Showing 39001 words to 42000 words out of 184118 words

Chapter 14 - Bakar Taada Hausa Novel Complete

kyau, asalin labarin da turka turkarsa yana littafi na biyu da na uku*
*Bisa soyayyar da kuke yiwa rubutuna ya sanya zan yi muku tsarin VIP.
*In Sha Allah babu jira.
*Babu posting ranar Lahadi*
*Sau biyu za'a yi posting a rana*.
*Ku zo mu yi tafiyar da babu nadama*
*Zaku dara, zaku koka, jikinku zai tsumu, zuciyoyinku zasu motsu. Tunani kuma zai tafi cancanken me zai faru a gaba*.


*Marubuciyar HALIN YAU da SABO DA KAZA*
*Yanzu kuma alk'alaminta yana tafe da BAK'AR TA'ADAH*

*500regular page*
*VIP 1k twice pages*
*2384876855*
*Surayya Ibrahim Dahiru*
*Zenith Bank*.
*Ko*
*7061488065*
*Surayya Dahiru Ibrahim.*
*Opay Bank.*

*08032773332.*


*KUN TUNA MAI GYARAN GUDUYO?*
*OK NA NUFIN FASEELAT BABBAR DILA TA G.H.T.*
*KO WANNE NAU'IN KAYAN GHT TANA SIYAR DA SU AKAN FARASHI MAI RANGWAME*
*KAWAI KU TUNTUBE TA A WANNAN LAMBAR DAN GANIN JERIN KAYAN DA TAKE DA SU*
*TUN DAGA KAN SUPPLEMENT, SABULAI DA LIPTON*.
*MASANIYA CE AKAN KAMFANIN DOMIN TA SAMU KARRAMA WA DAGA KAMFANIN A BANA, HANZARTA KI TUNTUBETA DAN SIYA DAI DAI KO SARI.*
*07039269802


*Surayya Dee*
*Yar mutanan Gwaram*

✍️

*WANNAN LITTAFIN NA KUDI NE, BIYA KUDIN KARATUNKI TA WANNAN ASUSUN DAN GUJE WA BAKAR TA'ADA*
*2384876855*
*SURAYYA IBRAHIM DAHIRU*
*ZENITH BANK*

*KO*
*7061488065*
*SURAYYA DAHIRU IBRAHIM*
*OPAY DIGITAL SERVICES*
*TURA SHAIDAR BIYA TA WADANNAN LAMBABOBIN*
*08032773332*
*09069067488*.

*UMM NIHLA COLLECTIONS*
*Ta k'ware wajen kawo yadina masu kyau da sauki, cotton da silk, embroidered, Batik*
*A Malaysia take daga can kuma take turo su Kano direct. Dan haka kayanta akan farashi sari take bayarwa, daga guda daya har zuwa dari zaku samu*
*Kayan ta masu aminci da rahusa ne, ku tuntube ta Whatsapp dan ganin JERIN gwanon yadinanta da basa kode wa ko jeme wa*.
*07020695644*
*What's app only*.


