Showing 147001 words to 150000 words out of 184118 words

Chapter 50 - Bakar Taada Hausa Novel Complete

zama da wacce baya so. Idan kishiya ta kere ka a wani fanni to kai ma da ikon Ubangiji sai ka samu fannin da zaka kere ta. Abu biyu ya dame ni. Nasiba suntumemiyar halitta ce irin matan da suke birge Bulkachuwa. Sannan mahaifiyarta kowa yasan bata barin mazanta haka, a hannunta suke, ko marigayi mijin Nasiba kullum a yunkurin mallake mata shi ta ke. Na tabbatar Tijjani ma za'a yi komai dan ta sha gabana, tunda a yanzu ma da bai aure ta ba idan ta gan ni kamar ta doke ni haka take ji. Da k'yar Babah ta shawo kaina na samu nutsuwa, na daina kuka.
Sai yamma muka baro Bulkachuwa. Dan haka sai dare muka iso.
Na daure na yi k'arfin zuciya ban cigaba da share shi ba. Na rungume shi da hannu biyu muka cigaba da zama lafiya. Duk dare kuma sai ya fita waje ya yi waya. Idan kuma yana gida baya amsa waya matukar bata shafi kasuwancinsa ba. Asalima kamar ya dakatar da a a kira shi idan yana gida ne. Da kaina na fahimci da gaske ya canja, wulakancin yin waya idan yana gida yanzu ya daina, asalima kaffa kaffa yake kada na tuntsire masa.

*Oriflame products*
*Daga make up artist din Guduyo*
*Idan kina bukatar Oriflame products ko wanne irin ne, ko Kuma kina sha'awar yin register da su*. *Ki tuntubemi babbar dealer din su Aisha lame*
*Ina kuma fad'a muku akwai da daddan ganyen shayi na Lame Tea*
*Akwai pop corn*
*07036662633*.

