Showing 255001 words to 258000 words out of 307403 words
Chapter 86 - Abban Sojoji Takun Karshe Hausa Novel Complete
Abra,Hankalinshi ya tashi sosai,A ranar ya kwashe su zuwa gidansu,sunyi kuka sosai sun nemi yafiyarshi,Yace masu komai ya wuce tunda sun shiryu,sati ɗaya suka yi a gida,Ya tattara su gaba ɗaya ya tafi dasu kano,Saboda zama maiduguri bazaiyiwu ba,mutane sun addabi rayuwarsu,Ko ƙopar gida ba damar su leƙa sai ahau zaginsu ana nunasu da yatsa,
Gidan haya ya fara kama masu,Sai kuma ga Kuɗi Amani ta turo masu ta account ɗin hayaam kusan miliyan ɗaya da rabi,dama yana da wasu kuɗi hannunshi na gidansu daya saida kafin su baro,kuɗi suka cika 3 million Ya sama masu gida irin na masu rufin asiri,Ya siya masu,Ba ƙaramin daɗi suka ji ba,Yanzu basu da sauran damuwa,rayuwarsu ta canza sosai,Har makarantar islamiyya abie ya sanyasu,wannan kenan,
*Very Soon Littafi zai ƙare sai dai kawai kuji nace Alhamdulillah,Ga azumi yana zuwa Allah yasa muna da rabon ganin watan ramadan👌Ga duk mai buƙatar littafin Abban sojoji yayi mun magana kai tsaye ta layina,Amma fa whatsapp kawai banda kira,08103884440*
[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋Boss Bature💋*
Join this link to follow my tiktok acct👇
https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1
قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*
*Father of soldiers*
*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*
_Double page ne,Saboda jiya da bana jin daɗi bansamu nayi ba,that's why na hada maku pages biyu💋_
Lokacin da Abusufyan ya fita a fusace ya shiga motarshi yayi mata key da gudun gaske ya fusgeta,shi kanshi baisan ina zai dosa ba,A ƙarshe gefen bishiya yayi parking ɗin motar Ya kifa kanshi jikin steering,tuni hawaye sun wanke mashi fuskarshi,Bai ta6a tunanin Sgr zaiyi mashi haka ba,duk irin yadda yake treating ɗinsu,tun suna yara yake hawa jirgi daga Turkey zuwa U.s don kawai ya gansu,saboda ƙaunar da yake yi masu shi da Omar Amma sai gashi yau Sgr Yayi mashi abunda bazai ta6a mantawa ba,Tsananin damuwa ne akan fuskarshi,zuciyarshi sai tafarfasa take yi,Zufa tuni ta wanke mashi fuskarshi,cikin shessheƙar kuka Ya furta"Why Rafayet!why!ban ta6a tunanin haka kake ba"lumshe idanuwanshi yayi,Anan Ya yini gefen bishiyar,
Duk ta damu saboda rashin ganin Sehrish ga wayarta dake ajiye saman side drawer tun safe,tun tana zarya acikin bedroom ɗin harta fara tunanin Zuwa nemanta,hijab ta zura ajikinta ta buɗe ƙopar ɗakin ta fito,miƙar hanya tayi tana tafiya,Adai dai ƙopar bedroom ɗinsu ta tsaya,Hannu tasa tayi knocking ɗin ƙopar,
Jahad ce ta buɗe mata ƙopar,jikinta na sanye da pakistan wando Burgujeje pink da Riga fara mai dogon hannu,daga ƙasan rigar anyi mata adon stones,Ta yafa mayafin a ƙafada,Yayin da ta saki sumar kanta,
Fuskarta ɗauke da murmushi tace"Amrish"ta ƙarasa maganar tare da yin hugging ɗinta,Suka rungume juna,bayan sun kammala gaisawa Amrish ta soma tambayarta
"dama ina neman Sehrish ne,tun asuba dana farka banganta ba,bansani ba ko tazo wurinku ne,ko ta fita daga gidan,"
Gaban jahad ne ya ɗan faɗi don ita kanta duk yinin ranar bata sanya Sehrish a idanuwanta ba,
"Gaskiya bansan inda taje ba,nima duk yau banganta ba,Amma abunda za'ayi bari na bincika cikin gidan may be ko tana wurin Aunty azeema ne,"
Juyawa Amrish tayi,da sauri jahad ta ce"Ki shiga mana,Ga Hosana can tana kallon drama,".
