Showing 114001 words to 117000 words out of 184118 words

Chapter 39 - Bakar Taada Hausa Novel Complete

hakan zai iya samu na a dalilin ganin wata a jikin ka ba?"
Ya fara sosa k'eya. Da k'yar ya ce "Ban san ya aka yi hakan ta faru ba. Ni gaba'daya am upset ma".
Na girgiza kai na ce "Hmmm".
Muka yi shiru sai kuma na ce "Kuma zaka zauna da ni idan ka gan ni a irin yanayin da na gan ka?"
Ba ja in ja ya ce "Ba zan iya ba".
Na zuba masa ido ina masa kallo mai tsananin gaske.
Na kaurara murya na ce "Amma kuwa son zuciyar ka azimin ne Tijjani."
Bai yi inkari ba. Bai ce komai ba, na kuma tabbatar da dukkan zuciyarsa ya bani amsar.
Kamar daga sama sai na ji ya ce "Mace daraja ne da ita sai wacce ta wula'kanta kanta. Duk matar auren da zata bada k'ofar da wani namijin zai mata waya, ko doguwar gaisuwa dama ai ba kamammiya ba ce. Ba kuma yadda za'a yi mijinta ya gasgata ta. Bare kuma a ce har ya ga ni da idanuwansa, tabbas ba zai zauna da ita ba, ko kuma idan ya ri'ke ta din ma bisa wani dalilin to fa har abada ba zata ji dadinsa ba."
Na sassauta na ce "Amma shi namiji idan yana sharholiyarsa ko da kuwa a cikin gidan aurensa ne dole ne matar ta yi hakuri ta zauna da shi ko?"
Ya kasa amsa mini.
Na zarce da ce wa "Ana rudarku da cewa duk abin da namiji ya yi ado ne, na mace ne kaico. To ka saurare ni da kyau abin da zan fa'da ka sani sai dai zan sake yi maka matashiya ne na kuma kafa maka hujja tunda yanzu ka sanya an tursasa ni na yafe maka.
Laifin namiji baligi da na mace baliga a banagaren barna duk daya ne a fuskar addini tunda duk hukunci iri d'aya Ubangiji ya zartar.
Al'amari irin wannan kuma bashi ne in ji Annabin Rahma. Idan mutum ya bata y'ar wani, shima za'a bata tasa. Idan ka yi da matar wani, kai ma za'a yi da taka.!
Na kaurara murya na ce "Na yarda baka yi zina ba Tijjani. Amma kana kusantar ta. Kana bin hanyar da ta bi. Ka sani kuma Allah da kansa ce wa ya yi kada mu kusance ta, ba wai kada a aika ta ba. Ina ro'kon ka, ka daina kusantar ta bare tsautsayi ya sanya ka fa'da yin ta da auren ka. Ina jin tsoro da zullumin kada na fara haihuwa a b'ata mini yara. Ina cikin fargaba kada laifin ka ya jefa ni cikin had'arin a lalata ni da aurena".
Ya zabura ya ce "To y'ar sarkin mugun fata da jawo bak'in alkaba'i."
Na kalle shi na ga ya shiga rud'u a dalilin furucina sosai. Kishinsa ya bani mamaki ainun.
Ban ji d'ar ba na ce "Gaskiya na fa'da maka, wacce Annabi ne ya fad'a tun gabannin kakaninmu su iso duniyar.
Bayan haka kuma ina son ka sani laifin da ka yi tabbas na ha'kura. Amma ina tabbatar maka idan na sake kama ka da irin wannan laifin to fa ka sani ka kuma ri'ke a zuciyar ka ba zan sake zama da kai ba Wallahi".
Ya matso kusa da ni ya rungume ni sosai yana fa'din "Da ikon Ubangiji bazan sake ba Asiya. Ki taya ni addu'a. Ina kuma ro'kon ki sake hakuri, ki shafe wannan al'amarin a zuciyar ki. Wallahi summa Tallahi iya abin da ya faru ke nan, kuma a wannan ranar na ta'ba yin hakan, kada shaidan ya rinjayar miki ce war na saba yi din ne.
Na kuma fahimci Ubangiji ya so ni da alheri ne shi yasa ma asirina ya tonu."
Na saki ajiyar zuciya mai nauyi na ce "Shike nan Allah ya yafe mana gaba'daya."