Yayin da ni kuma na tsananta addu'ar Ubangiji ya tsaremu akan duk abin da ake nufi da mu na sharri. Sa'a d'aya har yau Tijjani bai bar sallar dare ba. Yana wahalar gaske ya kwanta bai tashi ya yi nafila ba. Kullum kuma a cikin addu'ar duk kaddarar da zata hau kansa ta zama mai sassauci daga Ubangiji.
Na sani asiri zai kama shi, amma na yi imani zai zo da sauki tunda wadatar da ya samu bata sanya ya bar Allah ko ya koma BAK'AR TA'ADAR neman matan da ya yi a baya ba.
Na kira gwaggo na fada mata komai na roki ta tsananta yi mini addu'a.
Cikin rarrashi ta ce "Ina yi miki Yabi. Zan kuma ninka addu'ar da ne yi miki. Abin da zan fad'a miki shine ki barwa Allah ya yi miki zabi, ba wai ke ki yanke hukuncin idan ya aure ta kin bar shi ba. Allah ne ya halasta dan haka akwai bukatar ki nutsu, kada ki bari Ubangiji ya bar ki da dabarar ki."
Da kuka na ce ",To Gwaggo".
Cikin rauni ta ce "Allah ya yi miki albarka ya shiga tsakanin ki da duk abin da zai birkita miki auren ki. Da ikon Allah ba za'a kai ki k'asa ba. Kin yi sa'a kina cikin albarkar uwa da uba. Dan haka ki yi ibada tuk'uru ki kuma yi barci da minshari ba abin da zai same ki sai alheri da ke da dukkan zuriar ki Yabi".
"Na gode Gwaggo". Na furta cikin rawar murya irin ta kuka.
Sannu a hankali na samu sassauci na cire hankalina kan maganar Nasiba da Tijjani. Iyaka dai ban daina addu'a ba, ban daina tofawa Tijjani addu'ar tsari a cikin duk abin da zai ci ko ya sha ba.
Na rungumi zaman lafiya a tsakanina da shi. Na rungumi karatuna da y'aya'na.
Mussaman a yanzu da nake gaf da kammala N.C.E.
Twins sun girma domin suna shirin shiga shekaru shida da haihuwa. A lokacin suna aji daya na firamari. Hanif yafi Hamim kokari domin kullum na daya yake zuwa. Amma kuma ba shi da magana. Yayin da Hamim yake zuwa tsakanin bakwai zuwa goma. Amma kuma ba wanda bai san shi ba, saboda suruntunsa, ya kuma yi sa'a ya iya turanci. Kamar wanda ya girma a cikin masu yi. Surtunsa da fadansa ya sanya a ke fafatawa da shi. Sau tari sai ya yi tsokana ko laifi a hukunta Hanif a madadinsa tunda ba'a gane su. Shi kuma Hanif ba zai ce ba shi ba ne. Ko ni ma yana mini wannan iya shegen. Dan haka na daina binsu a guje. Sai ya manta yana ta surtunsa kamar aku sannan zan rik'e shi.
Duk sadda na je Toro bin mu kawai ake yi da ido ni da y'aya'na a dalilin yadda muke fita daban muke daukar ido.
Wadanda kuma basa iya boye wa hassadarsu a fili sai da kawai na ji suna fad'in iyalin babban direba shugaban masu kayan gwari na Bauchi gabad'aya. Ko yaushe aka nada masa wannan mukamin?
Ni da Nasiba kuwa muna gaisawa, bama gaba sai dai babu doguwar hira. Domin idan ta gan ni sai na ga tana d'ad'are wa bata da katabus duk da bata yi mini kallon raini ko na izgili. Shi yasa nima nake jarumtar mu'amalantar ta da sakakkiyar fuska.
Ina kammala rubuta jarabawar karshe. Na fara hutun zirga zirgar da na shafe shekaru uku ina yi. Hatta lalle sai da na tafi hutun wata guda a kokarina na son na dinga yin barci yana isa ta. Da zarar na sallami twins da babansu sun fita da yake shi yake kai su makaranta, sadda zasu tashi idan ya dawo yana gari sai ya dauko su. Idan kuwa baya gari sai su taho da yaran bayan layinmu.
Suna fita nake rufe gida na gama abin da zan yi na karya na kwanta na yi barci, bana tashi sai azahar.
Daidai wannan lokacin Tijjani ya k'osa na samu ciki. Har ta kai ya fara zargin ni nake yin wani abu dan kada na sake haihuwa.
Haka kawai rannan ya tuntsire akan ba zai yadda ba. Daga haihuwa d'aya zan kulle bakin mahaifa, to shi ba yahudu ba ne, ba kuma ba Caine ba ne da za'a kiddidge masa yawan y'aya'n da zai haifa. Ya riga da ya gano hak'uri kawai yake yi, to yanzu kuma ya gaji.
Na kalle shi a tausashe na ce "Ashe ba Allah ne ke kawo ciki da haihuwa ba Baban 2?"
Da kumfar baki ya ce ",Tun kafin ki zo duniya nasan da hakan Asiya. Akan me duk abokan aurenmu haihuwarsu uku amma ke sau daya tak. Ba dan Allah ya so ya bani biyu tashi guda, da yanzu d'aya ne jallin jal. Gaskiya ni yara da yawa nake so malama."
Na sake daure wa na ce "Allah bana shan komai ka yarda da ni".
"To akan me ina bakin kokarina ba zaki karbi cikin ba?"
Na zuba masa ido cike da fargabar ko dai ya fara afa wani abu ne. Tas
na gan shi babu alamun maye ko rashin lafiya.
Ido cikin ido na ce "Wato ma ni ce na ki karba ko?"
Fuska a daure ya ce "Eh mana. Nima ba haka kika yi ta yi mini sadda baki samu ciki ba, ce wa kike ni ne ban yi miki ba. To nima yanzu kawai ki karba Asiya na gaji, ki yi ciki abin da na sani, na ke kuma son ga ni ke nan".
Na yi dariya na daga hannu sama na ce "Allah kasa na samu ciki ya zauna kada ya zube ".
Ya saki ransa ya ce "Yanzu kika nemi zaman lafiya tunda kin roki mai bayar wa. Kuma na saka miki doka kullum ki dinga wannan addu'ar idan kin yi sallah."
Na gintse dariyar na ce "To mai sunan shehu".
Ya harare ni tare da ce wa "Kin dauki umarnina wasa ko?"
Na girgiza kai da sauri tare da ce wa "Wace ni da wasa da lamarin ka, indai ba so kake Babah ta ce na raina miji ba".
Da haka na lallaba na shiritar da maganar, dan kuwa da na dauka da zafi rikici zamu yi mai yawa. Tunda da gaske ya kosa na haihu kamar bamu da yara kwata kwata. Tun wannan lokacin na tsananta addu'ar na samu ciki ya zauna. Na cigaba da zuwa ganin likitan da na daina zuwa.
Na kuma yiwa Aisha lame maganar ta siyo mini Saiwowin maganin sanyi a wajen Surayya 08032773332.*

