Showing 57001 words to 60000 words out of 184118 words
Chapter 20 - Bakar Taada Hausa Novel Complete
sake cewa ba.
Sai tashin mashin dinsa na jiyo.
Yana fita na sauko na karya.
Na kai ragowar kicin.
Na tsinci kaina da son karewa gidan kallo.
D'akuna biyu ne a jere akan baranda.
Sai kuwa guda daya daga can gefe kusa da bandaki.
Sai kicin a dayan gefen.
Gini ne ba laifi gashi ya sha fenti. Kan barandar ma tayals ne. Haka kicin dinma.
A fili na ce "ko me ya hana a saka tayal a dakin?
Na kalli yadda aka k'awata
mini kicin din da kayayyaki. Na sani kuma mafi yawa dangin mahaifiyata ne suka zo da kayan.
Da sauri na nufi d'akin da yake mak'wabtaka da dakina wanda na tabbatar shine falon.
Ina shiga na ji sau'kin takaicin da nake ciki.
Domin dai falon ya yi kyau daidai na masu karamin buri.
Kujera ce irin mai L din nan. An saka ta a bango guda, da yake falon ma an saka tayals sai aka saka madaidaicim kafet a tsakiyar falon.
Ga kuma TV an mak'ala a bango, sai fridges daga can gefe.
Shikenan sai labulaye kalar kujeru da kafet din wanda suka kasance royal blue ne. Ga katon agogo mai kyau shima an kafa shi.
Na zauna ina jin da'din yadda na ga wajen. Na sani da ace Yaya J ne mijin tabbas da na kasance cikin farin-ciki mai yawa.
Na kunna fanka ganin da akwai wuta.
Na fita na nufi daya dakin da ya fi kusa da band'aki.
Na leka na ga bashi da girman wanda aka saka mini gado a ciki.
Ba komai sai labule. Gefe kuma akwatin kayansa ne da tarkacensa sai takalmansa.
Na janyo kofar kamar yadda na ganta a sakaye na fito.
Na koma falo ina jin dau'kin tv na kama ni.
Duk kokarina na kasa ha'da ta.
Dole na hakura na kashe na jona wayata a caji.
Na zauna iska.lr fanka tana kad'a ni.
Ina haka sallamar babbar mace ta saka na zabura ina amsa wa.
Na marabce ta da sakin fuska duk da dai ban gane fuskarta ba. Sannan a kallon farko na fahimci ba bahaushiya ba ce, tunda ga siffarta har tsagun da suka cika faffadar fuskarta
Na gaishe ta da girmama wa tunda na ga zata haife wacce ta fini ma.
Ta ce "Ni ce a waccar kofar. Suna na Gadatu. Ana kirana Maman Safiyanu. Mijina bara ya rasu, ina da yara maza da mata. Allah ya sanya alheri.
Allah kuma ya zaunar da mu lafiya.
Na yi k'asa da kaina. Na tashi na kawo mata cin cin da dubulan.
Bata ci ba. Na juye mata a leda ta tafi da shi.
Bata Jima da tafiya ba sai ga y'arta da alamu suka nuna zata girme mini. Gata da garin jiki. Doguwa ce sannan a koshe take ainun. Ta ce "wai Mamansu ta ce na bada kasko a kawo mini garwashi ko zan yi turare.
Na dauko na bata, fuskata a sake.
Ta kawo mini kuwa. Na tambayi sunanta ta amsa mini da cewa "Rafi'a" Na ce "To na gode miki".
Na zuba turare nan da nan gida ya kaure, ya zama na amaryar sosai.
Ba jima wa kuwa jama'ar Kangire suka zo motarsu guda, suka dinga addu'a da jan kunnena akan bawa marar d'a kunya na zauna lafiya da mijin da Allah ya za'ba mini.
Daga haka suka tafi wanda kai tsaye Kangiren suka wuce.
Haka kuwa aka dinga shigi da fice.
Hatta Babah ma ta zo kafin ta tafi Bulkachuwa ta dinga yaba yadda ta gan ni.
Tare da su Nasiru da Ihisan ta zo.
Da kulawa mai yawa ta ce "Duk abin da zai miki kada ki biye shi waya kawai zaki dauka ki sanar da ni, ni kuwa zan miki maganin matsalar. Ki yi hakuri, ki yi biyayya, ki yawaita addu'a. Sannan ban da rashin kunya.
Allah ya yi miki albarka."
