Showing 108001 words to 111000 words out of 184118 words
Chapter 37 - Bakar Taada Hausa Novel Complete
yarda ina amfani da duk abin da ya ba ni, ina iyakacin kokarina ban nuna masa ina bu'katar abu sama da k'arfinsa ba, na kuma ajiye dukkan burikana na son na dinga yin suturu masu tsada. Maimakon haka sai na tattara na sayi dan kunnen gold wanda shi da kansa na bawa ku'di ya siyo mini a Jos. Ko zan yi abu a gidan sai cikin dabara ko kuma na kara masa ku'din lallensa idan sati ya zagayo. Shi kuma tunda ya fahimci burina soyayya irin ta indiyawa sai yake ajiye komai ya yi ta kashe ni da kalolin soyayyar da ko indiyawa ma sai a shiri, tunda suma ai shirin fim ne. Shiri kuwa kowa yasan shirya shi ake yi.
Amma a hakan yake lalace mini. Ya zama tamkar mai irin shekaruna. Ko a littafai ba kasafai ake samun irin Bulkachuwa ba. Domin ya iya shiririta kala kala da mata suke son ayi musu. Idan yana gida barin komai yake ya tarairaye ni. Cinyarsa ita ce wajen zama na. Goyo kuwa zai iya goya ni, ya yi shara. Har k'aton baho ya siyo irin tafkeke na masu wankan jego. Ya cika shi da ruwa ya dauke ni ya tsunduma. Ya wanke ni tas.
A shimfida kuwa irin murza ni da yake yi, da da'din da yake jiyar da ni dole ma na so shi na rikice a kansa. Domin har cikin zuciyata na fara tunanin da ba shi na aura ba dan ban more ba. Har jin haushin son da na yiwa Yaya J na fara yi.
Gaba'daya na gama mutuwa a kansa, ba abin da nake so irin na gan shi a gida idan yamma ta yi. Yanzu da baya fita lahadi a gida yake yini. Da kaina na soke yin lalle da kitso. Komin girman mace bana yi a wannan ranar zan fa'da mata maigidan ya hana yi a wannan ranar.
Dan na fahimci ba a daina zuwa ana katse mana jin da'dinmu ba sai nake yawan rubutawa a status d'ina cewar babu lalle ranar lahadi haka ma kitso.
Mun yi kyau, mun shak'u da juna, komai yana tafiya dai-dai mussaman da na daina yi masa rikicin bai yi mini ciki ba.
Da kansa ya dauke ni muka je asibiti da muka cika shekara guda da aure. Dukkanmu aka auna mu aka tabbatar mana lafiyarmu k'alau cikin ko wanne lokaci zamu iya haihuwa. Shike nan sai na daina damuwa illah iyaka ban daina addu'ar ma samu ciki na haihu ba.
Muna cikin wannan yanayin mai da'di Rafi'a ta kammala karatunta na jamaia ta dawo gida gaba'daya.
Kusan kullum sai ta shigo mini. A zuciyata bana so amma tunda uwarta ba k'aramin kirki take yi mini ba. Sai nake share wa mussaman ita din ma mai kirki ce.
Amma haka kawai nake jin fargabar zakewarta a wajena domin na riga da na sani mijina yana son yan lukataye irin ta. Ni kuma yar firit ce. Sannan bazan yaudari kaina ba, zai iya sha'awarta tunda jikinta rugu rugu ne, kuma bayltw damu ta saka mayafi ba. Tunda tana ganin ba sai ta fita waje da ta shigo ba. Bugu da kari ba Hausawa ba ne. Wasu abubuwan nasu da namu akwai banbanci.
Haka dai nake ta daure wa ina ta k'ok'arin ban bar shi da kewa ba. Komai yake so sai na yi masa. Ba kuma na tab'a k'osawa da al'amarinsa duk da nima ina son harkar. Amma bana ja masa rai saboda kada ya ga ni a waje ya yi sha'awa. Ba kuma na nunawa ya gundure ni.
Ana cikin haka aka tashi bikin. Ihsan k'anwarsa. Tun saura sati biki na tafi, saboda a fara komai da ni, sannan ni ce zan mata k'unshi da kitso.
Babah sai ina ka saka take yi da ni. Yadda ta ga na murje na yi kyau ba karamin da'di ta ji ba. Na sani kuma da a ce da goyo na je mata da tafi haka murna.
