Showing 120001 words to 123000 words out of 184118 words

Chapter 41 - Bakar Taada Hausa Novel Complete

cikin b'argona yana da alak'a da sake jin ninkin soyayyar sa.
Na murmusa na masa ameen a zuciyata.
Ya mik'awa Yaya Ummi wanda yake hannunsa ya karbi d'aya yaron da ya kammala sha yanzu a hannun malamar.
Cikin nutsuwa ta kalle shi ta ce "Mr Tijjani kada Kaka ta rikita ka." Ta shiga fado masa muhimmancin fara bawa yaro nonon uwa a farkon awanninsa a duniya. Ta sake ce wa "Tunda mu musulmai ne mun yi sa'a kuma muna d'abbaka sunnar manzo. Da zarar uwa ko uba sun tauna dabino sun guntsawa yaronsu a baki bayan sun yi Bismillah. Ba abin da zai fi dace wa da lafiyarsa illah wannan nono da mutanan jiya suka tafi a fahimtar ce wa cuta ce. Babban sirrika ne da Ubangiji ya zuba a ciki".
Ya gyada kai cike da gamsuwa. Ya yi mata godiya sosai tare da bata ha'kuri akan maganganun Dada. Ta murmusa ta ce "Ai babu komai nima kafin na fito sai da muka haura da tawa kakar. Sai ana yi musu uzziri. Da zarar sun kai shekarun girma irin haka, sai an sake yin hakuri da sha'aninsu ana mayar da komai zasu ce a matsayin girma ne. Shi kuwa tsufa ba k'aramin nauyi ne da shi ba. Domin Allah da kansa sai da ya yi ta jan kunnenmu a cikin kura'aninsa mai girma akan idan iyayenmu suka kai shekarun girma kada mu fa'da musu munanan kalamai, komai zasu yi mana, kada mu ce musu uffan, balle a yi sa'insa da su".
Ya sake ce wa "Haka ne. Na gode sosai".

✍️.
*Oriflame products*
*Daga make up artist din Guduyo*
*Idan kina bukatar Oriflame products ko wanne irin ne, ko Kuma kina sha'awar yin register da su*. *Ki tuntubemi babbar dealer din su Aisha lame*
*Ina kuma fad'a muku akwai da daddan ganyen shayi na Lame Tea*
*Akwai pop corn*
*07036662633*.

*Masu fitarwa bazance muku komai ba. Kowa ya yi mai kyau kansa.*
*Wacce ta karanta mini labarin nan bata biya ba tabbas ina binta bashi*.
*Masu jiran na kammala su had'a mini document, kada ku yi hakan, na ro'ke ki a littafaina na baya amma still baku ji ba.*
*Bana son a had'a mini document*
*Bana son a had'a mini document*
*Wacce kuwa ta hada na kai ta k'ara wajen Ubangiji*.

Ta tattara kayanta ta fice ta bamu waje.
Ya matso ya zauna a gefen gadon da nake kai. Ya zuba mini ido tare da ce wa "Sannu little. Ban zaci zaki iya haihuwa da kanki ba. Mussaman da na ga Ubaida da Nasiba masu garin jiki sun gaza haihuwar da kansu".
A hankali na ce "Haihuwa ikon Allah ke sawa a yi ta lafiya ban da haka kam da iyayenmu basu taramu da yawa haka ba".
Ummi da take gefe ta murmusa ta ce "Yabi an je kusa da lahira an dawo."
Ya ce "Ummi ai ni da kaina na tausaya mata, haihuwar yara biyu tashi guda, sannan ki gansu manya tamkar ba tagwaye ba? Wani ikon Allah bamu yi zaton yan biyu ba ne, Ubangiji ya boye su ko sikanin din da aka yi bai nuna ba."
"Ikon Allah ya fi ga hakan ai" Yaya Ummi ta fa'da a hankali.
Ya sake kallona ya ce "Asiya kin ga yaran nan kuwa, kina ganin yadda Ubangiji ya mana kyautar da ba kowa yake yiwa irinta tashi guda ba?"
A hankali na ce "Ai ban gansu ba, ba'a bani na ga ni ba, kunya kuma ta hana ni na tambaya".
Ya yi hanzarin sake matso wa kusa da ni tare da d'ora mini yaron akan cinya a hankali. Cikin nutsuwa yake ce wa "kalle shi da kyau Asiyata. Kalli ki ga yadda suke kama da ni. Kalle shi, ki masa addu'a, ki kuma gode wa Ubangiji bisa d'inbin baiwar da ya yi mana".
