Showing 159001 words to 162000 words out of 184118 words

Chapter 54 - Bakar Taada Hausa Novel Complete

Masifar zafin da nake ji a zuciyata da kirjina ya wuce misali ina fatan na mutu kawai Asiya".
Na kasa ce wa komai. Yaya Salisu ya ce "Innalillahi wa inna ilaihir rajiun! Allah mun tuba."
Nazira kuwa kuka take yi tana fad'in "Dama nasan ba haka siddan ka runtse ido ka kafe sai ka aure ta ba."
Ni kuwa na zama tamkar mutum mutumi. Domin a yanzu na yarda Tijjani na bukatar na samar masa da nutsuwa. Tunda duk yadda yake cikin wannan tashin hankalin amma yana fad'in yadda yake ji game da al'amarin ta. Na tabbatar ba son zuciya ko tozarci ba ne ya sanya yake fad'a mini yadda yake ji akan Nasiba ba.
Cikin tausayi nake kallon sa gabad'aya ya zube, ya yi duhu. Tausayi, so, kauna suka sake yi mini rubdugu a dukkan zuciyata da gangar jikina.
Murya a tausashe na ce "Ka tsananta addu'a ka kuma yi hak'uri. Da kaina zan kawo ta ka ganta".
Ya zuba mini ya ce "Yaushe?"
Na ce "Gobe ko jibi".
Ya yi k'asa da kansa ya ce "Goben dai."
Da k'arfin hali na ce "To".
Ya kidime ya ce "Wanne irin to kike nufi Asiya?"
Na ce na gaskiya da gaskiyar magana ".
Ya saki ajiyar zuciyar samun nutsuwa ya ce "Ina twins, me ya hana ki zo da su na gansu?"
Idona cike da k'walla na ce "makaranta suka bi yaran gidan."
Haka muka ba shi abin da zamu ba shi. Aka tafi da shi.
Tuni kuma an saka ranar da za'a gurfanar da shi gaban kotu.
Sai dai Yaya Ammar ya tabbatar mana BAUCHI za'a dawo da shi. Tunda a cikin jahar Bauchi aka kama shi. Ba'a san dalilinsu na kawo shi Kano ba tare da sun sanarwa da kowa nasa ba har tsayin kwanaki biyu.
Da yammaci sosai muka isa Toro. Muka tarar da Nasiba a k'ofar Dada domin mijin babarta aka kwantar a asibitin koyarwa na jamiar Jos. Lokacin da abin ya faru tana can bata dawo ba, sai yau aka sallame su. Babar tata ta wuce gidanta da marar lafiya.
Ni da Nazira muna kallon yadda gabadaya ta takure ta kasa sakat tunda muka shiga. Akwai alamun tasku a tare da ita.
Na yi jarumtar ce wa "Nasiba Bulkachuwa na ta jajen ki. Ya damu da rashin ganinki cikin masu zuwa duba shi tare da jajanta masa. Gobe zan koma, sai mu tafi tare ko ya samu nutsuwa".
Ta kasa amsawa. Hatta Dada ma na kashe ta da kunya gabad'aya sun rasa me zasu ce. Yanayinsu ya sa na gane suma tamkar an tursasu ne akan sha'anin Tijjani.
Washagari kuwa na shirya yara na ce mun tafi Kano. Baba bai so ba, amma saboda lallaba farincikina yake yi bai hana ba. Sai ma ya ce "Ubaidun Inna ya raka ni.
K'ofar Dada na dire. Na tisa Nasiba a gaba muka tafi a kan dole ba yadda zata yi. Domin na lura tsoro nake bata.
Har muka isa Kano ba wata hira a tsakaninmu.
Sai kuma muka hadi da tasgadon y'an sanda. Wai ba zamu gan shi ba, ana yawan yi musu zarya da sunan ganin Tijjani bayan shi mai babban laifi ne.
Hanif ya fashe da kuka yana ce wa "Zamu ga Baban 2 dan Allah ".
Hamim ma ya fara kuka sosai.
Watak'ila tausayi suka bawa wannan babban dansandan sai kawai ya bada umarnin a fito da shi.
Ga mamakina sama da mintina goma da isowar Tijjani bai kalli inda Nasiba take zaune ba. Tunda ta gaishe shi ya amsa hankalinsa na kan su Hanif da suke kan cinyarsa bai sake bi ta kanta ba.