Murmushi ta ɗan saki tare da gyaɗa kai tace"okey,"Matsa mata hanya Jahad tayi ita kuma ta shige ɗakin,A kwance ta samu Hosana ta baje saman gadon,Ga laptop agabanta ta ƙura ido tana kallo,wuri ta samu daga gefe ta zauna,
"Hosana,ya kike,"
Juyowa hosana tayi fuskar nan a yamutse tace"Lahiya,"ta mayar da idanuwanta kan laptop din,zama sosai Amrish tayi suka cigaba da yin kallon atare,
Tana ƙoƙarin fitowa daga Toilet,tajiyo Muryar Mommy tana sallama,Ƙarasa fitowa Hajiya Azeema tayi jikinta sanye da bubu ta atampa ,fuskarta ɗauke da murmushi ta amsa mata"Wa'alaikum salam,Aunty ki shigo daga ciki mana,"
turo ƙopar mommy tayi jikinta na sanye da jallabiya fara,babu mayafi akanta,sam babu kwanciyar hankali atattare da ita,ganin fuskarta a hargitse yasa Hajiya azeema tace"Aunty Lafiya naga kamar akwai damuwa a fuskarki,"
Mommy tace"Ina fa lafiya,Rafayet yayi aika aika,yabarmu da zullumi,"tayi maganar yayin da take zama daga gefen gadon nata,
"Me Rafayet yayi"?
"Hmmmm,ɗazu Abban Junaid ke sanar dani,Nasan kinsan da auren sirrin da su kayi mashi ko"?
jinjina kai hajiya azeema tayi"Eh,nasani,"
"Oh ashe kema kinsani,Ni aka mayar shashasha,babu wanda ya sanar dani,"
Murmushi hajiya azeema ta ɗan yi"Naso in sanar dake Aunty,Kawai ina fargabar yadda zaki ɗauki abunne,"
Ta6e baki Alex ta ɗan yi,
"Amma meya faru ne"?
Nan Mommy ta kwashe duk abunda Abba ya sanar da ita,tun daga farko har ƙarshe ta sanar da ita,..
Hannu Hajiya Azeema ta ɗaura akai,Hankalinta amatukar tashe take ambaton"Innalillahi'wa'inna ilaihirraji'un!Nashiga uku!"duk tabi ta ruɗe,
Cike da takaici Mommy taci gaba dacewa"Wlh tun safe ake ta faman nemanshi ba'a ganshi ba,Ni yanzu babban tashin hankalina shine a wani hali yarinyar take ciki!Ina Rafayet ya kaita!Tana raye kota mutu"?.