Kuka kawai nake yi. Kukan da bansan dalili ba, ban saniba ko dan na ga ita ma hawaye take yi. Bansan kukan da take ta faman yi ba, na farin-ciki ne ko na tausayina ko kuwa na yadda aka juya al'amarin ne oho.
Ashe tare suke da shi ya coge a tsakar gida.
Sai da suka fito sannan ya bi bayansu ya rakasu.
*MARUBUCIYA*
*BINTA UMAR ABBALE🍒*
*Tana farincikin sanar muku da sabon littafin ta mai suna YA ZA A YI? Wanda za ta sake shi ranar d'aya ga watan Oktoba (first October) wannan karon ma marubuciyar taku ta shirya sosai domin nishad'antar daku tare da fad'akarwa🥰 Ba sai na tsaya yi muku bayanin rubutunta ba domin da yawa daga cikin masu bibiyar litattafanta sun san cewa tana k'okari gurin ganin ta yi rubutu akan abubuwan da suke faruwa, mussaman a zamantakewar aure da tarbiyar yaranmu, Uwa uba kuma litattafanta akwai soyayya mai tsafta da nishadi da 'karuwa! Kada dai ku sake a baku labarin wannan littafin mai suna( YA ZA A YI)❓ Zaku iya yi mata magana ta Whatsapp da wannan numbers*
*08089965176*
*07084653262*
✍️
*WANNAN LITTAFIN NA KUDI NE BIYA KUDIN KARATUNKI TA WANNAN ASUSUN DAN GUJE WA BAKAR TA'ADA!*
*REGULAR 500*
*VIP 1K*
*VIA*
*2384876855*
*SURAYYA IBRAHIM DAHIRU*
*ZENITH BANK*
*KO*
*7061488065*
*SURAYYA DAHIRU IBRAHIM*
*OPAY DIGITAL SERVICES*
*TURA SHAIDAR BIYA TA WADANNAN LAMBABOBIN*
*08032773332*
*09069067488*.
*Idan kina bukatar Oriflame products ko wanne irin ne, ko Kuma kina sha'awar yin register da su*. *Ki tuntubemi babbar dealer din su Aisha lame*
*Ina kuma fad'a muku akwai da daddan ganyen shayi na Lame Tea*
*Akwai pop corn*
*07036662633*.
37&38.
Da yamma lis sai ga Yaya Ummi da tarkacen su tsintsiya da sauran kayayyaki har da su kuloli masu kyau da zannuwan gado na sani wanda aka samu na gudunmawa ne aka karo zabo mini masu kyaun cikinsu.
Ta sake gyara mini kicin din. Na bata tarkacen robobi da wani flask din roba irin mai biyun nan.
Kayan lefena kuwa turamen atamfofi biyu na bata da hijabi hadi da kayayyakin kwalliya.
Ta dinga yi mini addu'ar Allah ya zaunar da ni lafiya.
Ta bu'de jakar hannunta ta dauko wata yar roba mai dauke da garin magani kore. Ta sassauta murya ta ce ko zaki dinga shan wannan a cikin madara ko yoghurt?"
Na kar'ba na ce "Na menene?"
Ta yi k'asa da kai ta ce "farin ciki da dokin juna zai sanya muku"
Na yi maza na mayar mata cikin jakarta. Tare da cewa "Da dai ba irin wannan mutumin aka aura mini ba."
Ta ce "shikenan da har da INGANTATUN SAIWOWIN DAHUWAR GIMBIYAR KAZA. Amma zan ajiye miki. Na sani wataran zaki nema da kan ki.
Idan kuma na yi amfani da su, sai a kawo miki wani ta hannun kanwar kawata Aisha Lame mai siyar da kayan kwalliya masu daraja (oriflame).
Tasan Surayya Dee da take kawo su daga chadi.
Baki na tab'e baki, ina kallonta kawai, domin har abada ni Yabi bazan yi wani abu dan na sanya Tijjani farin ciki ba.
Muna haka ya shigo, suka gaisa sosai cikin walwala da tsokanar juna.
Bai jima da dawowa ba, ta yi haramar tafiya nata gidan.
Da yake mutumiyarsa ce.
Ya ce "Ta jira ya kai ta a mashin".
Ta galla masa harara da cewa "Ni zaka goya Yaya Bulkachuwa?Wallahi ba zan sake biye wa tsokanar da kake yi mini ba, dan ka riga ka zama k'anina".
Ya kwashe da dariya ya ce wannan kuwa shine tatsuniyar gizo da k'oki. Ke yanzun nuna mini kika yi Asiya Toro ta fini a wajen ki?"
Ta mak'e kafa'da ta ce "Ato Wallahi ka kama k'afata dai".
