Showing 90001 words to 93000 words out of 184118 words

Chapter 31 - Bakar Taada Hausa Novel Complete

sunan shafar mai wanda ni kaina ina matu'kar jin sakon nasa a dukkan jikina.
Yana cikin murzar tafin kafata. Wanda kafin ya zo kafar ya shafe mintina sha biyar.
Murya dakushe tabbacin so yake ya koma ruwa ya ce "Nasiba ce asarrariyar Asiya?"
Na fizge kafata na tashi. Na ce "Ina dalilin gatsa sunan matar wani ne Tijjani? Kusan mintina ashirin da yin maganar ashe duk yadda na barka kake yin yadda kake so da sunan shafar mai, zuciyarka na tunanin suntumemiyar halitta ko? Wallahi bazan iya da bala'in ka ba Tijjani!
Ganin da gaske na fitittike, zan birkice masa.
Jikinsa na bari ya ce "Allah ya baki ha'kuri, na yi kuskure. Sai dai ya kamata ki mini shaidar tun ma kafin a mini babban alherin ba ni auren ki ai na fita a dukkan sha'aninta. Bare kuma yanzu da take matar wani. Dan Allah mu bar maganar, bana sonta. Ki yi hakuri."
Ya dauko mini wata riga ya ce "Ga gifts din ki na zama matar aure, tun first night dinmu nw so baki, to bata iso a lokacin ba."
Cotton yar kanti. Gaba'daya rigar tafi dacewa da yara y'an shekaru goma. Domin har da teddy wacce aka yi jakar goyo da ita. Sannan da hula irin mai malafar nan.
Kalar ruwan hoda (pink )da yarfin filawa mai ruwan lemon tsami (lemon green) ce. Ba karamin kyua ta yi ba.
Ya mik'o mini sabon pant. Ya ce na saka miki?"
Na juyar da fuska. Ban amsa ba. Sai da na shanye kunyar na na ce "Tijjani da gaske dai kallon yarinya kake mini. Ban da haka wannan rigar ai ta yiwa Iklima ka'dan bare ni. Kasan kuma Anas ne yake bina ba ita ba."
Kai-tsaye ya ce "Na sani. Sha'awa ta bani, shine na yi kundubalar d'auko miki ita, rabin ku'din na bayar. Abokina yake kawo su daga China. Ta kusa dubu ashirin, sonta nake yi, saka kawai".
Na ce "Tsakani da Allah da atamfa ka siyo mini, yanzu wannan ina zan saka na je da ita?"
Ya ce "Ba dan ki sa ki fita na siyo ta ba. Dan ki saka mini na kalle ki a yadda nake son ganin ki ne".
Ganin ya b'ata fuska ya sanya na juya na saka pant din. Ina juyowa ya bani sabuwar breziya yar mitsil kalar wando da alamu set ne tare suka zo. Ban ce komai ba na kar'ba. Ina ayyana wato ya riga ya gama gane wacce zata yi mini. Domin duk na lefena sun yi mini yawa duk da k'ananu ne sai dai ko nan gaba. Domin da na aikawa Gwaggo akan ta bayar, dawo mini da su ta yi, ta ce nan gaba zasu yi mini na adanasu.
Sai da na shafa hoda na goga jan baki kalar ruwan hoda.
Sannan na zura rigar. Ta shige ni tsab. Ta d'an zarce guiwata da ka'dan, kasancewar ba ni da tsayi. Ya ce "Wow This is Asi beauty lady".
Na dan yi murmushi. Ban ce komai ba. Da kansa ya sa mini hular ya d'auko sabon turare a cikin kayansa da aka rubuta Active woman. Ya bu'de ya hau fesa mini.
Kamshin turaren jikinsa da wanda ya fesa mini suka hadu suak bige ni. Suka isar da wani irin sako akan Tijjani a cikin zuciyata.
