Showing 102001 words to 105000 words out of 184118 words

Chapter 35 - Bakar Taada Hausa Novel Complete

gajiyar ba gaskiya".
A kunne ya ce "Amma kinsan na ce idan kina yin gardama komin kankantar ta cikin ba shiga zai yi ba".
Nan da nan kuwa na yi muk'us domin har zuciyata so nake na ganni da ciki, so nake na ganni da baby a hannuna kamar yadda nake ganin su Ubaida.
Har aka fara kiran sallar Bai samu nutsuwa ba. Kan dole ya tsallake ya bar ni. A gurguje ya yi wanka ya nufi masallaci.
Ni kaina a dole na sake wanka na sauke farali.
Yau da wuri muka kwanta domin ana idar da sallar isha da ya shigo ya rufe gidan, ni dama a kwance ya tarar da ni. Sai da ya karasa abin da bai ida ba sannan muka yi wanka, muka kwanta wajen tara da rabi. Washagari lafiya muka rabu, da zai fita na ce "Idan fita ta kama ni zan fita. Bai ce komai ba, ni kuma ban yi zaton bai amince ba.
Da yake na dora cewar na fara Home service akan status dina. Sai kuwa na dinga samun k'ira akan ana bu'kata ta a wuri kaza.
Na za'bi gida biyu, na bawa guda biyu hakuri akan wasu sun rigasu.
Na kammala gyaran gidan tsab.
Na fice. Wannan ranar har dare sannan na koma gida. A k'ofar gidan na tarar da shi, cikin wani irin yanayi. Yana ganina ya zabura ya mik'e.
Ni kuma ganin a waje muke yasa na zarta shi na shige. Sai kawai na tarar da k'ofar tamu da sabon kwad'o.
Na jinkirta amma bai shigo ba. Na gaji da tsayuwar jiransa. Na fara hassala ya gan ni amma ya kasa shigowa, yasan kuma ya canja kwad'o.
Na gaji na fita na tarar da shi yana zaune tamkar dutse ko motsi ba ya yi.
Na ce "K'ofar a rufe take fa".
Ko kala bai ce ba.
Na sake fusata. Na ce "Ka zo ka bu'de mini".
Nan ma tamkar da Dutse nake magana.
Allah yasa ma babu kowa a wajen. Zuciyata ta hauro matu'ka da gaske. Duk fa'din tashin da nake yi dan asirinsa ya rufu shi bai ga hakan ba. Murya na rawa na ce "Ni kake yiwa wula'kanci haka?"
A fusace ya ce "Wace ce ke? Gida ne bana bu'katar ki a cikinsa ba, ba sai ki koma inda kika fito ba, kin ga kin yi maganin wula'kancina, nima na huta da rainin da kike yi mini".
Jikina ya yi matu'kar sanyi, hawaye ya b'alle mini. Murya na rawa na ce yanzu a daren kake so na tafi gida?"
Shima murya na rawa ya ce "Ai ni a daren kika dawo mini gida. Dan haka ki koma inda kika fito ko ki je inda zaki, ai dai babu sisin ki wajen kama gidan har yanzu, bare ki yi mini sabon isgilanci".
Na fara kuka na ce "Na rantse da Allah Tijjani kai bahago ne na k'arshe. Duk tunanina mu ha'du mu rufawa kanmu asiri wani bai ji ko ba'a gane halin da muke ciki ba, amma gaba'daya ka murde ka canja, ka ki da'din azanci. Dan Allah ka fahimce ni, nifa ba jin da'din yadda kake yi nake ji ba".
A tunzure ya ce "Yo dama ni ina da abin da zan jiyar da ke da'di ne?"
Na yi sakare ina kallonsa gaba'daya ya juye ya koma wani azababben mutum.
A hankali na ce "To zo ka bu'de mini, tunda dare ya yi."
Ya girgiza kai ya ce "bana son ganin ki a cikinsa."
Na juya na ce "Shike nan na gode".
Na fara tafiya ni kad'ai ga shi wajen ba kowa, tsoro ya kama ni, da na ji kamar ana bina. Sai da muka iso wajen hasken solar na juya sai na ga shi ne yake bin bayana.
Na tsaya na ce "To mene ne kuma, ba dai ka kore ni ba?"
Da sanyin murya ya ce "Bakin titi zan raka ki, kada karnu ka su biki".
A tunzure na ce "Allah yasa ma kuraye su kama ni, su cinye ni!
Bai ce komai ba, har muka isa inda zan bi na yi gida. Na kalle shi na ce "Yanzu me kake so na fa'dawa Baban Marina?"
Kai tsaye ya ce "ki fa'da masa gaskiyar abin da ya faru kawai".
