Showing 48001 words to 51000 words out of 184118 words
Chapter 17 - Bakar Taada Hausa Novel Complete
Domin baka ta'ba ganina na yi ba.
Allah ne shaidar na yi tuba, Allah ne shaidar tunda na yarda aka zartar da hukuncin da ya yi a kaina ban sake yi ba.
Amma kun rike abu kuna ta faman jifana da shi."
*UMM NIHLA COLLECTIONS*
*Ta k'ware wajen kawo yadina masu kyau da sauki, cotton da silk, embroidered, Batik*
*A Malaysia take daga can kuma take turo su Kano direct. Dan haka kayanta akan farashi sari take bayarwa, daga guda daya har zuwa dari zaku samu*
*Kayan ta masu aminci da rahusa ne, ku tuntube ta Whatsapp dan ganin JERIN gwanon yadinanta da basa kode wa ko jeme wa*.
*07020695644*
*What's app only*.
Ya fa'da cikin wani irin yanayi na bacin rai mai tsananin gaske.
Dada ta zuba masa ido cikin son ta nazarce shi.
Ta k'asa ha'diye abin da ta fahimta akan sa cikin dak'ik'a.
Ta nisa ta ce "Mai sunan manya, shin ka fa'da komar Yabi ne har haka?"
Takaicin ta ya k'ume shi.
Bata ce da Jabir komai ba, da yake faman sakin maganganun da suke nufin tozarci a gare shi.
Amma tana neman shiriritar da maganar. Bai ce mata k'ala ba ya juya tamkar ya tafi, sai kuma ya toge a jikin bishiyar zogalen da take gefen dakunan ka'dan. Cikin bacin rai na sosai.
Yayin da jikin Jabir ya yi sanyi domin ya fahimci ba k'aramin son Yabi Tijjani ya afka ba. Sannan ya ji kunyar maganganun da ya ji yana yi a kansa.
Dada ta kalli Jabiru ta ce "gara ma da baka auri Yabi ba Jabir. Na fahimci irinsu ne matan jaraba. A kansu ba abin da namiji ba zai yi ba. Mafi yawa haka zaka gansu yan firit amma suna murza mazaje ingarmai. Yadda kake sanyi k'alau din nan ba zaka sarrafa ta ba. Ko mai sunan manyan da yake a tsaye, tun komai bai gitta a tsakaninsu ba, ga shi nan yanayinsa ya nuna ta riga da ta shiga ransa ta yi kane kane".
Cikin jin nauyin maganarta Jabir ya ce "wacce irin magana ce haka Dada da girman ki?"
Ta nisa ta ce "Gaskiya ne mana! Kawai murnar da nake yi masa d'aya ce. Ta iya sana'ar samun ku'di, dolenta ta fito da ku'di su ci abinci. Idan ku'din da suke saka ta yiwa iyayenta raini basa zama mata ai ta nutsu ta girmama manya".
Tana rufe baki Jabir ya ce "Haka su Baban suka fa'da miki shiyasa kika tirsasa aka yi wannan bahagon hadin?"
Ta yi dan tari kafin ta ce "Gaskiyarsu ne ai! Sannan shi mai sunan manya tunda ba shi da sana'a asirinsa zai rufu".
Jabir ya ce "Gaskiya kun kassara rayuwarta, amma akwai Allah. Ina fatan alheri ya biyo baya, sai dai har yau din nan ban hakura ba. Na sani *Hannu daya* baya daukar jinga. Bazan ha'kura da ita ba har sai na ga ranar da aka shafa fatiharta da wanina. Daga ranar na zubar da makaman nemanta. Amma matu'kar ban mutu ba idan an kaddara mini cikar burina zai zama gaskiya. Idan da rabona zata dawo mini, ni kuwa zan aureta komin tsufanta, domin ita nake so ba wani abu a tare da ita ba".
Dada ta kyabe baki ta ce "Idan k'asa ta rufe mini ido komai ma sai ku yi tunda ban ga ni ba".
Tijjani da yake jinsu zuciyarsa ta dinga bugawa da k'arfin da ya zarce ka'ida.
Yana son ya je ya fa'da wa Dada duk lalacewarsa bata kai mace ta ciyar da shi ba, bai yi mutuwar zuciyar da macen aurensa zata dauki nauyin kanta da nasa ba. Sannan ta fahimtar da y'ay'anta hakan.
Amma sai ya daure ya ha'diye. Ya ja jikinsa ya fa'da dakinsa ya fa'da kan katifarsa.