Ni da yara kawai ya ke kulawa.
Na mike na ce "Bari na baku waje tunda idona yasa ka kasa yin hirar".
A zabure ya ce "Zan ci mutuncin ki little! Jiya da yau ban ji azabar da nake ji ba. Akwai abin da ake yi mini wanda zalunci ne da k'eta. Alfarmar Annabi kuma Allah zai kawo mini k'arshen al'amarin tunda kwana nake ina fad'awa Ubangijin al'arshi ya warware mini wannan masifar. Ni ko wannan k'azafin da aka yi mini baya gigita ni, kamar yadda al'amarin ta yake gigita ni. Amma akwai Allah."
Ba Nasiba ba, ni kaina sai da na ji babu dad'i ainun. Na yi tsuru tsuru na kasa ce wa komai. Domin na tabbatar k'arshen muzanci Tijjani ya yi shi. Amma na sake gasgata surkulle ake yi masa. Ban da haka jiya k'iri k'iri ya fad'a mini yau na kawo masa ita. Ko tunanin rikicin da zan yi masa bai yi ba, saboda an ringa an kidima shi a kanta. Na daure na rakito ta, amma bai ko kalli inda take ba, sai ya b'uge da cin mutunci. Jikina ya mutu domin nasan zata zargi na kwaso ta ne dan na saka mijina ya wulakanta ta a gabana. Tunda a hakan kafatalin gidan Marina sun tafi akan na gama da Bulkachuwa tsorona yake ji. Sai abin da na shimfi'da zai bi. Har fad'i suke idan bana son mutum to ko kallon arziki Tijjani baya masa saboda gudun zuciyata.
Ta mike a kasalance ta ce "Bari na jira ku a mota Yabi".
Murya babu amo na ce "To".
Tana tafiya ya saki dogon tsaki mai karfi da na tabbatar zai je kunnuwanta.
Na zuba masa ido ba tare da na iya ce wa komai ba.
Da k'yar na ce "To da sun san zasu mayar da kai Bauchin me yasa suka kawo nan?"
Ya kalle ni ya ce "Akasi aka samu. Sun tsayar da ni a farko ban tsaya ba. Shine suka harbi tayar motar ikon Allah ne yasa motar bata yi bari da ni ba".
Zuciyata ta buga da tsananin gaske na ce "mene ne dalilin ka na k'in tsayawa Baban 2? Ta ya ya kana dan k'asa amma ka ce ba zaka girmama dokar k'asar ba? Ko dai kasan dama baka da gaskiya ne?"
Nan da nan ya kidime ya ce "Wallahi Tallahi ina da gaskiya, bansan an saka mini wannan abin ba. Ban sani ba, ki yarda da ni Asiya!.
Na saki karfaffan numfashi tare da ce wa "Rashin tsayawar ka ba k'aramin hujja zasu kafa da ita ba. Na yarda da kai".
Ya nutsu ya ce "Idan har kin yarda da ni to kowa ma kada ya gasgata ni Asiya! Nasan mahaifuyata zata shaide ni, duk fitina ta bana harkar maye bare kuma a yanzu da na girma. Ba zan shiga safarar abin da nasan illah ce ga al'umma ba. Ina miki ranstuwa da girman Allah ban san mugun abu aka bani ba. Waya kawai aka mini akwai sakon kaya da zan karba a Dutsen tanshi, idan na kai Kano za'a karba a biya ni. Kinsan kuwa ina harkar sakonni(Delivery). Ban tab'a zaton za'a mini kutse a cikin sana'a ta ba. Ni yanzu babban tashin hankalina ke ce. Ban san hukuncin da za'a yanke mini ba little. Kinsan k'asar nan waka sani ne waya sanka."
Idona taf da hawaye na ce "Nasan baka aika ta wannan BAK'AR TA'ADAR ba. Da ikon Allah ina tare da kai, komin tsanani".
Ya murmusa ya ce "Alhamdulillah! Na samu amincin firgicin da nake ciki. Dan Allah Asiya kada ki canja, kada ki juya mini baya a cikin wannan halin canka cakare da nake ciki." Idonsa ya kad'a sosai ya kasa cigaba da magana alamun ya shiga rudani.
