Showing 48001 words to 51000 words out of 307403 words

Chapter 17 - Abban Sojoji Takun Karshe Hausa Novel Complete

tamkar zata fashe da kuka tace"Amma yaya kasan da maganar auren nashi shine ba'a sanar dani ba?saboda me?
  "Saboda halinki"! Kai tsaye ya bata amsa,
  "Tabbas naso in sanar dake ko alokacin,saboda kinsan cewa ni bana jin shakkarki,hajiya ameenace ta rokeni akan cewar karna sanar dake,saboda hakan zai iyasa ki fusata harma ki yanke ma Abusufyan hukunci mai tsanani,kuma a ƙarshe zumuncin dake tsakaninki da ita ya tarwatse,dana nace akan zan sanar dake har kuka saida tayi mun,wannan dalilin ne yasa ban sanar dake ba,kuma ana haka daga baya kwatsam naji labarin mutuwar auren Abusufyan ɗin,hada ƙarin haka yasa akabar zancen gaba ɗaya,ashe yarinya ta fita da cikinsa ta auri wani,to kinji dalilin dayasa mu kanmu bamu san da ya'yan nashi ba,har suka kai wannan girman a hannun mijin da ta aura daga baya,"
  Dakatawa yayi da maganar,falon yayi shiru na wani lokaci,kafin ya mayar da idanunshi kan Sgr dake zaune,yace mashi"ka kunna mata audio din nan daka kunna mun itama ta saurare shi,"
  "Okey,"ya amsa mashi tare da,daddana wayar hannunshi,ya shiga audio din tare da kunnashi,sannan ya miƙe tare da ƙarasawa kusa da kujerar da Ammi ke zaune ya miƙa mata wayar,yatsun hannunta na kerma tasa hannu ta kar6i wayar tashi,ta ajiye asaman hannun sofa ɗin tana sauraronshi,wannan audio din na labarin da abusufyan ya bayar ne da kuma Labarin dasu sehrish suka bayar na irin ukubar da suka sha a hannun ya sayyadi,ashe ranar da abun ya faru,Sgr ya ɗauki audio na maganganun da sukayi kaf acikin wayarshi,tabbas shi ba ƙaramin jami'in Soja bane!yana Aikinsa wani lokacin tamkar jami'in sirri,Na jinjina masa,da irin baiwar da Allah yayi mashi da kuma irin kwazon dake gare shi,ta ko ina Sgr ya haɗa,shiyasa nace maku shi ɗin komai nasa Extraodinary ne~~~