Wani irin yanayi na shigar sa na tsananin bacin rai da ya sababa masa k'arfin zuciya.
Domin gaba'daya ji ya yi hatta dako na daukar buhun gero da na su wake zai iya yi, dan ya ciyar da Yabi da guminsa ba wai ta ciyar da su ba.
Idonsa ya ciko da hawayen tausayinta domin ya gane k'iyayyar da ake yi mata ne ya sanya aka bashi aurenta.
Ya yi shiru yana nazari wato saboda ana ganin shi din lalatacce ne. Ana ganin shi ba zai amfana wa kansa komai ba, bare ita ta amfana da shi. Ana kuma fatan ya dauwama cikin lalace wa da mutuwar zuciya.
Sai ya tsinci kansa da tambayar shi da Yabi wa aka fi tsana ne a gidan Marina?"
Take ya muskuta ya janyo wani kwali.
*Idan kina bukatar Oriflame products ko wanne irin ne, ko Kuma kina sha'awar yin register da su*. *Ki tuntubemi babbar dealer din su Aisha lame*
*Ina kuma fad'a muku akwai da daddan ganyen shayi na Lame Tea*
*Akwai pop corn*
*07036662633*
*Lame fa garin su Yabi ne*
Ya dauko memo da biro, ya yi rubutun magananun Jabir, da wanda su Baban Tsakiya suka yi da ya ji a harshen Dada.
Da irin manufar ba shi Yabi. Da yadda ake fatan ta tabbata cikin halin ni 'ya su.
Sai kuma ya je shafi na gaba sosai ya rubuta "Zan yi komai na halal dan na sauke nauyin da yake kaina.!
Allah ka sani ban sake aikata zina ba! Allah ka taimake ni ka cigaba da tsare ni.
Allah ka fahimtar da ni sarrafa mace ta yadda Yabi zata rayu cikin farin-ciki a hannuna.
Allah ka hore mini kofofin arziki ta yadda zan sauke nauyinta ba tare da tallafinta ba.
Na sani al'kawarin ka baya tashi, da kanka ka yi al'kawarin taimakon wanda ya k'udire niyyar aure saboda kai. Ga ni bawanka, Ibnu bawanka cikin kankan da kai, ka taimake ni, ka kubutar da ni kunyata a idonta da na dangimu. Allah ka hore mini lafiya, ka sanya mini hakuri akan sha'anin ta, sannan a mallaka mini zuciyarta da tunaninta." Sannan ya rubuta kwanan wata.
Ya rufe yana jin girman k'alubalen da yake gabansa.
Wani irin son ta da tausayinta yana sake bin dukkan jikinsa yana kutsawa.
Har yake jin anya akwai wanda ya so mace kamar yadda yake jin son Yabi ya sake shak'e shi a yanzu?
Domin shi son ta yake yi babu wani dalili na sha'awa ko na burge wa.
Na farko yafi son manyan mata masu manyan halittu. Yabi kuma yar mitsil mai k'ananun halittu, maimakon ya ga ba hakan yake so ta zo ba. Sai yake jin ko bata da komai na cikar mace yana sonta a hakan.
Na biyu yafi son mace mai sanyin hali, mai kawaici.
Amma daga ranar da aka jefa masa sonta shikenan ya ji da tsiwarta zai yi amfani wajen kutsawa dan ya sami kusanci a zuciyarta.
Ya sani ba zai yarda da rashin kunyar da ta wuce ka'ida ba.
Amma yana fatan a cikin rashin kunyarta ya dinga isar mata da sakwanni masu girma.
Na uku akan abin da aka yi mata na tirsasa Jabir auren Maijidda, da kuma yadda uwar Nasiba ta ture komai na zumunci ta fadi maganganu marasa dad'i a gaban mahaifiyarsa! Shike nan ya k'yamaci auren zumunci.
Amma a yanzu yadda yake jin Yabi zai iya yin komai dan ya same ta.
Ya gamsu tausayi da sonta sun masa rubdugu.
Ya rufe littafin ya mayar da shi ma'adaninsa.
Ya jima a zaune yana ta tunanin sana'ar da zai fara.
Ya saki gauron numfashi! A fili kuma sai ya ce "Allah ka hana Tijjani sanya Yabi kuka! Allah ka hana ni zaluntar ta. A hore mini ita ya Ubangiji".
Ya zabura ya mik'e yana ganin lokaci ya yi da zai daina buga buga ya samu tartibiyar sana'ar da zai dogara da ita tunda nauyi mai yawa ne zai hau kansa, wata'kila ma badi war hakan yana shirin zama Abba.