Cikin kasala irin wacce b'acin zuciya ke sababa wa, Baban Marina ya ce "waye kuke ganin ba zai auru ba, tamkar Yabina! Wane ne shi?"
Hatta Dada jikinta ya yi lubus da Baban Marina ya ce Yabinsa a akan idon ta da na y'anuwansa. Wanda hakan na alamta ce wa ya kai makura wajen kawaicin da yake yi amma ba'a yi masa kara.
Daga Baban Tsakiya har na Kasuwa ba wanda ya iya cewa kanzil domin sun shiga yanayi na jin nauyi da borin kunya.
Sun fahimci fishin da yake shinfid'e a fuskar yayan nasu ya tunbatsa.
Sai suka yi dabarar kame wa daga jaye jayen maganar.
Bai sake jiran komai ba, ya mike tare da yiwa Dada sallama ya fice.
Yana fita Baban Tsakiya ya ce "Muna cikin wani irin kalubale a wannan duniyar.
Ace ba dama ku tattauna da dan-uwanka ya fahimce ka, shike nan sai ya zama sanadin tabarbare war al'amura?"
Ya yi k'wafa mai nuna takaicinsa muraran.
Baban Kasuwa yana bu'de baki sai ce wa ya yi "To ai irin wannan al'amarin wuya ne da shi. Tuni Ubangiji yasan al'ummar Manzonsa zamu riski wannan zamanin shi yasa ya saukar mana suratul Yusuf dan ta zama izina ga masu hassada da k'yashi. Ta kuma zama gargadi ga masu hankali.
Wani abin kaicon ma mu babu y'an uba a cikinmu, amma babu yadda za'a yi a ha'du a yi hira da walwala cikin farin-ciki saboda kawai ka fi mutum haske?
Gaskiya zan fa'da miki Dada.
Tunda ke kin isa da shi, ba wanda ya cancanci Yabi sai Tijjani, su rufa wa junansu asiri, shine kuma zai iya biyar da ita, ya yi maganin shak'iyancinta".
Baban Tsakiya ya numfasa ya ce "Tunaninmu d'aya Iliya, sai dai ba lallai ne ya amince ba.
Tunda duk iyashegenta bai yarda ja'irar yarinya ba ce. Zai yi wahalar gaske ya ba shi tunda shi lalacewarsa ta bayyana a gida da dawa.
Ita kuwa mu na kusa ne muka fahimta kawai".
Dada ta saki ajiyar zuciya ta ce "Idan haka ta faru kuwa ina da yakinin mai sunan manya zai nutsu domin komin ginshirarsa ba zai kushe ta ba.
Ubangiji ya kyautata halittarta, gata yar shawalwala da zata da'de tana cin zamaninta".
Suka gintse fuska suna fa'din "Kyaun hali da tarbiya ai sune kyaun mace Dada."
Kawai dai ki sanya baki a ba shi ko ma sarara, domin idan shine mijinta zai karya dukkan lagonta."
Basu tashi ba, sai da suka tabbatar ta gamsu bawa Bulkachuwa auren Yabi fa'ida ne mai yawa a garesu bakid'aya.
Baban Tsakiya ya fi kambaba lamarin, a zuciyarsa kuwa so yake a yi a yi a auren ta tunda kusan kullum sai ya yi mafarkin Jabir ya bijire masa ya aure ta.
Sun ki kwamishina ne dan kada haske ya shiga k'ofar dan-uwansu, tunda sun tabbatar nagartacce ne, basa son ya'yansa su yi k'arfi.
Sun fi son a ce su da y'ay'ensu sune masu fa'da aji.
Auren Bulkachuwa kuwa sun san ba wani fiffika da y'ar iskar yarinyar nan zata yi musu.
Tunda a bayyane yake matu'kar mace bata samu miji na gari ba to rayuwarta ta na'kasa.
Washagari da sassafe Baban Marina ya yi sallamah ya ce ya tafi Azare.
***
Na fito sanye cikin uniform, na isa mashigar zauren Dada dan gaisuwa da kuma biya wa Nasiba. Sai na ji magana k'asa kasa daga dakin Bulkachuwa.
Na kasa kunne dan na ji me yake fa'da.
"Bazan sake turo kowa gidanku ba Bilki. Na yarda ki na sona, amma kuma ai ba zaki iya aurar da kanki ba, dole sai da wakilcin iyayen ki. Kema kin san ina sonki, amma tabbas bazan sake turo kowa da zummar a nema mini aurenki ba".
Na yi fakare, jikina ya yi laushi akan abin da na ji.
Waton ba karamin son Bulkachuwa y'anmata suke yi ba.
Bansan me yasa shi kuma yake da jarumtar juya wa soyayya baya ba, matu'kar aka nemi muzanta shi.
Na tsinci kaina da fa'din "Ina ma irin zuciyar Tijjani nake da ita?" Da tuni na yi watsi da tunanin Jabir da soyayyarsa.
Amma ina! Har yanzu ina jin sonsa, kawai na danne ne dan babu yadda na iya.
Na shiga cikin gidan na tarar da Nasiba ta shirya.
Na gaida Dada kamar yadda na saba.
Sai dai amsa mini da ta yi, ya banbanta da sauran watannin baya. Domin tunda kwamshina ya bayyana mini, da karsashi take amsa mini gaisuwa ta.
Amma a yau cikin wani irin yanayi da na kasa tantace wa.
Sai kuma ta zarce da fa'din "Wanda duk ya yiwa mahaifinsa biyayya ba zai tab'e ba. Ina da tabbacin ko wuta na rura na ce da tsohonku ya shiga zai fa'da ne kawai babu tambihi.
Ina rokonku ku dinga yi masa biyayya, ku yarda ya isa da ku, mussaman ke Yabi da tun shekarar da kika iso duniya ya shiga cikin tala jaurar duniya".
Ta fa'da kuka na subuce mata.
Jikina ya mutu murus a dalilin kalamanta, tunanina ya shiga canke canken akwai al'amarin da zai biyo bayan wannan jirwayen na Dada.
Muna tafe da Nasiba duk uban maganar da take yi mini akan Bulkachuwa na kasa ce mata uffan.
A dalilin zuciyata ta riga ta baci da yadda Dada ta ce wai tunda na iso duniya ubana ya fa'da cikin ibtila'i.
Na sani ba yau ake fa'da ba, Mama ta sha fa'da mini ni din tauraruwa mai wutsiya ce, haka ma ya'yanta su Yaya Indo.
Tun ina damuwa har na zo abin ya daina damuna, domin Baban Marina bai ta'ba yi mini wannan izgilancin ba.
Amma a yau sai na tsinci kaina da jin ciwon furucin Dada kwarai da aniya.
Na dinga hasashen me ya janye mini alfarmar da na a samu y'an watannin nan a idonta?
A daren ranar Babanmu ya zaunar da ni da matansa ya fa'da mana aurena da Alhaji ba zai yiwu ba, bisa wani dalili da bai bayyana mana shi ba.
Ya je shi da Alhaji Tanimu sun bashi ha'kuri. Ya gamsu sun yi masalaha, duk da ya shiga rud'ani sosai.
Ya kuma ce ya yafe duk hidimar da ya yi.
Jikina ya mutu, zuciyata ta tsinke.
Na kasa bu'de baki na yi magana.
Ya sallami matansa suka bar ni da shi.

