Showing 156001 words to 159000 words out of 184118 words
Chapter 53 - Bakar Taada Hausa Novel Complete
yi shirin fita. Murya babu amo ya ce "Zan fita Asiya sai na dawo".
Ko motsi ban yi ba bare na masa shi. Ya sa kai ya fice. Sai kuma ya dawo, ya gama kame kame ya fita.
Mintina kusan talatin ya sake dawo wa.
Ya tarar da ni a zaune. Ya ce "Gabad'aya jikina bana jin dad'i. Ga shi fitar ta zame mini dole. Kano zan je na kai kaya. Amma yau zan dawo komin dare in sha Allah ".
Na dauke kai na kasa ce wa A dawo lafiya.
Ya fita. Na ja tsaki tare da ce wa "Ka gama shige da ficen ka ba kula ka zan yi ba.
Azahar ta tayar da ni. Na yi sallah na d'ora abinci saboda yara.
A daddafw na yi shara na gyara dakin.
Na fito wanka su Hamim suka dawo.
Da yake alhamis ne babu islamiya.
Dan haka sai suka debe mini kewa, ban fada nazarin yadda zamana da Nasiba zai kasance ba. Tunda a duniya bani da matsalar da ta wuce hakan.
Ban ankara da rashin dawowarsa ba sai wajen goma na dare. Yana wahalar gaske ya yi dare. Idan kuwa hakan ta kasance sai ya bugo mini waya, ko da ni ban masa wayar ba.
Na fara tsorata da shadaya ta gota. Zuciyata na bugawa na d'auki waya na k'ira shi.
Abin mamaki wayar ta ki shiga, na dage da kira babu kakkautawa.
A karshe a ka ce a kashe take gabad'aya.
Na shiga zullimi sosai. Mussaman da ya tabbatar mini zai dawo komin dare.
Na rasa yadda zan yi. Na Kalli yara na barci. Hamim ya dora kafarsa jikin Hanif.
Hawaye ya tsinke mini domin yadda nake jin jiki da zuciyata suna bari, nasan akwai abin da zai biyo baya marar dad'i.
Duk yadda na so na tashi na yi sallah kasawa na yi. Daren ya mini tsayi ainun. Domin tunda muka dawo Bauchi bai tab'a tafiyar kwana ya barmu ba.
Na dinga kuka ina fad'in "Allah ka taimake ni ka dawo da shi lafiya."
Da asuba na cigaba da kiran wayarsa nan ma shiru.
Ina idar da sallaj na bugawa kaninsa Aliyu waya na sanar masa Tijjani bai dawo ba, kuma wayarsa a kashe. Ya yi yunkurin kwantar mini da hankali. Na katse wayata na kira Yaya Salisu na shaida masa.
Har karfe daya na rana babu labarin sa. Hankali dangi ya fara tashi. Da la'asar sai ga Babah ta Bulkachuwa tare da Aliyu.
Kuka kawai muke yi ni da ita. Aka rasa mai bawa wani hak'uri a tsakaninmu.
Yayin da Yaya Salisu da Yaya Aliyu suka nufi Kano tun hantsi.
Tashin hankalinmu ya sake tsananta da la'asar ta yi babu wani tartibin labari akan Tijjani ko motarsa.
Hatta Toro hankakula ya tashi ainun domin tabbas abu marar dad'i ya same shi, mutuwa ko mummunar hadarin da aka kasa gane shi.
Innalillahi wa inna ilaihir rajiun kawai muke ta ambata ni da Babah.
Babu abin da yake sake tayar mini da hankali irin idan na kalli twins.. gabadaya sun kasa sukuni. Duk fitinar Hamim ya zauna a gefe ya nutsu tamkar marar lafiya. Maganganunsa da ya dinga yi mini a baya akan mutuwa suka dinga dawo mini. Na fara kuka sosai ina ce wa "Sai da na sakankance ba mutuwa zaka yi ba shine zaka tafi ka bar omu, me yasa zaka tafi yanzu alhalin zukatanmu cike suke da gilli da bacin rai mai tsananin gaske?.".