Ya sake ri'ke ni sosai yana fa'din "Na gode sosai, Allah ya sanya ki cikin bayinsa da yake kar'ba daga gare su."
Hawayen da ban san dalilinsa ba ya dinga zuba mini.
A hankali na ce "Ameen".
Shike nan muka rufe maganar. A ranar ma mutum uku suka zo lalle amma hakuri na basu da gabatar da uzzirin ban warware ba. Domin gaba'daya na rasa karfin zuciyata. Rauni mai yawa nake jin yana bina. Sannan wata irin karaya da al'amarin Tijjani ya haifar mini da gajiya da kasala masu nauyi a zuciyata wanda gangar jikin ta rasa k'arfi da kuzari.
Bai ce komai ba. Amma jikinsa shima ya mutu domin ya fahimci k'arfin halin da nake yi iya gangar jikina ne kawai.
Da daddare ya ri'ke ni, ya dinga rarrashi, da ban baki irin wanda sai masanin falsafa ne zai dinga harhada kalaman masu nauyi a mizanin masalaha.
Na amsa da ce wa "Na ha'kura da gaske."
Ya ce "To me yasa ba zaki y lalle ba Asiya? Na sani kuma ke ma kin sani, rufin asiri ne mai yawa sana'ar taki take yiwa jama'a."
Murya na rawa na ce "Zuciyata ta karye, jikina babu k'wari."
Sai kuma na ke ce da kuka fiye da wadda na yi a gabansu Malam.
Ya kasa ce wa komai tsawon lokaci mai yawa ina kukan, shi kuma yana shafata tamkar jinjira.
Na jima ina kuka bai hana ni ba. Har sai da kukan ya tsaya cak dan kansa. Na koma ina ajiyar zuciya mai d'auke da shesshek'a.
Ya sassauta murya ya ce "Kin yi kuka Asiya da ikon Ubangiji ba zaki sake kuka akan irin wannan al'amarin ba. Ki yi ha'kuri, wannan rufin asirin da kika yi mini, ni ka'dai nasan yadda na sake jin ki a raina. Ni ka'dai nasan yadda girman ki da nauyin ki suka yi mini rubdugu. Ke yarinya ce k'arama amma hankalin ki na manya ne. Kin yi k'ank'anta kin tsunduma cikin irin wannan bak'in-cikin. Ina ro'kon Ubangiji ya sanya wannan ne kukanki na karshe akan wannan matsalar a dukkan rayuwarmu gaba'daya".
Na amsa da"Ameen" a hankali.
Murya babu amo na ce "Bana son wannan gidan, ba zan yi farin-ciki a cikinsa ba. Ka samo mini wani ko daki daya ne zan zauna".
A hankali ya ce "Da ikon Allah zan samo miki, amma ki d'aure zuwa lokaci ka'dan kin ji".
Na ce "To shike nan".
Ya dinga fa'din Na gode sosai my little. Allah ya bani dama da zan jiyar da ke da'di mai yawa".
Na ce ni "Ka tsare mini mutuncina da naka da kuma soyayya da tattali nake so fiye da komai".
Ya ce "zan miki Asiya, zan yi kokarin kiyaye ko wacce irin BAK'AR TA'ADAR da zata sanya ki kuka. Yanzu yaushe zaki fara yin k'unshin dan na tabbatar kin huce kin kuma yafe mini?"
Na shagwaba na ce "Sai ka yi al'kawarin ba zaka dinga yi mini sababi akan k'aramin abu ba. Bana son shouting".
Ya numfasa ya ce "Zan dinga k'ok'arin ina yin fa'dan a hankali. Amma bazan yi al'kawari ba, kin san wani lokacin ha'kurinmu k'wace wa yake yi, abin da zaki fahimta shine sab'awa a zamantakewar aure ba k'iyayya ba ce, matu'kar kuskure ne irin na zaman yau da kullum ko kuma sab'anin ra'ayi".
Na ce "Tom shike nan jibi zan fara yi In sha Allah"
Ya tsananta rik'on da ya yi mini yana fa'din"Thank you my little girl".
Daga hakan kuma ya shiga bai baye ni da zafaffar soyayya mai goge dukkan tsatsar zuciya.

Washagari muka yini cikin nutsuwa da walwala mai yawa. Tun safe kuma na yi status da cewar gobe idan Allah ya kai mu zan fara k'unshi.