Murmushi da kunya suka subuce masa ya dinga sosa k'eyarsa tamkar yana gaban manya ne.
A fili ya furta wa ya ga "Yabi as uwa?"
Sai dariya ta sosai ta kama shi, har bacin ran da Jabir da Dada suka cusa masa ya yi sauki.
Ya fito ya nufi wajen Alh Tsoho magini dan ya ji ko zai masa hanyar samun aikin ginin.
Yana tafe sanye da yadi na wando da riga bata kai guiwar sa ba.
Kamar kullum a wanke suke amma fa babu guga.
Sannan ya saka hular sanyi ya rufe gashin kansa.
Domin tunda aka furta za'a bashi auren Yabi. Bai sake yarda an ganshi da gashin kansa ba, duk da ya ki aske wa.
Ba wanda yake jin kunyar ya ganshi da sumar irin Baban Marina. Domin ya sani baya so, ya sha tisa shi a gaba ya saka a masa askin akan dole.
A yanzu kuwa wata irin kunyarsa yake ji ta sosai domin bayan kawunsa ne da yake yi masa adalci, yanzu shirin zama surukinsa yake yi.
Bulkachuwa da kansa ya yi amannar ba dan zuciyar Baban Marina irin ta daddako ba ce da ba za'a yi masa wannan k'arfin akan diyarsa ba. Ba dan alherinsa mai yawa ba ne, da ba zai ba shi aure ba, komai za'a yi kuwa.
Amma ya yi shahadar ba shi, babu dogon turanci. Yana tafe yana fa'din "Allah ka fitar da Tijjani kunyar Baban Marina".
Ya sha kwanar shiga cikin wani kwararo sai kawai ya fara jin k'amshin turaren da yake ji a jikin Yabi da kuma wanda yake shaka a jikin Jabir.
Ya shiga sai kuwa ya hangosu kowannensu jingine a garu.
Wani irin tashin hankali ya ziyarce shi.
Kishi mai tsananin gaske ya dabaibaye shi.
Tamkar ya juya sai kuma ya tsinci kansa da tunkararsu.
Ya zuba musu ido. Yabi na kuka sosai yayin da Jabir idonsa ya kad'a ainun.
Sau d'aya za'a kallesu a gane suna cikin tsananin soyayya da kuma halin cankacakare.
Ya kalli Jabir da yake tsab da shi cikin shadda ruwan toka ta sha guga. Farin gilass ya mak'ala.
Ga k'amshi mai da'di na tashi a jikinsa domin komin hassada baka isa ka ga wani abu na rashin tsabta ko gayu a tare da Jabir ba.
Yayin da Yabi take sanye da hijabanta har k'asa sai dai duk ya b'aci da hawaye har da ba'kin kwalli.
Kishi sosai ya turnike Bulkachuwa.
Har ji ya yi zukar numfashi na neman yi masa turjiya.
Amma a hakan ya motsa k'wanjinsa ta hanyar cewa "Jabir na tabbatar babu jahilci a tare da kai tunda ka yi zurfi a ilimummuka daban daban. Sai dai abin mamaki sanin naka bai amfana maka komai ba, tunda zaka iya tsayawa da wacce kwanaki kadan ya rage a daura mata aure a cikin lungu inda babu sawu.
Ni ba zan yi maka rashin adalci na yi maka kazafi irin yadda ka yi mini ba.
Sai dai na sha fa'da kai din azzalumi ne, ba masoyi ba. Ta ya ya an baka aure ka karba, dan kwadayin albarkar iyaye ita kuma ka dinga hure mata kunne da ga yiwa nata tsohon biyayya? Ban da ita din sakara ce har wanne kalami ne a bakinka da zaka tsara mata da yafi na ubanta da kannensa tasiri?".
Jabir ya sandare ya zuba wa Bulkachuwa ido, yana jin wata irin fargaba from no where tana shigarsa.
Yayin da ni kuma na dago ido jage jage da hawaye na watsa masa kallon kiyayya da raini na ce "Ba ruwan ka da ni Tijjani! Na saurare shi din, domin shi nake so, nake fatan kasance wa da shi".
Ga mamakina sai kawai ya ja kakkuran tsaki tare da ce wa "Ai ke din shasha ce! Kuma kin ji na saka maganata da ke?
Da shi na ke wanda na gamsu da hankalinsa da iliminsa, kawai adalcinsa ne bai gamshe ni ba. Amma ke da baki da hankali ina ruwana da ke?