Babah ta kasa ce wa komai illa hawaye da ita ma yake k'waranya daga fuskarta.
Ina cikin haka sai ga Yaya Ummi da Mama. Baban Marina ya turo su, su zauna da ni. A dalilin bai san Babah tana tare da ni ba. Ganinsu ya sake rikitini ina sake gasgata abu marar dad'i ya same ni. Ina kuka ina fad'in "Ni Yabi yaushe zan tsallake damuwowi ne a rayuwa ta?"
Gabadaya na rikice, sai tausa ta suke yi, duk da Yaya Ummi ma kukan take yi sosai.
Sai dare Aliyu ya k'ira Babah. Murya babu sukuni. Ya ce "Al'amarin dai sai hak'uri."
Abin da na ji ke nan na yanke jiki na fad'i ban sake gane komai ba.
*Akwai kaya masu kyau a cikin farashi mai sauki*
*Saiwowin maganin sanyi*
*Saiwowin Tsumi*
*Saiwowin dahuwar kaza*
*Saiwowin dahuwar tattabaru*
*Gumba*
*Tsumin kwakwa*
*Y'aya'n gadali*
*Hadadden daka*.
*Tsugunno mai sa a matse*
*Goran tula*
*Goran tula syrup*
*Garin goran tula*.
*Maganin gyaran nono*.
*Zuma ta mussaman*.
*Tsumi*.
*Da sauran kayayyaki na mussaman da basu da illah*.
* Domin kuwa asalin Saiwowin ne da ake kawo su daga Chad*.
*Abu mai kyau shi ke siyar da kansa ku tuntube ni dan samun naku kayan cikin sauki da mututantawa. Ina aikawa ko ina a fad'in tarairaiyar Nijeriya*
*08032773332*
✍️
*INA MUKU ALBISHIR AKWAI DUKKAN TSOFAFFIN LITTAFAN MARUBUCIYA HAJIYA SALIHA ABUBAKAR ZARIA*
*ZAKU SAME SU SOFT COPIES A HANNUNA.*
*SABO LITTAFIN TA ZAI ZO BA DA JIMAWA BA*.
*HAKA NAN AKWAI WASU DAGA CIKIN LITTAFAN MARUBUCIYA HAJIYA HAFSAT C SODANGI, SUMA SOFT COPIES*
*HAJIYA HANNE ADO ABDULLAHI?*
*MARUBUCIYAR WANKA DA GARI DA KUMA WACECE UWA?*
*TO ITA MA TAKANAS NA SAMO MUKU LITTAFANTA DOMIN KUN SANI TA YI RUBUTU MASU MA'ANA*.
*LITTAFAN DA YAWA, AMMA AKWAI DISCOUNT DOMIN SO NAKE KU YI TA SIYAWA Y'AYA'NKU DA KANNENKU LITTAFAI MASU DARASI DA MA'ANA*.
*BA DA JIMAWA BA ZAN ZO MUKU DA SU*.
*08032773332*.
Na farfado ne na gan ni ana k'ara mini ruwa sai fifita suke mini tare da kuka dukkansu.
Baki na rawa na ce "Babah ni din musulma ce! Ki fad'a mini Tijjani ya rasu ne?"
Da rawar murya ta ce "Bai ce ya mutu ba Yabi. Amma dai akwai abin da ya same shi marar dad'in ji, tunda har Aliyu ya jinjina lamarin".
Na fizge k'arin ruwan na zabura na ture su na tashi. Hijabi na raruma na yi hanyar waje ba tare ma da na saka ba.
Yaya Ummi ta ruk'o ni tana fad'in "Ina zaki a wannan halin Yabi?"