Na marairaice na ce "Tunda har ka rako ni nan, nasan ka huce, mu koma gida ka fa'da mini abin da na yi, ba sai ka ce na baka hakuri ba, zan nemi afuwarka".
Ya girgiza kai ya ce "A a bana bu'katar ki a gidan ne, ki je gida, ko ki je ki kwana a wajen neman ku'din ki".
Ganin zai sake tunzura da yawa yasa na tafi din. Amma tafiya kawai nake yi, bana ko sanin inda zan jefa k'afata. Tashin hankalina ace na je gidan Marina da sunan bacin rai. Na sani masu murnar ganina sai sun fi masu yin jajjabi yawa. Kuka nake yi sosai. Me zan cewa Baba da Gwaggo ni Yabi? Ko Ubaida k'aramarmu ba'a taba tura ta gida da sunan ta yi laifi ba sai ni? Ni kuwa dama akuyata ta yi shura.
Ina ganin hanyar da zan bi na isa gidan, amma sai na bi wanda zata kai ni gidan Yaya Ummi.
K'arfe tara da rabi na shiga d'akinta tamkar jifa. Cikin sa'a mijinta ya je Jos d'aurin auren yar kaninsa sai gobe litinin zai dawo.
Ganina a wannan daren ga kuka ina yi, duk sai ta diriri ce ta dinga fa'din mene ne, daga ina kike?"
Ina kuka, na fa'da mata Tijjani ne ya ce "Bazan shigar masa gida ba."
Ta dauki salati ta ce "To ke da ina kika je?"
Na fa'da mata gaskiya.
Ta yi shiru ta ce "Tsakani da Àllah laifinki ne Yabi. Tunda bai amsa miki ba, ai kinsan ba wai yana so ba ne. Sannan me yasa kika yi dare har wajen tara?"
Na yi shiru sai kuka kawai nake yi. Domin tskani da Allah ban san ina son Tijjani sosai ba sai yanzu da ya yi min irin wannan hukuncin. Ji nake kamar na yi ta zunduma ihu har kowa ya fahimci rad'ad'in da nake ji. Baya ga haka kuma fishin da na ga ni shinfide a kan fuskarsa ya sake dagula mini lissafi.
Cikin kuka na ce "Ni bana son na je gida Yaya Ummi. Baba fishi zai yi da ni, haka ma Gwaggo. Ga magauta su tasa mu gaba da dariya da zunde".
Ta nisa ta dauki k'aramar wayarta ta ce "ku'din ciki babu yawa, amma bari na gwada na ga ni.
Bugun farko ya dauka tamkar me jira a k'ira shi.
Ta gaishe shi da walwala.
Sai kuma ta ce "Yaya Bulkachuwa sai ga Yabi ta zo mini a wannan daren, kuma abin mamaki ta ce wai kai ne da kanka ka koreta, ai da sai ka yi hakuri da safe ka tura ta gidan."
Dake a sifika ta saka sai na ji ya ce "Na kasa yin wannan tsinkayen Ummilolo. Amma yanzu taimake ni ta kwana a gidan ki, gobe sai ta wuce gida".
Da sauri ta ce "A a kasan ni dakina daya ne. Zan dai rako ta, ko mene ne da safe zan dawo mu tattauna tunda dare ya fara yi".
Ya yi shiru tabbacin bai gamsu ba.
"Ka yi shiru Yaya Bulkachuwa".
Ya ja gauron numfashi ya ce "Kunyar ki nake ji ne Ummilolo. Kada ki shiga wannan maganar. Ba ke ce zaki yi alkalancin nan ba. Domin ban dauki al'amarin da sau'ki ba".
Ta sassauta ta ce "Ai tunda na gan ta na sani baka dauke shi da wasa ba. Amma tunda na yi maka waya ai sai ka mini lamini tunda ni da kai ai kasan tun fil'azal bata b'aci."
Ya ce "To shike nan".
Da walwala ta ce"Yauwa Yaya Bulkachuwa rabin raina na gode".
Daidai lokacin kuma ku'din wayarta ya k'are. Ta ce "Ai bu'kata ta biya."
Kafin ta yi mini magana, sai ga shi ya biyo bayanta. Tana dauka ya ce "Yi zaman ki Ummi ai ba zai yiwu ki fito b'akatatan a wannan lokacin ba. Bari na wakilce ki, na zo da kaina. Amma ki fa'da wa mijinki gobe, ki zo mu zauna".
Ta ce "Na kuwa gode! Gobe da ikon Ubangiji da wuri zan zo".
Ya ce "Na gode, ki gaida yaran namu".
Ba a wani dauki lokaci mai yawa ba, sai ga shi ya k'ira ya ce ya zo.
Ta raka ni har soron gidan sannan ta juya tunda k'ofar gidan nasu tamkar kasuwa yake shaguna ne reras gefe kuma teburan masu sayar da nama na gaba kuma masu kayan miya.
A mashin dinsa ya zo. Na haye ba tare da na ce komai ba.