*GUDUYO NA TALLATA MUKU INGANTATTUN SAIWOWI NA MUSSAMAN KUMA GANGANRIYA DAGA CHADI*
*IDAN KINA DA KANWA KI DIYAR DA ZAKI AURAR TO KI ZO KI JARRABA WADANNAN KAYAN DA BABU ASARA KO ALGUS A CIKINSU*.
*SANNAN KE MA DA KIKA KWANA BIYU A DAKI AKWAI BUKATAR KI SABUNTA KANKI*
*AKWIA SAIWOWIN SANYI*
AKWAI SAIWOWIN DAHUWAR KAZA*
*AKWAI SAIWOWIN DAHUWAR TATTABATU*
*AKWIA SAIWOWIN TSUMI*
*AKWAI PACKAGE DIN MAGANIN SANYI SADIDAN*
*AKWIA PACKAGE DIN AMARYA*
*AKWAI PACKAGE DIN MAIJEGO*
*AKWAI KAYAYYAKIN MASU INGANCI A FARASHI MAI RAHUSA*.
*AKWAI GORAN TULA SYRUP*
*AKWAI GORAN TULA FRUIT*
*INA AIKAWA KO WANNE GARI A FAD'IN TARAYYAR NIGERIA*
*, SO SU MINI MAGANA TA WANNAN LAMBAR 08032773332*
*DAN ALLAH SERIOUS BUYER'S*