Shi da kansa ya kai ni. Washagari ya tafi akan sai nan da kwanaki ka'dan zai juyo. Komai sai da na bar masa, hatta miya sai da na soya masa, na yi masa cincin. Kawai tafasa farar taliya ko shinkafa zai yi sai kuwa shayi.
Ana gobe biki y'an Toro suka iso. Aka yi hidima cikin rufin asiri taro ya tashi lafiya.
Kwanaki biyu a tsakani ya zo muka tafi shake da kayan biki masu yawa.
Tunda muka yi aure bamu ta'ba nisa da juna ba sai wannan karon.
Duk da dai a Bulkachuwan ma ranar biki sai da ya faki ido ya jani muka je wani waje ya yi abin da zai yi sannan ya dawo da ni.
Amma muna isa gida ko hutawa bamu yi ba. Daki ya ja ni bamu fito ba sai da ya samu nutsuwa.
Da daddare ina zaune a cinyarsa sai ce mini ya yi "Little baki da nauyi, shafal ban ji kin danne ni ba".
Na zabura na kalle shi, gabana ya fa'di sosai. Da rawar murya na ce "Sai yau ka fahimci haka? Wa ka d'ora a cinyar da yanzu baka ji yadda kake so ba?"
*KUN TUNA MAI GYARAN GUDUYO?*
*INA NUFIN FASEELAT BABBAR DILA TA G.H.T.*
*KO WANNE NAU'IN KAYAN GHT TANA SIYAR DA SU AKAN FARASHI MAI RANGWAME*
*KAWAI KU TUNTUBE TA A WANNAN LAMBAR DAN GANIN JERIN KAYAN DA TAKE DA SU*
*TUN DAGA KAN SUPPLEMENT, SABULAI DA LIPTON*.
*MASANIYA CE AKAN KAMFANIN DOMIN TA SAMU KARRAMA WA DAGA KAMFANIN A BANA, HANZARTA KI TUNTUBETA DAN SIYA DAI DAI KO SARI.*
*IDAN KUWA KINA SON YIN RIGISTA DAN FARA KASUWANCIN KAWAI KI TUNTUBETA DAN KUWA DA KYAKKWAR ZUCIYA ZATA MU'AMALANCE KI*
*07039269802*
Ya daburce ya ce "Wallahi babu kowa Yabi".
Fa'din Yabi da rudun da ya shiga sai yasa na kasa gasgata shi amma kuma na danne na ha'diye saboda babu kyau zargi.
Duk yadda na so na bar maganar amma a zuciyata sai wasi-wasi nake yi. Na kasa samun nutsuwa. Hakan ya fara shafar walwalata. Ban sauya masa ba, ba kuma na bijire masa amma kuma babu shiriritar da nake yi masa a baya.
Rannan na ce masa ina son na je gida na yini. Da rawar baki ya ce "To, yaushe zaki je?"
Domin ya takura da rashin walwalata.
Na ce "Duk ranar da ka ce".
Ya ce "To gobe sai na kai ki"
Haka kuwa da kansa ya kai ni, muka fara isa k'ofar Dada muka gaisa. Tana ta barkwancinta da karatunta. Ban wani jima ba na tashi na nufi k'ofarmu."
Ya shigo suka gaisa ya ce mini zai tafi da yaushe zai zo ya d'auke ni?
Na ce "ko yaushe ma".
A k'ok"arinsa na son ya kyautata mini sai ya ce "Tom idan an idar da Isha zan zo".
Na ce "Allah ya kai mu".
Ya tafi. Na yini cikin iyayena cikin nutsuwa da walwala.
Da yamma lis Gwaggo da Inna zasu je duba yar kanwar Mama da ta haihu kusa da unguwarmu ne.
Dan haka Baban Marina ya ce "Asiya sai ku je tare ki rakasu idan kin dawo sai ki shige gidanki".
Na amsa da ce wa "To Babanmu, domin idam Gwaggo ta fita ba jin da'din zaman zan yi a dakin ni ka'dai ba, tunda Ikilima ta tafi Islamiya, shima kuma Baban fita zai yi. Mama kuwa babu wata ma'amala mai yawa a tsakaninmu.
Dan haka muka tafi tare. Da muka dawo na yi lungun da zai sada ni da gidana, su kuwa suka mik'e suka koma nasu gidan.
