gama cin abinci. Ya kalle ni ya ce "Baba lafiya bata zo ba yau?"
Na yi murmushi na ce "Ta ce wai takuramu take yi, ba zata zo ba sai wani zuwan".
Murya babu amo ya ce "Da ta zo abin ta."
"Ni ma hakan na ce mata Wallahi".
Ya kalli yaran suna can nesa damu suna kallon bishiyar mangwaro da y'aya'n suka sauko kasa kasa ana iya mika hannu a tsinko.
Ya kankance murya ya ce "Little kina kewata ko?"
Na yi k'asa da kai, idona ya cicciko domin babu yadda za'a yi mu zo bai mini wannan tambayar ba. Na fahimci ita ce tafi damunsa. Na kalle shi na ce "Ina kewar ka sosai Baban 2. Kullum dare idan na kalli inda kake kwanciya sai na jika filo da hawaye! Amma ina karfafa kaina guiwar cewa tunda muna shakar numfashi daya a wannan duniyar akwai lokacin da zai zo da zaka dawo cikinmu mu cigaba da rayuwa. Ina kuma da tabbacin rayuwar da zamu yi zata Fi wacce muka yi a baya nutsuwa da kwanciyar hankali. Yaya Aliyu yana matukar kokari akan gidanka. Su Yaya Salisu da su Ammar suna taimaka, bamu da matsalar komai sai rashin ka."
Ya ce "Ke Baki fad'o naki k'ok'arin ba little ".
Na ce "Ka sha fad'a mini, ni kake da tabbacin ba zan gaji da hidimar y'aya'nka ba. So nake ka gane ba y'aya'nka ba kawai kai kanka da mahaifiyarka ba zan gaji da hidimar ku ba, muddin ina numfashi."
Ya kasa magana. Sai can ya nisa ya ce "Ina son ki sosai little. Ina rok'on Ubangiji ya taya ni son ki, ya k'ara miki hak'uri da jarumta".
Cikin rauni na ce "Ameen" domin ya yi matukar ba ni tausayi.
Ya saki ajiyar zuciya ya ce "jiya shekara ta d'aya a nan. Tunanin ki kad'ai yasa nake ganin na dade. Amma ban da hakan ba k'aramin gata aka yi mini ba. Domin tunda nake ban tab'a samun damar da nake yin ibada nake ambaton Ubangiji irin a wannan lokacin ba. Na gamsu akwia hikimar Ubangiji ta sakaye ni a nan. Ba ni kaina ba, ko ke addu'ar da nake yi miki little ta ishe ki, bare kuma y'aya'n ki. Shi yasa ban damu sosai ba, da aka kasa fitar da ni".
Na ce "Allah ya karba. Ina kuma ganin tasirin addu'ar ka garemu domin bamu tozarta ba Baban 2."
Ya ce "Ki tsananta addu'ar nan ta*RABBI INNI LIMA ANZALTA ILAIYYA MIN KHAIRUN FAQIRUN.* Kullum ina fad'a miki tasirinta mai yawa ne".
Na zuba masa ido, shi ma ya zuba mini tsawon lokaci muna kallon juna, idanuwanmu cike da k'walla.
Ya yi k'arfin halin danne nasa hawayen ya hadiye. Ya ce "So nake na gan ki da ciki Little"
Nasan yadda kike son haihuwa. Na kuma tabbatar renon ciki da hidimar bebi zaisa ba zaki ga nisan zaman da zan yi ba".
Na ce "Ta ya ya hakan zata kasance Baban 2?"
Domin ni kaina idan har zan samu cikin zan yi matukar farinciki mai yawa.
Ya ce "Kina so?"
Na daga kaina da sauri amma ban yarda na d'ago kaina ba. Domin haka kawai na ji kunya ta rufe ni.
Ya ce "Shike nan zan roki arzikin Ammar ko zai mini alfarma".
Na ce "Me zaka ce masa?"
Ya ce "Zaki ji daga baya."
Na d'ago na ce "Amma Baban 2 idan na samu ya bare kada ka ce na zubar maka fa, nasan halin ka".
Ya dan murmusa ya ce "Ai ina fad'a miki ne dan na rama rikici da tashin hankalin da kika dinga yi mini kafin ki samu cikin twins".
Na rufe idanuwana ina dariya sosai".
Na ce "wanccan satin dai aka daura auren Nasiba".
Ya ja tsaki ya ce "Ammar ya fad'a mini. Ya isa haka kuma".
Na yi maza na sauya maganar da ce wa "Ka saurare ni da kyau Baban 2 ".
Ya ce "Ina jin ki".
Na ce "Jiya wata baiwar Allah ta mini waya akan gobe suna son na je gidan gwamnati na yiwa mai dakin gwamna kunshi. Na ce su saurare ni kad'an. So nake mu tattauna me zaka ce game da hakan. Na fi son na yi komai da yardar ka".
Ya yi shiru. Sai kuma ya ce "Kuna da matsalar Wani ma abinci ko ma bukata ne?"
Da azama na ce "Wallahi bamu da ita. Kuma Ubangiji yana kawo mini mutane har gida babu yanke wa."