Ya tausasa harshe har ya bani tausayi.
Ya ce "Yabi kinsan Nura dan wajen Babanku Tanimu?"
Na daga kai tabbacin eh.
Ya numfasa ya ce "Madallah! To zai zo ku gaisa, shi na za'ba miki ya zame miki miji. Ubansa tuni yake ro'kon na ba shi ke ya bawa Nura, tunda ya samu labarin abin da y'anuwana suka yi mini, ina ta bagarar da maganar. Saboda ganin Alhaji ya shigo da k'arfinsa.
Amma a yau din nan na amince masa.
Ina ro'kon arziki Yabi, kada ki kunyata ni. Kinga shi namiji ma ubansa yana fa'da masa ya amince da farin-ciki da walwala. Ki kwantar da hankalinki irin k'alubalen da kike fuskanta da kananun shekarunki na alamta cewa zaki samu kyakkawar rayuwa a gaba".
Hawaye taf a idona na ce "Na amince Baba! Allah ya sa hakan shine mafi alheri".
Ya amsa da ameen ikin farin-ciki mai yawa, tare da sanya mini albarka.
Ya sallame ni bakinsa dauke da addu'a a kaina da lamarina.
Ina shiga d'akin Gwaggo na fashe da kuka.
Ta ru'ko ni sosai ta dinga bani ha'kuri.
Wannan rarrashi da Gwaggo ta yi mini ya sanyayya mini zugin da nake ji a zuciyata.
Da na nutsu sai na fahimci ba kukan rabuwa da Kwamshina nake yi ba. Domin ba wani sonsa nake ba, dama na yarda zan aure shi ne, dan na gaji da zaman Gidanmu. Sannan Bulkachuwa ya kitsa mini cewar da na yi kukan takaici a gidan babu, gara na yi a gidan wadata.
Amma sam babu soyayyar da zan yi ba'kin ciki irin haka.
Kawai ina kukan yadda al'amarina ya banbanta da na kowacce y'a a gidanmu ne.
Maganganun Gwaggo sun sake fahimtar da ni ita dama ba son aurena da Alhaji take yi ba, ta yi shiru ne dan gara aurensa akan na Jabir.
Amma ta ce bata fasa addu'a ba, bata fasa nema mini zabin Allah ba.
Dan hakan kuma ya kasance sai ta gamsu Ubangiji ne ya amsa mata.
Kwanki biyu na warware tamkar komai bai faru ba, na cigaba da harkokina.
A yammacin wannan rana ta litinin mun taso daga Islamiya sai ga aike wai ana sallamah da Yabi in ji Nuru Tanim.
Na dan diririce na kasa magana a dalilin yadda ya zamanantar da sunan na shi.
Na dinga canki canki wane ne Nura a y'ay'an, Baba Tanimu? Domin y'ay'an gidan yawa ne da su, matasa sun kai bakwai ko wanne ya isa aure.
Na kasa cankar wane ne shi a cikin jerin matasan gidan.
Inna da kanta ta cewa yaron ya je ya ce "ina zuwa".
Hijabina har kasa na sanya, bayan Gwaggo ta matsa mini na shafa hoda.
Na fita cikin zullumin yadda zan gan shi. Tunda bani da sauran za'bi akan lamarin.
A babban zauren na hango shi sanye cikin shudiyar shadda sosai, kansa sanye da hular da ta dace da kwalliyarsa.
Ko ka'dan ba shi da makusa, ya fi Yaya J cika, tsayi ne dai zasu yi taya.
Batki ne sosai, amma ma'abocin tsabta ne daga ga ni.
Take na ji abin da ya d'aure mini kirji ya fa'da mini domin ban ganshi a cikin mummunan yanayi ba.
Baya aikin gwamnati, amma yana koyar wa a wata firame mai zaman kanta, boobies a sannan yana da shagon caji da turin wakoki ko finafinai a wayar hannu.
Muka gaisa cikin yanayi na babu yabo, babu fallasa.
Muka yi shiru.