Shi kuma ganin na koma masa wata yar yarinya kankanuwa ya sanya ya sure ni. Ya yi falo da ni. Yana ta sakin maganganun da suke da nauyin bayyana wa.
Komai da barin jiki yake yi mini. Ya ajiye ni akan kujera ya ce "Bari na kawo miki abincin Little Angel."
Har cikin zuciyata na ji da'din sunan. Duk sunayen da Bulkachuwa yake fa'da mini babu wanda na ji dadinsa irin little. Domin ya dace da ni k'warai da gaske.
Shiru shiru bai dawo ba. Sai na yi kamar na leka shi, sai kuma na fasa.
Can sai gashi da tray da ya jero kayan abincin.
Da walwala ya ce"Sorry little na bar ki ke ka'dai, ga shi babu wuta bare kallo ya hana ki gundura da zaman jiran kukun naki"
Na k'yal-k'yale da dariya na ce "Wai kai ne kukun?".
Cikin gamsuwa ya ce "Ba ki aminta ba? To mene ne aikina ban da na fita na yi aiki tukuru dan na nemo miki abin da zaki ci.
Idan kuwa ina gida, idai baki bata mini rai ba. Still aiki zan miki dan na hutar da ke shiga kicin kullu yaumin".
Na murmusa ba tare da na ce komai ba, domin na yarda da dukkan zuciyarsa ya ke yin maganar.
Ya bu'de kwanon abincin ga mamakina sai ganin fanke na yi subu-subu sun soyu sun bada kala mai daukar hankali.
Na kalle shi da mamaki na ce "Tijjani yaushe ka iya fanke haka?"
Ya saki murmshin jin dadi ya ce "Ki bari sai kin ci sai ki tambayi na iya ko kuwa makwaki na yi".
Na sauko ya ha'da mini shayi mai madara da milo. Shi kuma ya zuba bak'i.
Muka fara cin fanke wanda ba karamin dadi ya yi ba. Na kalle shi na ce "Ya yi da'di sosai. Na ji har da k'wai da madara ka saka. Maimakon ka bar madara ka zuba a shayinka."
Ya rausayar da kai ya ce "Ke dai ki sha my little".
Ya kashe mini ido sannan ya ce "Ai ina ganin amfaninta. Addu'a nake yi sosai na samu damar da zan daina siyo miki ta sacet. So nake kullum ki sha ta ruwa gwangwani guda. Ta yadda ba zaki dinga gazawa da al'amarina ba".
Kunya ta yi matu'kar kama ni. Na sanya dukkan hannuna na rufe fuskata, ina wani irin murmushin da bansan ta inda yake bullowa ba.
Da k'yar na cigaba da cin abincin bayan ya ce "Duk a wajen Baba na koyi girki. Yadda kika ga Aliyu da Nasiru suna hidima irin ta y'ay'a mata nima irin wannan goyon ta yi mini.
Kullum fa'di take yi, tunda bata samu mace ba, ba zai yiwu a ce ba zamu tallafa mata da kaomai ba.
Kullum cikin fa'da mana take yi mu koyi aikin gida dan wataran mu taimaki iyalinmu. Annabin Rahma da yafi kowa daraja yana tallafawa iyalinsa. Ba mallakewa ba ne dan namiji ya yiwa mace hidimar girki, wanki, ko ta shara ba. Amma kuma ta ce "Ban da wanke wanke wannan na yan daudu ne".
Muka k'yal-k'yale da dariya domin kuwa munsan kawai ra'ayinta ne amma babu aibu idan mutum ya yi. Ya ce "rigar nan fa ta yi miki kyua my little. Tamkar na dauwama ina kallon ki".
Na murmusa ka'dan tare da ce wa"Thank you" a gayance.
Na marairaice na ce "Ya maganar tomfirint din?"
Cikin nutsuwa ya ce "zuwa wani satin zan kai ki da kaina".