*End of part 2.*

*MARUBUCIYA*
*BINTA UMAR ABBALE🍒*
*Tana farincikin sanar muku da sabon littafin ta mai suna YA ZA A YI? Wanda za ta sake shi ranar d'aya ga watan Oktoba (first October) wannan karon ma marubuciyar taku ta shirya sosai domin nishad'antar daku tare da fad'akarwa🥰 Ba sai na tsaya yi muku bayanin rubutunta ba domin da yawa daga cikin masu bibiyar litattafanta sun san cewa tana k'okari gurin ganin ta yi rubutu akan abubuwan da suke faruwa, mussaman a zamantakewar aure da tarbiyar yaranmu, Uwa uba kuma litattafanta akwai soyayya mai tsafta da nishadi da 'karuwa! Kada dai ku sake a baku labarin wannan littafin mai suna( YA ZA A YI)❓ Zaku iya yi mata magana ta Whatsapp da wannan numbers*
*08089965176*
*07084653262*

*WANNAN LITTAFIN NA KUDI NE BIYA KUDIN KARATUN KI TA WANNAN ASUSUN DAN GUJE WA BAKAR TA'ADA!*
*REGULAR 500*
*VIP 1K*
*VIA*
*2384876855*
*SURAYYA IBRAHIM DAHIRU*
*ZENITH BANK*

*KO*
*7061488065*
*SURAYYA DAHIRU IBRAHIM*
*OPAY DIGITAL SERVICES.*

*TURA SHAIDAR BIYA TA WADANNAN LAMBABOBIN*
*08032773332*
*09069067488*.

*MARUBUCIYA*
*BINTA UMAR ABBALE🍒*
*Tana farincikin sanar muku da sabon littafin ta mai suna YA ZA A YI? Wanda za ta sake shi ranar d'aya ga watan Oktoba (first October) wannan karon ma marubuciyar taku ta shirya sosai domin nishad'antar daku tare da fad'akarwa🥰 Ba sai na tsaya yi muku bayanin rubutunta ba domin da yawa daga cikin masu bibiyar litattafanta sun san cewa tana k'okari gurin ganin ta yi rubutu akan abubuwan da suke faruwa, mussaman a zamantakewar aure da tarbiyar yaranmu, Uwa uba kuma litattafanta akwai soyayya mai tsafta da nishadi da 'karuwa! Kada dai ku sake a baku labarin wannan littafin mai suna( YA ZA A YI)❓ Zaku iya yi mata magana ta Whatsapp da wannan numbers*
*08089965176*
*07084653262*


