Showing 144001 words to 147000 words out of 184118 words
Chapter 49 - Bakar Taada Hausa Novel Complete
bubbuga bayana cikin rarrashi. Tsawon lokaci ina kuka su kuma ba wanda ya iya ce wa komai. Sai da na yi kuka sosai, domin tsawon lokaci ina ta son na yi ban samu inda zan yi ba. Shi yasa yanzu na yi shi son raina. Sai da na nutsu sannan ta d'ago ni ta ce ",Fada mini damuwowinki Yabi". Na ce "Babu komai Babah". Na saci kallonsa na ga ya kidime sosai domin ya sani idan har na ce babu komai to kuwa abin da yake raina mai nauyi ne. Irin kukan da na yi kuma ya saka shi zullimi.
Babah ta hau fad'in "Wato ban isa ba ko Yabi? Na zaunar da ku dan na ji matsalalolinku amma kin ce babu komai alhalin ko makaho idan ya ji irin kukan da kike yi yasan kina cikin bacin rai."
Idona ya sake cika da hawaye na ce "Wallahi Babah ba isa ne baki yi ba, ke ma kin san yadda na dauke ki. Kawai ban san me zan ce ba ne. Abin da na fahimta kawai yanzu ya fi k'arfina ne. A yanzu ya samu damar da zai auro daidai da ra'ayinsa, irin wacce ta dace da shi. Ai dole na ga komai! Dole komai zan yi masa ya zama laifi, dole ya janye dukkan tausayi da sassauci a tsakaninmu, Tunda bana birge shi. Yana zaune da ni ne a kan dole, gane hakan da na yi ya sanya na koma gefe dan na ba shi dama ya yi komai tunda Allah ya ara masa damar."
Na goge hawayen da ya zubo mini da hijabin jikina.
Babah ta yi shiru tana kallonmu tare da nazari sosai.
Ta kasa gane waye yafi gaskiya a tsakaninmu. Amma kalamaina sun yi matukar dukansu gabadaya, shi kansa kallona yake yi ya kasa ce wa uffan.
Karshe dai Babah ta rinjayar da gaskiya a tare da ni.
A sanyaye ta ce "Ban yi mamaki ba. Domin mafi yawa maza haka suke yi. Da sun samu wadata kuma sai wulakanci ya biyo kan wacce aka sha gwagwarmaya da ita. Ba ko wanne namiji yake yin hakan ba, amma dai masu yin sun zarta marasa yin yawa. Sannu Yabi!"
Ta fada cikin wani irin yanayi, mai wuyar fasaltawa.
Kalaman Babah suka sake fadada zullimiin da yake ciki.
Murya babu amo ya ce "Babah kada kalamanta su rude ki, ki bata lasisin cigaba da gasa ni da ruwan sanyi da take yi. Ubangiji ya bata iya sarrafa harshe. Wallahi ita take k'warata. Satin da ya wuce muka dawo daga Kano. Na kuma shirya mana tafiyar ne dan mu samu sauyin muhalli watak'ila hakan zai sa ta huce daga murdewar da ta yi. Jikina na rawa na dinga siya mata komai na ga ni. Amma Wallahi yadda kika san mugun abu na yi mata haka ta sake botsare wa. Tunda muka dawo ta sake taurare wa. Wai a ce yarinyar mace kankanuwa kamar wannan ta iya BAK'AR TA'ADAR gaba da miji haka siddan?"
Na kalle shi na ce "TA'ADAR da baka yi ta sharri a baya, yanzu so kake ka k'ware a kanta. Bana gaishe ka? Masharranci kawai!
Babah ta ce ",Innalillahi wa inna ilaihir rajiun. Ashe kina iya zagin miji Yabi? A gabana kika ce masa masharranci? Ta jijjiga kai tare da ce wa "Tun baku je ko ina da zaman auren ba kun fara zaman da babu mutunci a ciki?"
Ta dinga sababi ta inda ta shiga bata nan take fita ba. Gabadaya ta hadamu ta ki yarda da gaskiyar kowa.