Da kuka sosai na ce "Kano ba zan tab'a samun nutsuwa ba, matukar ban san halin da yake ciki ba".
Fuskar kowa k'walla ce da tashin hankali. Hatta Mama jikinta a sanyaye yake ainun.
Da k'yar suka tirsasa ni na hak'ura na zauna. Sai ambaton Innalillahi wa inna ilaihir rajiun kawai nake yi. A fili nake fad'in Allah ka kaddara mini na ga dawowar Tijjani cikin gidan nan, ko da ba akan kafafunsa ba ne. Fatana ace yana numfashi. Ubangiji ka rufa mini asiri ni da y'aya'na".
Ba abin da yake sake tayar mini da hankali irin yadda Babah ta kasa tsayar da hawayen ta.
Akai akai take share hawaye babu kakkautawa.
Kwanaki biyu muna cikin wani irin zullimi mai tsananin gaske. Domin duk asibiti da yake cikin Kano su Aliyu sun karade a kwanakin nan amma babu Tijjani babu labarin sa. Kowa ya karaya. A ranar Baban Marina ya taho Bauchi tare da Gwaggo. Nasiha kan nasiha suka shafe lokaci suna yi mini akan yarda da kaddara na yi hak'uri mu bishi da addu'ar idan a raye yake Ubangiji ya tsare mana shi, ya kuma bayyana shi. Idan kuwa rai ya yi halinsa to Allah ya sanar da mu, ya kuma jik'an sa.
Na rarrafa na fad'a jikin Baba cikin matsanancin kuka na ce "Sai yaushe zan huta, yaushe ne zan ji dad'in da ake ta fad'in zai same ni? Gabad'aya walagigi yafi yaws a rayuwata Baba! Kalli k'ananun y'aya'n Tijjani wa zai taya ni tarbiyarsu da wahalarsu Baba?"
Muryarsa na rawa ya ce "Ubangiji da ya baki su shine jagoran da zai taya ki kulawa da su. Sannan matukar ina numfashi ko y'aya' nawa kika haifa zan kula da su iyakar yadda zan iya, tamkar y'aya'n da na haifa!
Yadda ya kare maganar da kuka ya sanya Gwaggo fara kuka duk kuwa da yadda take da jarumta mai yawa. Kowa na falo kuka yake, hatta Mama kuka kuma na gaske ba na ganin ido ba.
Tsawon lokaci muna kuka tamkar an tabbatar Tijjani ya k'are.
Hanif ya ce "Ku yi hak'uri" Hamim kuwa ya ce "Baban 2 zai dawo a motarsa bai b'ata ba."
Gabadaya yaran sun rasa kuzari da karsashi a tare da su.
Da yamma mun idar da sallar la'asar Yaya Salisu ya kira Baban Marina da yake zaune a cikinmu tamkar mace.
A sanyaye ya ce "Mun samu labarinsa, mun je mun gan shi".
Gabadaya dakin muka hau fad'in Alhamdulillah Alhamdulillah!
Sai dai Innalillahi wa inna ilaihir rajiun din da Baban Marina yake fad'i ya yi matukar tsorata mu, mussaman ni da zuciyata tamkar ta fad'o k'asa.
Na kasa fahimtar bayanin da ake masa. Nasan dai na ji ya ce mun gan shi.
Gumi ya dinga keto mini. Ina tambayar zuciyata wanne ibtilai ne ya samu Bulkachuwa irin haka?.
Sai da Baban ya ajiye wayar. Tsawon mintina bai iya ce wa komai ba. Gabadaya ya jike da zufa.
A sanyaye Gwaggo ta ce "Alhaji fad'a mana halin da ake ciki kada zullimi ya karasa kassara mu.
Murya babu amo ya ce "Yana hannun jami'an tsaro. Tun shekaranjiya suke tsare da shi. Kuma damln tsabar raina talakan k'asa suka kashe wayarsa bare wani nasa ya ji halin da yake ciki."