Na fa'dada murmushi na ce "Na gode Tijjani".
Ga mamakina sai na ji nauyin gatsa sunan da na yi, ta mamaye ni. Karon farko da na ji hakan a rayuwata.
Na lura shi kuma yana cikin maza yan ka'dan da basu damu da a fa'di sunansu kai-tsaye ba.
Tas muka cinye fanken.
Na kwashe kayan dan nasan idan ya mike zai kwashe ne.
Na kai wajen wanke wanke na ajiye.
Na koma wajensa na ce "Wai da yaushe ka yi kwabin ne?"
Ya nisa ya ce"kina barcin gajiyar da na tara miki. Ni fa duk kallon jaruma nake yi miki. Ashe a tsiwa da dambe da sana'ar k'unshi kike da jarumtar".
Na girgiza kai na ce "oh haka ka ce? Ai shikenan next time zaka gane ashe dazu ba karamin jarumtar na yi ba".
Ya jani jikinsa ya ce "Kin san bana wasa a wannan fannin tsokanar ki nake yi, idan akwai abin da yafi jarumta kin yi dazun".
Na kalle shi cikin nauyi nauyi, kunya kunya na ce "ka ji tsoro?"
Da sauri ya ce "Na ji".
Bai fita ba sai da ya dawo daga sallar azahar.
Muka ci abincin da tare muka yi da shi.
Sannan ya fita zuwa gidan Alh Ado Naira zai yi musu gyaran satellite tunda aka kawo wuta suke ta yi masa waya.
Kamar ana jiran ya fita aka fara zuwa lalle da kitso.
Shike nan muka shirya da Tijjani. Wata irin soyayya yake gwada mini mai wuyar samu. Da ya ga na canja fuska zai fara susuce wa, ya dinga jaye jaye magana, ko fita ya yo sai ya dawo. Matu'kar ban ware masa ba, ba zai samu nutsuwa ba. Ni da kaina na sani an jarrabe shi a kaina. Domin gaba'dayana a tsaye ban fi iya ruwan cikinsa ba. Duk zafin ransa baya son mu yi fa'da. Cikin rarrashi yake tafiyar da ni.
Komai da rawar jiki yake yi mini. Kullum safiya ya wajaba kansa share duka gidan. Ya sa tsintsiya ya wanke band'akin, sannan ya tashe ni na yi wanka. Mafi yawa da safe da burodi muke karyawa. Dan haka shayin ma sai dai na gan shi a filas ya riga ya dafa.
Da nutsu sai na ga ne tunda na daina gudunsa a shimfida shike nan ya tattara dukkan hankalinsa a kaina da lamarina.
Baya taba yin dare a waje.
Ana idar da sallar isha zai dawo ya rufe gidan shike nan sai gobe.
Idan kuwa uzziri ya yanko masa sai ya bugo waya ya sanar mini yana waje kaza. Na ce to tare da addu'ar ya dawo lafiya.
Ranar da yan rikicin suke kusa kuwa, na botsare masa idan ya dawo.
Ya yi ta barin jiki wajen rarrashi na.
Tuni muka fara jarrabawa har mun kusa kammalawa. Da kansa yake kai ni. Idan mun gama sai na yi masa waya ya zo ya dauke ni.
Muna tsaka da jarrabawa Nazira ta haifo d'anta lafiyayye.
Dan haka zarya nake yi tsakanin makaranta da gidanta. Har aka yi suna yaro ya ci sunan wan mahaifin mijinta Ahamd. Ni da kaina na lank'aya masa Abid.
Sosai na yi mata hidima ita da yaronta.
Ranar suna wanda a lokacin watan Maijidda biyu da haihuwa, y'arta Sajida ta yi gubibi da ita.
Tana hannuna ina kare mata kallo. Na rasa gane da wa take kama a tsakanin itayenta Jabir da Maijidda.
Saratu da Firdausi suka shigo. Ita Firdausi ta haihu. Saratu ce ta ke ja itama yau ko gobe.