Haka kawai nake jin nauyin jiki na saukar mini. Wani irin b'acin rai ya ziyar ce ni da na karyo kwanar da na fara hangen gidanmu. Haka nake tafe ina ta jin fargaba. Ina kuma ayyana abubuwa marasa da'di a zuciyata.
Nan da nan na fara ta'awizi ina kore shaid'anin da yake son yin wasan kura da zuciyata. Har cikin zuciyata ina son Tijjani, ina son na rayu da shi. Domin a zaman da muka yi na shekara daya da kusan rabi na tabbatar yana da kyawawan dabi'u. Na farko shi mutum ne mai mutunta sallar farillah. Sannan mai yawan tsayuwar dare ne na shaida hakan. Domin duk lokacin da zai shafe yana tiritiri da ni da daddare, to da zarar k'arfe uku ta yi kuma zai tashi ya yi wanka. Ya yi ta yin munajati da Ubangijinsa, wani lokacin ya matsa mini na tashi, wani zubin kuma ya k'yale ni na yi barcina. Sau tari kuma idan ban tashi ba, da asuba idan ya tashe ni sai ya ce "Tashi ki yi sallar farillah akan lokaci, na raba dare ina roka miki alherin duniya da lahira my little".
Bayan hakan na karance shi yana da matu'kar son ya kiyaye ka'idojin da shari'a ta d'ora masa mussaman na ri'ke gida da kula da tarbiyata. Sannan ba shi da mugunta ko ka'dan har yau din nan Tijjani bai ta'ba saka mini ido akan ku'dina ba. Asalima kullum cikin k'ara k'auwame kansa yake yi da abin hannuna.
Sannan ya iya Soyayyar da duk taurin zuciyar mace sai ya dargaza ta. Ga kuma girmama iyaye, yana mutuntata manya kwarai da gaske. Wadannan dabi'un da ya siffantu da su ya sanya nake hakuri da inda yake kuskure mini, hakan ne kuma dalilin da yasa na k'i yarda na k'arfafa wa kaina zargin ko ya koma Bak'ar Ta'adar sa ta baya.
Na shiga zauren na ga kofar tamu a rufe ruf. Na fara tunanin ai ban fito da mukulli ba, tunda mun yi shi zai zo ya dauke ni.
Na zaro waya da nufin na k'ira shi ya zo ya bu'de mini, sannan na wuce k'ofar Maman Safiyanu na jira shi. Sai na jingina da k'yauren k'ofar ga mamakina sai na ga ta bud'u.
Na tura a hankali na ga sakata a ture tabbacin an saka bata shiga ba ne.
Na shigo a hankali. Amma sai na ci birki na tsaya cikin tsananin tu'ajjibi da mastanancin mamaki mai yawa.
Jikina ya d'auki b'ari, zuciyata ta yi nauyi ainun. Amma idona ya bushe k'amas.
Na saka hannuna na murtsike idanuwana da tunanin gizo yake yi mini, tare da fatan ace sak'e sak'en zuciyata ne da wasi-wasi irin na shaid'an.
Amma ina zahiri nake ganinsu. Tijjani zaune akan baranda yayin da Rafi'a take kan cinyoyinsa da manyan mazaunanta. Ta kwanta luf a kirjinsa, shi kuma idonsa na kan k'irjinta yana kallonsu. A zahiri iya abin da na gani ke nan amma zuciyata sai ta shiga wassafo mini cewar yanzu ma suka sanya tufafinsu.
Na ki'dima ainun, amma na kasa yin kwakkwaran motsi, na tsaya cak ina kallonsu tamkar mutum mutumi
K'arar faduwar wayata ne ya ankarar da shi.
Ya d'ago da fuskarsa ai yana ganina ya yi wani irin zabura ya wancakalar da ita, ta hantsilo ta fa'do kan guiwowinta.
A matu'kar rude ya k'araso gare ni.
Ya rasa mai zai ce, sai kawai ya zube a gabana guiwa bibbiyu. Ya ru'ko hannuna na kalle shi na ce "Tijjani gizo idona yake yi, ko mafarki nake yi?".
A ki'dime ya ce "Zan so a ce mafarkin kike yi Asiya".
Daidai lokacin Rafi'a ta zo ta shige sum sum tamkar k'wai ya fashe mata a ciki.
Na dinga jin tukukin ba'kin ciki da tashin hankali. Amma kuma idona a soye duk yadda nake son hawaye ya zubo mini abu ya ci tura.