Ya tsugunna a gaban ta ya ce "Dai-dai ina zan kama Ummi?"
Ta yi gaba ta bar shi tana fa'din "Hmm sai ka yi kai ka'dai".
Ta goyi y'arta shi kuma ya d'aukar mata ledar kayanta.
Ya yi gaba ya na jiranta.
Da k'yar muka rabu. Cikin lallashi take ta nanata "Ki zauna lafiya, ki kwantar da hankalinki da na iyayenmu dan Allah. Kin ga dai an riga an yi auren nan. Allah ya taimake ki, ya hore miki shi. Nan da wata daya ki cigaba da sana'ar ki, domin mace mai neman na kanta ta huce takaicin babu".
Ta bata rai ta ce "kinsan dai ba'kin cikin da na kwankwada a dalilin bani da yar'uwar da aka aurar da muke daki daya. Yanzu murna nake yi kema an aurar da ke na samu abokiyar ha'di. Komai ya taso miki ni ce a hakku saura ki ce zaki bayar da ni a wajensu ta hanyar nunawa duk daya muke ni da su a wajen ki.
Gasu nan su hudu ne dakinsu daya."
Nima na bata rai na ce "To idan hakane ita kuma Ubaida dawa zata hada kai kenan?
Ko so kike ita ma ta fuskanci tsananin da kika fuskanta? Ni fa dukkan y'ay'an Babanmu ina sonsu da dukkan zuciyata".
Ta zaburo mini ta ce "Ban ce kada ki so su ba, amma ai wata kusan tafi wata".
Na yi dariya na ce "To kawai ki ha'da ni da Nazira da kuma Ubaida ki jamu a jikinki, ki dai-daita su da ni. Shikenan Kinga kin samu k'anne uku aurarru tashi guda.
Da sannu suma manyan sai su dawo cikinmu mu zama madaurin tsintsiya".
Ta yi gaba tana fa'din "To uwar Iyah! Ta ya ya zan ha'da shakikiyata da dan uba su zama duka daya ne?"
Na k'yal-k'yale da dariya tare da fa'din "Yaushe zaki dawo?".
Ta ce "sai an kwana biyu".
Na zauna ina nazarin Yaya Ummi mutumiyar kirki ce, amma rashin adalcin da manyanmu suke yi mata da kuma yadda kishiyarta ta jefa yan'ubanci a tsakanin y'ay'ansu ya sanya ta k'yamaci dan uba. Na yi mata uzziri domin ita da yaranta suna fuskantar zazzafan yan'ubanci.
Ina fatan watarana duka y'ay'an Babanmu mu zama abu guda, ina matu'kar son mu gane girman nasaba irin ta uba daya.
*KUN TUNA MAI GYARAN GUDUYO?*
*OK NA NUFIN FASEELAT BABBAR DILA TA G.H.T.*
*KO WANNE NAU'IN KAYAN GHT TANA SIYAR DA SU AKAN FARASHI MAI RANGWAME*
*KAWAI KU TUNTUBE TA A WANNAN LAMBAR DAN GANIN JERIN KAYAN DA TAKE DA SU*
*TUN DAGA KAN SUPPLEMENT, SABULAI DA LIPTON*.
*MASANIYA CE AKAN KAMFANIN DOMIN TA SAMU KARRAMA WA DAGA KAMFANIN A BANA, HANZARTA KI TUNTUBETA DAN SIYA DAI DAI KO SARI.*
*IDAN KUWA KINA SON YIN RIGISTA DAN FARA KASUWANCIN KAWAI KI TUNTUBETA DAN KUWA DA KYAKKWAR ZUCIYA ZATA MU'AMALANCE KI*
*07039269802*
***
Bai dawo ba, sai da ya sallaci Isha.
A falo ya tarar da ni, na yi wanka na zira doguwar riga cotton mai zuwa da mayafi babba.
Na shafa turaren oudi(concentrate).
Ya kalle ni ya ce "Ranki ya da'de Asiyata".
Na galla masa harara na ce "Ba taka ba ce".
Ya murmusa ya ce "Ta Ummi ce shikenan?"
Na yi shiru domin so nake na fa'da masa abin da zai bak'anta masa rai.
Amma tunda ya saki maganar bari na k'yale shi sai idan ya sake katobarar cewa ni tasa ce zan tabbatar masa ba tasa ba ce, ba kuma zan zama tasan ba.
Ya ajiye ledar hannunsa ya fita.
Sai gashi ya dawo da kananun bowls da kuma fork biyu.