Tsawon lokaci kafin ya katse shirun ya ce "Asiya! Zuciyata ta harba domin har cikin raina nafi son a ha'da mini da Yabi.
Na amsa a hankali da "Na'am".
Ya tausasa murya ya ce "Na da'de ina son ki, na sha fa'da wa Babanmu ya taimake ni ya nema mini auren ki, sai ya bada hanzarin dan-uwanki ne yake son ki, ba zai yiwu ya gabatar da maganata ba, tunda akwai nauyi a tsakaninsa da Baban nan gidan. Dan haka ko da kika gan ni anan ba turo ni aka yi akan dole ko biyayya ba, dama ina son ki tun ina zuwa makarantarku".
Na yi kasa da kaina ina sake samun nutsuwa mai yawa.
Ya sake sassauta wa ya ce "Idan har kina da matsala ko kina ganin ban yi dai-dai da ra'ayinki ba, zan san yadda zan yi na zulle wa maganar ba tare da an ga laifinki ba, domin al'amarin aure ba k'aramar tafiya ba ce da za'a yi ha'kurin dole a cikinsa."
Na tsinci kaina da cewa "Babu damuwa Allah ya tabbatar mana da alheri".
Dadi ya kama shi, ya ce" kenan Asiya ta aminta da ni?"
Murya babu amo na ce "Yabi bata da burin yin fatali da burin iyayenta ko da ya ci karo da nata ra'ayin."
Farin ciki ya sake lullube shi. Ya dinga fa'din ma sha Allah! Madallah da Yabi".
Na taya shi murmushi.
Ya ce "da alama kina son Yabi, ni kuma sai nake ganin karamci ne na kira ki da Asiya."
Na cuna baki na ce "Tunda na riga na sami wannan falalar ta zuwa gabas, kawai ka kira ni Yabi domin ina son sunan da dukkan zuciyata".
Ya murmusa ya ce "An gama Yabin Nuru".
Zuciyata ta tsinke yau ga abin da Yaya J ya guda, na jingina wa Yabinsa sunan wani ba nasa ba.
Mun jima muna dan tattauna wa duk da shine yafi yin hirar sosai.
Ya ciro ku'di ya bani, na ki karba.
A sanyaye ya ce "Matu'kar baki karba ba, to alama ce ta ban samu karbu wa ba".
Jin hakan ya sanya na mik'a hannuna duka biyu na karb'a.
Daidai lokacin Bulkachuwa ya shigo a hargitse rigarsa daban haka ma wando daban duk a yamutse. Da alamu ba nisa ya yi ba. Inda a ce d'an wanka ne sosai bansan irin rubibinsa da za'a yi ba, tunda a hakan ma ba'a fasa sonsa ba.
Nura ya mika masa hannu suka gaisa ya wuce babu walwala nasan kuma yana taya kwamshina kishi ne.
A lokacin na sake tabbatar da tsayi da cikar Bulkachuwa ya kai k'ure wa domin sai na ga Nuru bai kai kafadarsa ba.
Daga haka muka yi sallamah ya tafi.
Na shiga gida ana kiran magariba.
Bayan mun idar da salla na bawa Gwaggo ku'din da ya bani sababbin yan dari biyar guda goma cif.
Ta yi shiru sai kuma ta ce "Allah ka sawa al'amarin albarka, ya sa karshen wahalarmu kenan".
Na amsa da Amin a zuciyata domin ni kaina na gaji da yadda komai yake kwace mini.
Gaba'daya shekaruna sha shida ne da ka'dan amma na gaji tunda al'adar auren wuri ne a gidanmu.
Wai duk yadda nake da k'arancin shekarun nan, da yadda nake y'ar tsurut habaicin rashin aurena a ke yi mini, ko a jefi Gwaggo da bak'ar magana.
Har ta kai bani da kalubalen da ya wuce zaman gidanmu a rayuwata.
Rayuwar gidanmu da ta gidan Yaya Ummi ta sanya na k'yamaci zaman babban gida. Wani zaman idan an yi sa'a sai ya zama tsintsiya dan ha'din kai. Wani kuwa sai ya zama tamkar sansanin yaki dan fitina.