Hanif ya ce "Baban 2 kada yi kuka zamu zauna mu taya ka zama. Ammo ta tafi ta barmu tare da kai".
Hamim ya ce "No zamu je mu koyo yadda zamu kwace shi daga hannun yan sandan kawai".
Na yi k'asa da kaina kawai ina hawaye domin tausayin da suka ba ni ba kad'an ba ne.
Ban iya ce musu komai ba. Shine ya yi jarumtar sake rungume su tunda a akan cinyoyinsa suke. Murya na rawa ya ce "Baban 2 baya karya domin wanda ya yi karya ya zagi Allah, Wanda ya zagi Allah kuwa dan wuta ne. Dan haka am innocent, ban yi laifi ba. Sharri aka yi mini. Kowa ya yi sallah ya yi wa Baban 2 addu'ar ya zama free".
Suka had'a baki wurin ce wa zamu yi sosai ".
A sanyaye muka rabu domin gobe za'a dawo da shi BAUCHI dan shiga kotu.
A hanya Nasiba ta sake rasa kuzarin ta, dama kuwa bata iya sake wa a gabana na dade da fahimtar a takure take da ni. Abin da Bulkachuwa ya yi mata kuwa ya sake sanyaya mata jiki. Ina hankalce da ita, ina ganin yadda take son yi mini magana amma ta kasa.
Cikin kundubala ta ce "Yabi!.
Na amsa da "Na'am" murya babu amo.
Ta kalli twins da suke barci a jikina. Ta ce "Idan na ce miki bana son Yaya Bulkachuwa na yi karya domin na girma da son sa, ke ma kin sani. Idan na ce miki a yanzu dole aka mini a kan aurensa zaki yarda?"
Ban ce komai ba. Illah ido da na zuba mata.
Ta numfasa ta zarce da ce wa "Ni da kaina bani da yadda zan yi ne. Domin kuwa mutane da yawa suna haduwa da kalubalen a hadasu da iyaye karkatattu. Sai dai duk da hakan ba zamu ki sonsu ko janye wa daga gare su ba. Na sani tun farko soyayyar sa gare ni ba mai yawa ba ce, bare yanzu da yake auren ki. Dan Allah ki yi hakuri kada ki datse mu'amala da ni Yabi. Al'amarin zumuncin yau ya shiga rudani mai yawa, amma idan aka yi hak'uri aka danne, aka yi sassauci sai a samu masalaha a duniya, a kuma samu rabauta a duniya.
Zan yi iyakar kokarina na fita a harkar mijinki, na yarda Yaya Bulkachuwa ba mijina ba ne, ba kuma zai zama ba. Kada ki ce maganganun da ya yi cin fuska ya yi mini, zahirin gaskiya ya amayar".
Na rik'e hannunta murya na rawa na ce "Ban kullece ki ba. Amma idan na ce ban ji ciwon abin da ya faru ba na yi karya. Har abada ba zan iya auren mijin ki ba Nasiba. Amma na hak'ura na barwa Allah ya yi mini zabi akan lamarinku. Tunda ai ba haramun ba ne. Shi yasa na hak'ura na barwa Allah komai".
Dukkanmu kowa zuciya ta narke, muka dinga kuka.
Ubaid da yake gaban motar ya yi tsaki ya ce "Sai ku yi ai. Amma ai mu kam mun kudire matukar ya aure ta sai ya sako mana ke ko da kuwa a gaban alkali ne".
Na daskare da maganar sa. Na tuna na ba shi watanni shida. Gabadaya ma shekarunsa ashirin da uku ne. Amma ya yi magana kamar wani babban wanmu. Sai kuma hawayena ya sake zuba a dalilin yadda maganar auren Nasiba da Bulkachuwa ta zama silar samar da soyayya a tsakanin ahalin Baban Marina. Yan ubancin da manyanmu suke gwada mana ya yi matukar zangwanye wa.
Na yarda mafi yawan kalubale ya kan zo da wata nasarar komin kankatarta sai dai idan ba a kula ba, ko an bari hankali ya kwace an yi fishin da ya shallake hankali.