Na zuba wa yaron ido. Ina son ga ne kammannin da Tijjani yake fa'da. Amma na kasa tantance wa, domin ni kam bana ga ne kammannin jarirai. Na tsananta kallonsa, ina jin wata irin nutsuwa da kaunar yaron na shigata sannu a hankali. Na saka hannu ina duba yatsun hannunsa da na tabbatar irin nawa ne.
A hankali Tijjani ya ce "Yusuf ke nan (Baban Bulkachuwa) ki masa addu'a, shi ne babban".
A fili na furta "Allah ya raya shi, ya saka shi cikin bayinsa da yake sonsu. Allah ya masa kyakkawar rayuwa. Allah ya bashi basira da azanci, ya saukaka al'amarinsa, ya kuma ba shi kyakkawan rabo a lahira".
"Ameen ameen" Tijjani yake fa'da cikin wani irin yanayi.
Da azama ya ce "Ummilolo kawo shi, shi ma ya samu tabararakin addu'ar uwa."
Ya dauke wanda ya kira da Yusuf. Yaya Ummi ta d'ora mini na hannunta ta koma gefe. Ya gyara rikon na hannunsa ya ce "Kin ga yadda suke kama da juna ko? Tagwaye ne masu kama da juna kwabo da kwabo(Identical twins)".
Na gasgata shi, domin ni kaina idan aka jere mini su bazan iya banbanta su ba a yanzu.
Na zuba masa ido tamkar yadda na yiwa d'anuwan sa. A hankali Tijjani ya ce "Muhammad Sani ne wannan(Baban Marina)."
Haka kawai na ji tausayi yaron ya shige ni. Kaunar sa ta shiga mamayata.
Cikin rauni na ce "Allah ya raya shi, ya sanya shi cikin bayinsa da yake kar'ba daga garesu. Allah ya saukaka al'amarinsa, ya kimsa masa ilimi da azancin sarrafa harshe. Ubangiji ya sa ya dace da kyakkawan rabo a lahira".
Shi da Yaya Ummi suna ta fa'din "ameen".
Ya sake kusantowa gare ni. Ya ha'demu gaba'daya ya rungume. A fili ya ce "Allah ga ahalina, ka so su, ka taya ni kula da al'amarinsu, ka tsarkake mini su. Ubangiji ka basu kariyar da ni ba zan iya basu ba. Ka zame mini jagoran wajen sauke nauyinsu da ka d'ora mini. Allah ka bawa uwarsu lafiya da juriyar raino da tarbiya. Ina ro'kon ka saukar da albarka a cikin gidanmu da rayuwarmu gaba'daya".
Ya dinga kaiwa kuncina da goshina sumba.
Jaririn da yake hannuna ya fara mutsu mutsu da k'ananun kuka tabbacin an takure shi. Da azama Tijjani ya janye daga gare ni.
Yaya Ummi ta matso da nufin d'aukar yaron. Ya ce "Ashe ba ki fita rarashin Dada ba Ummilolo? Da kika ga sun fice ai sai ke ma ki bi bayansu ki bamu waje".
Ta ce "ka gama borin kunyar ka dai".
Ya matse ya ce "To ba daukarsa zaki yi ba. Taimaka wa zaki yi ya sha. Da alamu yunwa yake ji sai tsotson hannu yake yi".
A hankali ya na ce "A a ai ya d'an sha d'azu. Zafi Wallahi!.
Cikin tausayi ya ce "Ki yi ha'kuri, zafin na d'an lokaci ne k'alilan".
Kan dole na yarda na ba shi. Shi kuwa yaro sai zuka yake yi babu jinkiri da alamu sai yafi d'an uwansa tsotso.
Ana hakan na hannunsa shi ma ya fara nasa sukur sukur din.
Ya mike ya saba shi a kafa'da, yana dan juyawa.
Daidai nan su Babah suka shigo. Ta kalle shi ta ce "Bawa Ummi shi, ka zo ka tafi. Ka zo ka yi kane kane ko kunyar iyayen pka baka ji".
Ya bada yaron ya fice ba tare da ya sake ce wa komai ba.
Kwana na yi da yini sannan aka sallame mu. Yara lafiyarsu k'alau.