Ya zauna kusa da ni.
Ya bude ledar kamshin hadadden balangu ta buge ni.
Ya juyo mini dauri guda ya turo mini gabana. Tare da robar yogurt madaidaiciya mai sanyi, da kuma robar ruwa shima mai sanyi.
Sannan ya juyo nasa daurin. A hankali ya ce "Bismillah Amarya".
Ban kula shi ba. Na gama yaukina na dauka na fara ci. Sosai naman ya yi mini da'di, sannan kuma mai laushi ne.
Na cinye tas na bu'de yogurt na fara sha. Rabona da abinci tun karyawar safe.
Duk da an kawo mini daga gida amma ban iya ci ba.
Ganin na cinye yasa ya turo mini nasa ya ce "Kara Asiya".
Na yi kamar ban ji ba.
A sanyaye ya ce "Ba kyau a yi magana mutum ya yi kamar bai ji ba".
Nan ma tamkar ba na wajen.
Ya yi k'wafa alamun ya k'ulu.
Ganin hakan ya sanya na tashi na bar shi na yi dakina ko kwanon da na ci ban kawar ba, bare na kawar da nasa.
Ina shiga kuma na sanyawa dakin sakata.
Na cire mayafin rigar na haye gado na yi kwanciya ta.
Tunda na kwanta ban farka ba, sai da asuba shima kwakwasa mini kofa ya yi.
Kafin na fito tuni ya bu'de gida ya wuce masallaci.
Yau kam har na gama barcina na tashi k'arfe goma. Da na bu'de kofa na fito a zaune na same shi akan barandar. Babu alamun gaggawa a tare da shi.
Yana ganina ya mike da sauri yana fa'din "Bari na janyo miki, na roba da sanyi, na rijiyar kuwa dumi ne da shi.
Ya bu'de bandaki ya dauko botiki ta nufi rijiyar.
Na bishi da kallo. Mamaki nake yi dama Tijjani zai iya yin laushi haka?
Duk wula'kancin da nake yi ba ya fasa yi mini hidima.
Na sake bin kayan jikinsa da kallo. Alamu sun nuna ya yi wanka. Sabon yadi ne a jikinsa amma ba alamun karin guga. Na tabbatar yadda tela ya ba shi hakan ya saka su.
Na ja tsaki sosai. Dai-dai lokacin kuma ya zo daf da ni.
Ya ce "Asiya Toro wata rana za'a wayi gari a ga kin zama tsaka fa".
Ban kula shi ba, bare na tanka ya samu sanadin da zai jani da surutu.
Ya wuce ya kai mini bayin.
Na shiga na yi wankana na fito.
Yauma atamfa na dauko koriya Shar. Doguwar riga ce da ta manne a jikina.
Na gyara sosai.
Na gyara d'akin, na zauna. Ya yi sallamah na amsa a dole. Ya ce "Na shigo?"
Na ja tsaki, na kame bakina na tsuke.
Jim ka'dan ya shigo. Na daga kai na kalle shi. Fuska a daure na ce "Na baka izinin shigowa ne?"
Da walwala ya ce "Tunda baki zabura kin ce kada ka shigo mini ba, ai nasan kin kammala adana yan kananun abubuwan da kike yi mini k'yashin ganinsu".
Ba'kin ciki ya turnike ni.
Na murguda baki na ce "A a kiyasai ne k'arewar kankantar".
Ya zauna bakin gado ya ce "Ban da samun guri irin na ki Asiya. Ta ya ya zaki dinga rufe mini kofa, kina hayewa gadon da ba'a siya miki ba sai saboda ni, ni kuma ki bar ni da kwanan kasa. Kwana nake yi ina artabu da sauro. Amma ke babu ruwan ki, ba kya gudun maleriya ta yi mini illah?".
Na ki kula shi, bansan me yasa yake bani haushi ba, baya burge ni ko ka'dan.
Ya sake yin k'asa da murya ya ce "Ki yi kokarin kyautata lahirarki Asiya. Babu ruwan alkalami da cewar ba kya sona. Matu'kar ina kwana da ba'kin ciki ki sani kina cikin fishin Ubangiji".
Na rasa me zance masa domin dai ya sako wanda ban isa na fa'di bak'ar magana a kansa ba.
Kan tilas na share ban ce komai ba.
Ya tashi tsaye ya ce ki taso ki karya ga abin kari can a falo.
Bauchi zan je. In sha Allah ba zan wuce la'asar ba.
Za'a kawo miki abinci da rana. Ki shirya gobe zaki fara yin girki".