Tuni idanuwan hajiya azeema sun cicciko tab da kwalla,bakinta ya mutu,Jikinta yayi sanyi,
"Amma rafayet bai kyauta mana ba Allah,duk da nasan yayi ne saboda son da yake yi mata,Yaji tsoran su rabashi da ita ne amma....."tunkan takai ƙarshen maganarta,Mommy ta katse mata hanzarinta"aini banso Suka tursasa mashi akan ya saketa ba,Wannan shine kuskuren da suka aikata,Babu wanda baisan halin Rafayet ba acikinsu,tunda ya nuna yana son ya tafi da ita,to tabbas Yana sonta ne,Ni nasan wanene rafayet,Wlh da ace baison yarinyar nan,ko kallo bata ishe shi,balle har ya aureta,Amma tunda yayi accepting aurenta as a contract wlh yana sonta ne,So bana wasa ba,that's the reason why yaƙi sakinta,Shima kuma da laifinshi,komai sai yace zai nuna ƙarfi,Ai akwai abunda ƙarfi ko dukiya basa iya siyawa mutun,duk da ana siyan soyayya da kuɗi,Amma bakowace zuciya bace zaka iya mallakarta cikin sauƙi ba,kuma hada ƙarin shi bai ta6a soyayyaba,balle yasan yarda zai baiyanata,"
Jinjina kai Hajiya Azeema tayi"Allah sarki Sehrish,wlh na tausaya mata baiwar Allah,banji daɗin abunda ya faru ba,Yanzu ya zamuyi?wlh duk na ƙagu da insan a wani hali take,Ga Abusufyan ma,Naji kince Ya fita ba'a san inda yake ba,"ta ƙarasa maganar tana kallon Mommy,Duk sun shiga damuwa,
"Tun ɗazu suka fita nemansu,Amma har yanzu shiru babu wani labari,yanzu sai dai muyi ta jiran tsammani"acewar Mommy,
Kafin Hajiya azeema ta ƙara cewa wani abu,Jahad ta kwankwaso ƙopar dakin,
"Wanene"
"Ni ce Aunty azeema,"kallon juna sukayi ita da Mommy kafin tace"Shigo daga ciki,"
Da sallama abakinta ta shiga ɗakin,cikin girmamawa Jahad ta gaishe su,Suka amsa mata,
"Ina neman sehrish ne,Na bincika ko'ina banganta ba,Nayi tunanin ko tazo wurinki ne,"
Jin wannan maganar yasa hankalinsu ya tashi,shiru su kayi na wani lokaci batare da sun amsa mata ba,
ƙoƙarin juyawa tayi zata bar ɗakin,Da sauri Mommy tace"Zonan,Jahad ce ko Hosana?"
Cikin sanyin murya tace"Jahad ce,".
Azeema tace"Baki bambantasu ne,Ae wannan duk tafisu natsuwa,Hosana kuma tafi su jiki,har ƴan kumatu gareta,kuma ita sam bata da natsuwa,ta cika ƙiriniya,"
Murmushi Mommy tayi tare da cewa"masha Allah,Juliet ɗin Junaid ce kenan,ae ko jiya sai da yayi mun maganarta,"
cike da mamaki Jahad ta ɗanyi murmushi,jin tace Junaid yayi mata maganarta,bayan ita ko son kallonta baiyi,
"Amma Oummanku tasan cewa Sehrish bata nan"?hajiya azeema ce tayi mata tambayar,
Girgiza kai tayi"a'a bata sani ba,Nima Yanzu nake ji wurin Amrish,tace tun da safe bata ganta ba,"
Jinjina kai hajiya azeema ta ɗanyi kafin tace"Shikenan,koda ace Oummanku ta tambayeki game da sehrish,ki sanar da ita cewa Sun fita ita da babban yayanku,zasu dawo in sha Allah,"
"Shikenan,zan sanar da ita hakan,"
Gyaran murya Mommy tayi mata,ɗagowa Jahad tayi cike da jin kunyarta take kallonta,
"Munyi magana da Junaid,Na bashi shawara akan yazo wurinki kuyi magana,nasan zaki taimaka mashi sosai,"