Har muka isa gidan ba wanda ya yi magana.
Kai tsaye daki ya shige ya yi kwanciyarsa. Ni kuma na shiga kicin na sama wa kaina abin da zan ci. Sannan na yi wanka. Na gyara jikina sosai, na isa dakin na tsaya gaban madubi na bi ko ina na goga turare.
Na tarar da shi idon sa biyu. Na zauna na tausasa murya na ce "Fa'da mini abin da na yi, mu shirya kafin Yaya Ummi ta zo".
Ko motsi bai yi ba, bare ya yi magana.
Na zuba masa ido ina tuna yadda yake rawar jiki da tsoron fishina. Amma tunda ya fahimci na fa'da komar sa shikenan abu ka'dan zai fitittike ya yi mini fishi.
Na kai hannu na fara shafa sumar kansa da nufin lallashi tunda na gane shi mutum ne mai son a rarrashe shi tamkar mace.
Da kakkausar murya ya ce "Bari Asiya Toro".
Nan da nan kuwa na cire hannun nawa domin gargadi ya yi mini mai kauri.
Haka muka kwana duk rai babu da'di.
K'arfe takwas sai ga Yaya Ummi da alamu tare suka fito da yaranta yan makaranta su suka wuce ita ta taho nan.
A falo muka zauna.
Ita ta fara ce wa Yaya Bulkachuwa ka ga yadda ka koma kuwa me yake faruwa ne?"
Ga mamakina yana bu'de baki sai ce wa ya yi "Ba'kin cikin Asiya ne yake neman kassara ni".
Gabana ya takarkare ya fadi. Me nake yi masa ni Yabi?"
Yaya Ummi ta ce "me ya faru haka Yaya Bulkachuwa?"
Na kasa kunne sosai dan na fahimci abin da zai ce da kyau.
Sai ji na yi ya fara rattabo laifukan da nake yi.
Cikin nutsuwa ya ce "Ummi tunda aka rufe gidan burodi da nake zuwa na shiga yanayin rashin ku'di. Har ta kai bana iya yin abin da ya kamata. A farko rimi rimi Asiya ta ke ha'kuri da duk abin da zan kawo. Tare zata sarrafa mu ci, ko da garin kwakai ne. Amma tafiyar bata yi nisa ba sai ta fara gazawa. Ta fara raina kokarina saboda an riga an cusa mata akidar watarana ita ce zata rike mini gidan. Komai zan siyo na bata ba zata yi amfani da shi ba. Kwanaki na siyo sabulun wanka Gif har yau bata ta'ba ba, ta bayar an siyo mata wanda ya dace da ita.
Duk ban ce komai ba. Sai shekaranjiya kuma ta ce mini zata fita, ban zaci wai gida gida zata dinga bi tamkar dilalliya ba. Tun safe da ta fita sai yamma lis ta dawo wai ashe gida je ta dinga bi tana yin k'unshi ana biyanta saboda kawai ta fahimtar da kowa ita ce take ri'ke da ni!
Ya nisa ya zarce da fa'din tana shigo wa ta tarar na yi komai Kamar yadda ta sani tun farko ni aikin gida bai zame mini komai ba, amma kinsan me ta ce mini?"
Yaya Ummi ta girgiza kai cikin sanyin jiki.
"Tana bude baki sai ce mini ta yi wai na zama Yabi. Wato na zama mace mai zaman gida, ita kuma ta zama namiji mai fita ya yi gwagwarmaya. Duk yadda maganar ta buge ni hakan na daure na ha'diye maganar na kawar mata da kai!
Ya fa'da yana hucin b'acin rai.
Gaba'daya jikina ya mutu, zufa sai keto mini take yi. Na tabbatar duk abubuwan da ya lissafo ina yinsu tabbas. Amma ko ka'dan a zuciyata ban daukesu zasu b'ata masa rai ba. Domin ko ka'dan ban yi da nufin wula'kanci ko na muzanci ba. Asalima ni na yi ne da nufin kyautatawa.
Kafin Yaya Ummi ta ce komai sai ya cigaba da fa'din "Jiya kuma ta ce mini zata fita ban amsa mata ba. Sai kawai na dawo na tarar bata gidan, tun azahar nake zaman jiranta bata dawo ba sai tara saura. Fa'da mini Ummi me ta mayar da ni, me kuma take nufi da ni ne?"
Yaya Ummi ta yi shiru ta rasa abin fa'da domin ta fahimci ransa ba k'aramin baci ya yi ba.
Sai kawai ta buge da ba shi hakuri tare da ce wa"Tabbas ta yi kurakure, amma ka yi hakuri zata kiyaye."