*Akwai kaya masu kyau a cikin farashi mai sauki*
*Maganin sanyi*
*Saiwowin Tsumi*
*Saiwowin dahuwar kaza*
*Saiwowin dahuwar tattabaru*
*Gumba*
*Tsumin kwakwa*
*Y'aya'n gadali*
*Hadadden daka*.
*Tsugunno mai sa a matse*
*Goran tula*
*Goran tula syrup*
*Garin goran tula*.
*Maganin gyaran nono*.
*Zuma ta mussaman*.
*Tsumi*.
*Da sauran kayayyaki na mussaman da basu da illah*.
* Domin kuwa asalin Saiwowin ne da ake kawo su daga Chad*.
*Abu mai kyau shi ke siyar da kansa ku tuntube ni dan samun naku kayan cikin sauki da mututantawa. Ina aikawa ko ina a fad'in tarairaiyar Nijeriya*
*08032773332*

Na kallesu da murmushi na ce "Ni kam da wa Sajida take kama ne?"
Kafin na rufe baki Maijidda ta ce "Da Abbanta mana. Yo ko makaho ya shafa ai yasan kama take da Honey. Shiyasa yake kara sonta domin kullum ya dauke ta sai ya ce mata "Ta zabo uwarta da kanta".
Gaba'daya jikinmu ya yi sanyi domin kuwa kowa yasan neman magana kawai take yi.
Dan haka sai na mikawa Firdausi yarinya na shiga hidimar raba abinci. Amma k'asan zuciyata ya yi nauyi akan lamarin Maijidda. Har aka watse ban sake yarda na zauna a cikinsu ba.
Har dare duk mana gidan Nazira.
Muna zaune sai ga yaro ya zo ya yi sallamah ya ce "Wai Asiya ta fito su tafi".
Na kasa boye masa abin da Maijidda ta yi.
Tun a hanya na hau rattaba masa abin da ta yi mini.
Maimakon ya bi bayana ya fa'da mini maganganun da zan ji da'di. Sai ce wa ya yi "To mene ne na bacin rai a ciki? Ke ma Ubangiji ya za'ba miki wanda yafi mijinta son ki, to sai me kuma? Ki bar maganar nan inba so kike na ga ne kishinta kike yi har yau ba".
Takaici ya kama ni goma da ashirin. Na kame bakina na yi dif. Amma na riga da na harzuka k'warai da gaske. Ga mamakina sai kawai shi ma ya share ni. Muna isa gida ya gama uzzirinsa ya yi kwanciyarsa ya rabu da ni.
Ba'kin cikin hakan ya sanya na dinga kukan sharbe. Bai ko motsa ba, bare ya nuna ya ga ne halin da nake ciki. Da kaina na kwanta. Da asuba bayan ya dawo nan ma kwnaciya ya yi bai nemi ni ba kamar yadda ya sabar mini. Ai sai kawai na fashe masa da kuka mai sauti.
Ya janyo ni jikinsa ya ce "Yi shiru, na baki hakuri kin ga".
Cikin kuka na ce "Akan me zaka yi fatali da ni?"
Da rauni a muryarsa ya ce "Akan me har yau baza ki bar kishin Jabir ba? Kina tunanin zan ji dadi idan na ga ne har yau ban yi nasarar shafe shi a ranki ba?"
Na yi shiru sai shesshekar kukana ne yake tashi.
Haka ya ajiye fishin nasa ya dinga rarrashi tare da shafata cikin nutsuwa. Daga hakan kuma ya shiga yin abin da baya gundara da yinsa.
Sannu a hankali muke rayuwa. Duk yadda Bulkachuwa yake tarairaya ta, akwai abin da yake mini wanda yake ci mini tuwo a k'warya.
Duk yadda na so na dinga saka mana kifi ko nama a cikin girkinmu ya k'i yarda. Idan kuwa har na bayar aka siyo na girka to zai ci iya abincin ne ya bar mini nama ko kifina.
Rannan da na nuna b'acin raina.
A zafafe ya nuna mini yatsa. Ya ce "Iya abin da nake da shi zan ba ki, ba kuma zan zauna ki shiga cikin lamarin rik'on gidana ba. Ke dai tunda kina samun ku'di fiye da ni, komai kike so ci akan abin da nake da ikon ba ki, ba zan hana ki ba. Amma ni kada ki ajiye, ko ki ba ni, bana so".
Ganin da gaske baya so din, sai na daina. Iya abin da ya siyo shi zamu ci. Da na bi yadda yake so, sai muka samu dai-daito. Domin duk ranar da ya ga kifi ko nama alhalin ba shi ya siyo ba. To fa yini zai yi babu sukini da walwala. Sai dai wani zubin na kan auni mangyada ko manja na zuba a galan din namu, ko na sayi ledar maggi. Wannan bai cika fahimta ba. Tunda wani lokacin zai siyo gwangwani biyu a leda ya juye a ciki.
Dan haka a duk lokacin da ya samu sararin siyo kwalba, kwanaki ka'dan nima zan sake siya na zuba. To baya ankarewa da hakan.
Abin da na lura bai dauki maganar da aka yi na ce wa ba zai iya ciyar da mu ba da sau'ki.