Shike nan na ha'kurkurtar da zuciyata na manta komai.
Na rungumi mijina da sana'a ta. Illah iyaka na yanke mua'amala da Rafi'a. Mahaifiyarta kuwa ban fasa gaishe ta ba, ban fasa mutuntata ba. Illah iyaka shiga ne bana yi. Ita ma kuma Rafi'a din ta daina shigo mini.
Wata biyu da faruwar hakan na fara wani irin zazzabi mai zafin gaske. Domin kwana nake yi mutsutsukun ciwon jiki. Gaba'daya ji nake tamkar ana kwankwatsa mini kasusuwan jikina. Ga bana iya cin abinci.
Haka nake kwana ina yini cikin wannan halin. Sa'armu d'aya akwai kayan abinci tare da mu. Sannan yana k'ulla lallen da siyar da ruwa. Babu matsalar babu sosai a tare da mu. Kwana biyu ina ta shan maganin zazzabi da na rage rad'ad'in ciwo. Amma babu sau'ki kullum gaba ciwo yake yi.
Hakan ya sanya shi fita ya yi buga bugarsa ya samo ku'di ya ha'da da wanda muke da shi, ya kai ni asibiti.
Yini muka yi domin sai da aka k'ara mini ruwa. Aka yi mini gwaje gwaje.
Da yamma aka sallame mu bayan sun tabbatar ina da ciki na wata daya har da sati biyu.
Duk yadda nake jin rashin kwarin jiki amma sosai na yi murna. Ni da Tijjani ban san wanda yafi murna da zumudi ba.
Muna isa gida na dauki waya na k'ira layin Gwaggo.
Tana dauka ta ce "Yabi ya jikin dai?"
Da azarbabi na ce "Hmmm Gwaggo ashe duk wannan wahalar da murkususun da nake yi ciki ne da ni!"
Ta yi shiru, sai kuma ta ce "Ni kika kira ki fa'da wa hakan Yabi? Wacce irin marar kunya ce ke haka?"
Na yi sakare domin ni ban ga wani laifin ba. Ita ce uwata bani da wacce ta fita a halin yanzu. Ita ce mafi kusa na tattauna dukkan farin-cikina da ita. Zan yi kokarin na boye fa'da mata damuwar da nake ciki domin na yi amanna damuwata zata tsayar mata da dukkan farin-cikinta ne.
Na sanyaya murya na ce "Gwaggo ki yi ha'kuri. Ina cikin murna ne. Kin san kwanaki a gidan nan aka fa'da mini ce wa Tijjani ya gama zubar da yaransa a titi ni bazan haihu ba. Sannan kuma ke da bakinki kika ce sai na haihu da ki zo ki ga muhallina".
Ta sassauta ta ce "To ba sai ki bari na fahimta ba, ko na ji a bakin yayarku ko kuma Nazira".
Na ce "To sake yin hakuri Gwaggo ai yanzu na fahimta. Idan zan yi ta biyu, bazan fa'da miki ba. Sai dai kawai a ce miki Yabi ta haihu"
Ta ja tsaki ta ce "Allah dai ya baki lafiya" tare da kashe wayarta.
Tijjani da yake gefe yana ta faman murmushi ya ce "Burinmu ya cika.
Yanzu fa'da mini sunan nawa?"
Na yi dariya na ce "Ai sai na haihu".
Ya girgiza kai ya ce "Kin ce da zarar kin samu ciki zaki fa'da mini fa".
Na ce "Haka ne".
Ya ce "To fa'da mini na ji".
Na murmusa ka'dan na ce "Abbanta".
Ya kwashe da dariya ya ce "Wanne irin suna ne wannan? Duk yadda kika kwadaita mini zakuwar samuwar cikin a iya wannan sunan zan k'are?
Abbanta kuma. Wace ce?"
Na jingina a jikin kujerar na ce "Bebin mana."
Ya sake fa'dada dariyarsa ya ce "To idan namiji ne fa?"
Na ce "Ai kuwa sunan da zan fa'da maka mai wuyar samu ne indai namiji na haifo tunda na fa'da maka mai kama da kai nake so".
Dadi ya kama shi ya ce "Allah ka kula mini da Asiya. Ka taya ni son ta, ka shiga dukkan kasafinta. Duk al'amarin da zai dunfaro ta, Ubangiji kada ka bar ta da iyawar ta.