Jiyan nan na gan shi da matarsa a asibiti yana ri'ke da ita. Yana faman tattalinta. Wai matar da ya aure ta ba dan yana so ba yake yiwa irin wannan son da adalcin, amma ke kullum yana cikin dama miki lissafi. Da yake ya mayar da ke shargalle marar tunani."
Ai kuwa yana rufe baki kuka ya k'wace mini sosai.
Jabir ya kasa magana domin ya tabbatar Bulkachuwa ya gansu a asibiti ba k'arya ya yi masa ba.
Bulkachuwa ya sake yin k'uta tare da nuna Jabir da yatsa ya ce "Neman aure cikin aure haram ne in ji ma'aiki (S.A.W).
Da ku'din aurena akan ta, ko ba zaka yi mini kawaici irin na zumunci ba, to ka yiwa ka'idojin shari'a biyayya. Ka fita mini a harkar Asiya! Ubangiji ya baka Maijidda wacce ita ce mafi alheri a gare ka. Amma bar mini Asiya Toro domin ina da yakinin akwai babban al'amari a tsakanina da ita. Daga ranar da aka tabbatar mini an ba ni ita, na fara addu'ar na yi nisan kwana mai yawa dan na tabbatar ni kad'ai na mallake ta".
Still Jabir ya kasa magana domin gaba'daya almarin ba k'aramin bugunsa yake yi ba.
Kishin Bulkachuwa ya shak'e shi k'warai da gaske. Domin idan gaskiya zai fa'da ya ga son Yabi a idonsa irin wanda bai yi zaton Tijjani zai yi mata ba. Mussaman yadda bai dauki soyayya da muhimmanci ba. Mace tana bata masa rai zai juya mata baya duk yarda yake da ita kuwa.
Ina kuka, ina kallon Yaya J. Na sani dan na yi ba'kin ciki ya sanya Bulkachuwa sako maganar Maijidda. Ban da haka mene ne dan ya nuna kulawa akan matarsa ta aure?
Nan da nan zuciyata ta hassala cikin rawar murya na ce "Mene ne dan ya kula da lafiyar Iyalinsa? Tabbacin nima zai kula da ni ke nan tunda har ya yiwa wacce baya so adalci to ina kuma a ce ni ce da yake so? Kai sau nawa ana ganinka da tambadaddun matan banza?"
Take jikin Yaya J ya yi k'wari domin yasan yadda nake da kishi na gaske, maganar Bulkachuwa na iya tunzura ni na yi masa fishi. Dan haka ya dan murmusa. Sannan ya ce "Ko yanzu na mutu a sanadin rashinki ba ni da kaico tunda kin mini kyakkawar shaida Yabin J".
Da rawar murya na ce "Idan ka mutu, kuma ka bar ni da wa? Wanne irin ba'kin fata ne, akan me zaka mini fatan irin wannan asarar haka?"
Tijjani ya harzuka ya ce "Ba zaka mutu ba ka ga yadda Asiya Toro zata manta da al'amarinka ba Jabiru.
Ya sake sakin tsaki sannan ya ce "Idan kuwa har ka mutu ba wanda ya yi asara irin abin da yake cikin Maijidda, sai kuwa ita Maijiddan, da zata shiga takabar mijin da yake sonta yake gudun bacin ranta".
Na sake fasa kuka ina fa'din "Allah ga Tijjani nan ya takura ni, ya fitine ni haka siddan, ka sani bana sonsa, ka gaggauta cire mini shi a duniya ta".
Sai lokacin Yaya J ya ce "Yi hakuri kin ji Yabi! Ko zan mutu ba yanzu ba, da saura In sha Allah".
Na wuce na fara tafiya a hankali.
Bulkachuwa ya ja tsaki ya ce "k'aryar banza! Dan Allah ka mutu yanzu Jabir. Da an ga tsiya domin kuwa ana dawowa daga rufe ka zan lallaba na koma. Tamkar wanda zan yi maka addu'a. Nan kuwa fitsari zan tsula maka a kabarinka ta yadda sai ka shekara a kwance kafin addu'ar jama'a ta riskeka, mussaman ta Asiya Toro. Kai da addu'a ta riske ka sai damina ta zo. Idan na so k'eta ma, daminar na dauke wa na sake tsula maka wani. Kuma idan juninka tsiya ne Maijidda na haihuwa zan aure ta. Na ha'da su da Asiya Toro su yi ta faman buga competition a kaina".
Na juya da nufin na yi masa raddi ya nuna mini yatsa ya ce "Idan kika kuma tozarta ni sai na fasa miki bakin ki domin ban yi da ke ba, marar kishin kai".