Na saki nannuyar ajiyar zuciya, da kuka nake fad'in Allamdulillah!
Domin sai na ji tamkar an dauke mini k'atuwar masifar da ta nannad'e ni.
Tunda yana da ransa komai mai s'auki ne. Domin ban fahimci ana iya yiwa mutum talala ya zama ba shi da yancin yin komai a rayuwarsa ba.
Na kasa yin walwala a dalilin yadda Baban Marina ya yi laushi. Na tabbatar Tijjani na cikin k'ak'ani ka yi.
*Toro*
Baban kasuwa da Baban Tsakiya zaune a gaban Dada da take kuka face face tana fad'in "Ubangiji ka kare mai sunan manya, ka bayyana shi".
Baban Tsakiya ya ce "Ki daina damuwa sai ciwon ya tashi ne? An ce miki a gan shi. Sai dai fitowarsa sai ikon Allah. Tunda laifin da aka kama shi da shi idan a wata k'asar ne take za'a tabbatar masa da haddin kisa."
Hannun biyu ta d'ora aka tana kururuwa tana ce wa "Allah ka yi mini dan ma'aiki. Alfarmar Shehu Amadu Tijjani mai karama ka saukakawa wannan yaro".
Baban kasuwa ya ce "Allah ne ya yi sakayya ya toni asirinsa. Wai Tijjani ya rasa wadanda zai wulakanta sai mu? A fili yake nuna wa Yaya Sani ne kawunsa da zai yiwa hidima. Akan idonmu zai ta d'orawa yara kayan abinci da kayan miya ana kai wa kofarsa amma mu wayam. Wai shi mai suruki. Alhalin ba akan son ramasa ya bashi auren iblishiyar yarinyar nan ba. Mune muka so a bashi"..
Baban Tsakiya ya yi k'uta tare da ce wa "Allah ke nan! Ai duk mai gilli mai son ya wulakanta na gaba da shi ya dinga ganin jarraba ke nan."
Dada dai kuka take bil hakki. Domin tun farko tana son Bulkachuwa. Da ya samu wadata kuma ya jiyar da ita dad'i duk da dai ce wa take yi bashi yake biyan ta. Tunda dukiyarta da ya salwantar mata runduna ce babba.
Washagari muka dunguma Kano tare da Baban Marina. A babbar hedikwatar y'an sanda ta bonfai muka tarar da shi cikin mawuyacin hali. Hawaye ya tsinke mini. Domin gabad'aya ya fita a hayyacinsa. Babu alamun duka a tare da shi. Amma ya jigata k'warai da gaske. Abin mamaki a wajen muka tarar da su Yaya Jabir ya zo daga Kaduna da kuma Yaya Ammar yayan Nasiba. Duk da shi ma a BAUCHI yake aiki a gidan Yari. Tunda su Yaya Salisu suka fada musu, suka bar komai suka biyo su Kano dan sanin halin da Tijjani yake ciki.
Cikin tashin hankali Tijjani ya ke fad'in "Wallahi bana harkar. Ina gida aka mini waya akan na biya na karbi sako a Wunti. Ashe wiwi da koken ce ga shi an kasa samun lambar da aka kira ni da ita. Wallahi ba kayana ba ne, ba ni da alak'a da ita".
Ya fad'a idonsa ya kad'a ainun tamkar na rikakken mashayi.
Na rushe da kuka riris. Domin dai na riga na gane mun fad'a cikin garari mai girma. Kallon sa na yi na gane iyakar gaskiyarsa yake fad'a babu alamun karya ko kwaskwarima domin ya riga ya bani damar da na fahimci gaskiyar sa da kunbiya kunbiyarsa.
Babah ta kasa magana, yayin da Baban Marina ya ce "Tijjani ka fadamana gaskiyar magana, dan musan ta yadda zamu b'ullowa wannan azal d'in. Kasan wahalar da shari'a ma laifi ne babba."