Ta kalle ni ta ce "Da kam ni kad'ai nasan wulakancin da zan yi masa a kan abubuwan da yake yi miki. Amma tunda na gane ba ki d'auki tarbiyar gidanmu ta barranta daga zagin mijin aure ba. To ai bani da ta ce wa. Domin na gane dukkanku ne baku da mutunci, dukkanku ne kuke son yiwa auren tawili".
Ni da danuwana kuke son ku tozartawa, ku kunyata, ku jefamu cikin bak'in ciki da zunden jama'a ".
✍️
*Y'ar uwa, ya mukaji da bubukuwa?* *Daga nan fa har january kusan ko wanne sati akwai biki, in ba na kusa ba akwai na nesa, ban da tunanin gudunmuwa da ma kudin man da zakaje bikin ga tunanin abunda zaka saka.*
*Balle ace maaikaciya ce ko CEO ce kina business din ki, kinsan all eyes on you🧐, ke ba sayen atamfa ba komi tsadanta anyo copynta, shima lace haka, cabdi! To albishirinki yar uwa!*
*UMM NIHLA malaysianfabrics ta dauke miki damuwa, tana da fabrics kala kala masu sauki da inganci kuma babu inda zaki samesu in ba wurinta ba, kije taro ki haska kowa sai ya tambaye ki me kika saka ina kika samu💃 maza garzaya gurinta kusa labule.* https://wa.me/message/F3EWRSHQPQAAH1
Ta fashe da kuka tana fad'in ai bata san haka zamu yi mata ba. Da bata zo gidanmu ba. So muke mu kunyata ta ita da Baban Marina.
Dukkanmu kowa ya shiga tashin hankalin kukan da take yi. Domin kuka ne wanda yake bayyana tsananin bakin cikin da me yinsa yake ciki.
Da k'yar na bude baki na ce "Dan Allah ki yi hakuri Babah".
Bata kula ni ba, ba kuma ta fasa kukan ba.
Da k'yar ta yi shiru. Amma duk juyin da muka yi akan ta yi hak'uri ta tashi ta shiga daki bata ko yi motsi ba bare ta tanka.
A wannan ranar na gane ita ma kafaffiya ce ta gaske. Domin kuwa dukkanmu a falon muka kwana a zaune, don bata yarda ko kishingida ta yi ba.
Tashin hankalin da muke ciki tamkar idan an tsaga jikinmu ba za a ga jini a ciki ba.
Ana idar da sallar asuba kuwa ta fice ko sallama bata yi mini ba. Haka nan Tijjani bai kai ga dawowa ba. Na bita ina fad'in "Dan Allah Babah ki rufa mana asiri ki yi hakuri, ki dawo ki gafarce mu."
Tafiya kawai take yi. Muka yi kicibus da shi ya dawo daga masallaci. Duk kokarinmu akan ta dawo bata yarda ba. Duk rokon da Tijjani ya yi akan ya mayar da ita bata tanka ba, bare ta amince.
Akan dole na dawo gida a dalilin ya ce na taho saboda mun bar yara.
Na zauna ina hawaye domin ban tab'a ganin Babah ta yi fishi irin haka ba tunda na ke.
A sururuce na shirya yara, na basu abinci . Amma ko makaranta na kasa tafiya. Kan dole suma suka zauna. Har azahar babu Tijjani babu labarin sa. Na tabbatar bin ta ya yi dan ya bata hak'uri. Tun fil-azal yana gudun bacin ran ta. Bare kuma yau da ta yi matsanancin fishi.
Sai la'asar ya dawo gabad'aya ya yi zuru zuru, ya hargitse. Kallon sa kawai na yi na gane bai ci komai ba. A sanyaye na masa sannu. Ya zauna a falon ya amsa mini shi ma a raunane. Kaina a kasa na ce "Ya ya Babah?"
Ya ce "Bata huce ba. Ya zuba mini ido ya ce "Asiya taimake ni ki fada mini laifukan da nake yi miki."
Na yi shiru na k'i ce wa komai. Ya numfasa ya ce "Wallahi sai kin fada mini, na gaji da wannan jidalin na ki. Komai na yi miki babu gwangwaninta, kin tada hankalina kin tashi na ki. Mene ne haka. Kowa ya gan ki sai ya ce kina cikin damuwa ko jinya mai tsanani. Me nake yi miki hakan?"