Kai tsaye gida aka zarce da mu. A dakin Gwaggo muke yin jego. Hidima kan hidima Tijjani da mahaifiyarsa suke yi. Har sai da Baban Marina ya ce "Ka bi a sannu Tijjani kada ka yi bashi". Tun kafin ranar suna aka lankayawa Yusuf(Hanif). Muhammad Sani kuma (Hamim)
Har ranar suna ta zo aka yi taron sunan tagwaye cikin rufin asiri. Na yi kwalliya da leshi, da kuma kyawawan sabbin material din Umm Nihla....
Har kala biyu. Kyaunsu da sau'kinsu ya sanya Tijjani ya siya mini kala biyu. Leshi kuwa a cikin na lefena na dauka na dinka.
Fayyace irin kayan da muka samu ni da yan biyu bata lokaci ne. Domin gadajen Gwaggo duka biyu sai da suka cika da kayayyakin barka.
Babbar matsalar da ta fara damuna rashin warke wa ta. Tafiya ta a bubbude. Na je asibiti sun ware d'inkin. Suka ce na dinga kama ruwa da ruwan dumi da dan gishiri a ciki zan warke.
Sosai Gwaggo take kula da ni. mun warware mun ciko ni da yara. Na murje tamkar ba yara biyu nake shayarwa ba.
Matsala biyu ke damuna ta farko kukan yara. Domin idan dare ya fara nisa suka fara kuka, babu me yin barci a k'ofarmu. Da daya ya fara, d'ayan ma zai dauka, su taru su kidamamu. Basa dainawa sai an yi assalatu.
Dada kuwa sai fadi take yi "Ai kuka ma basu fara ba, tunda an riga an yi musu sanadin wahala. Waye zai sha mataccen nono ya share k'alau?"
Matsalar ta gaba kuma nake jin na bu'de. Ina jin yadda iska ke shigata. Nasan na karu amma ban yi zaton dinkin ba zai ha'de ni ba.
Ga shi ban fasa kama ruwa da ruwan zafi ba. Na kasa jin da'din kaina. Na kasa fa'dawa Gwaggo. Yaya Ummi na zuwa na fa'da mata. Ta ce "na sa a kawo sassake da saiwowi kalakala da ake kawo wa daga chadi."
A kunya ce na ce "Na gode.
Kwana biyu a tskani sai ga ta dawo da kayan. Da kanta ta dafa mini, ta ware mini butar da zan dinga zuba maganin.
Dan kama ruwan da na yi da ruwan maganin har na fara jin da'din jikina. Da zata tafi ta hada kan kayanta ta tafi da su. Ina son na ce ta bani koren maganin da na dafa kazar, amma na kasa a dalilin kunya ta yi mini k'awanya.
Na tuna ranar sunan Ubaida yadda su Nasiba da su Maijida suke koda kyaun kayan da suke siya daga Kano ta hannun Yaya Ummi. Na tuna sadda ta bani ina amarya na ki kar'ba.

*Masu bu'katar kayan gyara na chadi gangariya, su yi mini magana. 08032773332*
Amma da yake Yaya Ummi yar'uwa ce ta gaske sai da ta bani kayan nan duka. Kazar ma ta ce zata daho mini idan na kusa arba'in. Cikin dabara na kirgi ku'din da na samu a barka na sawa y'arta mai d'an dama a aljihunta.
A haka na kwashe sati hud'u da haihuwa. Tijjani ya fara rawar kai da son na koma gidanmu haka nan. Tunda na warware.
Idan ya fara wannan maganar shiriritar da ita nake yi.
Da safe an yiwa yara wanka suna ta barci tamkar basu ne masu kwana ido biyu suna kuka mai tsananin gaske ba. Amma da gari ya waye ba za'a sake jin motsinsu ba. Yini suke suna barci.
Ranar da muka yi kwanaki talatin ya iso daga Bauchi. Ya zaune kan sallaya a tsakar d'akin Gwaggo. Ya ci abincin da aka kawo masa. Ya kalle ni ya ce "Little ki girmama al'kawari. Ba irin cika bakin da baki yi mini ba akan idan kin haifi namiji suna na mussaman zaki saka mini. Cikin ikon Ubangiji kin haifo har biyu amma har yau ban ji sunan nawa ba. Anya kin yi daidai kuwa?"
Na dauke kai ina murmushin kunya. Tare da ce wa "gaggawa ne da kai. Ka bari sai mun koma gidanmu zan fara fa'da maka."