Ya girgiza kai ya ce "Ba fa zan yi hakuri ba tunda ba zan dauki wadannan BAK'AK'EN TA'ADODIN da ta fara tsirarsu tun daga yanzu ba. Gara manyammu su san halin da muke ciki kada abu marar da'di ya faru ace na bawa marar d'a kunya."
Yaya Ummi ta yi maza ta ce haba dai, haba dai Yaya Bulkachuwa ba abin da zai faru sai alheri. Ai gata nan duk ta ji abin da ka fa'da, za kuma ta kiyaye."
Ya girgiza kai ya ce "Kin san kafiyarta, ba ji zata yi ba, ni kuma ba zan yarda ba. Kin ga gara komai a yi shi a bayyane ba sai abu ya yi tsananin da rayuka zasu baci da yawa ba".
Ni gaba'daya ma mamaki ya ba ni, ya fitittike akan sai na tafi, ita kuma Yaya Ummi sai wani lallab'a shi ta ke yi. Yo ni ban da ina jin tsoron al'amarin da zan fuskanta a gidnman Marina ma zunde da dariya, da ba'kin cikin da zan jefa iyayena da na girgije na bar masa gidansa.
Ta kallo ni tare da mini signal din na ba shi hakuri. Na dauke kai na juyar da fuskata. Domin nima na hauro ai komai nake yi dominsa ne. Amma tunda shi ba zan yi masa alheri ya yaba ba, sai dai ya bini da sarhutu to shi kenan na daina yin komai. Fita k'unshi da sunan Home service kuwa na soke sai ya nemo wani laifin kuma. A k'asa zuciyata kuma sai hirji nake yi tare da fatan Yaya Ummi ta kashe wannan matsalar domin duk yadda na hauro nake kurarin zan iya tafiya din, zuciyata tafi son zaman, nafo son ya huce ko ba dan ahalin Marina ba. A karan kaina na damu da fishinsa.
Da k'yar Yaya Ummi ta shawo kansa ya ha'kura da maganar sai mun je gaban Baban Marina. Ta bu'de murya ta ce "Ki ba shi hakuri".
Fuska a daure, amma cikin azama na ce "Allah ya baka hakuri".
Daga haka na tsuke fuskata da bakina.
Tare muka karya da ita. Sai da zai fita suka tafi tare ya sauke ta a gidanta.
Ban zauna ba sai da na yi abinci na zuba a flask.
Na gyara ko ina, sannan na fara yiwa wata da ta zo k'unshi. Bai dawo ba sai yamma, kafin lokacin kuwa na yiwa mutum hudu duk sun tafi. Budurwa d'aya ce ta rage da yake ita zan mata bak'i da kuma kitso.
Da azama na saki kitson na fita ina yi masa barka da dawo wa, domin ya tsani ya dawo ban bar abin da nake yi, na je gare shi ba.
Idan wani ne ya fa'da mini Bulkachuwa zai dinga yi mini irin wannan mulkin mallakar zan k'arya ta shi kai tsaye. Ni da kaina mamakin kaina na ke yi. Na yadda nake rawar jiki a kansa. Wata'kila kuma yadda yake sarrafa ni ne sirrin. Gabadaya tsoron fishinsa nake yi tamkar me.
Ya mik'o mini ledar hannunsa mai dauke da karas da atile.
Hannu biyu nasa na kar'ba na dinga fa'din "Na gode, Allah ya k'ara budi.".
Na wanke hannuna, na yi kicin na ha'da abincinsa na kai masa.
Na debo pure water masu sanyi guda biyu na saka a plate. Na ajiye a gabansa.
Na fita na debo masa karas da atilen na zuba a bowl na wanke na kai gabansa.
Na dan yi jim na kalle shi yana cin abincinsa cikin nutsuwa. A hankali na ce "zan je na k'arisa kitso."
Da walwala ya ce "To".
Na fita, a raina kuwa sai fa'din nake yi sarkin son mulkin tsiya. Kai Tijjani baka bai ni haka ba, Yasin"
Da daddare ya dinga laluba ta, na maze ban yi masa abin da nake yi masa ba.
Ya fara ce wa "Amma dai kin san bana son haka, sannan kuma kin san kin ci bashina jiya".
Da sauri na ce "Ba wani bashin ka da na ci. Kai ne ka kawar da kai, alhalin ka ce ko mun yi fa'da kada mu saka aurenmu a ciki. Amma jiya sai da ka saka su tsundum."
Cikin kwantar da murya ya ce "Hankalina ne ya tashi matu'ka da gaske. A ce matar aurena tana garanranba a gidajen mutane har almuru da sunan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login