Na dauke kai daga kallonsa. Ya taso daga inda yake a zaune ya gurfana a gabana. Ya ce "Tun ban miki duka ba, ki bude baki ki fada mini musgunawar da nake yi miki"
Na ce "Doke ni kawai, ai ka fi ga hakan ranka ya dade Alhaji".
Ya damke ni ya ce "Tunda kika yi mini sanadin da uwata ta yi mini tofin Allah tsine Bilhillazi komai zai iya faruwa a tsakaninmu ".
Ganin ya rikice da gaske idonsa ya kad'a tamkar wanda ya sha kayan maye.
Yasa na bude baki na ce "Son ka ne bana yi, na gaji, kawai ka sallame ni".
Jikinsa ya saki, damkar da ya yi mini ta yi sanyi a dalilin ya rasa karfinsa.
Ya zuba mini ido tamkar mai son ya fahimci hakikanin abin da yake cikin zuciyata.
Murya babu amo ya ce "mene ne dalilin janye soyayyar da kika yaudare ni da ita, har na yi zaton babu abin da zan yi ki janye ta Asiya?".
Ban amsa masa ba. Ya kasa hak'uri ya ce"Mene ne bana yi miki? Duk abin da na gani burina na siyo na kawo miki, ko na siyo wa y'aya'n ki. Wanne nau'in abinci ne bana ajiye miki duk tsadarsa?
Wanccan watan kina ce mini kayan Oriflame kike son amfani da shi, haka na daure na ce ki fadawa yar lame din da take siyarwa ta aiko miki, kuma tuni na biya. Da me na rage ki da kika janye samar mini da nutsuwa?
Tunda muka dawo gidannan bamu jitu sosai ba, bamu samu nutsuwar da ta dace da mu ba. Na dauka bandakin da na samar miki a cikin daki zai sa ki yi farincikin ki gane komai kike so sannu a hankali zan yi miki shi "
Ido cikin ido na kalle shi duk da bai sake ni ba, na ce "Duk wadananan abubuwan da ka lissafa hakkina ne da ya zama wajibi ka yi mini su, ba wai taimakona ka yi ba. Idan kuma yinsu alfarma ce to ka daina bana so. Daki mai bandaki kuma bana sonsa, nafi son wanccan gidan da yake fallen falle mai bandaki a tsakar gida, domin nafi samun gamsuwa da mutuntawa a cikin sa. Ya sake ni yana fad'in "Innalillahi wa inna ilaihir rajiun. Asiya sai yaushe mata zaku gane hidimar da take kan namiji ba zata bar shi kullum ya mu'amalance ku yadda kuke so ba? Da din da kike marari ba ni da abin yi ne, ina rayuwa ne a takure saboda bana iya samar miki abubuwan da suka dace da ke. Yanzu kuma da na samu hanyar daukan nuyinmu sai ya zama tashin hankalin? Shi kenan sai ya zama laifin da zaki janye soyayyar da kike yi mini?"
Na ce ",Eh dama ai ba son ka nake yi ba. Kirki da ririta ni da kake yi ne ya janyo maka soyayyata. Amma tunda ka janye su, nima na fasa son naka sai ya ya kuma? Har kana kumfar bakin ka kai ni Kano ka mini siyayya to ga kayan can bana so. Tunda har zaka yi waya a cikin dakin da kasan ina ciki kana fad'in baka tsorona, zaka bayar da mamaki akan lamarina. To ina ce sai na damu da kai ko kuma idan na zauna da kai? Sannan zaka tozarta ta ni ta hanyar nunawa duniya ni din ba komai ba ce a wajen ka. Ni kuwa me zaka yi mini na ga farin ka Tijjani?"
Ya sake ni a matukar sanyaye. Domin ya gane da dukkan zuciyata na shirya wa ko wacce irin fitina. Ya zauna kawai ya jingina da bango sama da awa bai iya ce wa komai ba.