Ta sake kallona ta ce "Nasan yaron dan wajen Sahura ne, yana da zuciyar neman na kansa ga shi mai jin maganar iyaye ne, duk cikin matan gidan dakinta yafi na ko wacce fasali da kayan jere mai kyau, kuma duk shi ne yake yi mata, shi ka'dai ne namiji a d'akinta, y'ay'anta duk mata ne, amma da ya ke mai zuciya ne sai tafi mai y'ay'a maza biyar gata da kyan ga ni, ta bar uwar maza je da fankamar ita ce da gida.
Shikenan rabuwarmu da Kwamshina. Ya mini waya washagarin da Baba ya ce ya je Azare. Ya fa'da mini yadda Baba ya je ya ba shi hakuri.
Ya fahimci Baba suka rabu cikin girma da arziki, tare da ro'kon idan auren ya zo a sanar masa zai halarci dauri aure.
Nima ya mini maganganun masu taushi da nuna muhimmancin yiwa mahaifi biyayya.
Duk da ba wani sonsa nake yi ba, sai da na yi kukan yadda kalamansa suka dagargaza ni. Kewarsa ta taso mini ba ka'dan ba.
Ya dinga rarrashi tare da tambayar me zai siya mini na kayan aure dan na yarda ya gode da karamcin da na yi masa.
Na kasa cewa komai sai shine ya ce "Zan aiko miki da sako zuwa satin sama in sha Allah"
Ya k'are maganarsa da fa'din "Allah ya sa ki shiga gidan auren a sa'a, Allah ya zaunar da ke lafiya".
Bulkachuwa a bakin kwamshina ya ji maganar aurenmu ta ruguje.
Rannan da hantsi ya aiko yana kirana.
Zuciyata d'aya na je na tarar da shi a tsakar gidan Dada yana zaune kan kujerar tsuguno. Na zauna akan turmin da yake fuskantarsa.
Ya kalle ni da tarin kulawa ya ce "Asiya Toro me yake faruwa ne? Jiya na shiga Bauchi sai nake jin labarin da ya ki'dima ni a bakin Honarable.
Nasan ba zai mini karya ba, me yasa kika canja?
Me yasa dan Allah?"
Na yi k'asa da kaina haka kawai na ji hawaye ya k'wace mini. Domin idan aka cire yan kofarmu ba wanda ya nuna damuwarsa ko alhini akan shiririce wa da maganar Kwamshina ta yi sai Tijjani.
Na tabbatar bayan soyayyar da yake yiwa lamarin, to akwai kishin wula'kanta ni da aka yi a gidan, shi yasa yake son na yi auren ke ce raini.
Ganin hakan sai jikinsa ya yi sanyi ya ce "Ba kuka zaki yi ba, ya ce mini Baba ya gabatar masa da hujja mai k'arfi shi yasa ya ha'kura.
Wacce irin hujja ce wannan dan Nabiyur Rahmati?"
Ya fa'da a matu'kar zafafe.
Kafin na ce komai sai Dada ta rarrafo ta ce "Ni ce nan! Na barranta lamarin, na kwashe masa albarka, ba zai yiwu na ha'da jini da mai kafirtamu ba. Ba zai yiwu ta auri wanda iyayenta suka tabbatar ba mutumin arziki ne ba".
Da kakkausar murya ya ce "Dada me kika yi hakan?
Su waye iyayenta?"
Yana rufe baki ta ce "Su Badamasi mana".
Maimakon na ga ya sake fusata sai kawai na ga ya kwashe da dariyar iyashege ya na fa'din "wannan shine abin dariya kunama ta ciji danwanke. Shi Baban Tsakiya idonsa da kwalli har ya ce wani bai cancanci Yabi ba?
Sanin kowa ne Jabir da Yabi masoya ne tun suna yara k'ananu, amma shi da kansa ya datse soyayyar kuma yanzu Allah ya turo mata wani sai ya ce bai cancanci a ba shi aurenta ba.

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login