Ƙayataccen murmushi Jahad,ta saki daƙyar ta iya cewa"in sha Allah Mommy,"tana kai ƙarshen maganar ta fuce da sauri,murmushi suka saki gaba ɗayansu,daga bisani kuma suka cigaba da tattaunawarsu,
A 6angarensu Omar kuwa,Yinin ranar suna wajen neman Sgr,duk wani wuri da suke tunanin zasu same shi sunje basu gansu ba,lamarin ya fara bashi tsoro,
Har wuraren ƙarfe Goma na dare babu wani Labari me daɗi,duk sun shiga matsananciyar damuwa,ga Abusufyan yaƙi dawowa cikin gidan,Abu kuwa tunda Jahad ta sanar da ita cewa Sehrish sun fita tare da babban yayansu,bata wani sanya damuwa aranta ba,don tasan cewa duk inda take tana cikin ƙoshin lafiya,Tun da ba ita kaɗai bace,duk da ta ɗan damu ganin har goma tayi Basu dawo ba,
Damuwace ta ishi Abba,A ƙarshe ya yanke shawarar sanarma Ammi halin da suke ciki,wata'ƙil ta taimaka wurin shawo masu kan Abusufyan,A lokacin tana kishingiɗe saman gadonta,Abba yayi sallama daga waje,Amsa mashi sallamar tayi,A nutse ya tura ƙopar ɗakin ya shiga,cike da girmamawa ya samu wuri daga ƙasa ya zauna tare da lanƙwashe kafafunshi,cikin sanyin murya ya gaisar da ita,miƙewa daga zaune ammi tayi yayin da idanuwanta ke akan fuskarshi,tayi mamakin ganin jirwayen hawaye,
Hankali aɗan tashe tace"Hossein!Lafiyarka kuwa?Hawayen menene akan fuskarka"kamar jira yakeyi tayi magana,nan take ya fashe mata da kuka kamar ƙaramin yaro,duk tabi ta ruɗe,
"Ka faɗamun meya faru ne?Ka tasani gaba kana yi mun kuka,idan wani abu ke damunka bazaka fadamun ba!"
Cikin shessheƙar kuka ya soma magana"Abubuwa ne sunyi mun yawa ammi,daga wannan sai wannan na rasa yadda zanyi da rayuwata"
"Ka natsu ka sanar dani meke damunka,"daƙyar ya samu ya tsagaita da yin kukan,a tsanake ya kwashe duk abunda ya faru ya sanar da ita,
Jinjina kai ammi tayi yayin da idanuwanta ke akanshi sai da yakai ƙarshen maganarshi tukunna tace"Gaskiya banji daɗin wannan abun da kuka aikata ba,nayi masu auren yarjejeniya batare da kun sanar dani ba,sam bakuyi tunani ba wlh,Haba hossein da hankalinka da tunaninka...."ta ɗan dakata da yin maganar tana kallonshi,sosai hawaye ke zuba akan fuskarshi,
"Dama dole kuga ba daidai ba,kuskure ne tun farko kun riga da kun tabka,Ni yanzu bansan ya zanyi ba,tunda baku yi shawara dani ba lokacin da kuka shirya yi masu auren,bani da abunda zan iyayi maku.... "Tunkan takai ƙarshen maganar,Abba ya zukunna agabanta ya ruƙe hannayenta,"Duk duniya bani da mai sharemun hawayena in bake ba,Dan Allah ki taimaka mun Ammina,ni kaɗai nasan irin raɗaɗin da nake ji acikin zuciyata"
Jikinta ba ƙaramin sanyi yayi ba,tafin hannunta ta sanya tana share mashi hawayenshi,
"Shikenan,kadaina kukan ya isa haka,idan ba so kake nima in fara kukan ba,"
Da sauri yace"nadaina ammina,bazan ƙara ba,"