Sai lokacin na fashe takaicinsa da cewa "Ba zan yi ba.
Har abada ba zan dora tukunya saboda kai ba".
Babu damuwa a tare da shi ya ce "Babu laifi. Lokaci zai fayyace komai ai".
Ya juya ya tafi bai sake cewa komai ba.
Har shad'aya ina daki ban fita falon ba. Sai da cikina ya tsananta yi mini kartan yunwa.
A dole na fita. Na tarar da waina a karamin flask. Sai kunu a jug. Daga dukkan alamu siyowa ya yi.
Kan dole na zauna na karya.
Ina zaune har aka fara kiran sallar azahar. Na idar kenan sai ga almajiri yana kwankwaso kofar shigowa wajena. Da yake ni ce a farko su kuma su Mama na can ciki.
Bamu ha'da komai ba, sai kofar shigowa gidan.
Da sauri na fita na bu'de masa. Ya mik'o mini flask din abinci babba mai kyau. Wai wani ne ya bashi ya kawo wannan kofar.
Na kar'ba ba tare da na ce komai ba. Na sani abincin da ya ce za'a kawo mini ne.
Sai da na zauna a falo na bude na ga alalan gwangwani ya ji manja.
Da alamun kifi a ciki. Na ji wani iri a dalilin yunwa nake ji ba ka'dan ba. Ni kuma bana iya cin alala na koshi. Tabbas an gyara shi ne dan a burge ni. Na rufe, ina sake jin yunwa na taso mini gadan gadan.
Na yi shiru ina nazari. Sai na ji wayata na k'ara. Ina dubawa na ga Tijjani ne domin ina da lambarsa tun lokacin kwamshina da muka fara dan gaisawa. Na ki amsawa har ta katse. Ya sake kira ban dauka ba. Bai fasa ba, sai a karo na hudu na dauka a fusace na kan ga a kunnena, bayan na danna alamar amsa wa.
"Yaro ya kawo miki abinci?"
"Eh".
Na fa'da a gajarce.
Ya ce "kin ci na safen kuwa?"
"Wai ni kam jinjira ce ne da zaka dinga mini tambaya tamkar kankanuwar yarinya? Idan ma ban ci ba ai cikina ne ko? Tunda baka shawarce ni akan abinda zan ci ba, ka ajiye mini wanda ya yi maka".
Ya nisa ya ce "Asiya Toro kenan!
Cikin kuka na ce "Komai zaka ce Allah na ganinka ai".
A sanyaye ya ce "Kukan na menene Asiya?"
Na sake tsananta kukan na ce "Akan me za'a kawo mini alala? Ni bana ci".
Ya tausasa murya ya ce"Alalan gwangwani ne, saboda ke har kwai da kifi aka saka a ciki. Daga gidan abokina Abdul aka kawo miki fa, kema kuma kinsan matarsa mai tsabta ce".
Da kukan na ce "To ni ina ruwana, ni dai ba zan ci ba, kuma yunwa nake ji tunda kunun ma ban iya sha ba, ya riga ya yi sanyi k'arara."
Ya diririce ya ce "Ki yi ha'kuri bari na sa a kai wa Ummi macaroni da kayan miya sai ta daho miki yanzu. Hakan ya yi miki?"
Na yi shiru. Ina harara tamkar yana wajen.
Ya sassauta ya ce "Please mana Asiya ki ce to".
A shak'e na ce "Yanzu d'aya da rabi. Idan ya wuce uku da rabi bazan ci ba, gara yunwar ta kashe ni".
Ya dinga fa'din"Na gode sosai, bari na saka a kai mata yanzu. In sha Allah ba zai wuce hakan ba."
Ya katse wayar.
Na ri'ke wayar, haka kawai sai na tsinci kaina da mamakin yadda Tijjani yake rawar jiki a kaina. Gashi tunda na zo ban ta'ba yi masa wani alheri ko da ta magana mai da'di ba ce.
Yadda ya lank'awasa harshe yana rarrashi tabbas yana yi ne tunda ga kasan zuciyarsa. Na fara gasgata sona yake yi ba sha'awa ba.
Mintina biyar a tsakani ya sake kira.
Na dauka bayan ta kusa tsinkewa.
Da sauri ya ce "An tafi kai mata. Na ja mata kunne, na ce ta bar komai ta girka miki, tunda Nina sanya ta. Biyu da rabi zan aika a karbo mini. Dan haka zuwa uku za'a kawo miki in Allah ya yarda".
Na yi shiru. Ya numfasa ya ce "Asiya ba