Na ce "Ameen" a gajiye domin wai maganar da na yi har na gaji na fara haki.
Haka nake kwana da yini babu lafiya. Duk dare bama barci kwana muke muna fama. Domin gaba'daya ni dai babu sau'ki. Kwana nake magogo. Haka kuma Tijjani baya runtsawa. Tausa yake yi mini, da fifita idan babu wuta. Tin a lokacin muka fahimci zama iyaye ba karamin al'amari ba ne. Duk yadda na zaku na samu ciki sai da na fara sare wa. Murnata ta fara koma wa ciki dan tsananin wahalar da nake ciki.
Al'amura suka fara yi mana tsauri a dalilin ku'di ya fara yanke mana.
Haka da safe idan ya tallafa mini na yi wanka, ya shafe mini jiki da man zafi zai fita ya dan yawata. Idan an yi sa'a ya samu aiki ya samo ku'di, zai siyo mini 'dan abin kwadayi. Watarana kuma hakan zai dawo.
Baya kuma nisan kiwo, ko ya fita hankalinsa na kai na.
Sai na samu sau'ki, sai kuma jikin ya sake rikice wa.
Na fara gazawa. Rannan Baban Marina da ya zo duba ni, ya ga yadda na koma gaba'daya na yi yaushi.
Ya bashi umarnin ya kai ni gida, ko shima ya d'an huta.
Bai musa ba kuwa washagari da hantsi ya dauke ni da jakar kayana ya kai ni gida. Har da siya mini su maltina da madara da indomi da zan dan yi kwanaki ina ci. Wanda na tabbatar ya ha'da da bashi.
Da k'yar na shiga muka gaisa da Dada wacce bayyana farincikin da ta yi a dalilin samuwar cikin bata lokaci ne.
Ya kira Ikilima ta ri'ke ni zuwa cikin gida. Na sani kuma dan ya mutunta iyayenmu ne ya sanya bai ri'ke ni da kansa ba.
Yadda Tijjani ya ha'do ni da shirgi da maganganuwana. Sai ka rantse har cikin zuciyarsa yake nufin na zo na yi goyon ciki a gida.
Kwana na biyu a gida na fara samun sau'ki tamkar a gidana ciwon yake. Domin ina barci, da safe kuma ina shan koko na ci dumame.
Sannan Gwaggo da kanta take daddana mini jikina. Har gasa mini jiki take yi da tawul. Ga shi duk abubuwan da nake son ci na gargajiya ina samu.
Kwatsam ranar da na yi kwana uku sai ga shi ya ce shi ya gaji da rashina sai dai mu koma gida.
Na tubure akan sai na ji k'warin jikina.
Shima ya kafe. Kuma wai ni ce zan ce ina son komawa gidana.
Nan da nan na rantse akan bazan fa'da ba.
Ya jijjiga kai ya ce "Shike nan tunda babu taimako da fahimta a tsakaninmu. Ni zan fa'da wa Baban akan na gaji ina son ki koma dakinki. Dama kunya da nauyinsa ne suka sanya na kawo ki."
Da yamma ya dawo akan na taimake shi mu koma gida. Ya kasa fa'dawa Baban zai tafi da ni. Na ce "Ni dai na fi son zaman nan".
Nan da nan ya tunzura ya ce "Saboda bani da ku'di ko Asiya?"
Na kalle shi a razane. Ya ce "Haka ne mana. Inba hakan ba wace ce ta taba zuwa gida dan bata da lafiya a gidan nan?"
Na ce "Ubaida bata dawo ba?"
Da hanzari ya ce "Amma duk jinyar da ta yi da ciki ai bata dawo ba. Sai da ta haihu. Ke kuwa ai ba haihuwa kika yi ba. Idan ba gazawa ta aka ga ni ba. Mene ne zai sa ayi mini wannan umarnin?"
Na sake kallonsa cikin tu'ajjibi na ce "Baban Marina kake fa'dawa hakan ko kuwa wa?"
A tunzure ya ce "Asiya na ke fa'dawa saboda ita ce zata ce masa ta samu sau'ki."
Idona ya ciko da hawayen takaici na ce "To".
Daga hakan na k'ulle bakina ban ce masa komai ba.
Ganin hakan sai jikinsa ya yi sanyi. Ya ce "Ya muke ciki?"
Ko kallonsa ban yi ba.