Miƙewa junaid yayi tare da ruƙo hannun Mommynsu yace"Shikenan mommy tunda mun kammala discussion din,ki taso muje falo pls,kada kice baki zuwa,in ba haka ba raina zai 6aci,wlh ko abincin dare bazanci ba,indai kika ƙi zuwa gaishe da modibbo,"
Cike da mamaki tace"Modibbo?kana nufin mahaifin maryam oummunsu Omar?
  daga mata kai yayi alamar eh,
Shiru tayi tana wani tunani,a iya saninta modibbo mutunne mai mutunci sosai,saboda shine ya taka ma Ammi burki a lokacin da taso Abba ya sake ta,tabbas bazata ta6a mantawa da halarcin da modibbo yayi mata ba,
Ganin ta miƙe yasa junaid sakin murmushi yace"mommy zaki ko"? Jinjina mashi kai tayi alamar eh,
Janyo hannunta yayi har suka ƙaraso falon,ganin hankalin mutanen dake acikin falon gaba daya yana akan Audio din da ammi ke saurare,hakan yasa itama ta samu wuri ta zauna,junaid ma ya zauna gefenta,yayin da idanunshi ke akan su sehrish,sam basu lura dashi ba saboda hankalinsu duk ya tashi,a sakamakon Audio din da aka kunna,saboda sun tsani jin labarin rayuwarsu,ko miskala zarratin,
  Kowa ya natsu yana sauraron audio ɗin,lokacin da Abusufyan ya kammala bada tarihin rayuwarshi da abu,sai next audio ɗin ya shiga wanda Jahad ke bada labarin rayuwarsu,nan take hankalin AMMI yayi mugun tashi,jikinta har tsuma yakeyi,tuni wasu siraran hawaye suka shiga zarya a kuncinta,ita kanta Alexandra jikinta ba ƙaramin sanyi yayi ba,tunda take arayuwarta bata ta6a jin tausayin wani ɗan adam ba,daga ita har ammin kamar yadda sukaji tausayin waɗannan bayin Allahn ba,Very heart touching story,wanda duk wani mai imani In ya saurareshi dole ya zubda hawaye,in ma baiyi kuka ba,
   Ganin yadda hawaye ke sintiri akan fuskar AMMI yasa Omar ya cire hanky daga aljihunsa ya miƙa mata,dama kamar yasan cikin buƙatarshi take,a fuskarta ta kifa hankacif ɗin,ta fashe da matsanancin kuka mai cin rai,kowa yayi mamakin yadda Ammi ke kuka,cikin shessheƙar tace"ku kashe mun audio din nan ya isa haka,kunnuwa na bazasu iya jurar jin wannan tashin hankalin ba,'
  dama Audio ɗin yazo ƙarshe,junaid ne ya mike ya ɗauki wayar,tare da miƙa ma babban yayansu ita,ya kashe audio ɗin,
  "Shiyasa akeso ko da yaushe mutun ya kasance mai sauƙin kai,kada ya cika tsaurara al'amurransa,yanzu da ace banzo ba,da shikenan,haka zaki kora yaran nan,ke baki tsaya kinyi bincike ba,kuma baki saurari bayani daga gurin kowannansu ba kawai kin tashi kin yanke hukunci,sai daga baya kuma kizo kina danasani"
  daƙyar ammi ta iya furta"Astagfurullah Allah na tuba!ka yafe mun,rashin sani ne yasa na kirasu da shaggu,game da halin da yaran nan suka tsinci kansu,duk laifin mahaifinsu ne,shine silar komai,duk da daman Allah ya ƙaddara faruwar hakan babu wanda ya isa ya hana,amma Abusufyan bai kyauta ma rayuwarsu ba,meyasa bai sanar ma kowa ba don aɗauki mataki?saboda kawai yayi mashi barazana?Amma dai Allah ya tsine ma fasiƙin mutumin nan,Wlh bazan barsu ba,saboda me laifin kakansu zai shafe su?wannan wata irin mugunta ce mara kan gado,?bai tsaya a iya kan ya'yan salahudeen ba,hada jikokin duka yake ɗaukar fansa akansu,?kuma shima salahudeen ɗin daya kashe mahaifinsu ae don saboda mugayen laifukan da aka kamasu dashi ne,ɗaukar fansar ta mutun ukuce suke ɗauka,mahaifinsu da kuma mahaifiyarsu,da kuma wannan ɗan koran nasu,dukkansu Allah zai toni asirinsu,'
  Jinjina kai modibbo yayi yana sauraronta saida takai ƙarshen maganarta,tukunna yace"ba komai ne yasa na tako nazo ƙasar nan ba,face don abu uku,kuma ina fata zaki bani haɗin kai domin asamu maslaha atsakaninku gaba daya,saboda baza a ta6a cin nasarar gano waɗannan masu ɗaukar fansar ba,har sai ku na cikin gidan kun fara haɗa kanku,in ba haka ba,munafukan dake shirya maku zagwan ƙasa zasu samu nasarar cin galaba akanku,ta hanyar rarraba kawunanku,saboda ni inaji araina cewar masu shirya wannan maƙarƙashiyar suna ATARE DAKU!sun shiga cikinku,suna acikin rayuwarku!'