Jabir ya yi hanzarin ce wa "Kar ki ce komai Yabi cikin yanayi na kad'uwa sosai.
Ya kalli Bulkachuwa ya ce "Har zaka iya yi mini fitsari a kabarina Bulkachuwa? Sannan ka ce "zaka auri matata akan idona?"
Wani irin murmushi Bulkachuwa ya yi mai dauke da nisha'di da ma'anoni.
Ya ce "In dai son Asiya ya zama ajalinka zan tabbatar na hana adduarta riskar ka.
Sannan dan na auri Maijidda ai rufa maka asiri na yi tunda tare da abin da ta haifa zan ha'da na rikesu. Idan kuwa kana kishinta kamar yadda yanayinka ya nuna har ka kasa ha'diye hakan a gaban wacce kake kirarin kana so. To kawai ka k'yale mini Asiyata.."
*Akwai kaya masu kyau a cikin farashi mai sauki*
*Maganin sanyi*
*Saiwowin Tsumi*
*Saiwowin dahuwar kaza*
*Saiwowin dahuwar tattabaru*
*Gumba*
*Tsumin kwakwa*
*Y'aya'n gadali*
*Hadadden daka*.
*Tsugunno mai sa a matse*
*Goran tula*
*Goran tula syrup*
*Garin goran tula*.
*Maganin gyaran nono*.
*Zuma ta mussaman*
*Tsumi*.
*Da sauran kayayyaki na mussaman da basu da illah*.
*Domin kuwa asalin Saiwowin ne da ake kawo su daga Chad*.
*Abu mai kyau shi ke siyar da kansa ku tuntubi marubuciyar Halin yau dan samun naku kayan cikin sauki da mututantawa*.
*08032773332*
✍️
*WANNAN LITTAFIN NA KUDI NE BIYA KUDIN KARATUNKI TA WANNAN ASUSUN DAN GUJE WA BAKAR TA'ADA!*
*REGULAR 500*
*VIP 1K*
*VIA*
*2384876855*
*SURAYYA IBRAHIM DAHIRU*
*ZENITH BANK*
*KO*
*7061488065*
*SURAYYA DAHIRU IBRAHIM*
*OPAY DIGITAL SERVICES*
*TURA SHAIDAR BIYA TA WADANNAN LAMBABOBIN*
*08032773332*
*09069067488*.
*UMM NIHLA COLLECTIONS*
*Ta k'ware wajen kawo yadina masu kyau da sauki, cotton da silk, embroidered, Batik*
*A Malaysia take daga can kuma take turo su Kano direct. Dan haka kayanta akan farashi sari take bayarwa, daga guda daya har zuwa dari zaku samu*
*Kayan ta masu aminci da rahusa ne, ku tuntube ta Whatsapp dan ganin JERIN gwanon yadinanta da basa kode wa ko jeme wa*.
*07020695644*
*What's app only*.
"Shikenan idan ka yi haka ba zan maka fitsari idan ka riga ni mutuwa ba. Ba kuma zan aurar maka bebinka ba, tunda wani irin so kake yi mata wanda baka iya b'oye kishinta a gaban kowa"
Ba'kin ciki mai tsanani ya lullub'e ni.
Na kasa bu'de baki na ce komai domin na tabbatar yana iya fasa mini baki kamar yadda ya fa'da din tunda baya fa'dar magana da zummar wak'e.
Na juya na tafi, ina tafe ina hawaye, ina kuma ha'da hanya. Domin idan akwai abin da yake ci mini zuciya bai wuce a mini zancen Maijidda ba.
Na kuma fahimci Bulkachuwa yana son bani labarin irin tarairayar da J yake yi mata.
Na tuna tun kafin zancen aurena da shi ya b'ullo, ya sha fa'da mini yana ganin Yaya J goye da Maijidda a mashin dinsa.
Har na isa gida kukan sharbe nake yi.
Na shiga dakinmu na zauna bakin gado ina kuka sosai.
Domin abin ya ha'de mini, ga bacin ran auren dole da mutumin dana tsana ga kishin Maijidda da yake azalzalata tamkar zuciyata ta fa'do kasa.
Gwaggo ta kalle ni ta yi k'wafa tare da fa'din "ki yi ta kuka har hawayen idonki su k'afe, aure kuwa kinsan babu fashi".
Ta fice ta bar ni.
*Annur food Delicious*
*Da k'arfin zuciya da guiwa na ke muku shunen inda