✍️
*Y'ar uwa, ya mukaji da bubukuwa?* *Daga nan fa har january kusan ko wanne sati akwai biki, in ba na kusa ba akwai na nesa, ban da tunanin gudunmuwa da ma kudin man da zakaje bikin ga tunanin abunda zaka saka.*
*Balle ace maaikaciya ce ko CEO ce kina business din ki, kinsan all eyes on you🧐, ke ba sayen atamfa ba komi tsadanta anyo copynta, shima lace haka, cabdi! To albishirinki yar uwa!*
*UMM NIHLA malaysianfabrics ta dauke miki damuwa, tana da fabrics kala kala masu sauki da inganci kuma babu inda zaki samesu in ba wurinta ba, kije taro ki haska kowa sai ya tambaye ki me kika saka ina kika samu💃 maza garzaya gurinta kusa labule.* https://wa.me/message/F3EWRSHQPQAAH1

Annur food Delicious*
*Da k'arfin zuciya da guiwa na ke muku shunen inda zaku samu kayan da na zano a kasa cikin saukakkan farashi.*
*Shaida nake yiwa kayan annur domin dadinsu da ingancinsu ya kai kurewa*
*HANZARTA ki nemi kayansu dan ki gasgata batuna*
*Garin kunun tsamiya garin danwake, garin borkono, yajin daddawa, man shanu, nikekkakiyar gyada ta kunu da ta miya*
*08039183880*


Washagari duku duku Baba Maryo ta zo.
Domin na je gaida Dada na juyo muryarta tana ce wa "Ai ko baki bijire mini ba gabad'aya ba zai aure ki ba, wane shi. Ashe dama arzikin da ake ga ni a tare da shi kazami ne? To ba zata sabu ba. Aure kam tabbas ya fasu fas. Dama ai ba so kike ba, tunda kin ringa kin tsorata da iblishiyar mata tasa. To ta je ta samu sai ta tabbata a matar d'an safarar kwaya ita kad'ai. Mutane babu Allah a ransu. Ka dinga neman arziki yaki haram yaki halal. Dama so na yi na nuna wa uwarta da ita Yaya Hauwa iyakarsu. To tunda bai shiryu ba, huta toro an bar musu shi. Watak'ila ma daurin rai da rai za'a yi masa. Ai da a sau'udiyya aka kama shi fille wa d'an banza mai yiwa iyayensa kallon raini za'a yi".
A sanyaye Dada ta ce "Ai kuwa mai sunan manya ya yi hankali da girmamawa yake gaida kowa kamar ba shi ba. Kawai dai yana nuna son kai ne, ya fi nan nan da k'ofar Alhaji. To wannan kuma dariyar matarsa yake so, ya za'a yi tunda ya jarabtu akan ta.!"
Baba Maryo ta ce "Ban da ni din, ni ce ai ko gaishe ni ba zai yi ba, ya kullace ni ainun. Tunda ake fad'in labarin wadatar da yake ciki, ashana bata tab'a had'a mu ba. Kai ya taka ya je gidana bai san wannan ba. Idan ya gan ni tamkar zai doke ni. Amma yanzu da yake ba shi da kunya har zarya yake yi mini. To na fasa ba shi Nasibar. Ba zai yiwu ba, ya je dai ya k'arata da afiruwar matarsa mai izgili. Kai ahalin Tijjani da Yabi za'a yi majununai, biyu ta had'u y'aya'n iska marasa albarka".
Na sake jin cikin rauni Dada ta ce "Yanzu fa sun yi hankali suna girmama kowa. Yabi da kanta jiya ta zo har nan ta tafi da Nasiba wajen mai sunan manya. Kin san idan Yabin da ce ba za'a yi hakan da ita ba".
Ta saki tsaki ta ce "Yo tunda ya rikice mata ai dole ta kai ta. Amma daga yau zan yanke komai."
Dada ta kame bakin ta. Ita kuwa ta ci gaba da sakin maganganu masu nuni da dama ba Tijjanin take so ya zama surikinta ba. Wadatar da ake kallon ya samu ne ake son su lasa. A yanzu da ya hadu da ibtila'i kuma an janye saboda dama ba da zuciya d'aya aka yi abin da aka yi ba.
Na shiga daga bakin kofa na gaida Dada, duk da tana ce wa "iso mana, ina tagwaye ko basu farka ba?"
"Eh suna barci Dada".