Murya na rawa ya ce "Wallahi gaskiyar magana na fad'a. Bana harkar, ba ni da alak'a da kayan da aka kama ni da shi Baba".
Gauron numfashi Baba ya yi tare da ambaton "Subhanallah!
Baba ta kasa magana duk da idonta a soye yake babu alamun kuka. Na sani kuma tana cikin damuwa ne mai yawa.
Na tsugunna a gabansa ya sassauta murya ya ce "Asiya na rantse miki ba ni da alak'a da wannan al'amarin sharrin magauta na had'u da shi. Kaddarar da azal ce ta hau kaina".
Na zuba masa ido tamkar ba a gaban iyayenmu muke ba. Shi ma ya zuba mini nasa, tsawon lokaci muna kallon juna. A cikin wannan kallon na tabbatar Tijjani bai aikata laifin da aka jingina masa ba. Na kuma gasgata shi akan gaskiya yake amayarwa.
Ni na fara janye idanuwana da hawaye suka cika su taf. Da rawar murya na ce "Na gasgata ka Baban 2! Ina baka tabbas din ko baka samu mutum daya da ya gasgata ka ba. Ni Yabi na yarda bak'in k'azafi aka yi maka, tare da hak'a maka ramin mugunta. Dan haka ina tare da kai cikin ko wanne bigire har mu ga me Ubangiji zai zartar mana".
Daga hakan na fara kuka sosai. Yaranmu da suke jikinsa suka yi tsuru tsuru suna kallon yadda nake kuka sosai, shi kuma ya susuce ido ya kad'a.
Sai lokacin Babah ta ce "Allah ya warware maka, ya bayyana gaskiyar al'amarin".
Yaya Ummi kuwa da Mama kuka suke yi. Gwaggo ce bata um bata um tunda ta yi jaje cikin rauni da kasala bata sake iya magana ba.
Muna kallo da lokacin da suka bamu ya cika suka iza keyarsa hannunsa dauke da ankwa tamkar kasurgumin mai laifi.
Ni dai har muka dawo BAUCHI ban iya daina kuka ba.
Tun ana bani bakin na yi shiru har aka zuba mini ido.
Maimakon mu yada zango a BAUCHI sai Baba ya ce a wuce Toro kawai.
A k'ofar gida muka tarar da su Baban Tsakiya. Na kalle su na gasgata ce wa Baban Marina ne kawai ubanmu. Ba wanda ya bi bayan Tijjani ko na ahalinsa a cikinsu.
Dukkanmu a gaban Dada muka zube tamkar masu neman gafara. Tana kuka, matan cikinmu muna yi, tamkar dai mutuwar fuju'a Tijjani ya yi.
*INA MUKU ALBISHIR AKWAI DUKKAN TSOFAFFIN LITTAFAN MARUBUCIYA HAJIYA SALIHA ABUBAKAR ZARIA*
*ZAKU SAME SU SOFT COPIES A HANNUNA.
*SABO LITTAFIN TA ZAI ZO BA DA JIMAWA BA*
Sai ta dauko salatil fathi sai ta rikice ta dauko ashafa da k'yar dai ta fara karanta casa'a ta sauke ta. Tana yi tana ce wa "Rabbani a saukakawa mai babban suna, a tausayawa wadannan y'aya' nasa".
Da k'yar Baban Marina ya hakurkurtar da mu aka daina kukan.
A dakin Gwaggo na yada zango. Dakin da nake matukar samun nutsuwa a cikinsa. Amma a yau sai na ji ina cikin matsanancin kunci da zullimi domin sai nake ganin tamkar ana shirin raba ni da Tijjani ne. Na ga tsayin wannan dare tamkar dai ace gawa ce a dakin.