*Annur food Delicious*
*Da k'arfin zuciya da guiwa na ke muku shunen inda zaku samu kayan da na zano a kasa cikin saukakkan farashi.*
*Shaida nake yiwa kayan annur domin dadinsu da ingancinsu ya kai kurewa*
*HANZARTA ki nemi kayansu dan ki gasgata batuna*
*Garin kunun tsamiya garin danwake, garin borkono, yajin daddawa, man shanu, nikekkakiyar gyada ta kunu da ta miya*
*08039183880*

✍️
*MARUBUCIYA*
*BINTA UMAR ABBALE🍒*
*Tana farincikin sanar muku da sabon littafin ta mai suna YA ZA A YI? Wanda za ta sake shi ranar d'aya ga watan Oktoba (first October) wannan karon ma marubuciyar taku ta shirya sosai domin nishad'antar daku tare da fad'akarwa🥰 Ba sai na tsaya yi muku bayanin rubutunta ba domin da yawa daga cikin masu bibiyar litattafanta sun san cewa tana k'okari gurin ganin ta yi rubutu akan abubuwan da suke faruwa, mussaman a zamantakewar aure da tarbiyar yaranmu, Uwa uba kuma litattafanta akwai soyayya mai tsafta da nishadi da 'karuwa! Kada dai ku sake a baku labarin wannan littafin mai suna( YA ZA A YI)❓ Zaku iya yi mata magana ta Whatsapp da wannan numbers*
*08089965176*
*07084653262*

*Oriflame products*
*Daga make up artist din Guduyo*
*Idan kina bukatar Oriflame products ko wanne irin ne, ko Kuma kina sha'awar yin register da su*. *Ki tuntubemi babbar dealer din su Aisha lame*
*Ina kuma fad'a muku akwai da daddan ganyen shayi na Lame Tea*
*Akwai pop corn*
*07036662633

55&56.
Ranar asabar ya dawo da rana. Sai ga shi da macaroni guda biyu hakan ma taliya, da shinkafa mudu guda. Sai sauran kaya danginsu maggi da sauransu.
Na karb'e shi da walwala kasancewar ba kasafai nake yin k'unshi asabar da lahadi ba. Sai kitso ne yafi yawa a wadannan kwanakin, saboda ana hutun karshen mako.
Doguwar riga ce ta yadin material din *Umm Nihla collection*
*07020695644*
A lokacin kuwa watanmu kusan bakwai da aure.
Da na lura sai na ga kamar ba a cikin nutsuwarsa yake ba.
Na gabatar masa da ruwa da abinci.
A hankali ya ce "sai na dawo zan ci. Dauko mayafinki mu je gida".
Gabana ya takarkare ya buga. A ki'dime na ce "Me ya faru?"
Ya numfasa ya ce"Dada ce ta.."
Kafin ya karasa na katse shi ta hanyar saka salati mai tsananin gaske. Tare da ce wa "Ta rasu?" Na fara k'walla ina cewa "Dada yau kwana ya k'are Innalillahi wa inna ilaihir rajiun". Allah ka gafarta wa Dada!
Ya bu'de baki ya ce "Yaushe na ce "Ta mutu? Kin san yanzu damina ta tsananta. Ta je zagaya wa ne sai shaddar ta rufta da ita. Allah ya sa an ji k'arar ruftawar, da ba haka ba kam, da tuni ba wannan maganar ake yi ba. An ciro ta amma baki ga ba, duk ta daddauje sosai."
Bansan ya aka yi ba dariya ta sosai ta k'wace mini.
Na dinga k'yal-k'yale wa. Ya yi sak'are yana kallo na. Can ya kasa jurewa dariyar da nake faman yi babu k'ak'kautawa.
Ya kalle ni ya ce "Ban da dai lamarinki akwai k'uruciya mene ne abin dariya a ciki? Dada fa na ce miki ta fa'da shadda. Da kuma rai ya yi halinsa me zaki yi?"
Cikin dariyata na ce "Kuka zan yi mana. Baban Kasuwa nake yiwa dariya da ya kasa gyara band'akin gyatumarsa da take nuna masa soyayya ta daban shi da ahalinsa."
Gau na ji ya hambare mini baki. Ya d'aure fuska ya ce "Idan zaki iya yiwa k'anin ubanki rashin kunya, to amma kuwa ba a gabana ba. Domin kawuna ne k'anin uwata na kuma yarda k'aninta ne. Da zuwa na yi na dauke ki, ki gaisheta ganin kusan kowa na gidan har Ubaida. Amma tunda zaki dawo da rashin kunyar ki, sai ki zauna ki yi ke ka'dai".
Ya mike ya fice. Na bishi da gudu. Murya a marairaice na ce "Zan bika Tijjani dan Allah".
Ya zuba mini ido yana yi mini kallo mai tsananin gaske. Na sani so yake na ba shi hakuri, ni kuwa ban ga me na yi ba. Ai gaskiya na fa'da. Bayan haka ai ya buge mini baki, dan haka na waske na k'i ban bada

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login