***
Baba Maryo ta isa gidan yar'uwarta a Bulkachuwa da la'asar lis. Babah ta karbe ta da karamci da walwala. Har dare suna hirarsu da ta shafe su. Sai da daddare sun kwanta. Babah a kasa ta yi shimfida yayin da kanwarta yake kan gadon.
Cikjn hirarsu ta kutso da maganar Nasiba da Tijjani.
Ta ce "Na rasa ga ne inda matsalar take, sai sun shirya ya ce zai tura gidan iyayenta sai kuma magana ta kwanta. Sama da shekara guda yana mata yawo da hankali. Shi bai fito ba, shi kuma ya fantsama mata mane ma".
Da madaukakin mamaki ta ce"Ban fahimce ki ba Maryo!"
Ta kuwa ce "Maganar y'ar ki da Tijjani mana. Ai gara ki yi magana da waliyyinsa a yi komai a gama na gaji da wannan hirar tasu ba tare da an yiwa lamarin kai ba".
Babah ta sandare a zaune, ta cika k'warai da rashin kunyar kanwarta.
Amma sai ta ce "To shi ban da ma rashin tunani me zai sa ya nemi Nasiba da sunan soyayya. Ai ita matar manya ce. Sannan ta ya ya zai hada yan'uwan jini kishi?"
A ladabce Baba Maryo ta ce "Wa ce ce Nasiba da za'a ce tafi k'arfin Tijjani? Bayan haka zumuntar ta da Yabi ba zai hana su zama kishiyoyi ba, tunda Allah bai hana ba."
Ba ja in ja Babah ta ce "Gaskiya ba zai yiwu ya had'a Yabi da Nasiba a matsayin matansa ba".
Haka kawai ta fad'a Baba Maryo ta fashe da kuka tare da ce wa "Ta fifita bare akan Nasiba".
Babah ta ka'du da furucin yar'uwarta. Ta kasa daure wa ta ce "Wacce baren na fifta?" Ta yi tambayar da dukkan zuciyarta.
Da kuka ta ce "Yabi mana. Dama sai da na yi zargin ke ce baki d'aure gindin ya aure ta ba, saboda kina gudun zuciyarta da ta uwatata. To komin abin dai ni ce taki ba Asama'u ba".
A sanyaye Babah ta ce "Ni Yabi d'iyar Asama'u ce da ta zo da ita daga wani gidan ko kuwa tare da Yaya Sani ta same ta?"
Cikin ko in kula ta ce "Shine ubanta amma ai wata ce ta haife ta. Ni kuwa fa? Jikina Nasiba ta tsaga ta fito. Kuma tun lokacin Annabta zumuncin dangin uwa yafi na uba sahihiyar soyayya da tausayi".

*KUN TUNA MAI GYARAN GUDUYO?*
*INA NUFIN FASEELAT BABBAR DILA TA G.H.T.*
*KO WANNE NAU'IN KAYAN GHT TANA SIYAR DA SU AKAN FARASHI MAI RANGWAME*
*KAWAI KU TUNTUBE TA A WANNAN LAMBAR DAN GANIN JERIN KAYAN DA TAKE DA SU*
*TUN DAGA KAN SUPPLEMENT, SABULAI DA LIPTON*.
*MASANIYA CE AKAN KAMFANIN DOMIN TA SAMU KARRAMA WA DAGA KAMFANIN A BANA, HANZARTA KI TUNTUBETA DAN SIYA DAI DAI KO SARI.*
*IDAN KUWA KINA SON YIN RIGISTA DAN FARA KASUWANCIN KAWAI KI TUNTUBETA DAN KUWA DA KYAKKWAR ZUCIYA ZATA MU'AMALANCE KI*
*07039269802*