Jinjina kai ta ɗanyi kafin tace"abun da ciwo,banji daɗin abunda Rafayet ya aikata ba,Yanzu in mahaifiyar yarinyar nan taji ya kuke tunanin zata ɗauki abun?sam bakuyi tunani ba,Shi kuma Abusufyan baikyauta ba abunda yayi maka,Zai dawo ya same ni ne,Sannan inaso ka kwantar da hankalinka,ni nasan cewa duk inda rafayet yake a halin yanzu yana tare da yarinyar,koba komai ita ƴar uwarshice,Jinin dake yawo ajikinta shike yawo ajikinshi,zai bata kyakkyawar kulawa,tunfarko kuskuren da kukayi na tursasa mashi akan ya saketa shine duk yajawo wannan abun,da ace kun bi a hankali da duk baza azo ana danasani ba,"ta ƙarasa maganar tare da nuna mashi gefenta alamar yazo ya zauna,
Miƙewa Abba yayi tare da komawa gefen ammi ya zauna,kwantar da kanshi yayi asaman kafaɗarta,Wani irin ciwon kaine ke damunshi,
"Kayi hakuri da duk abunda ya faru,banason kana sanya damuwa aranka,in sha Allah komai zai tafi daidai,zan tayaku da addu'a akan Allah Ya bayyanar dasu"sosai ammi tashiga tausarshi,tana kwantar mashi da hankali,
"Ka kwanta ka huta,zanyi kokarin jaraba kiran layinshi,"
"To ammi,"ya amsa mata,kafin ya gyara kwanciyarshi A saman gadonta,
Miƙewa ammi tayi gaban drawer taje tare da kai hannu ta ɗauki wayarta,Layin Abusufyan ta kira,Cikin sa'a wayar ta soma ringing,yana ɗaga kiran ta kara wayar a kunnanta tunkafin yayi magana tayi saurin cewa"Duk inda kake kadawo gida yanzun nan,ina son ganinka aɗakina,Umarni nake baka,"tana kai ƙarshen maganarta batare da ta jira amsarshi ba,Ta katse kiran,
Safa da marwa ta shiga yi aɗakin tana jiran zuwanshi,kusan minti goma sha biyar da yin wayar,Motar Abusufyan ta kunno kai cikin gidan,bayan yayi parking ɗinta ya fito jiki babu ƙwari ya nufi cikin gidan,Yana shiga babban falon gidan Ya taras da mutanan gidan,bai bi takan kowa ba Ya wuce ɗakin Ammi,da sallama abakinshi Ya shiga ɗakin,
Tunda ya shigo ammi ta kafe shi da ido tana kallonshi,yaji jiki ba ƙadan ba,
Daƙyar ya iya gaisar da ita"ina yini ammi,"bata amsa mashi ba,Sai nuna mashi wuri tayi saman sofa ɗin dake dakin,Ya zauna yana faman sauke ajiyar zuciya,sai daga baya ya lura da Abba dake kwance ya rufe idanuwanshi,
"Meya haɗaka da ɗan uwanka'?tayi tambayar tamkar batasan komai ba dangane da abunda ya faru,a ruɗe yace"Wani abu yace nayi mashi"?
"Kafi kowa sani ae,meyasa Abusufyan kafiye son zuciya ne?Sam baka da kara duk irin halaccin da hossein yayi ma ƴa'ƴanka tunkafin yasan cewa jininka ne su,abunda kayi mashi sam bai dace ba,kuma abunda Rafayet Ya aikata ma ƴar wurinka,Ni banga laifinshi ba,Nafi ganin laifinku ku da kuka shirya auren yarjejeniyar,In har kayi niyyar bashi auran ƴarka don me zaka tursasa mashi akan ya saketa?Gashi yanzu kun jefa rayuwar yarinyar cikin hatsari.....'tunkan takai ƙarshen maganar,Abusufyan yace"Dama nasani,ba sona kikeyi ba,Shiyasa har kike goya mashi ba,yanzu duk girman laifin da rafayet ya aikata baki ga laifinshi ba,Saboda shi jinin Hossein ne,dama can kinfi sonshi ae......'