Ya yi murmushi ya ce "Gaskiya na matsu fa'da mini na ji kawai".
Na yi dariya na yi shiru.
Ya zuba mini ido sosai ya ce "So nake ku koma, mu yi kwanaki ka'dan kafin mu fara ha'da kayanmu. Kin san mun kusa cika wa'adin kudinmu. Bazan sake biya ba. Idan na samu dama a Bauchi nake son na samu k'aramin gida mu koma can. Zirga zirgar zata mini yawa ga tsadar ku'din mota. Zan fa'da wa su Baba zamu k'aura zuwa Bauchi."
A sanyaye na ce "Allah ya k'ara budi."
Domin na shiga zullumin yadda zan rasa jama'ar da nake da ita, tunda bazan samu jama'a a Bauchi kamar yadda na yi shura a Toro ba.
Ya ce "Ameen Asiyata! Amma fa ban bar waccar maganar ba.
Dai-dai lokacin Haneef ya fara kuka da alamun razana ya yi. Da azama ya dauko shi, ya shiga tofa masa addu'a. Sai kuwa ya yi shiru. Ya bu'de idonsa kirr yana kallon Babansa. Da murmushi Tijjani ya ce "Halo Babana, how you doing today?"
Na murmusa na ce "Kana jiran amsa ne?"
Ya ce "ko bai amsa ba, ya ji ni. Yasan yana tare da Babansa ba ki ga ya yi shiru ba?"
Na ce "Hakane".
Daga hakan ya tsoma hannu a baki ya fara tsotso.
Tijjani ya ce "shima shan hannu ya fara?"
Na ce "Eh! Shi ne ma yake yi kawai. Hamim din da ya fara, yanzu ya gane nono, baya yarda ya sha hannu, wannan yafi shi hakuri".
Ya d'aga shi ya ce "To ba shi ya sha kada a dinga amfani da hakurinsa ana barinsa da yunwa."
Na karb'e shi na gyara na fara shayar da shi. Tijjani ya tsura mini ido yana kallon yadda k'irjina suka cika, suna tsaye tunda k'ananu ne.
Ya kasa hakuri ya dauko Hamim da yake barcinsa ya ce "Ka ji Momi ta ce "Ba ka da hakuri. Baban Marina da ka ci sunansa kuwa hakurinsa mai yawa ne".
Shi bai bu'de ido ba. Barcinsa kawai yake yi.
Ya ce "Ta shi kai ma ka sha".
Na ce "kana shigowa, ina kwantar da shi. A koshe yake."
Ya kankace ido ya ce "Ba kya kewata ko little?"
Na ji kunya irin sosai. Na kawar da fuskata ba tare da na ce kanzil ba.
Ya yi kasa da murya ya ce "Na yi matu'kar gajiya. Na matsu sosai".
Na kasa amsa masa.
Ya sake ce wa "Yaushe Baba ya ce zaki koma?".
Murya babu amo na ce "idan mun yi arba'in mana. Ai yanzu ma saboda kukan yaran nan ne ya barmu da ana yin sati uku zai tattaramu."
Ya nisa ya ce "Idan ta kukansu ne ai zan iya da su Asiyata."
Na yi dariya na ce "baka san kalar kukan da suke yi ba ne."
Ya ce "Da gaske nake yi miki, zan bar komai na ji da su. Kinsan yadda nake jinsu a raina kuwa?"
Na girgiza kai na ce "Ina zan sani? Amma ni da su waye a gaba?"
Ya tillike da dariya sosai ya ce "Yanzu kishin ki har da y'ay'an ki Asiya?".
Na cuna baki na ce "Yo daga tambaya sai ka hau sarhutu".
Ya murmusa ya ce "Yaushe zasu fiki, to wa ya haifa mini su?"
Na murmusa ka'dan.
Ya ce then fa'da mini sunan da kika ce".
"Oh Allah! Bari na fa'da maka tunda kai gajen hakuri gare ka. Baban 2. Shike nan?"
Da'di ya kama shi, ya washe baki dukkan hak'oransa suka bayyana ya ce "Na gamsu da suna na mussaman ne. Ke kuma Maman 2?".
Na juyar da fuska ina murmushi na ce "A a ni ba Mama ba ce."
Ya ce to me ce ce?"
"Yaya".