Ya gama zamansa ban sake kula shi ba.
Da daddare ma ya dawo, ban yarda na kula shi ba. Domin idan akwai abin da yake b'ata mini rai da shi idan muna magana ya dinga sako babun shi ne. Na kuma lura idan ban taka masa birki ba, ba wanye wa k'alau zamu yi ba. Tunda yana nema ya mayar da ita sara.
Washagari sassafe sai ga Babah ta Bulkachuwa ta dira a gidan. Ina daga daki na ji suna gaisawa da Baba. Ya ce " Hauwa kamar ba kwanaki ka'dan da suka shud'e kika zo duba y'arki ba. Me ya sake dawo da ke kuma yanzu? Mata kuna da son sabgar yawo.
Ta ce "Ba hakan ba ne Yaya. Shi ne ya mini waya wai jikin Yabi ya yi tsananin da ka ce ya dawo da ita gida. Sai ya ro'ki na zo na zauna masa da ita. Ni kaina hankalina ba kwanciya zai yi ba idan ba zuwa na yi na ganta ba."
Baba ya numfasa ya ce "Ai shi Tijjani bai gamsu zan kular masa da iyali dan karan kansa ba, sai ya zargi na yi masa fin k'arfi saboda y'ata ce?".
Ta diriri ce ta ce "Haba Yaya ni Wallahi har kasa na ji babu da'di."
Ya ce "To ki ji mana. Ban da dai ke ma kin banbanta ta ya ya zaki zo ki ce mini "Zaki dauki matar Tijjani a gaba na?"

✍️

*UMM NIHLA COLLECTIONS*
*Ta k'ware wajen kawo yadina masu kyau da sauki, cotton da silk, embroidered, Batik*
*A Malaysia take daga can kuma take turo su Kano direct. Dan haka kayanta akan farashi sari take bayarwa, daga guda daya har zuwa dari zaku samu*
*Kayan ta masu aminci da rahusa ne, ku tuntube ta Whatsapp dan ganin JERIN gwanon yadinanta da basa kode wa ko jeme wa*.
*07020695644*
*What's app only*.

Ta shiga ba shi ha'kuri, shi kuma ya dinga yi mata sababi. Yana fa'din "Da kam nan da kwana biyu na yanke zata koma zan ha'da ta Mamarsu ta je ta zauna da ita ko na sati ne kafin jikinta ya yi k'wari. Amma yanzu na fasa ba zata koma ba. Ki fa'da masa na ri'ke ta, sai ta haihu tunda ba shi da kunya, ya banbanta, ya nuna uwarsa ce ka'dai zata yi wa iyalinsa hidima.
Ai kuwa Babah ta dinga ba shi hakuri, ta lallaba ta zame kanta ta bar Tijjani tsundum cikin maganar.
Ta shigo d'aki ta duba ni. Ta bani leda mai d'auke da soyayyun kaji. Da kuma soyayyar awara da ta sha yaji mai da'di fal leda (K'ara'i).
Na fahimci duk yadda Babah bata shiga al'amarin Bulkachuwa Amma bata dauki abin da ya shafe ni da sau'ki ba. Samuwar cikin jikina kuwa sai na fahimci k'arfin soyayyar da take yi masa. Domin farin cikin da take ciki duk wanda ya rab'e ta sai ya gane hakan. Kusan kullum sai na amsa k'iran abokan arzik'inta. Suna mini sannu da jiki. Daga samuwar cikin zuwa yanzu na manta adadin da ta zo duba ni.
A dakin Gwaggo ta shigo ta same ta suka hau cakar juna, tunda k'anwar miji ce. Gwaggo ta ce "Oh ni Asma'u ina ganin kananci a wajen Hauwa. Kina zazzame wa akan sha'anin yara. Amma tunda kika ji zaki yi jika sai b'are b'are kike yi da sintiri a hanya tamkar a kanki za'a fara yin jika".
Ta ce "kya yi kya gama. Y'ay'ana nawa ne suka haihu? Yanzu ina ce duk sa'anin aurenta sun haihu dama wandanda suka riga ta auren. Duk ba jikokina ba ne?"
Gwaggo ta ce "wace ni na ce ba jikokin ki ba ne. Gani na yi Ummi yar hutun ki ma baki ta'ba zuwa dubiya idan tana laulayi ba, sai idan haihuwa ta yi.

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login