Wannan maganar ba ƙaramin jijjigasu tayi ba,don sai da kowannansu ya ɗago yana kallon fuskar modibbon,
"Nasan zakuyi mamaki amma nan gaba sannu a hankali zaku shaida maganata,yanzu dae bari inyi abunda ya kawoni,"
"AISHA" Ya ambaci sunan Ammi,muryarta asanyaye ta amsa mashi da Na'am,
"Banaso in ƙarajin wani ƙorafi akanki!wannan ne na farko kuma wannan ne na ƙarshe!idan har kinaso ki zauna lafiya,to ki gyara tsakaninki da ya'yanki!da kuma tsakaninki da Jikokinki,na uku kuma shine tsakaninki da surukarki fatima,"ya ƙarasa maganar yana nuna Alexandra da sandar hannunshi,ɗagowa ammi tayi tare da kai idonta kan Mommynsu junaid wadda itama kallon nata takeyi,kawar da kanta tayi gefe batare da tace komai ba,
Cigaba da magana modibbo yayi,"Allah ma mukanyi masa laifi kuma ya yafe mana,balle mu ƴan adam,fatima bata yi maki laifin komai ba,tun farko koda kike mata magana take mayar maki saboda kin nemi cin zarafinta ne!wanda kuma ba kowa ne zai iya jurewa ba,balle ita da take jar fata,yanayin rayuwarsu ko ince tarbiyarsu ba irin tamu bace,don da a ƙasarsu ne kikayi mata haka zata kaiki ƙara kotu ne a yanke maki hukunci,babu ruwanta da Cewar ke surukarta ce,sannan kuma bai kamata ki nuna mata ƙiyayya ba,duk maison naka ae masoyinka ne!ɗanki fa takeso,kuma saboda son da take mashi tabar iyayenta da kowa nata tazo ƙasar nan,inda bata san kowa ba,ko tsoron acutar da ita batayi ba,bakowa ne ma zai iya wannan kasadar ba,don haka yakamata ki so fatima saboda masoyiyarki ce,ba maƙiyiyarki ba,idan don ta kasance farar fata ce,damu dasu shin ba Allah bane ya halicce mu ba?ya banbanta mu ne?ko wani yafi wani ne"? Ya ɗan jinkirta da maganar yana kallonta,
Kafin ya ɗaura da cewar"Yakamata ki ajiye wannan gabar dake tsakaninki da ita,Yanzu fatima ta wuce suruka a wurinki,tamkar ƴ'a take a wurinki,tunda ta hayayyafa da ɗanki,yakamata kiyi alfahari da ita saboda itace ta haifa maki ɗaya daga cikin jikokinki wanda duniya take alfahari dasu,waɗanda suka ɗaukaka darajar mu a idon duniya,"
  Nauyayyiyar ajiyar zuciya Ammi tasaki tare da gyaɗa kai tace"Insha Allah komai ya wuce,"
  Murmushi Abba ya saki ranshi fari tass kamar an yi mashi albishir da gidan aljanna,
  "Sannan kema Fatima inaso ki ajiye dukkan wasu makaman yaƙin ki,kibi surukarki tamkar mahaifiyarki,kiyi mata biyayya amatsayinta na wadda ta tsugunna ta haifi uban ya'yanki,"
  Fuskarta ɗauke da murmushi tace"Nima a wurina komai ya wuce,dama saboda ƙiyayyar da take nunamin ni da ya'yana ne yasa nima nake ƙinta,amma daga yanzu insha Allah babu wanda zai ƙara jinkan mu,"
  Tana kai ƙarshen maganar junaid yace"Gaskiya,wannan sulhun bai cika yadda akeson shi ba,Mommy da Ammi basu ta6a yin koda musabaha ba,yakamata yau su tashi su rungume junansu ta hakan ne zamu gane cewar sun shirya da junansu,"