Na gaida Baba Maryo a gajarce. Ta amsa fuska babu walwala. Har na juya sai ce wa ta yi "Yabi ashe haka ya faru da Tijjani?"
Na ce "Eh!
Sai ji na yi ta ce "To wadannan kadarorin da suke yatsun ki da kunnawan ki sai ki hanzarta kad'ar da su dan ki dauka masa lauya domin dai a gindinki da na iyayen ki ya k'are. Gyatumar sa ma yar amshin shata aka mayar da ita. Watak'ila hakkin ta ne ya sanya yake gani a k'waryarsa.
Na juya da nufin bata amsa sai na tuna kanwar mahaifina ce. Ba zai yiwu na yi fad'a da ita a yanzu da hankali ya ratsa ni ba. Nasan kuma dole ni ce a ciki tunda shi da kansa Baban Marina zai ce ai kanwarsa ce ta shiga rigarsa mana.
Dan haka sai na hadiye na ce "To Baba Maryo zan yi hakan".
Ta tunbatsa domin ta washi mu fad'i sunan ta.

***
*BAUCHI*

Kotun ta cika makil domin sharioi za'a yi masu daukar hankali.
A kuma wannan ranar za'a yanke wa Tijjani hukunci.
Da wuri muka iso. Da ni, da Yaya Salisu da Baban Marina da kuma Yaya Salamatu.
Sai ko Yaya Ammar da yake Bauchi.
Karfe shadaya aka fara shari'arsa. Babu wata hujja da zata wanke Tijjani. Domin lambar da ya ce an k'ira shi da ita kwata kwata bata shiga. Sannan an tambaye shi me yasa da aka ba shi kaya bai bude ya duba ba? Tunda ya dauki delivery a matsayin sana'a. Me yasa ba ya nazarin kauce wa dukkan wata matsala da zata taso. Wajibi ne idan zaka karbi sako, ka duba ka ga mene ne a ciki tunda idan aka kama ka ai kai ne a ciki.
Sannan me yasa bai binciki ainihin inda mutumin yake ba?"
Lauyan da k'aninsa Aliyu ya daukar masa, ya kasa inkarin hujjojin lauyoyin gwamnati tunda tabbas Tijjani bai yi bincike ba ya karbi kaya. Bai kuma bude ya duba ba. An ba shi abu a d'aure cikin buhu kawai ya danna a mota. Sannan bai san mutum ba. Kawai ance idan ya je Kano za'a karba a biya shi.
Sannan lauyan gwamnati ya k'ara kafa hujja da ce wa "saboda Tijjani yasan ba shi da gaskiya ya dauko wiwi da koken mai nauyin tam goma shi yasa ya ki tsayawa da jami'an tsaro suka tsayar da shi wanda hakan rashin da'a ne da raina jami'an tsaron da k'asa ta wakilta su duba shige da ficen al'umma."
Na zuba wa Tijjani ido da yana tsaye jikin kantar da ake tsayar da wadanda ake tuhuma. Ya zube aiun, ya sake yin duhu.
Zuciyata ta karaya, na hangi rashin sassauci a shari'ar. Ta zo fiye da yadda muka tsammace ta.
Domin maganarsa d'aya ce ba shi kayan aka yi, bai san kuma san mutanan ba. Lambar wayar da ya gabatar a matsayin wacce aka kira shi da ita bata yi.
Jikin kowa ya yi sanyi. Bayan dogon rubutu da alkalin ya yi.
Ya yi gyaran murya ya ce "Duba da hujjojin da lauyan gwamnati da kuna jami'an tsaro suka gabatar kotu ta yanke wa Tijjani hukuncin shekaru biyar a gidan yari babu tara. Bisa kama shi da safarar kwaya wanda hakan ya saba kashi na goma sha takwas b cikin baka. Bayan haka kotu ta sake d'aure shi shekara d'aya bisa cin zarafim jami'an tsaro da ya yi ta hanyar yi musu gaddama. Har ila yau kotu ta daure Tijjani na watanni uku ko tarar dubu ashirin saboda rashin kiyaye kaidojin kasuwanci. Ba zai yiwu mutum yana hulda da jama'a ba amma babu taka tsantsan da sanin me mutum ya dauko ko mai zai kai. Yana cikin dab'iun d'an kasa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login