Sallah ta fitar da shi. Ya dawo ya zauna a inda ya tashi, gabadaya ya zube tamkar mai amai da gudawa. A sanyaye ya kalle ni ya ce "Ba ni shayi na sha. Yau ko ruwa ban kai bakina ba. Ban yi masa musu ba na hado na kawo masa. Yaran namu su kansu sai suka zama babu walwala a dalilin sun ganmu a birkice.
Yana dawowa daga sallar isha ya rufe gida. Da yake da yaran ya je. Suna dawowa Hamim ya yi barci. Hanif ne ya dan jima yana kallon cartoon kafin shi ma barcin ya sure shi bai sani ba.
Har lokacin muna zaune jigum jigum tamkar masu zaman makoki. Ya numfasa ya ce "Asiya mu fahimci juna mana. Ko motsi ban yi ba. Bare na tanka masa. Ya ce "Na rasa gane halin da nake ciki. Gabadaya jina nake yi a juye. Amma mu fahimci juna. Kin ga Babah ta yi fishi da mu mai tsanani. Mu shirya kanmu, gobe sai mu je mu bata hak'uri."
Na ce "To".
Ya ce "Ban gane to ba Asiya".
"Allah wahidun! Me zan ce maka to?
Na ce a,a?"
Ya kalle ni kawai.
Ya mik'e ya sure ni tamkar yar tsana ya yi dakinsa da ni. Yana fad'in "Mu je kan katifa na rarrashe ki, domin na gane rarrashi akan katifa yafi na kan gado ratsa jiki".
Na dinga mutsu mutsu tare da son na kwace amma ina.
Ya mini kamun kazar kuku. Duk fizge fizgen da nake yi bai kula ba. Sai da ya dangana ni da katifar. Ya bini ya mini rumfa da jikinsa. Karshe ma ya sakar mini nauyinsa ta hanyar danne ni. Na daure na ki na nuna na kosa.
Ya bini da kisses da sauran al-amura masu nauyi.
Tun ina dauriyar kin karbar rarrashin nasa har na kasa jure wa na fara karba ta hanyar sakar masa jiki da daina ture shi. Sai da ya gama jagwalgwala ni, sannan ya kankance murya ya ce "Da gaske ba kya sona Asiyaty?"
Na dauke kai ina jin kunya na kama ni. Domin ni kad'ai nasan yadda nake jin sa a zuciyata. Kawai wulakancinsa ne yake neman kwantar da ni.
Sai da yasan yadda ya yi muka shirya, ya zangwanyar da fishin da na yi.
Bayan ya jaddada mini, ba abin da yake so nan duniya sama da ni.
Cikin saa'a bai mini zancen mutuwa ba.
Bamu yi barci ba, a wannan dare, domin ko da muka samu nutsuwa. Maganganu muka cigaba da tattauna wa. Haka ya dinga bani hak'uri tare da rokon na daina yi masa irin wannan fishin mai tsanani. Na daina damun kaina ta hanyar kaurace wa abinci da kuma walwala.
Sai da muka karya, muka shirya sannan muka dauki hanyar Bulkachuwa.
Da k'yar Babah ta sauraremu. Mun shafe fiye da awa ban da sallamarmu bata sake kallon inda muke ba. Harkokokin ta take yi ita da su Hanif. Su kawai ta bawa ruwa da abinci, mu kuwa ko kallon inda muke bata sake yi ba.
Ni na fara yin kundubalar bin ta daki. Yayin da ya biyo bayana, amma ya toge a bakin k'ofar tabbacin jiya bai ji da dad'i a hannunta ba. Na zauna a gefenta. Na lankwasa harshe na ce ",Dan Allah Babah ki yafe mana. Idan ba ki huce ba, ba zamu ga haske ba. Kuma tun jiyan ma mun sasanta kanmu."
Sai lokacin ta bude baki ta ce "To ni kuma ina ruwana da al'amarinku? Ni da kika ganni bana shiga kasafin da babu mutunci a cikinsa. A gabana ki zagi mijin ki Yabi?" A sanyaye na ce "Ban zage shi ba Babah". Ta ce "Kalmar da kika fada masa ai zagi ne
Na yi shiru. Ta dinga yi mini fad'a
tamkar zata doke ni. Ganin ta tsananta ya sanya na ce ",Babah Wallahi ni kad'ai nasan kuttun da yake cusa mini. Yanzu ba dama ya dawo ya zauna mu yi hira, sai dai ya yi da wayarsa, na sani kuma da y'anmata yake yin hirar ni ya bar ni gaho. A Kano kuwa da kunnena na ji yana zancen zai tura gidansu".