✍️

*Y'ar uwa, ya mukaji da bubukuwa?* *Daga nan fa har january kusan ko wanne sati akwai biki, in ba na kusa ba akwai na nesa, ban da tunanin gudunmuwa da ma kudin man da zakaje bikin ga tunanin abunda zaka saka.*
*Balle ace maaikaciya ce ko CEO ce kina business din ki, kinsan all eyes on you🧐, ke ba sayen atamfa ba komi tsadanta anyo copynta, shima lace haka, cabdi! To albishirinki yar uwa!*
*UMM NIHLA malaysianfabrics ta dauke miki damuwa, tana da fabrics kala kala masu sauki da inganci kuma babu inda zaki samesu in ba wurinta ba, kije taro ki haska kowa sai ya tambaye ki me kika saka ina kika samu💃 maza garzaya gurinta kusa labule.* https://wa.me/message/F3EWRSHQPQAAH1


*KUN TUNA MAI GYARAN GUDUYO?*
*INA NUFIN FASEELAT BABBAR DILA TA G.H.T.*
*KO WANNE NAU'IN KAYAN GHT TANA SIYAR DA SU AKAN FARASHI MAI RANGWAME*
*KAWAI KU TUNTUBE TA A WANNAN LAMBAR DAN GANIN JERIN KAYAN DA TAKE DA SU*
*TUN DAGA KAN SUPPLEMENT, SABULAI DA LIPTON*.
*MASANIYA CE AKAN KAMFANIN DOMIN TA SAMU KARRAMA WA DAGA KAMFANIN A BANA, HANZARTA KI TUNTUBETA DAN SIYA DAI DAI KO SARI.*
*IDAN KUWA KINA SON YIN RIGISTA DAN FARA KASUWANCIN KAWAI KI TUNTUBETA DAN KUWA DA KYAKKWAR ZUCIYA ZATA MU'AMALANCE KI*
*07039269802*



Babah ta kasa ce wa komai domin ita gabad'aya ma alamarin tsoro ya shiga bata. Tana kuma mamakin rashin kunya da son kai irin na Maryo.
Bata yi zaton son zuciyarta ya kai hakan ba.
Ta kasa ce wa uffan saboda tsananin kaduwa da ta yi.
Ita kuwa ta dinga kuka tana face majina tamkar Dada ce ta kwanta dama.
Washagari ko karyawa bata yi ba ta ce zata juya. Da k'yar Babah ta roke ta akan ta bari ta karya.
Rai a bace suka rabu a dalilin Babah ta tabbatar aure kam babu a tsakanin Nasiba da Tijjani.
Rai a matukar bace ta isa Toro. Ta gurfana gaban Dada tana kuka tana fad'a mata karya da gaskiyar cin mutuncin da Hauwa ta yi mata.
Dada ta taya ta bacin rai tare da rarrashinta tamkar yarinya karama. Tana cin alwashin sai ta ci mutumcinta tunda bata san yakamata ba.
Bijirewar da Babah ta yi akan auren tare da fitowa baro baro da ta yi ta ce alamarin ba zai yiwu ba. Sai ya zama d'an zani. Domin hakan ya fusata Baba Maryo tare da cin alwashin sai Tijjani ya auri Nasiba ko zata yi yawo tsirara, ta ga karshen rashin kara da nuna banbanci.
Takanas ta tafi cikin jeji can kudu da Jos. Ta samo asiri da surkullen da muradinta zai cika.