  Gaba ɗayansu suka saki murmushi,miƙewa Alexandra ta farayi kamin Ammi itama ta miƙe,suka ƙarasa tare da rungume juna,tafi su Abba suka shiga yi wanda hakan yaja hankalin sauran matasan gidan,har suka firfito cikin falon don suga me ke wakana,ae koda su kayi arba da Ammi da Alexandra rungume da juna,nan fa suka shiga sowa,abun ba ƙaramin farin ciki ya sanyasu ba,musamman su Fawan don sun jima suna jiran wannan ranar tazo,ashe da rabon zasu ganta da idanuwansu,
  "Ki yafe mun duk abubuwan da nayi maki,kuma inaso ki sani ba don bana sonki bane yasa nayi maki hakan ba,kawai haline irin nawa,da kuma sharrin shaiɗan" Ammi ce tayi maganar ayayin da take raba jikinta daga na alexandra,fuskar kowanansu ɗauke da siraran hawaye,
  Murmushi alex ta saki kafin tace"Allah ya yafe mana gaba ɗaya,inaji kamar nafi kowa farin cikin wannan ranar,"tayi maganar fuskarta ɗauke da dariya,suna cikin rahar nan sukaji ana ɗaukarsu hoto ket ket!!
  Da sauri suka waiga don su ga wanene,ashe wai fawan ne ya ɗauko camera ɗinsu,yana ɗaukarsu hoto yana faɗin"yau a daily trust dole su buga wannan gagarumin labarin,zazzafan gaske,Ammin mu wato kakarmu a yau ta rungumi surukarta wadda ta kasance mahaifiyarmu bayan sun dade suna shan gwagwarmaya ,"
  Dariya sosai su kayi,ganin ya sanyasu raha,yasa shi cewa"Abba mu shigo ciki a ƙarasa tattaunawar tare damu?
  Fuskar Abbansu ɗauke da murmushi yace"why not,a yanzu an sasanta komai,an samu maslaha,zaku iya zuwa ku zauna,"
  Jin haka yasa suka ƙaraso ciki,gaba ɗayansu ne hada su twins jabeer,khaleed irfan dasu kanal,wuri suka samu suka zazzauna a ƙasa,
  Junaid yace"Yawwa Amminmu,yanzu saura Uncle ɗinmu bawan Allah,yayi missing ɗinki sosai yakamata shima ki rungumeshi,ko yaji sanyi aranshi,"ya karasa yana langa6ar da kai.
   Juyawa Ammi tayi tare da kallon abusufyan wanda ke a zaune,idonshi na kallon ƙasa,
  Gyaran murya ta ɗan yi mashi,ya ɗago da idonshi ya kalleta,cike da zolaya tace"So kake sai nace ka taso"?
  Fashewa yayi da dariya,kafin ya miƙe da sauri ya faɗa jikinta,sosai ta rungume shi ajikinta,tana ɗan bubbuga hannunta a bayanshi tace"nayi kewarka sosai,ka sani kuka Abusufyan,fiye da tunaninka,hakanan ka tafi ka barni shekara da shekaru...."tana maganar hawaye na fita a idanunta,
  ɗagowa yayi daga jikinta,idonshi na fitar da kwalla yace"Ki yafe mun Ammi,nasan ban kyauta maki ba,nayi maki abubuwa da dama wanda bakyaso,nasan cewa hada haƙƙinki ne ke bibiyar rayuwata shiyasa ma harya shafi ya'yana,...."
    Hannu tasa tana share mashi hawayenshi tace"Na yafe maka abusufyan,dama ni burina shine ka dawo kusa dani,kuma Alhamdulillah,gashinan ka dawo cikin yan uwanka,naji daɗin hakan sosai,Allah ya ƙara haɗamun kanku,"
  gaba ɗaya suka amsa da Ammin,
"AMMI saura su rishi,su baki rungumesu ba,kalli fa kiga yadda duk suka shiga damuwa,bayin Allah,"
junaid ne ya sake yin maganar yana raku6e fuska,alamar tausayi