Ban yi barci ba. Karfe uku na ga Gwaggo ta fita ta dauro alwallah. Duk yadda na ke cikin zullimi sai da na tuna irin wannan yanayin muka shiga a lokacin da aka zartar mini da hukuncin auren Bulkachuwa. Yau kuma ina kukan bak'in cikin nisanta ni da gidansa da aka yi.
Gwaggo tana shigowa da alwalarta, nima na zabura na mik'e na doro alwalar.
Muka dinga nafila muna shigar da bukatunmu. Ina kuka hannuwana na sama "Tijjani, Tijjani kawai nake iya fad'a gabad'aya kaina ya kulle. Domin dawo da ni gida ya yi matukar sake tsorata ni.
Me yasa za'a raba ni da dakina?
Kwanaki biyu kacal a gidan Marina na gane masu farinciki yadda na shiga cikin garari sun rinjayi masu tausayi da rarrashina.
A k'ofarmu kam babu wanda yake takura mini ko habaici. Amma da zarar na fita da NIYYAR zuwa wajen Dada sai na samu wanda ya yi mini yarfe ana mini habaicin dama karyar arzikin da a muke yi ba mai tsarki ba ne.
Har ta kai bana k'aunar na fita. Amma idan ban je ba sai ta aiko wai na je, a wannan lokacin k'warai Dada take tausayina ni da yara. Kullum a cikin sadaka da addu'a take yiwa Tijjani. Kuka kam bansan wa yafi yi a tsakaninmu ba. Ta damu k'warai har jininta ya hau.
Ban sake samun damar gano Tijjani ba har aka yi sati da zuwanmu. A lokacin kuma na fara gazawa.
Tashin hankalina na sake hauhawa.
Baban Kasuwa da na Tsakiya babu wanda ya tako kafarsa da nufin yi mini jaje.
Ashe wai na yi laifi da ban bisu kofofinsu na gaishe su tare da yi musu jaje tunda ai su d'ansu ne tun kafin ya zama mijina.
Ni luma damuwata ta girmi tunanin zuwa gaishe gaishe. Sannan mafi yawa a wajen Dada nake ganinsu na kuma gaishe su a mutunce.
A lokacin na sake fahimta tare da gasgata idan Baban Marina ya kauce bamu da wanda zai tsaya kai da fata ya tallafemu idan mun shiga cikin kalubalen rayuwa. Tausayin k'ananun y'aya'n Baban Marina ya sake rub'anya tashin hankalina. Gabadaya na zama tamkar wata zararriya, na k'are na fige tamkar kudin guzuri. Bayan addu'ar da nake yi wa Tijjani da y'aya'na, sai na sake tsananta addu'ar Ubangiji ya sanya soyayya da tausayi mai yawa a tsakanin y'aya'n Baban Marina.
Domin kam al'amarin Baffaninmu sai shukuran. Kullum mutuwa na daukarmu daya bayan d'aya amma bata zame musu izna ba.
Abin da na sake fahimta kawai shaidan da son zuciya gami da hassada ne suka yiwa zumuncin yau k'awanya.
Sassaucin rayuwar da Baban Marina ya samu a dalilin y'aya'n sa ya zama wani abin tattaunawa. Kullum a cikin fad'in ai yanzu ya farfado suke.
Na tabbatar ba za'a bar ni na ji da ibtilain da ya fad'o mana ba, sai an tusa ni gaba da muzanci kala kala. Dan haka na kudire da na yi sati biyu zan fad'awa Baban Marina zan koma dakina tunda dai Tijjani bai mutu ba.
Washagari muka tafi Kano da ni da Nazira da Yaya Salisu.
Gabadaya Tijjani ya fita a hayyacinsa. Ina kuka nake fad'in "Basa baka abinci ko?"
Ya girgiza kai ya ce "Abin nan da nake fad'a miki. Da zarar hantsi ko yamma, ta yi sai gabad'aya na rikice, zuciyata kamar ta yi bindiga wajen son na tafi Toro na ga Nasiba.