Na sunkuya na d'auki waya ta na k'wace hannuna na yi d'akina ina jin jiri na katantanwa da ni.
Kai tsaye na hau cire rigar cikina domin zafin da nake ji a zuciyata har jikina yake kutso wa. Zufa sai yanko mini take yi.
Na cire komai na d'aura zani. Na zauna amma ban daina jin zafin jiki ba.
Na fita har lokacin yana durk'ushe a inda na bar shi.
Na dauki botiki na nufi rijiya. Da azama ya tare ni, ya ce " Bana hana ki jan ruwa da kan ki ba?".
Ban ce komai ba na matsa gefe ya janyo mini ruwan. Ya kinkima ya kai mini band'akin.
Na shiga na yi wanka. Amma dana fito ina goge jikina da tawul, zufar na sake keto mini.
Na dauki rigar barci marar nauyi na saka, bayan na saka gajeran wando ta ciki. Na d'aure kaina da dan kwali mai taushi.
Kicin na fa'da na hau girki, ina yi ina hailala. Gaba'daya jina nake yi tamkar ba ni ba. Na yi matu'kar kad'uwa da abin da na ga ni a cikin gidan aurena.
Ban san falalar kuka ba sai a yau, domin gaba'daya hawayen ya k'i zuba.
Shi kuma ya takure, a gefe tamkar ka ce k'yat ya zura a guje. Cikin lokaci k'alilan nadama mai tsananin gaske ta bayyana a dukkan jikinsa. Ya kasa sukuni, da alamu kunya ce ta hana shi sukuni. Tunda ni dai ban bu'de baki na ce masa komai ba.
*Annur food Delicious*
*Da k'arfin zuciya da guiwa na ke muku shunen inda zaku samu kayan da na zano a kasa cikin saukakkan farashi.*
*Shaida nake yiwa kayan annur domin dadinsu da ingancinsu ya kai kurewa*
*HANZARTA ki nemi kayansu dan ki gasgata batuna*
*Garin kunun tsamiya garin danwake, garin borkono, yajin daddawa, man shanu, nikekkakiyar gyada ta kunu da ta miya*
*08039183880*
✍️
*Dandano*
*DAGA Littafin BAK'AR TA'ADA*
*NA SURAYYA DEE*
*MARUBUCIYAR HALIN YAU DA SABO DA KAZA*
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/GICSrs9TfxG1Q6FUXiu1Qg
*Ina tallata muku make up artist din Guduyo*
*Aisha Lame mai kayan kwalliyar yan gayu*.
*Jakadiyar oriflame, duk wani nauyin kayan oriflame tana kawo su cikin farashi mai sau'ki*.
*Ba iya kayan kwalliya masu daraja ba, ita din GWANAR sarrafa pop corn ce(gugguru), ni shaida ce ta hakika*.
*Sannan tana da spices kasaitatu. Masu mayar da girki ya zama na alfarma*
*07036662633*.
*INA SANAR MUKU ZAMU BUGA LITTAFIN KANA NAKA ZUWA HARD COPY*.
*MASU BU'KATAR MALLAKAR NASU SU TUNTU'BE NI, KO SU TUNTU'BI MARUBUCIYA JANAFTY*.
*BISMILLAHI RAHAMANIR RAHIM*.
Na gama komai na kai falo kamar yadda na saba. Shi kuma ya zama mutum mutumi.
Na fito na ce "Ga abinci ko sai ka dawo daga masallaci?"
Ya zuba mini ido ya rasa abin fa'da.
Ya tashi ya ce "Da sauran lokaci ai."
Na zuba mana kamar yadda na I'm. Amma gaba'daya mun kasa ci sai faman juya shi muke yi.
Gara ni na ci loma biyu na ji mak'oshina ya cushe na ajiye. Shi kuwa yama kasa kai wa ba'kin nasa.
Ya gaji ya kalle ni ya ce Dan Allah Yabi ki yi ha'kuri, ki yafe mini".
Ba ja in ja na ce "To".
Daga haka kuma ban sake ce wa komai ba. Ya yi maganganu na ban ha'kuri da nuna nadama masu yawa amma ban ko kalle shi ba. Aka kira sallah ban yarda na bu'de baki mun yi magana kamar yadda yake fata. Ya yi alwala ya tafi masallaci.