   Kallonsu Ammi tayi,sun cunkushe wuri guda kamar kifin gwangwani,musamman Sehrish jikinta har lokacin sae kerma yake,a hankali Ammi ta taka izuwa inda suke,ta zuƙunna agabansu,sannan takai hannunta tare da shafa fuskokinsu,kafin tace"dole in nemi yafiyarku,saboda na jefebku da mummunan kalma,bisa rashin sani,ina mai matuƙar baku Haƙuri akan abunda ya faru a rayuwarku!ba laifinku bane laifin wasu ne akeso a ɗaura maku shiyasa aka biyo ta hanyarku duk don a ƙuntata mana,amma nayi maku alƙwarin cewa ɗaya daga cikin waɗanda sukayi sanadiyar wulaƙanta rayuwarku,Wlh bazai sha ba!daga rana irin ta yau zansa a fara bincike akansu har sai Allah ya tonu asirin kowannansu,kuma nayi maku alƙawarin cewa,zansa akawo maku wannan fasiƙin mutumin har inda kuke don ku wanke mun mummunar fuskarshi da tafukan hannayenku,"
  Jin wannan maganar ta Ammi yasa Hosana fashewa da dariya,har white teeth ɗinta suka bayyana,dimples ɗin fuskarta suka lotsa,Jahad ma murmushi ne ya bayyana a fuskarta,sehrish ce kawai batayi murmushi ba,da alama kamar akwai wani abu dake damunta,duba da yanayin jikinta dake ta kerma,
  Ruƙo hannayensu ammi tayi tare da miƙar dasu tsaye sannan ta haɗasu duka ta rungumesu sosai,ajikinta,
Wani irin matashin murmushi ne ya bayyana a fuskar kowannansu dake a falon,haƙika sunji daɗin wannan ranar,tsakaninsu da Allah sai godiya daya bar Modibbo a raye har zuwa wannan lokacin,saboda shine silar komai daya faru ayanzu,da bai zo ba da akasin hakan ne zai faru,
   Addu'oi' Ammi ta shiga karantowa tana tottofa masu akawunansu,a ƙarshe tace"Allah yayi maku ALBARKA,"suka amsa mata da Amin,
  Komawa su kayi kowa ya zauna,itama ammin ta zauna,bayan kowa ya natsu Modibbo yace"ko akwai mai magana acikinku"?
  Da sauri Abbansu junaid yace"Ina da magana,"
Modibbo yace"faɗi kai tsaye muna sauraronka,"
   "Yawwa kawuna,dama akan maganar fatima ne da Abusufyan!har yanzu basu shiri a tsakaninsu,tun wani sa6ani da suka ta6a samu a lokacin baya,to har yanzu basa jituwa,yakamata aduba lamarin,'
Sunnar dakai ƙasa Abusufyan yayi,kamar yadda itama alexandran tayi,
"Ae yanzu ko banyi masu magana ba,zasu shirya kansu ne ko don zumuncin dake a tsakaninsu,da kuma ƴa'ƴayensu,"
Murmushi kowannansu,yayi abusufyan yace"Insha Allah komai ya wuce a wurina,dama can ni ban ta6a ruƙeta araina ba,nasan rashin kunyar da nakeyi mata ne a lokacin baya yasa take fushi dani har yanzu,amma ina neman afuwarta,"
Yana kai ƙarshen maganarshi,Alexandra tace"Nima komai ya wuce a wurina,Allah ya yafe mana baki ɗaya,kuma ya ƙara haɗa kawunanmu,"
Wani irin ihu junaid ya fasa,saboda tsabar farin ciki,hankalin kowa ya koma kanshi,ganin sun zuba mashi ido yasa shi sanya tafin hannunshi ya rufe fuskarshi,saboda kunyar data rufe shi,ƙasa ƙasa yake sakin dariya,bakomai ne yasa shi wannan farin cikin ba,face Shiryawar da Momnynsu tayi da Uncle ɗinsu,ko ba komai zai samu amincewarta wurin auren ɗaya daga cikinsu,💃