Bai ƙarasa maganarba,Sakamakon tsawar da Abba ya daka mashi,a lokacin ya miƙe daga zaune ya sauko da kafarshi ƙasan gadon,
"Dama abunda kake tunani kenan!?Meyasa Abusufyan?Wlh idan ka biyewa zuciyarka Zata kaika ta baroka ne,dani dakai duk abu ɗaya ne awurin ammi,baikamata ka furta mata haka ba,ni a tunani na ƴa'ƴana naka ne,Ƴa'ƴanka nawa ne,Ban ta6a tunanin ina da bambanci dakai ba,wlh nafika jin raɗaɗin abunda Rafayet ya aikatama Sehrish,Yinin yau ko ruwa bansa abakina ba saboda damuwar halin da suke ciki...."hawaye ne suka wanke mashi fuskarshi,
Maganganun Abusufyan sunyi matuƙar ƙona mashi rai,musamman ammi,tayi mamakin yarda harya iya furta mashi hakan,Son ƴa'ƴa ya rufe mashi ido har yake ganin tamkar ba'ayi mashi adalci,
"Ammi dan Allah ki ƙyaleshi kada kice komai,kibarshi kawai ya tafi,Abusufyan yanzu baya acikin hayyacinshi,komai ya fito bakinshi zai iya faɗa mana,"
Ranta a6ace tace "Banji daɗin kalamanka ba Abusufyan,ban ta6a tunanin zaka iya furta mun haka ba,kada ka manta dakai dashi dukanku ni na haifeku,kuma banta6a nuna banbanci atsakaninku ba,Abu ɗaya danasani shine Hossein yafika sauƙin kai,Zan iya cewa duk cikinku babu wanda yakaishi haƙuri,yana yi mun biyayya sosai,aduk lokacin dana shiga wani hali hossein shi nake fara gani,yana faranta mun rai sosai ba kamar kai ba.....'daƙyar takai karshen maganar,idanuwanta sun cika tab da kwalla,hankalin Abusufyan ba ƙaramin tashi yayi ba,ganin ammi na shirin zubar da hawayenta kanshi,sai ma lokacin ya farga don baisan ya furta mata maganar ba,ranshi ne ya 6aci sosai,idanuwanshi sun rufe,
Saukowa yayi daga saman kujerar,Ya zuƙunna saman guiwowinshi agabanta,
Cikin sanyin murya ya soma magana"dan Allah ammi kiyi haƙuri,banaso nayi silar da hawayenki zasu fita,hakan zai ƙara jefa rayuwata cikin matsala,na tuba bazan ƙara ba,Komai kikeso wlh shi zanyi,yaya hossein...."ya ambaci sunanshi tare da mayar da idanuwanshi kanshi"Kayi haƙuri da abunda nace yayana nakaina,nasan kalamaina sun 6ata maka rai,zuciyata ce sam batayi mun daɗi,Nafi kowa sanin yadda kakeson Jini na..."duk yabi ya ruɗe,
"Ka tashi ka koma ka zauna,inason magana daku,"miƙewa yayi jiki na rawa ya koma saman kujerar ya zauna,gwanin ban tausayi ammi ke kallonsu,
"Kada ku bari son ya'ya yayi silar da zaku raba kanku,bana fatan hakan ya faru,Ban goyi bayan abunda Rafayet Ya aikata ma ƴar wurinka ba,Kuma ban goyi bayan kowannanku ba,dakai dashi,duk abunda ya faru Laifinku ne,Tunda ku kuka haɗa aurennasu,Sannan kuma kuka soma ƙoƙarin tursasa mashi akan ya sake ta,wanda silar hakan ne yasa shi Rafayet ɗin yayi mata aika aikar da yayi,maimakon daya nuna yana son Ya tafi da ita ku ƙyaleshi yayi rayuwarshi da matarshi,amma sai kuka matsa lamba akan ya saketa bacin kuma kunfi kowa sanin halinshi,Wannan shine kuskuren da kuka aikata......"