Ta ce "Akan me ba zai yi aure ba? Akan ki zata zauna, me ce a cikin kishiya ne da kika tsananta wa kanki k'in ta. Allah ya ce su yi mataye sama da d'aya idan zasu iya adalci. An janye ayar ne, ko kuwa rushe ta zaki yi, ki kafirta?"
Tana rufe baki na rushe da kuka ina fad'in "Kin bi bayansa ya yi mini kishiya ko Babah?"
Ta janyo mafici ta shiga kwada mini tana fad'in "Na bi bayan nasa sakarya. To hakan da kike yi masa ne zai hana shi k'ara auren. Tun yanzu kin tattara kin bar shi, idan ta zo ba sai ta karbe shi gabad'aya ba."
Cikin kuka sosai na ce "Babah na rantse da Nasiba yake soyayya. Ya auro kowa amma ban da ita. Ni Wallahi bazan yi kishi da ita ba. Mutuwa zan yi, idan kuwa ban mutu ba, daga ranar da ya aure ta. Billahi a ranar na haramta gare shi!"
Na fada cikin matsanancin kuka.
Ta saki maficin hannunta ta ruko hannuna ta ce "Ni ma matukar bai nisance ta ba Wallahi sai dai ya nemi wata uwar. Na yafe shi. Share hawayen ki har abada ba zaki yi kishi da ita ba. Na miki wannan alk:awarin".
Ya shigo a sanyaye ya durkusa a gabanta ya ce "Ki tsananta yi mini addu'a. Ban san me yasa nake jin ina zakuwa akan lamarinta ba. Idan na je wajenta kwata kwata bana jin sukuni dan tsananin takurar da nake shiga. Ko ganin ta bana son yi. Amma da zarar na taho kuma sai na ji zuciyata tana azalzalar na koma Toro dan na ganta. Ku mini addu'a, ku mini uzziri dan girman Allah. Wallahi addu'ar da nake yi ne ma take saisaita mini al-amurana, amma abubuwan da suka sha kaina masu tsanani ne. Ku taimake ni, kune mafi kusa da ni a yanzu."
"Tirkashi"
Babah ta furta a fili domin ta fahimci ba haka aka bar shi ba tabbas.
Ta nisa ta ce "Allah mun tuba, Allah kada kasa shaid'an ya yi galabar tsinka siriryar igiyar zumucin gidan marina da ta yi saura."
Kukana ya tsaya cak a dalilin yadda na ga Babah ta tsorata da furucinsa ainun. Yayin da zuciyata ta shiga zullimi sosai. Ke nan Tijjani da gaske yana burin auren Nasiba.
Wani irin k'ullutu mai ciwo ya tokare ni.
A matukar sanyaye take fad'in "Zan dage da addu'a, kai ma ka dage da addu'ar da kuma danne yadda kake ji akan lamarinta. Sannan ka saka a ranka ba matar ka ba ce, domin matukar ina raye ba zaka had'a su ba, kai gabadaya ne ma ba zaka aure ta ba. Dalilin da ya hana a baka ita a farko, shine dalilin da yasa ba zaka zama mijinta ba a yanzu"
Ta juyo gare ni ta tausasa harshe ta ce "ki yi hakuri kin ji Yabi. Yana cikin canka cakare. Ki tallafe shi har ya tsallake wannan siradin. Mutanan yau da yawansu mugaye ne, zuciyarsu cike take da gilli mai yawa."
Na kasa ce wa komai domin na kidime, idan har Tijjani da yake kawaici a gaban Babah zai bude baki ya ce yana zakuwa akan lamarinta a gabanta to lah shakka abin da yake ji babba ne.
Hawaye ya dinga tsere a fuskata. Tabbas ina cikin tashin hankali. Bana jin tsoron karawa kishi da ko wacce mace, domin na yi imani namiji baya