"Gobe da safe zan wuce damaturu,tunda naci nasarar haɗa kawunanku,ina fata zaku kasance a haka ko bayan tafiyata," atare suka amsa mashi da cewa"Insha Allah,"
"Amma mun jima bamu haɗu ba,bazaka ƙara kwanaki ba"? Ammi ce tayi maganar,
murmushi modibbo yayi kafin yace"kada ki damu,tun da dai na shigo ƙasar zaku dinga ganina ne akai akai,insha Allah,"


Alhamdulillah,The end🥱🤣😂😅 nan bada jimawa ba,zan rubuta hakan insha Allah,nasan wasu har gabansu ya faɗi rass.........




*SANARWA SANARWA*💃💃💃💃


*ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$*

*MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.*


*LOCATION KANO*

08062073990
Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka
Wadrobe balls
Madarar kulleccham
Vaseline kulleccham
Kajiji
Halut
Couscous
Khumrah
Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku


Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka
Wadrobe balls
Madarar kulleccham
Vaseline kulleccham
Kajiji
Halut
Couscous
Khumrah
Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku

It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining.
Snack
Awarah
Farah
Zobo
Samosa
Cup cake etc
Contact me 09063302182or 09012179727.
[3/19, 2:56 PM] +234 810 388 4440: *💋Boss Bature💋*



Join this link to follow my tiktok acct👇

https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1




قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*

*Father of soldiers*

*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*

_Ga duk mai son karanta littafin Abban sojoji,kai tsaye ya tuntu6eni ta numbar wayata 08103884440_

Special thanks to hafsat Usman Abubakar🥰,


"Koda ace baka samu zuwa ba,xamu zo nan damaturun,dama mu ya dace ace mun je can gaba ɗayan mu bayan komai ya lafa,ko don saboda ƴan ukun abusufyan,zamu je dasu don suma suga danginsu dake acan da kuma na zariyya,dana sauran state,"acewar ammi,
Modibbo yace"hakan ma yayi,Allah yayi maku albarka gaba ɗayanku,"suka haɗa baki wurin amsa mashi da ameeeen,

Duk wannan abun dake faruwa Aunty babba da hayaam suna acikin ɗaki,kowannansu ya dafi waya sai danna yake yi,gaba ɗaya tunaninsu ya tafi akan cewa An kori su sehrish,hakan yasa hankalinsu ya kwanta luf,

miƙewa zaune aunty babba tayi daga kishingiɗen da take,fuskar nan a washe tace"Oh ni ƴasu,ko ina waɗannan ƴan ukun suka dosa yanzu?
Hayaam tace"Wama ya sanin masu,suna can suna gagari acikin gari,ƙarshenta ma a samu wata babbar mota zubin ɗan gotte tayi mana awon gaba da kawunansu,"
  Fashewa su kayi da dariya,sai da suka tsagaita dayin dariyar Aunty babba tace"duba mun ƙarfe nawa yanzu,agogon wayata ba saiti,"
   "kusan Ƙarfe tara fa yanzu,gashi ko abincin dare ma ba mu nema ba,"
  Tsoki taja"mtsww,wannan wani irin gidane!A tunani na Azmee ya kamata ace ta kawo mana dinner ɗin mu har cikin ɗaki,ni bansan menene amfanin matar nan ba a cikin gidan nan,bata wani aiki,sae dae ta dafa masu abinci,ta zauna taci ta ƙoshi ta tara tumbi,ta mayar da gidan kamar na ubanta,"
  Hayaam ta ɗaura da cewa"Ae kwanaki har magana taso ta gayamun,saboda waccen korarriyar yarinyar,Sehrish take da suna ko wa ma......."dakatawa tayi da yin maganar sakamakon turo ƙopar da taji anyi,atare suka kai idanunsu wurin,
  Azmee ce ta shigo hannunta ɗauke da tray,koda su kayi arba da ita,nan fa suka shiga yin ƴan kame kame na rashin gaskiya,
   Basu amsa mata sallamar da tayi masu ba,ƙarasawa tayi ta ajiye masu tray ɗin a ƙasa,sannan tace"abinci ne na kawo maku,bansan ko kuna buƙata ba,naga baku fito kun nema ba,shine nace bari na kawo maku a ɗaki,"
Washe baki suka shiga yi,hankalinsu harya kwanta,da alama bataji gossiping ɗinta da sukeyi ba,
  "Mun gode sosae Azmee,wlh kina ƙoƙari sosai acikin gidan nan,ke kaɗae kike duk wasu aikace aikace na gidan nan,shekara


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login