Har muka haramar kwanciya ban bu'de baki na ce k'ala ba. Duk jaye-jayen maganarsa kuwa. Da muka kwanta ya fara lalubata ban hana shi ba, amma ko kwakkwaran motsi ban yi ba. Ya yi duk abin da zai yi dan na motsa ko na mayar masa martani amma tamkar an shuka dusa.
Ya gaji ya koma ya kwanta yana fa'din "Innalillahi wa ilaihir rajiun" .
Ya ru'ko ni da rawar murya ya ce "Yabi ki yiwa Allah, ki bu'de baki mu yi magana".
Yana rufe baki na ce"To".
"Asiya ki yi ha'kuri, ki yafe mini, dan Allah, dan Annabi, ki yafe mini".
Na yi shiru. Ya sake ce wa Bansan me ya same ni ba Yabi. Dan Allah ki mini uzziri ki yi ha'kuri ki gafar ce ni".
Nan ma na ce "To".
Ya yi iya ban hakuri, amma ban yarda na ce komai ba.
Da gari ya waye da wuri ya dawo daga masallaci ya hau hidimar gyaran gida.
Ya yi abin karya wa. Har d'aki ya kawo mini amma ina ci sau daya ban sake kai wa na biyu ba, na ce na koshi. Ya yi shiru ya rasa yadda zai yi.
Bai fita ko ina ba. Yini aka yi ana zuwa lalle amma ban iya yiwa ko mutum daya ba. Sai ha'kuri nake basu tare da uzzirin cewa bani da lafiya ne.
Hakan da ya ga ni ya sake rib'anya tashin hankalinsa. Domin yasan yadda nake matu'kar son sana'ata. Bana son abin da zai hana ni yin lalle ko kitso.
Amma da bakina nake sallamar mutane yasan al'amarin da yake zuciyata ba k'ank'ani ba ne.
Kwanaki uku muna cikin wannan halin. Daga ni har shi, mun yi matu'kar rame wa tunda bama iya cin abinci ga rashin nutsuwar zuciya.
Ya yi juyin duniya mu yi magana na ki, domin har yau ban yarda na yi masa korafi ba. Komai kuma zai ce sai na amsa da "To". Kullum safiya zan gaishe shi, zan kuma amsa sallamar sa idan ya shigo. Daga hakan kuma bazan sake yarda na ce komai ba. Rashin yin lallen har zuwa lokacin ya fara ta'bamu tunda shi ma baya iya fita, ko ya fitan ma baya nisan kiwo zai dawo.
Ranar da aka yi kwanaki biyar da faruwar al'amarin, ya zauna ya bani hakuri tamkar yawun bakinsa zai k'afe. Har da k'wallarsa. Amma ban ce komai ba, sai ma murmushi mai ciwo da na yi na ce masa "To me ka yi ne?"
Duk da k'arancin shekaruna amma na fahimci shirun da na yi masa ba k'aramin dafa shi take yi ba. Ba abin da yake so irin na yarda mun yi magana ko da rashin kunya ne na yi masa. Amma ban yi hakan ba. Ni a karan kaina so nake na yi kuka, na caccaba masa maganganun da zasu gasa masa zuciya tamkar yadda ya yi dalilin da tawa zuciyar take gasuwa, amma na kasa.
Tsawon sati guda muna cikin wannan matsanancin halin, daga ni har shi mun zama wasu iri. Gidanmu ya koma tamkar na zaman makokin mutuwar uwa mahaifiya.
Sannan na k'i yin k'unshi har lokacin. Al'amarin da ya sake damalmala mana komai.
Shi kam kawai k'arfin halin da aka san maza da shi ne. Amma kana kallonsa kasan yana dandanar kudarsa da shiruna. Yadda bana cin abinci haka shi ma baya ci. Gara ma ni da daddare na kan yi barci, amma shi duk juyin da zan yi zan gan shi kan sallaya ko yana zaune ko kuma yana sallah.
Da asuba ya dawo ya tarar har na koma na kwanta.
Ya zauna a bakin gadon. A sanyaye ya ce "Yabi wai a haka zamu rayu ne? Bazan iya wannan rayuwar ba. Ki yiwa Allah da ma'aiki ki bu'de baki ki fa'di duk abin da kike so. Na ro'ke ki ba dan ni ba, da Allah nake ha'da ki."
Ko motsi ban yi ba. Bare na tanka masa.
Ya tsananta da magiya. Sai kawai ji na yi cak ya dauke ni ya yi nufin d'ora ni