Ya sake cewa wanne irin Yaya kuma?. Ko da yake tare zaku taso tunda kin yi haihuwar wuri. Amma dai su ce miki Ammi tunda ba kya son Mama".
Na ce "To."
Su Hanif basu bar kuka ba sai da muka kusan arba'in. Kafin lokacin kuwa sun yi girma na ban mamaki tamkar sun yi watanni biyu. Amma tunda ana fa'din da Bulkachuwa suke kama dole su yi girma.
Ana jibi zamu yi arba'in Baba ya ce a shirya ni, domin ranar da na cika arba'in zan koma dakina.
Haka Gwaggo ta hau shirya mini kayanmu, tana ha'de su waje guda. Sannan k'anwar mahaifiyarta ce zata zo ta zauna ta taya ni rainon tagwaye har su dan yi k'wari.
Ranar da muka yi arba'in tun da sassafe Tijjani ya zo daukarmu, ko kunyar su Baba baya ji.
Baban kuwa bai yarda ya tafi da ni ba. Kayanmu dai ya yi ta diba yana kaiwa. Mama Baba ya ce ta rakamu, bayan ya dauko shatar mota ta fara kaimu asibiti a yiwa yara allurar rigakafi. A cewarsa baza mu hau mashin da jinjirai a kwasar musu sanyi ba.
Mamah ta tab'e baki ta ce "Alhaji da alamu dai y'ay'an Yabi sun zarta na kowa daraja a wajen ka".
Kai tsaye ya ce "To ai su tudu biyu suka ci, kin san Tijjani ne ubansu. Jikokin Hauwa ne fa".
Takaici ya kume ta ainun.
Ni kuma na dinga mata kallon ko sai yaushe zata daina Bak'ar Ta'adar rashin ri'ke girmanta. A shekarun ta ai ta wuce ta dinga irin k'ananun maganganu marasa kan gado. Wanda babu azanci a cikinsu sai tarin k'yashi da hassada.
Akan dole ta raka ni, a asibitin duk inda muka wulga sai an yi sha'awar tagwaye tare da yi musu addu'a. Wajen goma da rabi na safiya muka gama da asibitin sannan muka zarce gidan.
Muka tarar da gidan a gyare tamkar ina ciki. Ban yi mamaki ba domin ya riga ya saba da gyaran gida.
Jimawa ka'dan ta yi mini sallama tabi motar ta tafi abin ta.
Tijjani ya tisa ni gaba da rawar jiki. A sanyaye na ce "Duk gajiyar asibitin da na sha. Ka bari mana dare ya yi".
Ya hau jijjiga kai yana fa'din "Ba zan iya ba. Na yi hakuri Asiya! Ke ma kin sani. Kawai ki bani hadin kai. Da daddare rainon twins zan yi, ke kuma ki yi barcinki son ran ki".
A hankali na ce "Dama dai ba Baban 2 ba ne".
Ya yi dariya ya ce "me kika ce?"
Na girgiza kai tare da cewa "Ban ce komai ba".
Ya mikar da ni, ya ja ni zuwa d'akin. Na yi turus ganin su Hamim kwance akan sabuwar katifa madaidaiciya daga gefe. Hakan ya saka dakin ya cike. Na zuba ido ina kallon yadda ya shimfida zanen gado sosia, su kuma ya jere su, duk da akwai tazara a tsakaninsu. Na ce "wannan katifar fa?"
Ya ce "Tasu ce. Tunda ba ni da halin siya musu gado, shine na siya musu katifa. Kinsan ba yarda zan yi su dinga shiga tsakiyarmu ba. Can ne makwancinsu. Idan sun yi kuka zan koma na kwanta a cikinsu".
Na yi k'aramar dariya ban ce komai ba.
Ya ja ni jikinsa ya rungume tsam tsam yana shakar kamshin jikina. Al'amarin da ya biyo baya ba mai sau'ki ba ne. Na gamsu ya yi kewata, na kuma gasgata shi da ya ce a matse ya ke. Duk yadda na takura a dalilin yadda kayan chadi suka saka na matse, na daure na bar shi ya samu nutsuwa.
Shi kuma sai fa'din "anya ba cs aka miki ba little? Ni ban ji alamun tana nan twins suka fito ba".
Ni dai ban bude baki na ce masa uffan ba, amma ni da kaina na gasgata kyaun saiwowin da na yi amfani da su. Na ji dadin maganin sanyin da na sha

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login