Shiru ta ɗanyi tana kallon kowannansu,gaba ɗaya sun natsu suna sauraronta,cigaba da magana tayi"Abusufyan amadadin Rafayet ina mai baka haƙuri,tabbas ya cutar da ƴar wurinka,Abunda yayi sam bai kyauta ba bai sa hankali ba,Amma inaso ka sani,Duk yayi wannan ne saboda tsananin son da yake yi mata,Yana gudun ku rabashi da ita ne shiyasa ya yanke shawara ya aiwatar da hakan,A tunanin shi in yayi mata hakan ba zaku iya raba shi da ita ba,Sai dai kash ya tabka babban kuskure,Ya kusanceta a lokacin da yake cikin fushi,shi kanshi yanzu nasan yayi danasanin abunda ya aikata mata fiye da tunaninku,kuma duk yacce kuka kaiga jin ɗacin abunda ya aikata mata wlh baku kaishi ba,Yafi ku jin raɗaɗin abunda yayi mata acikin zuciyarshi,da ace da son ranshi yayi mata wlh bazai gudu da ita ba,Anan zai bar maku ita,Ya tafi yabar kasar,Ya zakuyi dashi?tayi tambayar tana kallonsu,duk jikinsu yayi sanyi,
"Duk inda yake yanzu nasan cewa yana tare da ita,Kuma zai gyara 6arnar da yayi ne,Sannan inaso ku kwantar da hankalinku,in sha Allah zasu bayyana ne,kuma kudaina tunanin cewa ko ta rasa ranta ne,tana araye bi'iznillah,kuma zata ji sauƙi ta dawo kamar yadda take ada"sosai ammi tayi masu nasiha,duk ta kashe masu jikinsu,
A ƙarshe tace"idan har Allah yasa Rafayet ya dawo da yarinyar nan,zan zaunar dasu agaban kowa zan tambayi ra'ayinsu,idan har duka suka amince zasu rayu da junansu,To bana so wani daga cikin ku ya ƙara tada maganar saki,Idan kuma har ita jikar tawa ta nuna cewa batason shi,Zanyi adalci atsakaninsu in raba auransu,'
Ajiyar zuciya kowannansu ya sauke,Abusufyan yace"In sha Allah,nima bazan ƙara tursasa mashi akan ya sake ta ba,"
Abba kuma yace"Duk hukuncin da kika yanke masu dai dai ne,mungode sosai da irin nasihar da kikayi mana,kuma in sha Allah,ba zaki ƙara jin kanmu ba,"
"Allah yayi maku Albarka,Allah ya ƙara hada kan zuri'armu,"
Atare suka amsa mata da Ameen,
"Amma ammi,bansan ya zanyi da zainab ba"acewar Abusufyan
"Kada ka damu,idan ta tambayeka akan Yarinyar,ka sanar da ita komai game da auran yarinyar,amma bance ka faɗa mata ainihin abunda ya faru ba game da abunda rafayet ya aikata mata,Idan kace mata Mijinta ya tafi da ita,Bazata damu ba,"
Jinjina kai yayi"shikenan nagode sosai,Zan sanar da ita hakan,
"Yanzu yakamata mu mayar da hankali wurin neman inda ya tafi da ita,",'
"Zamuyi kokarin yin hakan,Yanzu haka Omar tun safe suke gararin nemansu acikin garin nan,Amma har yanzu shiru bamu ji daga gare shi ba,"Abba ne yayi magar,
"Allah ya taimaka,zasu bayyana ne nasan zai dawo da ita ne"daga haka ta basu iznin tafiya,Miƙewa sukayi atare har sun kusa fita daga ɗakin,Ammi ta kuma kiran Abusufyan Dakatawa yayi tare da juyowa ya dawo wurinta,
Dafa kafadarshi tayi"game da abunda ka yiwa yayanka,Ya tsaya mashi arai,yaji zafin abun har hawaye saida ya zubar akanka,sam banji daɗi ba daka buge mashi hannunshi don yana ƙoƙarin dakatar dakai,kafi kowa sanin yadda