*Bayan waatanni biyu*

A hankali Tijjani ya fara rikice mini fiye da bara. Sai mu kwana gari ya waye bai ce mini uffan ba. Zan masa magana goma bai fi ya amsa ni sau biyu ba a gajarce.
Ya daina shayin yin waya a gabana. Yanzu har an kai jallin da zai bawa twins waya su gaishe ta. Duk da dai bai tab'a kama suna ba.
Sai ya ga dama yake cin abincina. Jiya ma da na zauna kusa da shi ce mini ya na tashi yana bukatar kad'aici. Murjewar da na yi, nan da nan na fara tsomare wa. Sosai ya murde irin yadda ban taba zaton zai yi ba. Na hakurkurtar da zuciyata na dinga ba shi hak'uri tare da rokon ya fad'a mini laifin da na yi masa.
Yana bude baki sai ce wa ya yi "Haihuwa yake so. Tunda ba zan haihu ba, shi aure zai yi, idan zan zauna na zauna idan kuma bazan zauna ba, to bai rik'e ni ba."
Na zuba masa idona da suka soye. Na ce "Tsakanin ka da Allah kana mini adalci Tijjani?"
Ya hassalo ainun tare da ce wa "Ta ya ya zan yi miki adalci Asiya? To ko kawai zaki yi gaba ko zaki samu adalin?"
Na sake daskare wa. Na yi maza na kame bakina domin na gane komai na iya faruwa a tsakaninmu.
Amma hawaye ke tsere babu jinkiri kuncina.
Ya ja tsaki ya fice ya bar ni. Yana fad'in "Me za'a yi da mace mai rainuwa da azababben kishi. A ce mace ba zata taimake ka ta rufa maka asiri, ta taya ka son abin da kake so ba. Sai sarhutu da mance alheri kawai ta iya ".
Na yini cikin bacin rai. Yayin da shi kuma ya yi tafiyarsa Toro da yara bai damu da halin da ya bar ni a ciki ba.
Ina kuka na d'auki waya na bugawa Baban Marina karon farko da na yi hakan tunda ya aurar da ni. Na kasa magana sai kuka nake yi masa mai tsuma zuciya.
Bai katse ni ba. Sai da na gaji dan kaina na katse wayar.
Baban Marina ya dawo gida cikin sanyin jiki a dalilin yadda kukan Yabi ya buge shi.
Ya leka kofar Dada dan ya bata man zafin da ya siyo mata sai kawai ya ga Tijjani da Nasiba a gefen bisihiyar zogale suna zance. Dada na daki abin ta. Duk da ba yau ya saba ganinsu ba, amma yau din sai da zuciyarsa ta buga da tsananin gaske.
Ya amsa gaisuwarsu cikin k'arfin hali. Ya shiga wajen Dada ya fito, ya fita.
Ya zauna kan tabarma amma zufa ta rufe shi. Ya dinga jin wani iri. Duk yadda ya so jurewa kasa wa ya yi. Yana tambayar kansa yanzu Tijjani yana da rigar da za'a bashi aure ke nan?.
Ya tuna irin kukan da Yabi ta kira ta yi masa dazu, ya san kuka ne na neman agaji, kuka ne mai harshen damo. Daren ranar ya yi masa tsawo ainun.
Washagari ana idar da sallar asuba ya ce Salisu ya raka shi Bauchi.
Tamkar jifa haka Yabi ta gansu. Zuciyarta ta karye. Domin ta hango rauni da wata irin soyayyar ta a kan fuskar mahaifinta.
Tare da Tijjani suka musu iso zuwa falo.
Yana amsa gaisuwarsu ya yi gyaran murya ya ce "Zuwa na yi takanas dan na fad'a miki ce wa ki yi hakuri ki zauna a dakin ki. Ki kuma sauke dukkan hakkina da kika san Ubangiji ya dora miki. Daga nan har zuwa lokacin da Allah ya kaddara muku zaman kada ki yarda ki zalunce shi. Kada kuma ki fito babu izininsa. Aure da kike ga ni darajar sa ta wuce duk zaton mai zato. Sai dai bisa adalcin Ubangiji ya kewaye shi da dokoki da kuma sharudda daban daban. Bai barmu kara zube ba. Ina rokon ki, ki k'ara hak'uri a cikin wannan tsukun da ake son kaimu k'asa da bak'inciki mai tsanani. Idan har kika yarda kika yi hak'uri, ni kuma na miki alkawarin zan jaddada damar da shari'a ta baki na zabin cigaba da zaman ko akasin hakan matukar zalunci da cin fuska ya shigo gidan auren ki".
Cikin kuka da rawar murya na ce "To Babanmu".
Ina fad'in haka ya mik'e tare da ce wa "Allah ya yi miki albarka. Ya fice bai ko bi takan tagwaye da suke ta rige rigen gaishe shi ba. Yaya Salisu ne kawai ya amsa musu tare da ciro ledar alawowi a aljihunsa ya damka kowa tasa ledar.
K'warai Tijjani ya muzanta da yadda suka fice basu bi takansa ba. Ya bi bayansu. Ba jimawa ya shigo ya zauna. Ya ce "Baban Marina ya canja, ya yi bangaranci. To wai a kaina aka fara k'arin aure ne da za'a mini wulakanci irin haka?"

*Oriflame products*
*Daga make up artist din Guduyo*
*Idan kina bukatar Oriflame products ko wanne irin ne, ko Kuma kina sha'awar yin register da su*. *Ki tuntubemi babbar dealer din su Aisha lame*
*Ina kuma fad'a muku akwai da daddan ganyen shayi na Lame Tea*
*Akwai pop corn*
*07036662633

Ban kalle shi bare na ba shi amsa. Maimakon

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login