Ya ce "To bana son zuwan ki gidan mutane Asiya"
Na zuba masa ido na ce "Bajq zuwa, ba Kuma zan je ba. Amma sai nake ganin da ka yi hak'uri na je wannan din. Domin ina son a shiga jikin matar gwamna. Watak'ila ta sanadin ta sai Ubangiji ya fito mini da kai, tunda ka hana ni dauko maka lauyoyi, ka hana ni neman taimakon manyan mutane. Ka bani dama yanzu,tunda ita mace ce kuma komai sai da sabab"
Ya yi shiru. Kafin ya nisa ya ce "Tsoro nake ji Asiya. Ina jin tsoro kada ki samu dama mai yawa ki fi k'arfina ki k'asa yi mini hak'uri da kike yi yanzu"
Ya fada hankalinsa a tashe ainun. Na ce "Haba mana Baban 2! Me yasa kake wasiwasi a kaina? Har duniya ta nade ni taka ce. Ina fad'a maka idan shekaru hamsin aka daure ka Wallahi zan jure na jira ka. Da bakinka ka fad'a mini akwai iyaye mata da suke sadaukar da kuruciyarsu saboda y'aya'nsu. Ashe ni baka gamsu zan yi irin wannan sadaukarwar idan kasa ta rufe maka ido ba. Tunda ga shi da ranka ma kana kallon ba zan iya sadaukar da komai saboda na reni yayanka ba."
Ya girgiza kai ya ce "Ba hakan ba ne Asiya. Na sani zaki yi mini komai. Sannan ke yaranki basi yawa".
Na ce "Ba yanzu ka gama mini albishir din zaka samo hanyar da zamu bi mu samo wasu yaran ba? Har na fara tunanin zan ga likita dan a d'ora ni a maganganun da zan zasu taimake ni wajen samun ciki da wuri.
Ashe da wasa kake yi, ni kuma have nasa rai".
Ya ce "Ba wasa nake yi ba. Na ce "To ka ba ni wannan damar. Bana son na yi abu ba tare da ka sani ba, bana son na bata maka rai Baban 2 ".
Ya saki ajiyar zuciya ya ce"Shike nan. Amma tare da yara da Babah za'a dauke ku".
Da sauri na ce "Dama tare da su zamu je. Na gode, Allah yasa hakan ya zame mana sanadin alheri".
Ya ce "Ameen.
Daga haka na shiga ba shi labarin Aliyu da Iklima. Ya murmusa farincikin zuciyarsa ya bayyana akan fuskar sa.
Haka muka dinga hira. Har lokacin tafiyarmu ya yi. Hanif ya ce "Baban 2 sai mun sake dawowa. Hamim kuwa ya ce "To bude ka bamu biscuit din naka"
Ya kuwa bude ya bawa kowa a hannunsa.
Suka had'a baki suna fad'in"Mun gode, Allah ya fito mana da kai!
Ya ce "Oya ku je office din Uncle ku ce masa zaku tafi ".
Suka ruga a guje, suka nufi office din Yaya Ammar.
Ba jimawa ya fito rik'e da hannuwansu. Ya kalle ni ya ce "Zaku tafi Yabi?"
Na ce "Eh Yaya mun gode sosai."
Ya ce "Dafatan dai kin fad'a masa ya dinga cin abinci. Ba kasafai yake cin abinci ba. Kullum sai na taho masa da abinci daga gida. Amma baya wani cin na kirki."
Na yi murmushin kunya na ce "Ina ce wa "Na yi masa".
Daga hakan muka taho ya bude mana k'ofa, har titi ya kawomu. Ya tarar mana Napep ya biya sai da ya ga mun tafi sannan ya koma.
Muka isa gida na fad'awa Babah ya amince amma ya ce mu je tare. Ta ce "To sai mu je taren. Allah ya tabbatar mana da alheri.
Ai kuwa har kofar gida Hajiyar nan ta zo ta kwashe mu ni da zugata. Tunda yara na hutu.
Sai gamu daredare cikin fadar gwamnati. Aka baibaye mu da abubuwan motsa baki. Ashe Hajiyar nan mai magana da yawun matar gwamnace. Ba'a bata mana lokaci ba aka yi mana iso zuwa dakin da zamu yi kunshin.
Zuciyata tana harbawa na fara yi mata. Sai addu'a nake Ubangiji ya ba ni sa'a na yi wadda zai yi kyau ta kuma yaba.
Cikin nutsuwa nake yi. Tana yi tana kallona. Na kammala kunshi. Na fara yarfa mata kitso akan dogin gashinta da ya sha gyara na garari.
Na kammala. Ta ce hadinaeta ya dauko matso mata dogon console mirror din da yake gefe. Ta ga yadda na yarfa mata kitso. Ta murmusa alamun ta gansu da abin da ta ga ni. Ta kalle ni ta ce "Kin kammala sakandire ne?"
Na kasa amsawa domin na tabbatar k'ank'anta ta ya sanya ta yi zaton ko ban yi Kandi ba. Ta lalli Babah ta ce "Hajiya kar dai bata zuwa makaranta?"
A tausashe ta ce "Ta kammala tuntuni. Ta nuna su Hamim da suka lafe a jikinta ta ce "wadannan ai y'aya'nta ne ba kanne ba."
Ta dauki salati tare da fad'in "Wonderful. Yanzu ke ce uwar wadannan samarin?"
Babah ta ce "Ita ce kinga Kuma sai da shekara biyu a daki sannan ta haife su. Tana shatakwaas ta haife su".
First lady ta sake tsananta mamakinta ta ce "Yanzu shekarun yaran nawa tunda masu garin jiki ne ba irin ba ne tsaba"
Babah cikin dariya ta ce "Shekarunsu bakwai."
Ta sakki ajiyar zuciya tana kallona ta ce "Shekaru ashirin da biyar a wannan yarinyar. Ikon Allah. Tunda na ganta na ce kyakkwar yarinya Allah dai yasa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login